AUREN HUCE HAUSHI 1-90
AUREN HUCE HAUSHI 1-90
❤️
MAMAN FATIMAH.
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIKAI SALATI DA DAUKAKA DA AMINCI SU TABBATA GA FIYAYYAN
HALITTA ANNABIN RAHAMA MUHAMMAD BIN ABDULLAHI DA ALAYENSA DA SAHABBANSA WANDA SUKA
BISHI HAR ZUWA TASHIN ALQIYAMA.
Wannan littafin kifkirarran labari ba'a yishi Dan wani ko wata ba duk abinda akaci karo dashi Arashi ne
kawai.
Paga one
..........A hankali motar da shigo layin dai dai wani katafaren gate ta tsaya, yanayin yanda take fidda wani
Dan Kara alamune dake nuna motar tayi dogon zangon tafiya, direban Bai Danna Horn ba bara a kaiga
bude gate din gefen wata bishiyar dorawar tururawa ya karasa da motar, wasu dattawa ne su buyi suka fito
daga bayan motar yayin da wani matashi ya fito daga mazaunin direba, Mika yayi dareban tare da salati.
Kofar gidan suka nufo da kafarsu Dan matshin be yayi nocking kamar day biyu kafin wani dattijo ya leko ta
wata karamar kofa jikn gate din.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin "A'a Alhaji barkan ku da zuwa kin Sha hanya sannunku" tare da Basu
hannu sukayi musabiha suna fadar "wlh kuwa malam Sani ya muka sameku?".
Cikin fara'a yake fadar "Alhamdulillahi".
Kafin yayi gaba Yana cewa "Bari nayi Muku iso gurin Alhajin Allah ya taimaka Yana nan".
Harabar gidan suka shiga suka rufawa malam Sani baya zuwa bangaren Mai gidan inda yake ganawa da
bakinsa.
Lokacin da suka karaso gurin kofar shi Kuma Malam sanin ya fito Yana fadin "Bismillah ku shiga, sannunku".
Yayi gada da sauri Dan cika umarnin Alhajin na Kiran babban Amininsa na kankankan Malam Bukar.
Da sallama suka shiga falon, Masha Allah komai najin dadin rayuwa akwai shi a falon tamakar fadar wani
sarkin.
Cikin fara'a da sakin fuska Alh Jafar Mai Yadi ya nufo bakin nasa Yana fadar "A'a! Alhaji Sulaiman kune haka
cikin wannan ranar ga nisa".
Amma kasan zuciyarsa mamaki ne fall a cikinta shi dai yasan ba wani abu daya taso da zai kawosu a irin
wannan lokacin a kalla suna da sauran kwanaki uku kafin duzo duk da sun bada duk abinda ake da bukata
lokacin kawai ake jira. Amma dai ko meye Allah yasa Alkhairi ne.
Bayan gaishe gaishe na al'ada daya daga cikin 'ya'yan Ahj Jafar ne yayi sallama ya shigo Yana gaishe da
bakin Yana aje musu lemon da ruwa ya fita.
Wani matashin ne shima ya shigo da manyan warmers da wata yarinya da basket Mai dauke da plates da
cokula da cups Suma suka gaishe dasu suka fita.
Tunda aka Fara shigo da wannan karamar arzikin Alhaji sulaiman ya sadda Kai kasa zuciyar idan tayi dubu
to a bace take.
"Bismillah kuci abinci kafin mu shiga sallah tunda Azzahar ta gabato".
Alh Jafar ya fad'a Yana nufar kofar fita.
Bayan fitar Alhaji Jafar Alhaji Ismail ne ya kalli Yayansa Alhaji sulaiman "Nifa duk na rude wallahi har na
rasa ta inda zamu Fara fad'a musu irin wannan magana duba da irin karamcin wannan bawan Allah".
Ya fad'a yana Jan siririn tsaki.
Dan matashin daya tukosu ne yayi magana "wlh Daddy naso kun hakura da zuwa ita Hajiyar tazo da kanta
ta fad'a musu abinda ta kulla, ni ban taba ganin irin wannan ba anyi Abu cikin mutunta juna har an kawo
wannan gabar Amma Rana tsaka irin wanna ta taso Babu Dadi ni wallahi tausayin Musbahun nakeyi ya
shiga wani hali Amma ita ko a jikinta".
Shi dai Alhaji sulaiman Bai Kara magana ba haka Bai ko kalli abincin ba duk da yunwa da yakeji leonm da
ruwa kawai ya sha, Alhaji isma'il da Al-Amin ne sukaci abincin suka fita zuwa masallacin kofar gidan.
Tare suka shigo gidan bayan idar da sallar har da Malam bukar domin shine limamin masallacin.
Sabuwar gaisawa suka karayi Amma wannan lokacin Al-Amin Bai biyosu ba.
Alhaji sulaiman ne yayi Qarfin halin Fara magana Yana kallon Malam Bukar "Dan Allah malam ayi hakuri da
abinda mukazo dashi WALLAHI badan Nan gidan bane Babu abinda zai Kara dawo Dani garin Nan".
Yayi shiru ya kasa karasa maganar saboda wani abu daya tsaya Masa a makogwaronsa yana masa tukuki.
Shima Alhaji Jafar wani abune ya tsirga masa har tafin kafarsa ga wata irin faduwar gaba taba gaira ba
dalili.
Shiru falon ya dauka na wucin gadi kafin Malam Bukar ya magantu "Alhaji ka Fadi ko menene ba wata
matsala ita rayuwa ba yanda Bata zuwarwa bawa ko Dadi ko akasin hakan, Kuma duk musulmin kwarai ai
yasan kaddara, ba damuwa ai and Zama daya".
Alhaji Ismail ne ya karbi maganar ganin yayan nasa bashi da niyyar cigaba da maganar.
"Ayi hakuri Malam kan maganar auren yaron gurinmu ne da yarinyar gurinku, wata fitina ta taso yau
kwana uku kenan ana Abu daya mahaifiyarsa ta kafe kaida fata Bata amince ya auri Zahra ba duk yanda
mukaso gyara abun ya gagara karshe ma cewa tayi idan har Musbahu ya auri Zahra Bata yafe Masa
nononta daya sha munyi munyi da fad'a Mana dalilinta na wannan cin zarafin Amma ta kekashe taki fad'a
karshema abun ya zamar Mata lalura kamar ta jinni". Tunda ya Fara kora bayani Alhaji Jafar ke maimaita
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, domin duk wani karfin gwaiwarsa ya Kare wannan wace irin musiba ce
kullum idan auren yarinyar nan ya taso sai an Sami wani akasin ya taso shi Lamarin Nan ya rasa yanda zeyi
dashi.
Malama Bukar ma rasa abin fad'a yayi duk wani kuzarinsa ya Kare.
Yayin da su Alh Sulaiman suketa nanata ban hakuri.
Cikin muna juriya da dattako Malam Bukar yace "haba Alhaji ba komai kasan komai nufi ne na Allah Daman
Bai Qaddari shine mijinta ba, Allah yasa hakan yafi musu Alkhairi su duka'.
Gaba data suka amsa da Amin.
"Amma dai Abu baiyi Dadi ba wallahi ba Baki nayi musu ba Amma kafin a Sami Mai nagaratr yarinyar Nan
zasu Dade suna nema" cewar Alhj Ismail.
Har gurin mota suka raka bakin, har suka daga bakinsu Bai Dena bada hakuri ba.
Bayan tafiyarsu falon su Malam suka dawo jiki a sanyaye duk Lamarin ya cakule wannan wace irin kaddara
ce ke bibiyar karamar yarinya haka aure dai dai har uku ana fasawa.
Cikin nuna damuwa Alhaji Jafar ya kalli Malam Bukar yace "malam inshallah Allahu wannan karon zan
aurar da Fatima tunda Naga lamarin bana arzki bane ko meye in Sha Allah sai Naga bayansa'.
Tunda Alh ya Fara magana Malam Bukar ke girgiza Kai shima lamarin ya kaishi makura yasan lamarin
yarinyar akwai magauta a cikin Amma ganin an samu rata Mai yawa a tsakani ya dauka abun ya wuce ne.
Cikin nuna alhini Malam ya kalli amininsa yace "Dan Allah Alh kayi hakuri kada kayi Abu cikin fushi da kace
zaka aurar da ita kada azo ayi aikin Dana sani".
Kujerar dake daura da Malam din ya zauna kafin ya sauke ajiyar zuciya.
"Ko daya banyi fushi da ikon Allah ba kawai dai na gaji da wannan wasan ne kullum na Zama karamin
mutum saina Raba I.V na daurin sure azo ace an fasa wasu ma sai su zageni ace Dan bani na haifi Fatima ba
na saka ido ana Mata wannan cin zarafin wlh da banyi alkawarin daina hada auren zumunci ba da yau ba
sai gobe ba zan aurawa Abdul Hakeem ita. Amma yanzu ma Bata baci ba ka nemi shawarar Mahmud na
Nan gurinka idan ya amince na bashi auren ta".
Cikin kaduwa Malam Bukar ya kalli Alh Jafar yace
"Wane Mahmud din, ba dai na Nan gurina ba?".
Cikin yadda da Kai Alh Jafar yace "shifa nake nufi ko akwai wani Mai wannan sunan a gurinka?".
Gargiza Kai Malam din yayi tare da fadar "Babu, Amma Alhaji al'marin Mahmud ba boyayye bane a gurinka
kada duniya ta zagemu fa".
Gyara Zama Alhajin yayi kafi ya fuskanci amininsa sosai.
Wallahi Malam bana gudun duk abinda za'a fad'a na yaba da nutsuwarsa idan kaga ba'ayi ba to shima
Allah Bai nufi mijinta bane Amma na jima Ina yiwa 'ya'yana sha'awarsa".
Kai kawai Malam yake jinjinawa shi lamarin duk yazo Masa a baibai ya jima Yana nazari akan lamarin
Fadima kullum Abu daya yake gani mijinta ba Nan kusa take ba bil hasal ma wani lamari yake gani Mai
girma dangane da mijin nata da wani irin Haske Amma koda Wasa Bai taba fadawa Alhajin ba sai dai Yana
yawaita saka almajiransa gurin yi Mata addu'a.
Sun jima suna kullawa da kwancewa a tsakaninsu daga karshe suka tsaya a malam ya tambayi ra'ayin yaron
idan yana so la'ba'as.
_______
A hankali take sakkowa daga stair din tamkar wani dawisu Tasha make-up da wata gawon Mai azabar kyau
Sai karamar pos a hannunta daga bayanta 'yan Mata ne su biyu ko wacce Tasha nata gayun, tun kafin su
karasa sakkowa kamshinta Mai saka nutsuwa ya gauraye ilahirin falon.
Falon a Cike yake da jama'a kowa ka gani ta amsa sunanta sai tsirarun yara.
Da sauri wata ta matso gurin su tana rangada buda, tana fadar "Masha Allah Amarya Allah ya kade hau da
bala'i ya bada zaman lafiya Hajiya Zahra suga bayi farin banza jikar hardon fulanin Mubi jikar larabawan
Jodan da larabawan madinatul munawwara kaga musu kyawun asali Amarya a gidan Mushahu alherin
Allah yakai Miki".
Wata daga cikin matan dake zaune ta tashi ta sunga zubawa marokiyar kudin ita Kuma tana Kara Koda
Amarya Zahra.
Aunty Hasana ce ta fito daga wani Dan korido ta karaso tana kallon kanwar ta ta, tana Kara tasbihi ga
ubangiji daya halicci wannan kyakykyawar surar.
Hannaun Zahra ta rike tana kallon Baba Tabawa Mai aikinta yanda ta zage tana jero kirari kamar wata
marokiya.
Dan murmushi tayi tana fadar "Masha Allah, Baba Tabawa yaushe Kika Zama marokiya bani da labari?"
Dariya tayi tana fadar " ai ko ban iya ba na koya mu Abu namu bikin uwar dakina guda kinsan biki na d
farar kaza balbela ba gayya ce ba, yakuwar kan kabari kenan baking cikin 'yan taushe, murucin kna dutse
Baki fito ba sai da kika shirya"
Dariya sukayi gaba daya, har gurin da zasuyi bridal shower din kawar Aunty Hasana da Baba Tabawa suka
raka Zahra.
Sun chashe, sunyi hotuna kamar ba gobe sai dai duk Wanda yasan Zahra yasa Bata cikin walwala haka nan
take Jin wata irin faduwar gaba da rashin dadin zuciya Amma ita kanta Bata San taka maimai me yake
damunta ba gashi tun jiya take neman wayar Mushahun ta kasa samun shi, haka ta abokinsa Deeni itama
shiru a yanda sukayi dasu yau ne ranar da zasuzo Dan har hotel din da zsau zauna sun Kama mukullan ma
suna hannun magaji.
Dadin dadawa yau sukayi za'a kawo ya'yan yayar shi da wasu cussing dinsa.
Sai gurin karfe Tara suka Gama shagalinsu, Zahra Bata koma saman ba inda akayi musu masauki Sai ta nufi
bed room din Aunty Hasana na kasa dakin ba kowa sai kamshin freshner da turaren wuta yake tashi ga
danyi AC ya gauraye dakin. Head din ta cire ta aje kan bed side locker kusa lamp, gadon ta hau ta kwanta
lamo kamar ba mutum akai Dan ko kwakwkwarwn motsi Bata sonyi wata irin kasala ce ta sauko Mata.
Ta jima a dakin kafin taji alamun bude kofar Bata daga Kai taga ko wanene ba kamshin da taji ne ya sanar
da ita Auntyn ce.
Kusa da ita ta zauna tana Kai hannu jikin.wuyanta tare da tambayar "me yake damunki? tun safe Ina Kula
da mood dinki Sam bakya cikin nutsuwa".
Ta fad'a tana kafe Zahrar da Ido.
Yunkurawa tayi ta tashi zaune tare da fadar "Nima bansan me yake damuna ba wlh Aunty Sam bana Jin
dadin zuciya ta sai zafi take min Kuma gabana sai faduwa yakeyi".
Ta karasa fad'a tana shashhshekar kuka kasa -kasa.
"Meye Kuma abin kuka? keda zakiyi farin cikin Allah ya kawo lokacin bikin ba kamar lokutan baya ba da aka
dunga samun akasi".
Kanta ta kifa a jiki Auntyn taci gaba da kukan ta marar sauti.
Bata hanata sai tayi Mai isarta kafin ta Sami zarafin magana.
"Aunty wlh Ina ji a jikina kamar wannan ma za'a Sami matsalar kinsan jiya saida nayi irin mafarkin da
nakeyi idan za'a fasa aurena".
Ta fad'a tana Kara goge kwallar data ciko Mata Ido.
Kallon ta kawai Aunty Hasana take ita fa lamarin yarinyar Nan Yana Bata tsoro kada fa namijin Aljani ya
aure ta suna zaune Basu Gane ba.
Karo biyu ana saka bikinta abun Yana lalacewa toga wannan ma, itama fa kawai daurewa tajeyi tunda
Zahra ta fad'a Mata Musbahun Bai kira ba Bai kumazo ba ba wani Kuma nasa da yazo alhalin ba haka aka
tsara abunba, Amma sai tayi ta maza tace.
"Haba Zahra ya Zaki ringa fadar irin wannan maganar kiyi addu'a ba abinda zai Sami aurenki wannan karon
sai Alkhairi, Ina ga da abinda ya hanasu karasowar har yanzu ki jira zuwa gobe Mana maza kiyi sallah kici
abinci a sakonki can ki dauko zuwa an jima sai kiyi amfani dashi.
_________'
GIDAN MLM BUKAR
Bayan idar da sallar insha'i Malam da sauran manyan Almajiransa suna Zama ana karatun littatafan fiqihu
da hadisan Manzon Allah s.a.w.w, a Nan cikin baban falonsa ake karatun an kwata shi sosai a zuba kujeru
na alfarma, saida aka Gama karatun sannan sukaci abinci kamar yanda aka Saba kafin Kuma kowa ya nufi
nasa gurin duk da makarantar ta Sami cigaba sosai kamar ba makarantar amajirai ba anyi Mata tsari sosai
a zamanace Dan har hostel garesu sama da kasa da gurin koyon sana'a Kuma ana musu abinci basa zuwa
bara, sannan akwai malamai da aka dauka suna koyar da karatun boko tun daga mataki primary, junior,
zuwa senior, secondary suna kokarin Fara turo dalibansu zuwa manyan makarantu, sun Sami wannan
cigaban ne karkashin wata kungiyar NGO ne.
Lokacin da Mahmud da Habib zasu fita Malam yayi gyaran murya duk su biyun suka juyo, Mahmud yayiwa
alama daya dawo shi Kuma Habib ya fice..
Nan kusa da Malam ya zauna ta lakwashe kafafuwansa kamar zaman daukar karatu.
A hankali Malam yake Kare masa kallo shi kadai yasa abinda yake kissimawa a zuciyarsa sai Kuma Allah
daya hallice shi.
Sun dauki kamar minti uku a haka kafin Malam ya magantu.
"Mahmud"
Malam ya Kira sunansa.
Cikin ladabi ya amsa Masa da "na'am Malam".
"Kasan dalilin dayasa nayi kiranka?".
Cikin ladabi ya amsa da "A'a"
Cikin wani irin yanayi Malam yace "wani nauyin Kuka aka Dora min Wanda na rasa ta inda zan Fara maka
bayani".
Zamansa ya gyara Yana Kara fuskacin Malam din Yana fadin "Malam ka fad'a min ko menene ni maiyi maka
biyayya ne In Sha Allah".
"Ai kasan gidan Alhaji Jafar nawa za'ayi bikin yarinyar gurinsa ko?"
Kai ya gyada Masa tare da cewa "Eh na Sani ba Zahra za'a aurar ba?"
"Eh ita fa, to an samu wata matsala ne wadda ta haddasa kasa auren a wannan karon ma kamar lokutan
baya Amma wannan sai yafi na bayan Muni domin kuwa saura ba kaiwa ga Fara bikin Amma wannan Saida
abun ya kurace har an saka yarinyar a lalle sun Fara duk kwaramniyar su ta Mata a lissafi saura kwana uku
daurin aure sukace sun fasa, shine shi Alhajin yace na meni shawararka idan ka amince zaka iya auren
yarinyar ya baka za'a daura muku aure ranar juma'a inshallah Allahu".
Da sauri Mahmud ya dago Yana kallon Malama bakinsa har rawa yake yama kasa furta maganar dazai fad'a
Kai ya shiga girgizawa dafa shi Malam din yayi Yana fadin "ka nutsu bazamuyi maka dole ba idan bass sonta
sai a nemi wata mafutar"
Da kyar ya tattaro nutsuwarsa ya kalli malam yace
"Ba haka nake nufi ba, gani nayi yaushe nakai matsayin da za'a bani irin wannan yarinyar aure kamar tafi
karfina ni almajiri ne wanda ban aje ba banba wani ajiya ba, kuma tana da ilimi Mai zurfi ba lallai ta yadda
ta zauna dani ba".
"Ba wannan nake son jiba daga bakinka fadin Kai ko wanene ba taso ba Alhaji shi yafi sanin Kai ko waye
amsa muke bukata zaka iya aurenta ko bazaka iya ba ?".
Cikin alamar sarewa yace "wane ni ice bana son wannan yarinya na karba na gode Allah ya saka da
Alkhairi".
Ya fad'a cikin wata irin murya Mai sanyi.
"A'a kaje ka nutsu kayi shawara sai ka fad'a min duk huku cin daka yanke, tashi kaje dare ya farayi".
Yunkurawa yayi ya tashi Yana fadar "sai da fade"
"Allah ya tashe mu lafiya" cewar Malam.
Daga falon malam Mahmud bakin titi ya nufa inda yake tunanin ganin Habib Yana son ya karbi lifan dinsa
zaije wata unguwa.
Gurin Ashiru Mai shayi ya Fara zuwa baya nan sai su salisu da Bashir Suma duk mutanen Mahmud ne
hannu ya Basu saka gaisa sannan ya tambayesu Habib wani ne daga can gefe yace "ai yanzu ko runhu ka
rike yana gurin Ubaidat kasan mutumin naka Yana neman dauko dala ba gammo".
Ya karasa fad'a Yana dariya Bashir ne yace "ko wani Abu ne Naga ko Zama bakayi ba"
Da tsaki yayi Yana Dan dafe kujerar kusa dashi Yana fadar "wlh lifan dinsa zan karba zan danje unguwa".
"Kai haba saboda lifan kake wannan zagaye zagayen ga nawa kayi amfani dashi mana".
Ya fad'a Yana Miko Masa makullin ya karba Yana godiya.
Kai tsaye zaranda hotel ya nufa.❤️AUREN HUCE HAUSHI❤️
MAMAN FATIMAH.
✨Page two✨
________
Safa da marwa take tun bayan gama sallar insha'in ta, ta Kira layin wayar tafi sau shurin masaki Amma ta
kasa samun Wanda take nema, gumi ne yake fama tsatsato Mata daga goshinta, ta kasa zaune ta kasa
tsaye.
Gafen gadonta ta koma ta zauna Kara kiran tayi cikin ikon Allah sai Kiran ya shiga da sauri ta nufi kofar
toilet dinta na daki ta shige.
Bata tsaya amsa sallamar wadda ta Kira din ba ta Fara magana "Asabe me yake faruwa ne tun jiya nake
neman wayarki Bata shiga Ina cikin tashin hankali komai fa Yana nema dagulewa, ba alamun nasara a
wannan karon tunda komai ya kankama".
Shiru tayi tana sauraran wadda ta Kira Asube ta jima tana sauraran ta kafin tayi dariya tace "haba yanzu
naji magana da har hankalina ya tashi ki rike sauran maganar sai kin shigo gobe ma karasa".
Ta kashe wayar ta bude kofar toilet din ta fito cikin farin ciki da walwala sabanin yanda ta shiga.
___
Mahmud.
Ya jima a cikin hotel din kafin ya fito zuwa gurin securities din da alama sun saba sosai Dan yanda suke
bashi girma sai abin ya baka mamaki makullin lifan din Wanda ya barwa ya miki Masa tare da fadar
"Yallabai an zubo petrol din".
Lokaci daya Kuma Yana Miko Masa kudi, kallon na mine yayi masa.
"Kudin sunyi yawa ne a sayan man Saida naje na duba maga yawansu". Ya fad'a Cike da ladabi, hannunsa
ya zura a aljihun wandon jikinsa ya dauko wasu ya Kara Masa, sannan ya Kuma dauko wasu ya bashi
alamar ya baiwa abokan aikinsa.
Godiya suka dunga jero Masa Dan inda sabo sun saba da Alkhairinsa.
Kai tsaye gurin Ashiru Mai shayin ya nufa duk da dare ya Fara Amma yasan yanzu 'yan term din nasa Basu
Isa tafiya gida ba Dan sukan Kai har daya na dare suna hira.
Makullin lifan din ya mikawa Bashir Yana fad'a "Jazakumullahu khairan".
Habib ne yace "Wai Dan Allah Ina kaje a rufe wayarka tun dazu nake nemanka fa daga inje in dawo kawai
na nemeka na rasa sai su Salisu ne sukace kazo nemana ka wuce unguwa".
Kusa da Habib din ya zauna na fadin "wash Allah wlh duk na gaji".
"Da kayi aikin me".
Cewar Habib.
"Bari kawai ba aikin da nayi Amma Wanda yake fuskantoni ba sauki kazo muje gida akwai sakonka da
Malam ya bani na baka".
Ya fad'a Yana kikewa tare da mikawa su Bashir hannu yayi gaba gurin lifan din Habib.
Dakinsu Mahmud ya bude daki ne madaidaici da gado guda biyu da wardrobe ta jikin bango sai mirror irin
na croom din Nan da AC, kasan dakin shimfide da tayil, lokacin da akazo aikin NGOs din ne aka yiwa Malam
nashi falon da Kuma irin wadannan dakunan guda uku sai Kuma dakunan Yara almajirai sama da kasa.
Dakin sai kamshi yakeyi, sau da yawa Habib kanshi Yana mamakin wasu abubuwan na Mahmud sai dai ba
fuskar da ze tambaye shi duk kuwa da amincin dake tsakaninsu.
Saida Mahmud yayi wanka ya saka kayan barci sannan ya
Zauna a gefen gadon Yana fuskantar Habib kafin yace.
"Kai inaga fa nan da kwana uku zan ankwance".
Ya fad'a yana wani killer smile.
Zabura Habib yayi ya tashi zaune sosai Yana fadar
"Kamar Yaya?"
"Kamar yanda na fad'a maka, tsayar Dani da Malam yayi kenan yace Alh Jafar ya bani auren yarinyar Nan
da ake bikinta wadda Abdul Hakeem ya kawo Mana IV last week".
"Ban Gane ba bafa ta Yaya hakan zata faru?"
Kafada ya dage alamun shima Bai Sani ba.
"Dan Allah kayi min bayani yanda zan fahimta a sakani a duhu wallahi".
"Iya abinda na Sani kenan kawai ance an bani idan inaso inyi shawara".
Cikin madaukakin mamaki Habib yace "to Kai ya kace masa?'
"Me zance kuwa na karba na gode, kasan har abada ba jayayya tsanina dasu iyayene sak, sun min abinda
kowane uba yakewa dansa sun min gata sun Kula Dani lokacin da bana Gane gabas bane Gane yamma
bana Gane fari bana Gane Baki,
Sun zamar min garkuwar data Hana kowane harbi ya sokeni, Toni kuwa wanen irin butulu ne da zan watsa
musu kasa a Ido sufa sun san waye ni Amma suka runtse idonsu suka bani basu nuna min kyama ba,
sannan ka dubi yarinyar da aka bani diamond ce fa a cikin gold kasan bani da abinda zan tunkari irin
wannan yarinyar da sunan soyayya bare har aje ga maganar aure".
Tunda ya fara magana Habib yake Masa kallom mamaki Yana jinjina karfin ikon Allah, lallai wani lamarin sai
Allah.
Da kyar ya Sami zarafin fadin "Masha Allah! Allah ya Sanya Alkhairi Abu yayi Dadi amma fa ka daina fadar
Wai baka da abinda zaka tunkare ta wlh kafin wanna lagwanin Wanda zata aura say millions shi har wani
namiji ne kawai Abu daya Sani yana da kudi mu Kuma bamu dasu Amma muna da abinda bashi dashi".
"Kamar Yaya me muke da shi Wanda shi bashi dashi? ka duba fa kaga irin yanda yake shiga babban yaro ne
ga manyan motoci mu Ina muka gansu"
Dan karamin tsaki Habib yayi Yana fadain "ana gabas kana yamma ana maganar nagarta da mutunci da
cikar Kamala da siffar mazantaka kana wata maganar, mu an fad'a maka haka zamu dawwama bazamyu
arzikin ba".
Dariya Mahmud yayi "maida wukar abin Bai Kai haka ba ko Daman haushinsa kakeji ne ban sani ba?"
Habib tsayawa yayi galala Yana kallon Mahmud kafin ya karayin wani tsakin "Allah ya sauwake zanji
haushinsa Ina ruwana dashi kawai da Daman can no banga dacewar su ba Kai Nifa idan Malam yasa Yara
suyi Mata addu'a har cewa nake suyi Mata addu'a Allah ya Bata gwarzon miji na nunawa sa'a".
"Amma wallahi Habib baka da mutunci shi wannan ba gwarzo bane?"
"Ina fa namiji Yana rausaya kamar mace".
"Kaga Yi closing din wanna chapter din yayi zamuyi da wannan lamarin kaga dai komai fa Sai a hankali Dan
abinda nake Sami daga wannan organization din ba Isa wannan shidimar zasuyi ba ga yarinyar Mai zafi ni
kamar ma tsoronta nakeji fa".
Ya fad'a Yana dariya.
Sun jima suna tattaunawa yanda zasu bullowa lamarin.
_______
Tunda garin Allah ya waye Amma take ta kaiwa da kawowa tsakanin kitchen da dakinta zuwa dakin Baki,
Saida aka kammala abincin breakfast aka babba mutane sannan ta samu ta koma daki inda ta samu
kanwar Babarta Inna Maimuna a uwar daki.
Kallonta tayi "Asma'u ya kamata ki karya kinsan Ina tunanin zuwa anjima gidan ze Fara cika bazaki Sami
damar Zama kici wanti abun karki ba, waini ina Hajiya Mama ne Naga yau Bata leko ba?"
"Tana bangaren Alhaji Nima nayi wannan tunanin Amma ai lafiya ita keyin shiru".
"Hakan ne Kam".
Cewar Inna maimuna.
******
Katagum road
A dakin Aunty Hasana Zahra ta kwana ita da Autart Haneefa, sai kusan goma ta tashi daga barci wayarta ta
Fara dubawa ta tarar da missed calls rababa Amma Sam babu nasa ko na wani daya dangance shi, duk na
kawayen da abokanin arziki Bata bi rakansu ba ta shiga toilet wanka tayi, lokacin data fito Sajida ta Samu a
dakin ta shigo Mata da breakfast dinta nan, tunda ta fito Sajida ke kallon ta har ta karaso gurin mirror inda
sajidar ke zauna murmushi Zahra tayi Mata tana fadin "wannan kallon fa ko na canza Miki ne?".
Kai ta gyada Mata "gaskiya Kam ba haka na Saba ganinki ba, meye yake faruwa ne? nifa tun jiya nake
nema Deeni da wannan cussing din na Mushahu Aliyu, ta Aliyun tana shiga ba'a dagawa Amma su sauran
wayoyinsu switch off".
Da rausayar da kanta tayi tana Dan watsa hannuwa "wallahi bani da masaniyar me yake faruwa nima
hakan take kamar ke Amma nasan dai kome aje ciki yau dole su shigo garin. Ni wallahi da Aunty Hasana
zata yadda da an hakura da wannan mother's day din nifa duk abin ya fice min daga Rai gani nake shima
wannan aure ba yuwuwa zaiyi ba nasan dole da wata a kasa ai ba haka muka tsara abubuwan ba Amma
kin ko daya fa basuyi attending ba".
Ta karasa maganar idanunta na cikowa da hawaye.
Hannunta Sajida ta kamo ta rike tana fadar. "Hqba Bestie kada kiyi Kika in Sha Allah ba wani matsala sai
Alkhairi kada ki Bata lokacin farin cikinki mana".
Aunty Hasana ce ta shigo da sauri alamar wani Abu zata dauka turus tayi tana fadar "ke me zan gani Zahra
kukan dai? haba you have to be very strong Mana kada ki yadda aga rauninki a kowane janibi ki Zama
jaruma Mai iya fuskantar ko wane kalubale, kada ki kara saka damuwa a zuciyarki zan fita Amma in Sha
Allah bazan Dade ba ki shirya kuje sama naji suna cigiyarki".
A bangaren Mahmud kuwa bayan anyi sallar Asuba a masallaci ya zauna yayi azkar dinsa Saida gari ya Fara
haske sannan ya fito lokacin su Malam sun Gama karatun da sukeyi da maza magidanta.
Da sallama ya shiga falon nasa lokacin Abubakar Yana mayar da littatafan mazauninsu, sai da ya zauna
sannan ya Dan rankwafa Yana gaishe da malam, Amma sai ya moko Masa hannu sukayi musabiha Yana
fadin. "hakan shine sunnar Annabin Rahama Muhammad s.aw.w."
Shiru falon ya dauka bayan fitar Abubakar Malam Bai tofa ba haka Mahmud shima, Malam ne ya kauda
shirun "Ya ake cikin Mahamuda wace shawara ka yanke?".
"Ba damu Baba Malam na karba na gode ayi min godiya Allah yasa hakan yafi Alkhairi".
"Allahumma Amin. Allah ya Sanya Alkhairi ya Baku zuri'a Mai Albarka Allah yasa ace gara da akayi hakan"
A zuciyarsa yake ta amsawa da Amin.
Harya yunkura zai tashi Malam yace "koma ka zauna, Ina zaka bamuyi maganar inda zaka ajeta ba da
sauran shirye-shirye".
Sadda Kai yayi haka Nan yaji wani irin nauyin malam din ya taso Masa.
Kansa Yana kallon kasa yace "so nake muyi shawara dasu Habib yanda muka yanke saiya fad'a maka".
"A'a ba haka za'ayi ba nizan bada sadaki da kayan goro da alewa sai Kuma shaddoji da za'a kawo an jima
Suma dinkakkune tunda abun yazo a kurace, sai Kuma gidan Nan na Hayin Banki mukullin na gurin Binya
tun jiya na bashi nace yau zakuje a duba abinda za'ayi Masa".
Mahmud kasa magana yayi shi wannan gatan har yayi Masa yawa komai anyi Masa.
Rarrafawa yayi kamar yaro har gaban Baba Malam ya rinka godiya har Saida yayi Masa fad'a.
********
Amma ce da Inna a uwar dakin Ammar bayan dawowar Ammar daga bangaren Alhaji cikin tashin hankali
Innar ta kalli Ammar tana fadin ke Asama'u wace irin magana ce wannan yaushe hakan ta faru duk bamu
da masaniya?"
Dan nisawa Ammar tayi.
"Wallahi Nima ban sani ba Amma yace kada yaji kada ya gani naja bakina nayi shiru yana zargin kowaye
yake lalata lamarin auren yarinyar Nan na kusa yake tunda yace min Malam Bukar ne yayi binciken Dan
haka bazai cewa kowa komai ba har sai bayan daura auren tukunna".
"Ya fad'a Miki waye mijin?"
Kai ta girgaiza Mata alamar A'a.
Nifa Ina gudun garin AUREN HUCE HAUSHI a kwaso bara gurbi Wanda za'azo ana Mana dariya".
"Gaskiya bana tunanin haka Inna mu bita da addu'a kawai Allah ya Zama gatanta yasa albarka a ciki.
❤️AUREN HUCE HAUSHI❤️
Story & written
By
✨MAMAN FATIMAH.✨
Page three 🔷
.............. Tunda Mahmud ya fito daga gurin Baba Malam yake nazarin yanda zai bullowa lamarin, baya son
ko kadan a Sami kurkure, guri ya Sami nesa da makarantar kasancewar Alhamis ce Yara basa karatun safe
sai ya zamana yawancin su suna dakunan su.
Waya ya Ciro daga aljihun wandonsa yayi dialing din number Bata jima tana ringing ba kada daga magana
ya Fara "kana jina Sameer sakon Dana turo maka kada a samu kuskure kayi kokarin ganin komai yayi yanda
ya kamata fa".
Dan Jim yayi alamun ana fad'a Masa wani abu
"Ok to shi kenan take care".
Ya kashe wayar.
__
Nama ne da kayan miya ake ta shigo dasu cikin gidan da manyan kuloli sabbi Hajiya mama ce a kofar
kitchen din na tsakar gida tana bada umarnin abinda za'ayi, yaran dake shigo da kayan ta kalla "wannan fa
daga Ina?".
Magaji ne ya Bata amsa kafin yaron data tambaya ya fad'a Mata "tare muke Mama na abincin bakin Abba
ne".
"Ikon Allah Naga ai an kawo wasu da sassafe dazu gasu nan har an kusa Gama aikinsu".
"Eh to shi dai yace a kawo wadannan ma".
Magajin ya fad'a Yana shiga dakin Amma.
"Kai dawa Kuma kake tafiya kana magana"
Cewar Inna maimuna.
Kusa da ita ya zauna Yana fadin "nida Hajiya mama ne kayan miya ne da Naman rago Dana kaji Abba ya
Kara badawa aka kawo shine take magana ko yayi yawa kame?"
Dan murmushi Amma tayi "Abban Nan naku baya son a zauna lafiya wallahi magaji kamar zai aurar da
Yara uku sai irin wannan shidima yake haka".
Kai magajin ya jinjina "Amma kenan kin manta yanda Abba keson Zahra ai kawai kowa ya zuba Ido ana
auren uwar masu gida tab ai kowa sai yasan anayi Yasin, ki Bari kawai Ammah Nan zan kawo nama a ajiye
min".
Ya fad'a Yana dariya ya nufi kofar fita saboda sallamar wasu Mata da yaji a kofar dakin.
___
Daki Mahmud ya koma ya samu Habib a tsaye a tsakar dakin da alama daga wanka ya fito, saida ya Gama
wayar sannan ya kalli Mahmud.
"Wai ina kaje ne? Naga fitowarka daga gurin Baba Malam kafin na saka caji na nemeka na rasa, Bilya ne ya
kirani Wai mu sameshi a hayin Banki shi Yana can yaje da masu aiki su duba yanda za'ayi gyaran"
Dan Dafe Kai Mahmud yayi ya Dan fesar da numfashi.
"Ikon Allah Wai Daman kamar jira kuke ace za'ayi min auren Nan kowa sai rawar jiki yake yi, daga fad'a
shine har ya want kwashi jiki da masu aiki ya tafi tun garin Bai Gama watstsakewa ba".
"Naka wasa ne Alaji, aini yanzu haka mun Gama magana dasu Bashir sunce mun gasu Nan zuwa har suna
cewa shegen zurfin ciki ne da Kai baka fad'a musu ba jiya ko kunya kakeji irin ta Mata".
Ya karasa maganar Yana dariya.
Har ya nufi gurin mirror ya tsaya "kaji na manta ba Salis yace na tura Masa cikakken sunan da ze saka a IV
da zeyi a waya ya turawa friends na kusa".
"Ok ba matsala ka tura Masa kawai da sunan aika Sani ba saina maimaita make ba".
Misalin karfe Sha daya na safe wata bakar Hilux sabuwa kar ta dira a kofar gidan Malam Bukar.
Lokacin yaran sun firfito suna sugogin su masu wanki nayi masu wasa nayi Amma idan ba fada maka akayi
bazaka taba cewa yaran Almajirai bane kowa cikin tsabta Kuma a lokacin anyi hutun makarantar book shi
yasa basayi tunda suma tsarin makarantar gwamnati suke bi.
Mutane biyu be suka fito daga motar da sauri 'yan samarin dake kusa taso da sauri suna fadin barkan ki
da zuwa kasancewar sun saba dasu sosai sune wadanda suke kawo musu tallafi daga organization din.
Da sauri suka bude musu falon saukar bakin Malam kafin wani ya shiga ya fadawa Malam din.
Ba jimawa Malam din ya fito suka gaisa a mutunce, sannan suka gabarwa da kayan abincin da suka kawo
sannan suka gabatar Masa da bukatar daukar Mahmud zuwa wani taron karawa juna Sani na makarantun
tsangaya Wanda za'ayi a kano, tunda shine Wanda suka dauka aiki a Nan tsangayar yake wakiltar su kuma
gobe juma'a za'ayi taron na Rana daya ne kawai.
Dan Jim malam din yayi kafin yace " Ikon Allah malam Sameeru ga koshi ga kwanan yunwa WALLAHI shi
Mahmudan dai baze Sami damar halartar taron nan naku ba, domin a goben in Sha Allah za'a daura Masa
Aure".
Cikin wani irin madaukakin mamaki Sameer dake kusa da Malam din Kuma jagaban tafiyar ya kalli Malam
Yana cewa.
"Aure! Kuma Malam?".
Kai ya jinjina Masa alamar tabbatarwa, "yanzu haka suna can gidan da ze zauna ana dudduba gyaran da
za'a Masa duk da gidan Bai jima da kammaluwa ba kasan kullum abin duniya sabuntashi akeyi".
Kai ya jinjina ya hadiye wani yawu da kyar shifa duk ya shiga rudu meye hakan Wai Kuma.
Fara'ar dole Sameer ya kirkiro Yana kallon Malam yana fadar "Masha Allah Abu yayi Dadi to ai mu wannan
lamarin namu ne munzo a dai dai kenan tunda Abu ne na ma'aikacin mu koma kunya zatayi Masa malam
kada kuyi komai yanzu zanyi waya za'ayi duk abinda ya kamata tun daga abinda ango ze saka har abinda
za'aci duk Yana karkashin kularmu tunda mu yakewa aiki, Kuma zamu zauna sai an daura auren damu in
Sha Allah. Maganar taron Kuma sai dai a daga zuwa wani lokacin Dan bamaso wani yayi missing gaskiya".
Tunda Sameer ya Fara Kora bayani malam ke jinjina Kai saida yake Aya sannan ya Sami zarafin magana.
"To malam sameeru anyi haka abin fa da yawa kids bakuzo da Shirin wannan abun ba kunzo Kuma kuyi ya
kuyi makarbiya ai da wahala abun".
Dariya Sameer din yayi Yana fadar "malam ba abunda ze gagara kungiyoyin masu karfi ne, yanzu ma ga
wannan saboda biyan sadaki".
Ya aje Masa cheque na Banki suka Mike Yana fadar "Bari na Nemo shi a waya sai muje muji meye shirye-
shiryen nasu, a huta lfy".
Suka kad'a suka fita.
_____
Kyakykyawan guri ne Aunty Hasana ta kama inda za'ayi mother's day din gurin ya kayatu ba karya kudi dai
an kashe su gurin Kama event center din, anyi taron Mata 'yan gayu kamar ba gobe amarya tasha kyau
kamar a dauke ba boye.
Ga wani slow music da mc din ya saka na wakar Amarya da ango kowa ka gani cikin nishadi yake sabanin
Amarya da Yayarta Banda ta Riga ta gayyato mutane harda wadanda sukayo Mata tafiyayya sukazo da ba
abinda ze saka tayi wannan taron to Amma mutum Bai Tara Sani ga Allah ba.
An raba kayayyaki na alfarma na bikin, sai magariba taron ya tashi, zuwa yanzu 'yan Qananan maganganu
sun Fara fita a tsakanin kawayen Zahra tunda har zuwa lokacin ba wani duriyar Ango ko wani nasa, sai Dan
kus-kus ake abinda yafi bada mamaki bai wuce ganin anata faman programs ba normal.
Su Mahmud Basu samu kansu ban sai bayan sallar insha'i lokacin suka zauna Dan wuni guda suna ta faman
sunturi daga can zuwa can abin dai ba sauki dan su sameer suna zuwa gidan suka babbago aikin da sai anyi
sati ba'a Gama ba Dan sunce tsarin gidan gaba daya za'a sake, basunda ta cewa tunda oganninsu ne sai
godiya suka dunga zubawa harda su Bashir.
Gurin karfe goma malam ya Kira Mahmud a waya yace yazo cikin gida ya same shi.
Saida ya leka falon iya Abu suka gaisa tana faman jansa tana ita ce ta karfen Dan haka ita zata koma sabon
gidan a kawo Amarya nan.
Da haka ya karasa turakar malam Yana zaune a falo Yana sauraren wa'azi a TV, yayi sallama Malam din ya
bashi izinin shiga, Nan kasa ya zauna Yana gaishe da malam din.Wasu manyan ledoji malam din ya nunawa
Mahmd Yana fadin.
"Dauko wadan can kayan ka duba daya Wanda nasa a kawo maka ne biyun Kuma wadannan masu
kungiyar ne ta taimakon tsangayu suka kawo ga lemuka can da ruwan roba sun kawo yafi catoon dari
sunce kada ayi abinci ma duk za'a kawo, har na rasa da wane bakin zan gode musu, sai dai Ina rokon
Ubangiji s.w.w yafi mu yabawa, naji su Habibu ma sun ce sun dauko aiki Mai yawa a wancan gidan ko?"
"Eh wallahi munyi-munyi su Bari suka Kiya Wai haka aikin Qungiyar yake in dai kana musu aiki idan wani
Abu ya sameka Mai Dadi ko marar dadi su zasu tsaya maka".
"Alhaji yace min kun shiga dazu bayan sallar magariba har da bakin kunyi Masa godiya, kun kyauta haka
ake so".
Lokacin Mahmud ya koma dakinsu Habib baya Nan gurin da yake aje makullin lifan dinsa ya duba ya kuwa
you sa'a yana nan, lodojin ya zube a kan gado ya dauki makullin ya rufe dakin ya hau mashin din yayi gaba.
Bai dawo ba sai kusan Sha biyu da rabi har lokacin kuma Habib baya dakin yasan suna can suna kujuba
kujuba.
Yauma Zahra taso kwana a dakin Aunty Hasana saboda tana bukatar kadaicewa Amma Sajida ta matsa
Mata da mita Saida suka tafi Amma fa zuciyarta Bata da nutsuwa gashi tana ankare da Aunty Hasana tun
jiya da dare a taje can gida cikin gari Bata da nutsuwa ko alama Amma tana ta kokarin ta basar sai dai ko
Yaya mutum ya shiga damuwa indai kayi Masa farin Sani zaka fahimta, ita Abu mafi Bata mamaki yanda
aketa kwaramniyar bikin ba wani canji sai dai abunda baza'a rasa ba duk da Daman ba wata muguwar
bidi'a ba ta had'a, walima ce kawai Bata Sami ba saboda tace ita malam Tijjani Ahmad zeyi Mata Kuma
bayanan yana Umara.
Tunda tayi sallah ta kasa tashi daga gurin tana kallon su Sajida sunata sabgarsu, Amma ita da wata irin
faduwar gaba ta tashi ta rasa nutsuwarta kwata kwata da kyar ta tsahi sauko kasa gurin Aunty Hasana a fall
ta sameta tana hadawa Abbansu Haidar break fast.
Gurin dining din ta karasa tana gaishe shi sannan gaida Auntyn.
Dakin Auntyn ta shiga kwanciya tayi tana ta faman sakawa da kwancewa zuwa yanzu dai tasan tabbas da
matsala sai dai yanda ba Wanda ya fad'a Mata shi yasa itama ta zubawa sarautar Allah Ido taga iya karshen
film din tasan ko menene yau dai za'a yita ta Kare tunda yau ne deadline duk wata kunbiya kunbiya za'a
zazzageta.
Tun karfe goma Mai yiwa Amarya make up tazo Amma kememe Zahra tace ita bataso a kyaleta aka dunga
yiwa kawayenta, ganin guri ze kure ne Sajida take ta fadawa Aunty Hasana Saida tazo sannan akayi Mata
light makeup Amma fa duk da hakan tayi karshen kyau, farin material ne ta sakata Mai touching din sky
blue sai aka daura Mata head shima sky blue din takalman da pos din duk sky blue din ne.
Wani san sanyan kyau tayi na ban mamaki, komai na Zahra Mai kyau lallai zaharar ce Dan duk cikin
kawayen Bata da mahad'i.
A babban masallacin juma'a za'a daura auren Masha Allah, ango ya fito Shar abokansa sai mamakinsa suke
Basu taba sanin kyawunsa da cikar haibarsa ya Kai haka ba sai daya fito sun Sha mamakin kwarai har wasu
suka Fara kokonto a kansa, Yana kallon yanda idanun sukayi Masa caa.
Dan dakakkiyar getzener ta saka ga takalman da agogo ga hula, Sam bazaka taba cewa Wai alamajirin
malam bane ba, ga wani irin kamshin tunda ta tumkaro taron abokanensa kamshin ya hade gurin.
Daga gefe sameer ne da abokinsa Naraddeen suna tsaye lokacin da Mahmud ya fito Sameer ya kalli
Naraddeen din yace "wallahi wannan guy kwallon Dan duniya ne na rasa Gane kan alkiblar daya kalla Wai
aure zai daura shi kadai kamar marara gata, ni so nake Naga karshen wannan wasan kwaikwayon nasa.
Daga inda yake tsaye ya kafe Sameer da Ido ko Bai fad'a ba yasan me yake nufi tun jiya yake tuhumarsa aka
zuwa da abokinsa da yayi duk da ya nuna Masa wannan ba wata matsala bace Amma har yanzu Yana
hukunta shida idanunsa.
Masha Allah dubban mutane ne suka shaida daurin Auren FATIMAH ZAHRA AHMAD SANI da Angonta
MAHMUD MUHAMMAD DANGE akan sadaki dubu dari uku lakadan ba ajalan ba.
Daurin aure daya bawa dubun mutane mamaki bare wadanda sukazo daga bangaren Mushahu sunyi
mamaki kwarai sunan Amarya dai shine Amma ba mijin daya gayyato su bane yayin da yan unguwa ya
Zama abin kasawa a faifai ana yawo dashi, da yawa na ganin beken Alhaji Jafar na aurawa bakon da
ba'asan asalinsa ba yarinya kamar Zahra yayin da wasu ke fadar ai Dan ba 'yarsa bace shi yasa yayin
wannan danyan aikin.
.......
❤️AUREN HUCE HAUSHI ❤️
Page four🔷
___________''
Wata marokiya ce irin dattawan Nan da suke bin manyan marok'a ta biyo tawagar masu dawowa zuwa
gida kasancewar gidan ba nisa daga masallacin juma'ar, itace ta rangad'a guda har sau uku ta Kara da fadin
"Alkawarin Allah ya tabbata an daura auren Fatima Zahara'u da zukeken Angonta Mahmud Ubangiji Allah
ya bada zaman lafiya da kazantar daki Bata shara ba, munzo much arziki mubar arziki a gurinsa.
Kamar saukar aradu haka maganar ta shiga kunnen Hajiya mama, batasan lokacin data tsallake mutanen
falonta ta fito ba dankwalinta a hannu, tana fadin "me naji ana fad'a wa aka daurawa aure da Mahmud
naji kowa".
"Eh haka ne Kam Alkawarin Allah ya ciki Zahara'u ta Zama matar Mahamuda"
Ta debo wata gudar ta Kara rabsawa.
Dai dai lokacin Hajiya kaltume aminiyar Ammah ta fito ta dukulawa wannan marokiyar kudi sannan ta Mika
Mata babbar leda Mai abincin biki har da ruwa da lemo.
Cikin rashin nutsuwa Hajiya mama ta nufi dakin Amma ko sallama Babu ta Fara fadar "Hajiya kinji abinda
naji ko kunnena ne ya jiyo min ba dai dai ba?".
Kallonta duk 'yan dakin suke kafin Ammar tace Mata "nima haka naji kamar yanda kikaji sai dai ko shirme
takeyi ita Mai rokon tunda ba sanin su tayi ba".
"Eh gaskiya Kam sai dai hakan".
Ta juya ta koma daki. Bata zauna a falon ba uwar daki ta wuce, Asabe ce ta rufa Mata baya, a tsaye ta
sameta ta Goya hannu a baya tana Dan Kai kawo a tsakanin gado da madubi.
Waiwayowa tayi tana kallon Asaben kafin ta zauna a bakin gado, kusa da ita Asaben itama ta zauna.
Tana fadar "Haba Hajiya Dan Allah ki nutsu bana son ki bada wata baraka a sabgar Nan keda na fad'a Miki
Daman malam na BANDE yace wannan karon aure sai anyi Amma ba da Mushahun ba, Amma abinda yake
daure min Kai malam na banden yace Wanda zata aura a nesa yake Kuma yaga haske so sai akan lamarin
duk yanda yaso ya Bata lamarin abin Bai yuwu ba shine nace kawai a kyale tunda dai Wanda muke son a
fasa da shin din aikin ya yuwu, nasan dai da wuya ta Sami irin Wanda ta rasa a bay".
"Haka ne Amma abin dubawar waye wannan din sanan me yasa aka kudundune zance? Wai fa Dan
munafurci Hajiya Asma'u cewa tayi Bata Sani ba ke kin yarda Alhaji ze aurar da Zahra Bata da masaniya, ko
meye ma dai kyawaun ya kare a auren Hadi tunda nasan ba wani sai Mushahun shi Kuma ya Kara gaba
kamar sauran".
Ta fad'a tana kwafa, mikewa tayi tana gafar "Bari na fita sai Naga kul uwar daka".
"Allah ya taimaki uwar dakina, aikinki Yana kyau".
Asabe ta fad'a tana mikewa itama.
**********
Daga gurin daurin aure Kai tsaye gidan gonar Alhaji Jafar suka wuce har tawagar angon bisa umarnin
Alhajin tun safe ya turo Mai sunasa (magaji) yaje ya fadawa Baba malam.
Anci an Sha kamar ba gobe mutane sunyi mamakin irin wannan karamar arzikin dan duk zarin mutum sai
dai yaci ya Bari ruwa da lemo kuwa kamar banza.
Abokan Mahmud kuwa sai Dan biki suke Masa.
A gidan malam ma Masha Allah anci an Sha Yara sun san ana biki a gidansu, Iya Abu ma tayi nata taron
komai baja baja makotanta ma sunsan ana hidimar arzki a gidan Kuma Suma sunzo Mata harda masu riko
abin arzikinsu su kawo Mata.
******** A guje Faruq ya Fado falon Aunty Hasana,danta ne na uku Yana rungume da babbar rigarsa ta
daurin aure daya saka Yana Fadi "Aunty Zahra wallahi Naga mijinki ba wannan Uncle din bane na kano
wallahi wanna yafi shi kyau Baki gani ba yanda yake rabawa marok'a kudi ba, Kuma Dan gayu ne sosai
Naga Uncle Abdul Hakeem ma ya rugume shi Yana ta dariya, Dana tambayi Auncle Imam yace min sunansa
uncle Mahmud".
Tunda ya shigo Yana karadin Nan ta zuba masa Ido tana sauraren abinda yake fad'a, kana ganinsa kasan har
zuciyarsa abinda yake fad'a din gaskiya ne, wani irin gingirin taji kanta yayi mata, nan ta sulale ta kwanta
kan kujerar ta saka hannunta ta rufe fuskarta wasu hawaye na zubo Mata masu zafi.
Sajida da Amatu suka nufi gurin Faruq din suna neman Karin bayani.
Yayin da wasu da yawa suke ta sabgar ciye ciyensu Dan Suma Kam an kawo koma enough.
Kamar yanda ya fad'a haka Suma ya mayar musu Dan su harda Karin bayanin yayi musu kasancewarsa Mai
surutun tsiya.
A hankali Sajida ta kamo hannun Zahra Dan Bata fatan wani daga cikin bakinsu su fuskanci an samu
matsala gaskiya, kamar masu you shawara suka shiga dakin Auntyn saboda Nan ne baza'a shigo ba.
Bakin gadon ta zaunar da Zahra ita Kuma ta janyo stool ta zauna har lokacin Bata saki hannunta ba,tana Jin
yanda ilahirin jikinta yake rawa.
Hannun ta Kara jimkewa cikin nata tana fadar.
"Cool down Mana bestie haba take it easy, kada ki tada hankalinki Taya Zaki kama maganar faruq kinsan
dai ba wani hankali ya Gama Masa jiki ba".
Kai ta shiga girgizawa cikin muryar Kuka tace.
"Wallahi Saji akwai matsala kema Kuma kin sani sai dai kik'i fad'a idan ba matsala Ina su Maryam da
mukayi dasu zasu zo tun kwana ukunda suka wuce Ina shi kanshi uban gayyar ina su Deeni dasu Aliyu,
kowa ka Kira sai dai kaji switch off baka haka ba".
Ta fad'a tana fashewa da wani irin Kika.mai taba zuciya.
"Kiyi shiru Dan Allah kada ki janyo hankalin mutane Mana kinga ga Amatu can zataji dasu ki nutsu har muji
meye gaskiyar maganar Mana".
"Ki barni nayi kuka wallahi na gaji nikenan kullum matsala daga wannan sai waccan na rasa a Ina matsalar
take ni wallahi bana son kowa ma a kyakeni haka Nan bana son auren, bana so wallahi ni nagaji Allah
Jordan zan tafi bazan zauna ba, bazan Kara Zama a kasar nan ba".
Ta fusge hannunta daga na Sajida ta yunkura ta tashi ita dai Sajida Bata San ta Yaya akayi ba sai ganin Zahra
tayi ta kifa kan gadon tana wata irin fuzga da gudu ta karasa kusa da ita tana jijjigata tana fashewa da kuka
tana fadin "ki tashi Dan Allah wayyo Allah na".
Baba Tabawa ce ta bude kofar ta shigo, Dan tunda tana kusa dasu Faruq ya shigo da wannan maganar duk
da tasani Dan Aunty Hasana Bata rufe Mata komai ba ta fad'a Mata tun jiya, shi yasa data ga sun nufo
dakin hankalinta ya kasa kwanciya ta biyo su tasan koya Sajida zatayi Mata kalamai ba kamar ita ba tunda
abinda babba ya hango yaro koya hau iccen rimi bazai gano ba.
Turus tayi tana kallon Sajida dake Kuka bil hakki tan jijjiga Zahrar.
Da sauri ta karaso tana fadar "ke 'yan Nan menene haka?".
Hawaye jage-jage Sajida ta dago tana fadar "wlh Baba Tabawa kawai tana kuka tana maganganu tana tashi
kawai sai Naga ta yanke jiki ta Fadi?.
Wani ruwa Baba Tabawar ta dauko a kan bedside fregde din Nan ta zubawa Zahrar a fuska Amma shiru ta
Kara watsa Mata Nan ma shiru cikin tashin hankali ta lalubo Yar wayarta rakani toilet ta mikawa Sajida
"ungo maza Kira min Aunty zakiga an saka Maman Ali yi sauri".
Bugu biyu Auntyn ta dauka tare da sallama, gani Sajida ta rasa me zatace ne yasa ta mikawa Baba Tabawa
wayar.
Can Kuma tana ta faman" hello Baba"
Abinda taji kenan lokacin data Kara wayar a kunne cikin sauri Baba tace "yi sauri ki turo a Kai Zahara'u
asibiti wallahi gata Nan a suma min yayyafa ruwa a banza".
Bata jira taji me za'a fad'a ba ta kashe wayar.
Abdul Hakeem Aunty Hasana ta lalubo a waya lokacin suna tsaye shi da Mahmud suna magana wayar
Abdul Hakeem dince ta Fara ringing Sunan Aunty Hasana ya gani ya daga har zai Fara Mata abunda ya saba
ta tsayar dashi tana fadin "Dan Allah maza kaje gidana ka dauko Zahra ku wuce asibiti mu hadu a can wai
Suma tayi"
Kit ta kashe wayar.
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un yake ta Nanatawa da sauri Mahmud ya tambaye shi "lafiya meya faru".
"Bari kawai ba komai Ina zuwa yayi gaba da sauri jikinsa har rawa yake Yana tafe Yana laluben key din
motarsa. Da sauri Mahmud ya biyo bayansa' Sam baiji key din ba sai daga baya ya tuna tana hannun
mustapha yaje gari ya dawo.
Tsaki yayi daidai lokaci da Mahmud din ya karaso Yana fadar"Dan Allah Wai menene Naga duk a rude".
"Bari kawai Wai Zahra ce ba lfy zan kaita ASIBITI".
Kallon yayiwa Abdul Hakeem din kafin yace "shine Kuma zakaqi fad'a min".
Hannu yasa ya yafito Sameer, cikin bada umarni yace
"Dauko motar can kuje da Abdul zaku Kai madam asibiti". Ya juya ya koma gurin su Habib.
Har sukaje gidan Auntyn Abdul Hakeem Bai daina mamakin Mahmud ba, yanayin yanda yayi maganar
kawai kasan da abinda ya taka umarni fa ya bada, su dai a zahiri ai Sameer ne uban gidan Mahmud tunda
kowa yasan aikin NGO's ya kawo shi garin har suka hadu da Mahmud din suka dauke shi yake musu aiki a
sauran makarantun tsangayun na cikin gari Dana kauye.
Da sauri Abdul Hakeem din shiga gidan Auntyn ta kofar baya gurin kitchen ya shiga koridon dakunan
barcinta.
A tsaye cirko cirko ya samu su Baba Tabawar har lokacin numfashinta Bai dawo ba.
Da sauri ya karasa gaban gadon yasa hannu ya dauketa kamar wata Baby yayi waje da ita. Sajida da Baba
Suka rufa Masa baya.
Da sauri Sameer ya bude Masa seat din baya ya sakata Sajida ta shiga ita da Baba shima Abdul Hakeem ya
shiga gaba da gudu Sameer ya fizgi motar. Saida ya daidaita a titin sannan ya kalli Abdul Hakeem din "ina
muka nufa?".
"F.M.C zamuje tunda yafi kusa".
Nan da Nan aba karbeta likitoci suka rufu a kanta, suna Nan tsaye Aunty Hasana tazo ita da Inna maimuna
sai Hajiya kaltume.
Suma tsayawa sukayi a gurin Baba Tabawa tana maida musu yanda akayi ita dai Sajida ba baka sai sharar
hawaye take.
Su Abdul Hakeem suna suna gefe daga zuwansu Mahmud ya Kira akai sau biyar idan ya Kira Sameer sai ya
Kira Abdul Hakeem, daga Jon yanayinsa kasan Yana cikin damuwa abinda ya Kara daure Abdul Hakeem Kai
yandq Sameer yake amsa wayar Mahmud cikin kulawa da bada girma.
Sun dauki a kalla minti arba'in kafin babban likitan ya fito sannan sauran Suma suka fito.
Su Abdul Hakeem sun bin bayan likitan kamar yanda ya bukata Amma ganin an gungoro Zahrar a gadon
daukar marasa lafiya yasa suka nufe ta da sauri suda su Aunty Hasana.
Wanda ya turo gadon ne yace "ai ta farfado ba wata matsala ana so ne dai ta samu hutu sosai jininta ne
yaso Hawa Amma cikin ikon Allah anyi controlling dinsa".
"Oh no 'yasu Allah ka dubi lamarin wannan 'yar maraiya duk da Bata tashi da rashin gata ba sai yanzu ka
kawo Mata Tata jarabawar Allah ka shiga cikin lamarinta".
Aunty Hasana ta fad'a itama tana goge hawaye.
A can gidan biki Kuma Amma ta rasa inda su Hasana da Inna suka tafi Dan hankalinta Bai kawo Mata
Hajiya kaltume ma Bata Nan ba sai da abokiyar zamanta tazo sannna ta fuskanci itama Bata Nan din
wayarta ta dauko ta Kira Hasana, lokacin tana zaune gaban gadon da aka kwantar da Zahrar.
Sunan Ammah ta gani sai lokacin ta tuna Ashe Bata fad'a Mata ba.
" Assalamu Alaikum Ammah".
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, wai Ina Kika tafi ne babu ke Inna maimuna ma
Bata Nan Hajiya kaltume ma banganta ba".
Dan Jim tayi har Saida Ammah tace "kina jina?"
"Eh inaji Ammah duk muna tare dasu, muna Nan gurin Zahra Bata Jin dadi ne Amman da sauki yan haka
barci take".
"Wane irin zance ne wannan kamar Bata Jin dadi Kinga Hasana fadi min gaskiya yanzu kina Ina?".
" Muna F.M.C wlh jikin da sauki sosai kawai sunce ana dai San ta huta ne, kada ki tada hankalin Dan Allah".
"To Allah ya kyau Amma Ina hankali ze kwanta".
Waje Aunty Hasanar ta fito gurin su Baba tabawa da sajida tace
"Baba tabawa Dan Allah kuje gida da sajida tasan inda aka aje abubuwan da zasu bawa kawayensu tunda
yau zasu wuce sai ki fad'a musu tana gida gurin Abba, ta kalli Sajida ke Kuma duk tmbayar da saying Miki
kice Baki Sani ba mu barsu a haka".
Kudi ta mikawa Baba tabawan sannan ta karasa gurinsu Inna maimuna da Hajiya kaltume, Suma bayi tayi
musu na Kiran Ammah tace suje gidan Dan hankalinta ya kwanta.
*********
Da kyar Amma ta Bari akayi sallar magariba ta shiga bangaren Alhaji Jafar ta same shi da Hassan da Abdul
Hakeem suna magana akan Zahra Hassan Yana ta mitar meyasa Abban yayi haka ai da hakuri kawai akayi
har lokacin da Allah ze kawo Mata wani.
Dan murmushinsu na manya yayi Yana "fadin wannan ma in Sha Allah Babu Dana Sani a cikinsa ni nasan
nagartar Dana gani tare da yaron yasa na bashi, Kuma ko bayan Raina zakuce na fad'a muku".
Jiki ba kwari Amma ta gaishe da Alhajin tana Masa ban gajiya tare da godiya.
Sannan ta Dora da fadin "Dan Allah ko zaka Bari naje Naga jikin nata?"
Tsai yayi Yana kallon ta "da kinyi hakurin zuwa Suma da anjima zasu taho gida yanzu ma daga cen muke ko
zuwan mu Bai isar ba?"
Cikin Jin nauyinsa tace "A'a ya badatar"
Ta tashi ta nufi kofa da kallo Abban ya bita ita kanta tausayi take sashi da gani zuciyar ta ba Dadi.
Da sallama suka shiga dakin lokacin Aunty Hasana tana sallar insha'i ita Kuma zahra farkawarta kenan tana
kokarin tantance Wai inane ma Nan din inda ta gani idan dai ba gizo idanunta ke Mata ba kamar asibiti.
Sallamar ce ta katse Mata tunani ta Dan dago kanta kadan sukayi arba dashi Ido cikin Ido da sauri ta runtse
idanunta zuciyar ta na wata irin bugawa tana ambaton Allah a zuciyar ta, meya kawo wannan dodon nata
gurinta, Kara rufe idanun tayi it fa wallahi zata iya rantsewa Allah duk duniya ba idanun da suke figitata
kamar nasa.
Strory
&
Written
By
MAMAN FATIMAH
Page five
_______ Shiru dakin ya dauka har zawan lokacin da Aunty Hasana ta idar da sallar.
Dan juyowa tayi kadan tana fadin "wa'alaikumus Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, sannunku
da zuwa Bismillah ga kujeru nan ku zauna".
"To mun gode Aunty" Sameer ya fada.
Cikin ladabi da mutuntawa suka gaishe ta tare da tambayar Mai jikin, ta amsa musu da sauki, sai kuma
dakin ya Kara daukar shuru Zahra dai tunda ta rufe ido Bata Kara gigin budewa ba, ita ji take duk ya cika
dakin ita tun ganinta na farko dashi a duniya ya birkita Mata lissafi, Kuma saboda Allah meya kawo shi
gurinta asibiti duk da tasan mutumin Ya Abdul Hakeem ne Amma sai taga kamar ba sai yayi Masa Kara ba,
ko Kuma yazo wata sagbar ne asibitni ya Sami labarin shine ya shigo ya dubata.
Magaji ne ya shigo dakin da sallama sai Kuma ya Dan tsaya baiyi tunanin ganinsa ba Sam da fara'a ya
karaso Yana fadin "Ashe Kuna Nan ai tare muke da Ya Abdul Hakeem ma".
"Ok" abinda Mahmud ya fad'a kenan
Shi Kuma Magajin ya karasa gurin Auntyn Yana gaishe ta.
Abdul Hakeem ne ya shigo Yana rike da wayarsa a hannu da sauri ya karasa gurinsu Mahmud din Yana
fadin "A'a angon ne da kansa" Yana Mika masa hannu.
Saroro Aunty Hasana tayi ita wace iri ce kawai dai taga sun shigo sun gaisa wallahi Sam Bata kawo ba ita da
akace Mata Alamajirin Baba malam ne ai ta dauka irin wannan gaddawan ne, yo ta Ina wadannan sukayi
wani Kama da kolaye ai ita zallar ilimi ta gano da wayewa a tattare dasu.
Hanyar wajen ta nufa tana janye da hannun magaji duk sai taji kunya ta kamata Ashe sukanta ne.
Ita kuwa Mai gayya Mai aikin ai tana jin an ambaci ango ta bude idonta girjinta Yana wata irin dokawa
"ango a nan to waye a tsakaninsu da suka shigo tare?
Abdul Hakeem ne ya kalli gurin gadon Yana fadi.
"Masha Allah! Ashe kin tashi, ya jikin?"
Ya fad'a Yana karasawa jikin garon Sameer ma Dan matsawa yayi Yana dubata Kai kawai ta gyada musu,
tana kallon Ya Abdul Hakeem din, kallo irin na neman Karin bayani.
Yi yayi kamar Bai Gane ba ya juya yana yiwa Sameer magana suka fita.
Har suka fice Bai dago ba Yana ta faman tab'a waya sai da ya Mula Dan kan shi sannan ya tashi ya tunkari
gadon.
"Ya jikin?"
Ya fad'a Kai tsaye, Bai Kuma jira ta amsa ba Dan ko kwakwkwaran motsi ta kasa sai tunanin da yake Mata
Kai komo.
"Badai wannan bane ake nufin an daura min auren dashi Amman da Naga ta kaina".
Shine ya katse tunaninta.
"Ki kwantar da hankalinki ki daina saka damuwa a ranki da kannan shekarunki, ki kuma dagawa Ammah í
nata hankalin, idan nine bakya so ba damuwa Nima kusan hakan take. Amma kada mu watsawa iyayen mu
kasa a ido Mana tun yanzu gara ki nutsu ki kwantar da hankalinki daga baya sai a duba Mai yuwuwa
tunda nasan bazaki so Zama da almajiri marar karatun boko mai zurfi, ga karqncin wayewa ga rashin
madafa ta yau da kullum, Nima kasada ce tasa na yarda da tayin da akayi min tunda Naga nema ake a
tozarta min da iyayen a kunyata su a idon duniya aci mutuncin su".
Ita da'i ko motsin kirki ta kasa da gaske gani take duk ya cika dakin, ga wani fitinan kamshinsa duk ya cika
Mata hanci.
A bazato taji ya Dan shafi gefen fuskarta idan ba kunnenta ne suka jiyo Mata ba da'i dai ba sai taji kamar
yace "my previous" a hankali sannan ya Mike Yana fadin "Bari a kawo maganin ki saimu wuce gida tunda
doctor yace zamu iya wucewa, Amman yace ki rage yawan tunani Yana haddasa cututtuka".
Har dakin Amma Abdul Hakeem ya raka Zahra lokacin duk yawancin bakin sun tafi sai 'yan uwan Amma na
Mubi Dana Jimeta sai Kuma Aunty Hasana da take dakon dawowar su, ai tunda magaji ya Kara Kora Mata
bayani akan Mahmud ta tafi daga asibitin tunda Mai dungurungum din yazo ita bataga ta Zama ba.
Saida ta matsawa Zahrar tayi wanka Tasha tea da magungunan ta kwanta sannan tayi haramar wucewa
gida.
Sai wurin karfe Tara sannan Hajiya mama ta shigo dakin tana fadin "wallahi daga idar da sallar ta barci ya
dakeni sai Dana tashi zilai Mai wanke wanke take fad'a min an dawo da Zahra har sun shigo sun duba ta".
"Wallahi kuwa ai jiki da sauki yanzu Tasha magani ta kwanta"
"To Allah ya Kara lfy, Wai Hajiya wanene mijin yarinyar Nan ne naji ana fadar Wai cikin Almajiran baba
Malam ne, shine nace haba yaushe Alhaji zeyi wannan danyen aikin ya rasa bazai bawa aure Sai a cikin
Almajirai".
Inna maimuna ce tace "ai mu Hajiya ko waye Alhaji Jafar ya aurawa Fatima wallahi mun karba da hannu
biyu mun gode tunda mun San har abada Babu cutarwa a tsakanin Asama'u da dashi da ita Fatiman da
abinda ya Haifa bamu taba ganin banbanci ba, Dan haka mun karba da kyakykyawan niyyarsa Allah ta
tabbatar Mana da Alkhairi".
Gaba daya suka amas "Amin"
Hajiya mamar ta Dan jima a dakin kafin ta koma dakinta.
Bayan Zahra tayi sallar Asuba ta gama Azkar dinta komawa tayi ta kwanta har lokacin kanta Yana Mata
ciwo kadan kadan, sai gurin takwas da rabi Inna maimuna ta tasheta tana fad'a Mata tayi maza ta kimtsa
Abbansu Yana nemanta.
A gurguje tayi wankan ta fito lokacin an kawo Mata kunun gyada da fanke, kunun gyadar kawai tadan Sha
kadan ta shafa lotion dinta ta saka doguwar rigar atamfa ko dankwalin Bata daura ba ta fito cikin takunta
na nutsuwa Wanda da yawa mutane ke gani a matsayin yanga da jiji da Kai.
A tsakar gidan suka rinka gaisawa da tsirarun yan uwansu na Mubi da sauran ma'aikatan gidan Mata.
Da sallama a bakinta ta shiga falon Abban nasu, tayi mamakin ganin kusan duk 'ya'yan Abban suna Nan sai
su Ammah da Inna maimuna da kanwar Abban Maman lafia.
Hajiya mama ce ta fasa Kuka tana fadin "Haba Alhaji wannan wane irin danyan hukunci ne? ya zaka dauki
'yar marainyar Allah ka baiwa Wanda ba'asan asalinsa ba, ai duniya saita zage ka Dan Allah ka janye
maganar Nan da wannan ba gara kaba salmaun gidan Hajiya Dago ba tunda ya jima Yana son yarinyar Nan
Amma ka Hana shi"
Kowa a falon kallonta yake ba Wanda ya tofa sai danta Hamza yace "haba mama menene haka kikeyi Dan
Allah kiyi shiru da wannan maganar salmanun me Allah ya sauwake me za'a da wannan zuri'ar".
Hannu Abban ya dagawa Hamza Yana fadin "ya Isa haka tunda ka Bata amsa basai nace komai ba,
Amman ki rubuta ki aje in Sha Allah sai wannan auren ya Zama abin kwatance Kuma abin alfahari duk
Wanda ze zageni ya Dade Bai zageni ba, Kuma duk Mai ganin zalunci ne yasa na aurawa Fatima Mahmud
na barshi da Allah wallahil Azeem ban taba kallon Uwata a matsayin 'yar wani ba kullum Ina Mata kallon
'yata malak malak a makaranta ne kawai ban saka Mata sunana ba shima nayi haka ne Dan tasan nata
mahaifin ta rinka Yi musu addu'a".
Addu'a Abban yasa Imama yayi yaba kowa izinin tafiya Amma yace Ammah ta tsaya ita da Hajiya mamar da
Inna maimuna da Maman lafia.
Aunty Hasana ce ta kamo hannun Zahra zuwa dakin Ammah tana kuka, yarinyar tausayi take Bata kamar
yanda Abban ya fad'a ana walagigi da rayuwar ta.
Cikin bed room din Ammah suka wuce, bayan sun zauna ne Auntyn ta riko hannun Zahrar "kiyi hakuri kinji
Allah Yana sane da halin da kike ciki, Dan Allah kad'a ki watsawa Abba kasa a Ido ki bijirewa auren nan
wallahi irin wanna auren Yana albarka fiye da tunanin".
Wasu sabbin hawayen ta goge. Cikin shashhshekar kuka tace "wallahi Aunty nifa tsironsa nakeji idan muka
hada Ido wani Abu nake gani a idonsa".
Sororo Auntyn tayi kafin tace "ban Gane ba tsoronss kamar Yaya, Daman kinsansa ne runtuni?.
Kai ta gyada Mata alamar Eh.
"Allah ya kyauta" kawai Auntyn tace.
"Ko meme ma dai wannan tsakaninku ne kin gyarota can".
Ta Mike tana fadin "Bari na koma gida sai zuwa an jima zamu shigo da Sajida da Amatu itama Bata tafi ba
jiyan.
********Tun bayan suka dawo daga sallar Asuba Mahmud yake ta faman aiki a cikin laptop dinsa, Yana
kallon Sameer Yana kwasar barcin gajiya. Bai gama aikin ba sai kusan karfe takwas na safe, kai tsaye toilet
ya nufa ya jima a ciki kafin ya fito daure da towel a kugunsa karami Kuma a hannunsa ya goge sumar kansa
me baka sidik Mai laushi Saida ya shirts cikin wani farin yadi filtex marara nauyi ya feda turarensa Alburaq
sannan yaje gefen bedside ya dauki wayarsa ya kunna.
Abinci ya bukata a kawo musu, yana Gama wayar Kira ya shigo sunan Habib ya gani, ya daga da sallama
daga cen Habib Fara fadar.
"Habe Dan Allah dukka tadawa Baba malam hankali baka kwana a gida ba abinda baka Saba ba Koda wasa
duk dare zaka dawo Amma jiya daga Bari kaje ka dawo shi kenan kayi layar zana Kuma ka Kama ka kulle
waya".
Dariya yayi Yana cewa "kana tunanin Kona bi dare nayi Gudun auren dole ko?"
Shima Habib din dariyar yayi.
"Ka Gudun Mana idan ka Isa mai wannan tsaleliyar Ina zaya ya barta koka gudu ka dawo da kafarka, kawai
da malam ne ya matsa yaji kana ina".
"Ok shi kenan Bari na kira shi Dan hankalinsa ya kwanta Ina Nan tare da Oga Sameer shine ya rikeni nayi
Masa wani aiki".
Yana kashe wayar ya nufi sofa ya zauna yana janyo stool din da aka Dora abincin.
"Oh ni Sameer yaushe na rikeka? ka rikeni dai ka Hanani tafiya ka barni da kame kame ga madam can tana
fama da kanta ba mataimaki gaskiya yau in Sha Allah sai kano".
Ya fad'a yana nufar toilet shima.
Can hayin bankin suka Fara zuwa gurin masu aikin gidan Masha Allah aikin yayi nisa kamar ba jiya aka Fara
ba Sam an canzawa gidan fasali kamar bashi ba, duk abinda ake bukata Sameer ya danka shi a hannun
Binya.
Sannan suka nufi cikin gari.
Wani mall suka shiga Mahmud ya jido kayan fruits dasu kayan tea sai chocolates dasu farm fresh yogurt da
fresh milk. Leda uku aka cika manya Saida suka dauki hanya Sameer ya kalli Mahmud yana fadin
"wadannan kayan fa yallabai na waye".
"Dubiya zamu saika Bata tunda ni dai kowa yasan bani da kudin sayansu.
🔷 Page six🔷
________Sun jima a gurin Baba Malam Yana yiwa Sameer godiyar dawainiyar da yasha akan wannan
lamarin, sannan yayiwa Baba Malam din sallama akan zai wuce sai hutu ya Kare zasuzo da mutanen su
suna son su kawo wasu ayyukan da za'ayi.
Har gurin mota Malam dasu Habib sukayi Masa rakiya, Baba malam Yana fadin "Bari muyi addu'a".
Nan yaja doguwar addu'a akan Allah ya tsare hanya, har Sameer ya shiga mota ya fito ya nufi Malam
Wanda har ya Fara tafiya, sai Kuma yaja ya tsaya Yana jiran karasowar Sameer din.
Dan risinawa yayi Yana fadin "ko za'a samu Wanda ze rakani na Kara dubo jikin wannan yarinyar?"
Wani kallon kasan ido Mahmud ya bashi dashi "Wai yarinya".
"To! To! Masha Allah ai sai kuje da Mahmud din da Habibu kuga jikin, ai wannan tunani ne Mai kyau.Nima
na shiga da safe gurin Alhajin naji yata kwana".
Har cikin harabar gidan Sameer ya shiga da motar, Abdul Hakeem Habib ya Kira kafin su shigo ma ya fito
Nan Harabar gidan Yana jiransu.
Shi yayi musu jagora zuwa falon Abban, yayi murna sosai da ganinsu sun gaisa sosai sun masa godiya sosai
da karamcin da yayi musu, yaji dadi sosai Dan har ya ringa tsokanar Sameer Yana fadar "wato tunda kazo
gabatar da aikinku ban sake ganin kafarka ba a gidan Nan sai yau dana baku Mata ko? Dan na lura baka da
aminin daya wuce Mahmud a garin nan. Masha Allah, Malam ya fada min duk Fadi tashin ku akan lamarin
Allah ya saka da Alkhairi yabar zumunci".
Suka Amma da "Amin ya Rabbi".
Mahmud Alhajin ya kalla Yana fadin "kayi hakuri fa Mahmud munyi maka nauyin kuka".
Kai ya gairgiza Yana fadin "ko daya wallahi ba komai nagode, Allah ya saka da Alkhairi ya Kara lafiya Nisan
kwana Mai albarka"
"Allahumma Amin. Allah yayi Albarka, ya baku zaman lafiya ya baku zuru'a Mai Albarka, sai ayi ta hakuri
da lamarin Mata fa. Abdul Hakeem ku shiga ciki su gaisa da Iyayen nasu".
Wannan shine shigar Mahmud na biyu gidan, na farko lokacin da magaji yayi accident da mashin suka
shigo shida Abdul Hakeem da Hamza ya duba shi a dakin Ammah, dan ma lokacin ba kowa a gidan sunje
gaisuwar mutuwa.
Directly dakin Hajiya Mama Abdul ya nufa dasu, Zilai Mai musu wanke wanke ce tayi zuruf ta shiga dakin
Ammah.
Tana fadin "Ammah Ina Jin fa ga mijin Zahara'u Nan sun shiga dakin Mama shida Abdul Hakeem da wasu
inaga abokansa ne".
Ta juya ta fita.
Gyalen Inna maimuna Ammar ta dauka dake kusa da ita ta yafa a jikinta.
Da sallama Abdul Hakeem din ya shigo Yana fadin Bismillah ku shigo Mana, a nan kan carpet a kasa suka
zauna suna gaishe dasu Ammar tare da tambayar Mai jikin.
Abdul Hakeem ne yace " Inna mijin Zahra ne da ubangidansa suka shigo duba ta shi yau ze wuce shine yace
a rako shi ya Kara dubata da jikin nata".
"Kai Masha Allah an gode madallah Allah ya saka da Alkhairi ya maida ka gida lafiya". Inna maimuna ta
fada sannan ta kara da cewa "to waye angon nawa Dan nice ta karfe ita wannan Farafarar ba wani abun
azo a gani zata iya ba ni kuwa ko banza na tuka maka tuwon dawa da man shanu ko ba haka ba?" Ta
tambaye shi tana kallonsu.
Duk dariya sukayi Amma shi gogan Dan murmushi yayi kadan Yana basarwa.
Abdul Hakeem ne ya nuna Mahmud Yana cewa.
"Ga angon naki nan nagama kamar kunyarki yakeji"
"A'a! Masha Allah tubarakallah Mai gidan nawa wanke hannu daka taba ne, kaga dago ka kalleni ni Kaka ce
kada kaji wata kunya ta".
Kara sadda Kai yayi shifa duk jinsa yake wani iri Wai shine a zaune a dakin surukai Ashe da gaske ana jin
kunyar shi wallahi da ji yake kawai fada ake ba wani nauyin da akeji Saida ya same shi yanzu yake gaskata
hakan.
A kaikaice Ammah ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a zuciyar ta, ita bataga wata makusa ba a tare dashi
Kuma idan ba idon tane yake Mata gizo ba sai taga duk cikin Wanda zasu auri Zahrar a baya bataga Mai
nagarat wannan yaron ba.
Albarka da nasiha dai ya Sha ta gurin Inna maimuna.
A haka suka fito daga dakin har suka fito compound din Abdul Hakeem Bai fito ba sai duba agogo Sameer
keyi Yana mita.
"Nifa bana son nayi Rana a tafiyar Nan gaskiya, Naga alamar kuma neman kuke kusa nayi yamma ma".
Kafin Mahmud ya bashi amsa Abdul Hakeem din ya fito da sauri da key a hannunsa Yana fadin "kuyi hakuri
key din ne ba'a gani ba da wuri ku karaso ciki kafin Zahrar ta fito ku gaisa".
Mahmud ne yace "Kai haba da an kyaketa ta huta ita da Bata da lafiyar kirki".
Karamin falo ne da kujeru masu kyau sosai da kayan kallon alama an tana deshi ne saboda Yara Mata na
gidan da Kuma dai dai kun Baki.
Bayan fitar Abdul Hakeem, Sameer ya kalli Mahmud.
"Dan Allah my man yaushe idonka ya koyi kunya? Naga sai wani sadda Kai kake, nifa lamarinka ya Fara bani
tsoro na rasa wace alkibla ka kalla kazo garin mutane ka Mike kafa kana wata irin rayuwa a takure nace zan
dauki mataki ka aje min sharadi, da kasan bazan it's tsallakewa ba, yanzu Kuma Rana tsaka a tarko aure Kai
kadai kamar marar gata sai walagigi kake alhalin kana da madafa".
Tsaki yayi " kana da matsala wallahi ko me zance fada maka bazaka Gane ba, amma idan lokaci yayi zaka
fashinmta,yanzu duk bayanin da zanyi maka ba fashinmta zakayi ba, kawai mu bar maganar kawaai"
Kanshin turaren ne ya alamta musu zuwanta. sallama tayi cikin siririyar muryarta.
Sameer ne ya amsa Mata sallamar a zahiri Dan shi Dan gogan a saman lebensa ta amsa sallamar. Sameer
din ne ya Dan Mike Yana fadar.
"Masha Allah jiki yayi sauki kam, "Bismillah". Yana nuna Mata kujerar gefen Mahmud. Kai ta dangirgiza
Masa tana dan murmushi kasa kasa.
A Nan kan carpet ta zauna daga gefe tana gaishe da su a jimlace.
"Lafiya kalau"
Sameer ya amsa Yana fadin "ya jikin naki?"
"Alhamdulillahi" ta amsa masa.
Sai Kuma duk sukayi shiru, ganin lokaci Yana qurewa Sameer ya Mike tare da kallon Zahra Yana fadin " To
madam bako zeyi halinsa Allah ya bada zaman lafiya. Amma fa sai kina hakuri da halinsa gaskiya ba kirki ya
cika ba Ina son idan na dawo Naga canji na zahiri a tare dashi, sunan Sameer Sa'ad koko, zeyi miki
cikakken bayanin koni waye a gurinsa Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a mai..albarka Allah yasa next year
by now muna bkin suna"
Da sauri Mahmud ya kalli Sameer a zuciyarsa Yana fadin "Allah ya shiryeka Sam baka girma".
A hankali tace " Mun gode kwarai Allah ya tsare ya kiyaye hanya".
"Amin" ya amsa Yana kallon Mahmud.
"Ni zan wuce saina sake shigowa ayi kokarin ganin aikin Nan ya kammalu".
Ya fada Yana nufar kofar fita.
Sai lokacin Mahmud din yayi magana "pls ka jirani minti biyar Dan Allah".
Tunda Sameer din ya fita take wasa da karamin zoben da yake hannunta. Bata dagon kalle shi ba shi Kuma
Bai tofa tasa ba amman idonsa Yana kanta, Kare Mata kallo yake Yana fadar "Masha Allah tabarakakkahu
ahasanil kaliqin".
Tsam ya taso daga inda yake ya sauko kasa inda take zaune.
"Ya jikin naki?".
Ta tsinkayi maganarsa kusa da ita daf Sam bataga lokacin daya taso ba.
Cikin daburcewa saboda kusancin nasu yayi matukar yawa ji tayi kamar ma iskar gurin ta tsaya sai
munfashinsa take shaqa kawai.
A mamakance taga yasa hannunsa ya dago fuskarta suka hada Ido hudu dashi. Da sauri ta runtse
idanunta zuciyarta na wata irin bugawa.
"Bude idon Kona Baki mamaki".
Marmar ta Fara da idon tana budewa a hankali Amma taki kallon nasa idon.
"Ya jikin?".
Ya Kara maiamaitawa, a hankali ta bude bakinta tace "da sauki"
Gamshin Lister mint ne ya daki fuskarsa. Banda Yana daf da ita ba yanda za'ayi yaji abinda ta fada.
"Allah ya Kara lafiya".
"Ameen"
Ta fada.
Hannunsa ya cire daga fuskarta yana Dan furzar da iska daga bikinsa ya Mike tsaye, a hankali ta sauke wani
numfashi.
A bazata taji yace "bani wayarki"
Ba musu ta Mika masa, aljihu taga ya saka Yana fadin "ki shiga gida ki kwanta kiyi barci sosai kada ki
yawaita hayaniya ki samu hutu sosai, zan tambayi magaji idan bakya hutawa yanda ya kamata ni Ina da
inda zan kaiki ki samu isolation, tashi muje ki shiga gida ana jirana".
Saida ta shige ciki kafin ya juya ya nufi gurin da Sameer da Abdul Hakeem suke suna Hira.
Lokacin data shiga dakin ta Samu Aunty Hasana dasu sajida sunzo har da yaran duka.
Da guda ta karasa cikin suka rungume juna da Sajida Nan da Nan sai hawaye itama sajidar kukan ta fara.
Ammah ce tace "Naga abinda ya isheni meye haka zaku tasa mutane a gaba Kuna kuka, to kukan maganin
me ze muku aikin Gama ai ya Riga ya Gama Saida hakuri da addu'a kawai".
Uwar dakin Ammah suka shige.
Magaji ne yayi sallama ya shigo da manyan ledoji guda biyu niqi-niqi da kaya Auntyn Hasan na
tambayar"daga Ina?"
Ya fice da sauran Yana fadin "ina zuwa Aunty"
Wata ledar ya shigo da ita Yana fadar"kayan dubiya ne aka kawo Mata" ledar daya kawo daga karshen ya
bude rafar 'yan dari bibiyu hura biyu ya dauko daga saman kayan, Aunty Hasana ya
Mikawa yana fadar "gashi nan inji abokin mijinta Wanda suka shigo dashi dazu".
Godiya su Inna maimuna sukayi tayi kamar Yana nan a gurin suna ta Saka albarka.
********* Bayan tafiyar Sameer can gurin aikin gidan suka wuce, ba karamin mamaki Habib yayi ba har ya
kasa hakuri ya tambayi Bilyaminu lokacin Mahmud Yana ciki. "Dan Allah wane irin kudi gayen Nan ya bada
haka Nan da Nan gidan ya juye ya Zama kamar daukowa akayi daga wata kasar".
"Wallahi Nima bazance ga abinda ake kashewa ba, iya kudin aiki Dana abinci kawai suke a hannuna, bakaga
wash bakin fuska ba su biyu?'
"Eh nagansu"
Habib ya fada. "To ai tun jiya sukazo da komai na aikin bakaga Nata'ala ba shima lebura ya koma kaga ai da
malam shi yasa a Kira saboda 'yan gyare gyaren amman da masu iyawar sukazo shima yaronsu ya koma".
Ya fada Yana dariya.
"Wallahi Bilya sai a kyaleka Kai kowama sai ka tab'a".
"Gaskiyar kenan ni wallahi burgeni ma yayi tunda baiyi zuciya ba ya tafi, ko banza nasan Yana lure da koma
Dan gyaran nasa aikin".
*****A bedroom din ammah Zahra ce da Sajida suke tattaunawa akan abinda ya faru,sunyi iya nasu
hasashen amma sun kasa gano bakin zare Sajida ce tace "nifa Zahra Ina hasashen wani Abu akan lamarin
ki"
"Kamar me kenan?"
Dan Jim tayi kafin tace "Anya ba asiri ake yiwa duk wani Wanda yazo da niyyar aurenki ba? Ki tsaya kiyi
nazarin abun Mana ko mafarkan da kike yi duk lokacin da maganar aurenki ta taso abin dubawa ne"
Dan murmushi Zahrar tayi "kin jiki kema bestie wane irin asiri Kuma,ana zaune lafiya to waye har ze bata
lokacinsa da kudinsa gurin yi min wani Abu kawai daga Allah ne kinsan kowa da yanda Allah make
jarabtarsa ni tawace tazo a haka".
"Eh na yarda daga Allah ne bana inkari Amma akwai sanadi, inaga gobe ma zan wuce duk da nacewa
Umma sai Wednesday Amma na fasa wallahi Rimi zanje gurin Baban Umma na fada Masa ai kinsan shi
farin sani Kuma zeyi duk abinda ya kamata tunda ke wani lokacin kanki ba Maths".
Kwarkwar tayi da ido Dan Allah Saji kada ki tafi ki Bari a Gama komai saiki tafin".
Wani kallo tayiwa Zahra "tafiya dole na tafi Amma zan dawo kwana kusa in Sha Allah, kinsan Zama da
Baffa yasa Ina Gane wasu abubuwan tunda Yana fadw min ire -iren abubuwan da suka shafi sihiri Kinga
yace min duk wani ciwon da yake da lokaci misali ace kullun sai dare mutun yake kasa barci kinsan da
matsala, ko ace mace duk ranar girkinta Bata da lafiya ko duk ranar girkinta tana zubar da jini amma idan
ta Gama aikin shike nan sai ya dauke babu, ko kamar taki matsalar sai an saka Miki ranar aure sai ana gaf
da biki abun yake lalacewa, Kika sani ko Abban naku ma ya Fara irin wannan tunanin ne yasa ya yanke
wanna hukuncin cikin sirri ki tsaya kiyi tunani Mana"
Sosai magungunan Sajida sun sakata a tunanin da Bata tabayi ba.
Sauke zazzafan numfashi tayi tana fadin "Allah ya kyauta ni duk kin sakani a tunani wallahi"
Haba "Bestie ai kinsan ruwa baya tsami a banza me ake nema a gurin mace Allah Bai Baki ba Amma sai an
Yi abu kama-kama ya lalace zance da muka Dade munayj da Aunty Hasana kenan jiya Kuma ta bain go
ahead na naje na faduwa Baffan rimin, tace ma zata fadawa Ammah, ma".
Kiran da Aunty Hasana tayi wa Sajida ne ya katse musu tattaunawar, ta tashi ta fita.
Washe gari duk bakin Ammah suka tafi, Inna maimuna kadai suka Bari sai Amarya taje dakinta zata koma
gida.
Part din da bakin suka zauna Ammah tasa su Zilai suka gyara sosai tunda Daman nasu Zahra ne, kafin
yamma gurin yayi tas kamar ba'ayi wata dabdala a cikinsa ba.
Bayan sallar insha'i zahra da Sajida suka koma part din.
Suna zaune a kan gado Autan Ammah musaddiq ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da leda fara Mai
kyau ya mikowa Zahra yana fadin "gashi Aunty inji wannan na gidan Baba Malam din yace a kawo Miki
Kuma yana duba ki, Kinga Nima ya bani".
Ya Mika nata 1 k din dake hannunsa.".
"To angode madallah".
Ledar Sajida ta dauka ta bude waya ta gani sabuwa kar a ciki.
"Wow gaskiya ba karya ke! Irin wannan babbar harka haka, Dan Allah Yi min bayani naji yace wannan na
gidan Baba malam din waye ko angon namu ne da ake Raina mana ya Fara tsula Mana abun arziki haka?".
Baki ta Zahra ta zunbura.
"Nace Masa Ina bukatar sabuwar waya ne da zai kawo min, ni wallahi a mayar Masa".
Ta fada tana kokarin amsar ledar faga hannun sajidar.
"Ke tsaya da Allah yi min bayani yanda zan gane, Ina taking wayar naji kina wata magana".
"Tana gurinsa tun safe ya karba ni bansan abinda zeyi da ita ba, ya dai ce na bashi kawai ni kuma na bashin
shine Kuma maimakon ya bani tawa shine ya Aiko min da wannan".
Musaddiq Sajida ta kalla 'kai auta maza kaje kace tace ta gode Allah ya Kara nudi"
Sai da ya fita sannna ta juyo gurin Zahra. "Amman wallahi kin bani mamaki Allah ya tarfawa garinki nono ki
nemi ki Bata rawarki da tsalle to kici gaba har ki nuna b'araka a gaban 'yan uba, Koda wasa kara ki Kara
ba'a yiwa miji haka ko bakaso Abu baka nunawa a gabansa, kika san da Yaya yayi sawo Miki danya faranta
Miki Rai Amma Zaki wani kwasale shi kice a mayar Masa kina son tun yanzu ki kashe Masa Gwiwa ko".
❤️AUREN HUCE HAUSHI❤️
JINJINA TA MUSAMMAN GA MALAMAN MAKARANTA ALLAH YAYI JAGORA YA QARA BASIRA DA JURIYAR
SAUKEN NAUYIN DA AKA DORA MUKU NA AMANAR YARA QANANA✍️
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
This page is deducted to you Families of late Alhaji Isah Musa Bakin kasuwa kazaure jigawa state.
🔷PAGE SEVEN🔷
_______Mika tayi tana salatin ma'aiki s a.w.w sannan ta Zoro kafafunta kasa, tunda ta farka tasan tabbas
karfe biyu tayi na sulsulin dare har ya zamar Mata jiki. Dubanta ta kai inda Sajida ke kwance barcinta take
sadidan cikin kwanciya hankali, sai taji Ina ma ita ce haka, wasu hawayen ne suka ciko idanunta a hankali
tace "Ya Rabbi ga baiwarka Mai rauna ka jibinci lamarina dan Isar Manzon Allah s a.w.w. kada ka barni da
iyawata ka iya min da iyawarka kada ka Bari makiya su yi min dariya ka bani rinjaye ka dorani akan duk
Wanda yake son Hawa kaina".
Ta Mike tsam ta nufi toilet din cikin dakin sai Kuma ta fito saboda shaf ta manta kafin su kwanta taga
famfon ya dauke Kuma da alama ba'a kunna layinsu na tanki ba. Cikin rashin tsoro ta bude kofar ta fita
zuwa bayan part din Mama don ta kunno ruwan, gurin ta dosa gadan gadan sai Kuma tayi turus, magana
take jiyowa daga wurin da sauri ta koma baya dan bata San abinda zata gani ba. Tana tsuma ita fa duk da
Bata da tsoro amma tana tsoron ganin abinda yafi karfin idonta ko Kuma wani mugun abun.
Dole tayi hakurin yin sallar a koma ta kwanta tana ta sake-sake har kusan Asuba, ba Kuma taji motsin wani
na tada hankali ba.
Saida Sajida ta tashe ta lokacin har an Fara sallah a masallacin gidan nasu.
A gurguje tayo alwala da alama Sajida ce ta shigo da ruwan.
Bayan sunyi sallah zaman Azkar sukayi har lokacin da gari yayi shahhh alamar wayewa, sannan suka koma
suka kwanta. Dukkan su ba barci suke ba, Zahra ce ta danyi tsaki kadan ta tashi zaune.
Kallonta Sajida tayi.
"Yaya Bestie akwai damuwa ne?"
Dan juyowa zahrar tayi tana kallon sajidar tana Kara wani tsakin "nifa wallahi na fada Miki tsoron mutumin
nan nakeji tun ranar Dana Fara ganinsa a gidan Baba malam nake Jin wata irin shakkarsa. Dan Allah a haka
zamu rayu bana ko son kallon idanunsa? Kinsan wani tarin abin haushin jiya fa hannu yasa ya dago fuskata
Wai dole saina bude idona na kalle shi ko Kuma ya bani mamaki, Kuma fa ranar Nan a asibiti har wani
shafar min fuska yayi Yana fadar nayi hakuri da wannan hadin shima ba so yake ba, kawai yayi biyaya ne
tunda baze iya yiwa su Abba musu ba, amma ni Ina iya fada musu bana so".
Baki Sajida ta rufe tana kunshe dariyar ta. Kai ta shiga girgizawa tana fadar Babbar magana ki fadawa su
Abba bakyaso! Wato ke ga marar ta ido ko? Shima har yasan kimarsu da baze iya yin musu dasu ba saike
ce marar kunya Zaki Fadi Baki so, ki rabu dashi kwaai abinda nake so dake yanzu ki koyi dakewa a gaban
nasa sannan ki daina tsoron idanun nasa, Wai tsaya fada min menene a cikin idon nasa da yake firgitaki
duk girmanki da wayonki da wayewar ki?"
Wani shagwabe fuska tayi kamar Mai Shirin fasa kuka.
"Bazaki gabe ba, ni kaina bansan ya zanyi ba saboda shi fa na daina zuwa gidan Baba malam tunda lokacin
kullum Yana tare da shi kuma sai yayi ta kallona yana tsareni da wadannan idunuwan nasa kamar Mai jin
barci".
Yanzu dariya sosai Sajida keyi harda kwalla tana fadar Babbar magana tab kice abin asali ya Samo shi ai
kaya ne suka tsinke Masa a gidin kaba kece dai kike bulayi"
"Kamar yaya?"
"A'a bazakiji mutuwar sarki a bakina ba ai tunda an hada anyi Mai walahar...".
Sautin kiran waya ya dakatar da shegantakar da sajidar ke mata.
Wayar da aka kawo Mata jiya ce ta dauki kida, Sajida ce ta Mika hannu ta dauka M.M DANGE ta gani Yana
yawo akan screen din.
Zahra ta mikawa tana fadar oga ne da alama a Sha soyayya lfy. Tayi waje tana fadin Bari naje nayiwa
Ammah shara.
Bata daga Kiran ba har Saida ya kusa katsewa kana ta daga tasa a kunnenta. Daga can taji Yana fadar
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
A zuciyar ta a amsa Dan da gaske in dai zata ganshi ko taji maganarsa kasa samun nutsuwa take.
Sake maimaita sallamar yayi, da kyar ta amsa masa tare da fadar " Ina kwana?"
Shiru taji ba'a amsa ba kamar ma an sauka daga layin, amma ga mamakinta tana dubawa sai taga Yana
nan, itama shirun tayi kudin sunata tafiya saita saka handsfree ta aje wayar kusa da daga gefe tana kallon
ikon Allah.
Saida ya mula Dan kansa "yace ya jikin naki I hope kin shan maganinki?"
"Eh" ta fada a takaice.
"Fine"yace shima a takaicen.
Ita mamaki ma yake Bata har wani turanci yake jefawa a magana kamar gaske.
"Sai an jima ta fada tana kokarin katse Kiran.
"Kada ki kuskurs ki kashe min Kira" ya fada in serious tongue.
Shiru tayi tana mamakinsa sai wata izza yake Mata kamar wani abin azo a gani.
Muryarshi ta tsinkaya Yana fadin ki bude data na turo Miki sako idan da abinda kike bukatar ayi ko a Kara
sai ki fada min, take care".
Kit ya kashe kiran.
"Kutt!" Ta fada "amman gayen nan yama Raina ni wlh Wai kada na kashe Masa waya"
Kwafa tayi "zakaga na kiraka ganin idon ka" ta Jafar da wayar tana mita.
Taso yin barci Amma ta kasa dole ta hakura, wayar ta Kara daukowa tana kare Mata kallo.
Number din Hameeda ta Fara sakawa tunda taga sabon layi ne ya dauke natan, ga mamakinta sai taga
sunan Hameedar ya bayyana ba bata lokaci ta kira.
Tana ta ringing kamar baza'a dauka ba sai Kuma ta daga da sallama ai tana jin muryar Zahra ta Fara mita
"yanzu Dan Allah kin kyauta tun jiya nake neman layinki Amma shiru na Kira Mama nace ta Baki tace min
bakya Jin Dadi kina barci, wallahi Kinga yanda hankalina ya tashi kuwa ki Bari lokacin da Sajida ta fada min
halin da ake ciki wallahi daba final muke ba Allah da barinta zanyi c/o na taho gida har fada mukayi da
Salma Wai ai sai inje na baiwa Mushahun hakuri ya dawo ya aure maganganu dai gasu nan ki Bari kawai ai
jibi zamu Gama in Sha Allah komai dare a gida zan kwana".
"Allah ya yarda ki Bari kawai wallahi Ina cikin yanayi akwai damuwa Dan Allah kizo ko naji sauki
abubuwan".
Ta fada tana share hawaye, sukayi sallma Dan it ma Hameedar kukan take.
Wai ita Mushahu ya yiwa haka, duk wadanda suka fasa aurenta Bata taba Jin Wanda ya Bata Mata Rai ya
Kuma tsaya Mata kamar wannan ba ai ko wace irin matsala ce ita ya kamata ya Fara fadawa ba ya yanke
mu'amala da ita ba a lokacin da take matukar bukatarsa ya manta shakuwar dake tsakanin su da
alkawarirrikan da suka yiwa juna.
Kwantawa tayi tana tunanin baya a haka wani wahalallan barci yayi gaba da ita.
**********Tun Yana tsammanin ganin ta bude data ta duba sakon har ya cire Rai da hakan.
Lambar Abdul Hakeem ya Kira sun jima suna waya kafin suyi sallama.
Laptop dinsa ya janyo yaci gaba da aiyukansa sai kusan azzahar ya Gama. toilet din cikin dakin ya shiga ya
dauro alwala,a masallacin hotel din Yaya sallah lokacin daya fito Kiran Habib ya shigo Masa "Wai Dan Allah
kana Ina ne tun dazu muke nemanka kazo masu aikin hada furniture's din Nan ne suka Gama da cabinet
din kitchen".
"Ok gani Nan inaga kada kayi nisa zuwa an jima su Aunty zasuzo suga gurin"
Ya fada.
Yana nufar gurin da ya saba aje lifan din Habib.
Wayar Ammah Abdul Hakeem ya Kira ya fada Mata Mahmud yace a turo a gano gidan an Gama gyaran,
dakin Mama Ammah ta shiga ta fada Mata sannan Kira Aunty Hasana ta fada Mata kafin ta wuce gurin
Alhajin ta fada Masa tunda shiya dawo daga gidan gonar sai su Abdul Hakeem ya baro suna yiwa shanu
Allura da Basu magunguna.
Wurin karfe biyar Aunty Hasana ta debesu a mota harda Sajida suka nufi Hayin bankin cikin jagorancin
Habib, lokacin Inna Bata Nan taje MIYA gurin wata aminiyar ta da sukayi aikin Haji shekara daya.
Duk cikinsu ba wadda Bata kadu da ganin gidan ba domin ba karaya an narka mahaukatan kudi a gidan
bazaka tab'a cewa renovation akayi Masa ba, bedroom's ne guda uku biyu suna kallon juna dayan Kuma
daga gefe da alama yafi sauran girma Kuma shi kadai ne a rufe, sun zagaya ko Ina sai santin gidan Sajida
tace tana ta daukar video, falon kadai abin kallo ne duk da ba komai a cikinsa sai fitilu da aka kunna sai
Kuma AC da aka ware.
Hajiya mama ce ta kasa hakuri ta leka ta Kira Habib Nan falon ya shigo Yana fadin "gani Mama"
Yana Dan rankwafawa.
Aunty Hasana mama ta kalla "Hasana Dan Allah ki tayani tambayar yaron Nan tunda shi namu ne na gida
baze cucemu ba, Wai wannan yaron sana'ar me yake daya iya Kama hayar wannan uban gidan"?"
Kara risinawa yayi Yana fadar "ba haya ya Kama ba Baba malam ne ya bashi kyauta, sai Kuma kungiyar yake
yiwa aiki suka kawo masu aiki suka yiwa gidan 'yan gyare -gyare harda kayan daki ma suka zuba masa,
Bismillah Bari na bude muku ku gani yanzu ba dadewa zuka Gama hadawa da kitchen din suka tafi".
Dakin ya bude musu ba Hajiya mama da take ta kwana biyu ba, ko Aunty Hasana da Sajida Saida suka
Zama 'yan kauye Dan tunda suke Basu taba ganin irin wanna gadon a zahiri ba, ita kanta aunty Hasana
lamarin Yana neman ya gagari tunaninta fa ance Almajirin Baba malam to Amma idan aka saka mizanin
hankali abin yafi karfin yanda aka fada to wane irin NGO's ne da suke irin wannan aikin akan daidaikun
ma'aikatan su haka?" Gaskiya abin akwai abin dubawa.
Lokacin da suka fito harabar gidan ne wata Hilux ta shigo da kaya a bayan motar mutane uku ne a motar
bakar fata biyu fari daya Kamar balarabe Kamar kwara.
Kameme Hajiya mama ta hanasu tafiya sai da aka sauke kayan ta gani abinda da suka Gane irin katuwar
plasima din Nan Mai cin Rabin bangon Nan ne kawai amman sauran tarkacen Basu Gane komai ba, haka
suka kada suka tafi mama nata mitar "A'a da sake Alhaji ya titsiya yaron Nan saiya nuna Iyayen shi kafin a
Kai Masa yarinyar Nan haka kawai aje ayi kitso da kwarkawata mutanen yanzu ba abin yarda bane sai kaga
mutum har mutum Amman a Baki malam a ciki Kuma Fir'auna".
Maganar data Basu Aunty dariya kenan.
❤️
❤️
❤️
AUREN HUCE HAUSHI
❤️
❤️
❤️
STORY
AND
. WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE EIGHT
Lokacin da suka shigo gidan ana ta kokarin daura alwalar sallar magariba.
Sai bayan sallar insha'i ne Mama ta shigo dakin Ammah suka hadu da Aunty Hasana suna fadawa
Ammah yanda suka gano gidan da Kuma yanda abin ya daure musu kai.
Nisawa Ammar tayi tana fadar "Mama ki Sami Abban kiyi Masa bayani yanda ze fahimta kinsan yanda
suke da malam bana tunanin wannan abun ze saka ya canza ra'ayinsa duba da yanda ya yanke hukuncinsa
Bai nemi shawarar kowa ba".
"Aiko dai ya kamata ayi wani Abu gaskiya Nima lamarin ya tsaya mini a cikin zuciya".
Aunty Hasana ta fada.
Sun jima suna tattaunawar kafin Mama ta koma daki tabar Autty Hasanar da Ammah.
Zama Aunty Hasanar ta kyara ta fuskanci Ammar ta Kira sunanta "Anya wannan Mahmud din ba abinda
yake boyewa kuwa Ammah Kinga gidan kuwa ga wannan uwar wayar daya canza Mata kinsan kudinta
kuwa ? gaskiya I doubt much, ni dai kiyiwa Abban magana da kanki Kamar zefi daukar abun serious akan
na Mama".
Can Kuma sajida ce tasa Zahra a gaba tana ta faman zuba.
"Innalillahi! Kinga gidanki kuwa? Allah ya bamu ya taku wallahi Zahra ki godewa Allah. Wallahi Allah ya
Gama miki duk wata ni'ima ta ko Ina kinyi gaban da Nan kurkusa dai kafin a fiki za'a Dade ana lalube. Zahra
Naga mijinki har mun gaisa ada Ina adawa da auren Amma tunda na ganshi Naga Yana yinsa nasan yanzu
ne kikayi aure da mijin daya Dace ke.Kawai dai matsalar za'ace ba Mai kudi bane,amma a yanda gidan da
zaya ajeki yake wallahi ko minister ne sai hakan, akwai abinda na gani a gidanki wallahi ban taba gani a
gidanki kowa ba duk yawona sai dai a film amma dai a zahiri A'a ban taba gani ba Allah Bai kaini gurin ba".
Tunda ta Fara zuba Zahrar ke bin sajida da idon lokaci daya duk ta wani rude sai zuba take Kamar 'ya 'yan
kanya.
"Kin Gama?"
zahrar ta tambayi sajidar.
"Eh na Gama aini an ma yanka ta tashi na fasa tafiyar zanyi waya da Mom taje can Rimin sumailar gurin
Baffan kawai, tunda Daman zatazo nan din ba suna kwantagora".
"Ke Kika sani dai tunda Naga kina nema ki Zama wata daban ko dai an canza min ke da wata ne ko Kuma
wani abun ya fada Miki ya goge Miki hadda ne?".
"Eh da alama Kam Dan ya fiki iya lafazi gaskiya inaga na Zama 'yar team dinsa fa tunda Naga ke Baki da
wayo".
Washe gari tun safe Abba yasa aka Kai furniture's din Zahra gidan Daman Aunty Hasana sunyi magana da
Wanda zasu hada musu kayan, kayan kitchen da sauran kayayyakin duk suna gidan Aunty Hasana daga can
aka ringa daukowa, masu aikin su suka hada komai na gidan hatta kitchen su suka gyara komai, gidan ba
karamin kyau yayi ba, ba karya duk Wanda yaga gidan yasan na 'yar gata ne.Dan wasu irin mahaukatan
Turkish furniture's ne wanda kakanninta ta gurin uwa sukayi Mata duk wani abun more rayuwa akwai shi a
gidan Nan, bangaren electronics ma sai a cikin lockers aka zuba wasu, komai yayi.
Lokacin da aka Gama gyaran Aunty Hasana da sajida ne sukazo gani ba karamin burgesu gidan yayi ba Dan
sai yanzu ne ya fito a asalinsa na kyau da kayatar da Mai gani, komai na gidan unique ne Masha Allah.
A waya sajida ta daukowa Ammah komai. Ita kanta Ammah Kai Kawai take jinjinawa Dan ba karamin
burgeta abin yayi ba, sai dai can kasan ranta rudani ne kala-kala domin abin ne duk yazo a hagunce.
Tana tsoron lamarin sosai sai da har abada baza iya jayayya da Alhajin ba Dan da gaske ubane tsayayye
Wanda baya nuna banbanci tsakanin abinda ya Haifa da Wanda yake bashi ya Haifa ba, amma harga Allah
tana zulumin wannan AUREN HUCE HAUSHIN da Alhajin yayiwa 'yar marainiyar Allah, mazan yanzu sunce
suna sonka ma ya kukan kare idan Zama yayi Zama ballantana matar cushe ta San komai Daren dadewa
ranar da yaga irin matar da yake so Sai dai zahra tayi hakurin zama Kawai, duk da tasan Bata da haufi akan
yarinyar Tata Dan macece har mace abin alfaharin kowa ne namiji ace ya mallaki Kamar ta, to Amma shi
lamarin so daban yake duk kyan mutum da asalinsa ba lallai ne ace yana burge kowa ba domin shi dai so
makaho ne.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali duk jikinta yayi Mata wani irin Sanya ta kalli Aunty Hasana tace "Hasana
Ina jin wani irin rauni a zuciya ta game da lamarin nan Ina tausayin yarinyar nan rayuwa tana ta walagigi da
ita sai nake ganin Kamar laifi nane Dana kafe a barmin yarinyar Nan na hana kakanninta ita ni Kuma nayi
sakacin da aka maida rayuwar ta Kamar kwallo ana ta dokata daga Nan zuwa nan".
Ta karasa maganar hawaye na zubo mata.
Abinda tunda Allah ya kawo Aunty Hasana duniya Bata taba gani ba a zahiri gurin Ammah Nan da Nan
hankalinta ya tashi sajida ma kukan ta Fara duk da batasas takamaimai man abinda ya saka Ammah kukan
ba, tashi tayi ta fice daga dakin jin an Fara Kiran sallar magariba.
Aunty Hasana ce tace "Haba Ammah duk yanda Kika jure bakin cikin baya na abubuwan da suka faru Baki
taba zubar da hawaye ba sai yanzu da Allah ya nufa akayi ai godiya Zaki yiwa Allah daya kawo karshen
wahalar ba kuka ba".
Gefen zani tasa tana goge hawayen.
"Hasana Ina hango abinda ke bakya hangowa ne,masu iya magana suna cewa matar shige Bata daraja ba
irin wannan rayuwar na sowa Zahra ba to sai dai kana naka Allah Yana nasa Kuma nasan ne gaskiya. Ba
komai haka Allah ya tsara komai mukaddari ne daga gare shi, naji Alhaji Yana maganar zuwa juma'a za'a
kaita".
*******Tun bayan kammala karatunsu na bayan insha'i da suke na littafin iziyya yake zaune a kusa da
Baba malam har kowa ya watse ya rage saura su biyu tunda malam yaga haka yasan da magana a bakin
Mahmud ne.
"Ya ya akayi ne Mahmuda?"
Malam ya jefo Masa tambayar, Kara dukar da Kai yayi kafin yace "Daman maganar kayan lefe ne dazu Oga
Sameer ya kirani yace ya hado tasa gudunmawar kenan, shine nace Bari na fada maka Dan kasan da
zuwansu".
"Ikon Allah shi wannan yaron baya gajiya ne Kamar baisan ciwon nema ba tunda yazo ya riski maganar Nan
yake Yi kan jiki kan karfi. Allah ya saka Masa da Alkhairi yabar muku zumunci".
"Ameen" ya amsa.
Harya Mike ze tafi sai malam din ya dakatar dashi, dawowa yayi zauna.
Gyaran murya malam din yafa kafin ta jefo Masa tambayar.
"Sai zuwa yaushe ne kake ganin zamuje ga mahaifan naka kaga dole muje musu tunda wannan lamarin ya
faru".
Kai ya sadda kasa Yana fadin "zamuje in Sha Allah Amma Dan Allah a Kara min lokaci da kaina zanyi
maganar ayi hakuri".
"To ba laifi Allah ya iya Mana kaje ka Samu su Habibu kuje acan gidan ku kwana kaga sun zuba dukiyar
kasan yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba".
"To in Sha Allah za'ayi hakan amma ni Ina Nan sai dai su Habib din suje".
"To ai hakan ma yayi Allah yayi Albarka".
Saida ya dudduba dakunan yaran ya tabbatar da komai lafiya lokacin sha biyu ta wuce, dakinsu ya nufa
wanka yayi ya saka kayan barci sannan ya hau gado ya bude laptop dinsa. Email dinsa ya shiga Yana duba
sakknnin daya samu sakon daya shigo ne ya dauki hankalinsa.
"Ya Salam!".
Abinda ya iya ambata kenan sai Kuma sautin daddad'an ringtone dinsa ya karade dakin.
"Sameer!" Ya fada a hankali yasan za'ayi haka, ya haga wayar Yana fadin "Ta Yaya hakan ya faru?"
Daga can bangaren Sameer din yadan furzar huci Mai zafi Yana fadar "wallahi nayi duk yanda zanyi Amma
abun yaki yuwuwa dole ka daura ka kawar da komai muje gaskiya Dan kasan tunda akaje Nan zuwan nake
ne Kawai mafita".
"Amman ai kasan halin da ake ciki so kake ace na gudu nabar 'yar mutane Eyeh?".
"Cool down Mana my man abin Bai Kai nan ba aikin daine ya taso na gaggawa Kuma dole sai da Kai za'ayi
Dan haka suyi hakuri su aje maka ita zuwa sanda ka dawo ko Kuma ka dauko abarka ku tafi, kaga ai tafiyar
tafi yi maka armashi ko?"
Ya fada cikin zolaya.
"Dan Allah ka Zama serious mana, kayi duk abinda ya kamata a Nan goben ka hakura da zuwan ka turo
wannan friend din naka tunda yasan gurin ya kawo kayan kawai, Kai Kuma ka Kira Baba malam ka fada
Masa daga can sun nemi ganin wakilansu na kasa da jahoshi da kananan hukumomi nasan dai kome ake
ciki baze wuce kwana buying zuwa uku ba kaga lokacin na tare a gidana nafi son na barta a Nan gidana
akan na tafi Bata tare ba".
"Ko dai.......?"
Sameer ya fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka ko dai me? kasan ni salihn ne ba ruwana da wannan sabgar sai ku".
Kit ya kashe wayar sannan yayi switch off dinta.
Misalin karfe Sha biyun Rana wata tamfatsetsiyar mota Parker a kofar gidan malam.
Akwatuna Yara suka dunga saukewa suna shiga falon malam saida suka Gama sannan baki nufi falon
malam din bisa jagorancin Habib sun gaisa sosai da malam suka gabatar Masa da kayan daga Sameer.
Malam yayi godiya ya saka Albarka ba adadi.
Falon malam ya bar musu sukaci abinci suka huta sannan Habib ya rakasu can gidan suka gaisa da
Mahmud din.
Sai bayan Azahar suka tafi malam yayi musu Sha Tara ta arziki.
Kayan malam yace suje su duba su gani saboda da an jima za'a Mika musu can gidan Alhajin.
Kaya ne na gani na fada an zubasu Kamar ba gobe, an shigarwa da iya Abu ciki ta gani malam yace ta
turawa makotanta na kusa suzo su gani anjima za'a Mika musu.
Bayan fitowa daga sallar la'asar ne Malam Bukar ya fadawa Alhaji yanzu su malam Mudi da Alaramma
malam Haruna zasu kawo kayan Zahara'u.
Fada Alhajin yayi akan kayan da za'a kawo Yana fadar "Haba malam Dan me za'ayi min haka ko wancen da
aka fasa auren Kai sheda ne ban karbi lefe ba da suka matsa cewa nayi suje da kayan idan tazo saiya ba
matarsa".
Kai malam yanjinjina Yana fadin "Anyi hakan Kam amma wannan shima bamu muka hada ba wannan yaron
Sameeru ne ya turo dasu dazu yace gudunmawarsa ce aba Amarya"
"Ikon Allah shi baya gajiya da dawainya haka daga wannan sai wance Allah ya saka da Alkhairi ya
bar.zumunci na jima banga yaro mai karqmcinsa ba abin duniya Bai rufe Masa ido ba".
Da yamma su sajida suna zaune suna Shira ita da Zahra da wata kawar Zahra Mujiba Nan take makotansu
suna dasawa da Zahra sosai sun Kuma yi sabo sosai da Sajida tun lokacin da sake zuwa hutu da Sajidar
lokacin suna makaranta.
Ba zato ba tsammani Yara suka shigo da manyan jakunkuna dasu cylinder din gas, ai Zahra na ganin haka ta
tashi da sauri ta nufi hanyar shigowa gidan da gudu ta karasa Kamar karamar yarinya suka rungume juna
da Hameeda Kamar zasu fadi. Suna rike da hannun suka shigo ciki su Mujiba suna ta faman yi Mata sannu
da zuwa, sai daga baya Salma ta shigo tana wani shankanshi Bata kula su Zahra ba Suma ba Wanda ya kula
ta, directly dakin Mama ta nufa.
Kamar jira ake Salma ta wuce saiga su Magaji da manyan Akwatunan lefe suna shigowa da sauri Zilai Mai
aiki ta warto Babbar tabarma ta baza tana rabsa guda tana fadin "Masha Allah! Alherin Allah ya sauka. Fara
Mai farar aniya sukari bakai farin banza Fatima Zahara'u 'yar Muhammadu sani, jikar hardon fulanin Mubi,
Amarya gidan Mahmud Kuma uwar gidansa Alherin Allah ya Kai Miki, Mama!Ammah ku fito ga abin arziki
ya sauka". Har rige-rigen fitowa a key tsakanin Mama da Salma yayin daga dakin Ammah Inna maimuna ta
fito.
❤️
❤️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE NINE🔷(9)
____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan
jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara
daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin
kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro
yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga
karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama
bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani
kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya
hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata
dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya
lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke
game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya
ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana
ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa
kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana
tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai
yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada ta shige uwar daki.
A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.
Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga
Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.
Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana.
Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi
barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara
karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa.
Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake
faruwa
************_
_
TUSHEN LABARIN
******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne
iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka
rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna,
kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji
day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.
Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa ba daga
gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin
hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan
Miya daaya kafawa Nanna jarinsu.
A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan
yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka.
Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da taimakon wani uban
gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana
sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo
nasa kayan zeyi Masa kokarin shago kafin ya dawo.
Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon
Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission
Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course din da ya nema Agricultural science.
Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level
300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar
da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.
Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire
ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.
Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina
kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa.
Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa tunda tasan shagon
nasa.
Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya
fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"
Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce
ta Aiko ni".
Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa
suka tafi gida.
Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar gidansu da sauri ya tashi ya
nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan
ya fada Masa Amininsa Kuma Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan
bugi karfe.
Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da hankalinsa sosai.
Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna Alhaji Dauda ne yayiwa
Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana so ba matsala ba inda aure baya Kai mace
Nasarawa batayi nisa ba.
Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata iya aurensa duk da fada
Mata Yana da Mata harda Yara biyu.
A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da uba yake aka kaita can
Nasarawa state cikin garin Akwanga.
Wannan kenan.
Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp.
Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos yayi murna sosai ko banza
Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi.
Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi wata biyu ba Allah
ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa tana Kuma da irin Qualities din da yake
fatan Samu a gurin matarsa.
Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga.
Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi bikinsa da Rabi'a suka tare a
gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda
baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna.
Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara fuskanta na Rashn
zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi
BARDA.
Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina gida Mai kyau sunje
makka shida Nanna.
Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa.
Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin hausa za'a fata
nemawa Rabi'a ne.
Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani idan ba wani cigaba
sai ayi na hausan.
A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara bunkasa gashi Allah yayi
shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai
Suma mutane suna tausaya Masa akan rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba
magaji.
Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI.
Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya shigo cikin tawagar vice
president.
Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na gwamnatin tarayya sanan
an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da
Ardon filanin Yana Karayi Masa bayanin abinda ya faru.
Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri Ardon ya juya Yama
fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?"
Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin shiga take ta Kamala Riga
da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da mayafinta farare.
Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji Jafar yake ta gaishe shi.
Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai ya kammala".
Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi ko me"
❤️
❤️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH
PAGE NINE🔷(9)
____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan
jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara
daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"
Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko".
Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin
kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro
yau ga xanzaro a bene" .
Ta Kara kwarara wata gudar.
Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga
karamar Arziki"
Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama
bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani
kasheni komai na ciki classic ne.
Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.
Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya
hada arzikinsau.
Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata
dole sai ta zaune a gurin.
Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.
Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra.
Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya
lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke
game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya
ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana
ba.
Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa
kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana
tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki".
Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.
"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai
yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"
Tana Gama fada ta shige uwar daki.
A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.
Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga
Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.
Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana.
Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi
barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara
karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa.
Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake
faruwa
************_
_
TUSHEN LABARIN
******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne
iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka
rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna,
kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji
day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.
Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa ba daga
gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin
hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan
Miya daaya kafawa Nanna jarinsu.
A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan
yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka.
Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da taimakon wani uban
gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana
sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo
nasa kayan zeyi Masa kokarin shago kafin ya dawo.
Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon
Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission
Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course din da ya nema Agricultural science.
Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level
300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar
da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.
Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire
ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.
Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina
kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa.
Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa tunda tasan shagon
nasa.
Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya
fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"
Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce
ta Aiko ni".
Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa
suka tafi gida.
Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar gidansu da sauri ya tashi ya
nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan
ya fada Masa Amininsa Kuma Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan
bugi karfe.
Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da hankalinsa sosai.
Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna Alhaji Dauda ne yayiwa
Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana so ba matsala ba inda aure baya Kai mace
Nasarawa batayi nisa ba.
Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata iya aurensa duk da fada
Mata Yana da Mata harda Yara biyu.
A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da uba yake aka kaita can
Nasarawa state cikin garin Akwanga.
Wannan kenan.
Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp.
Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos yayi murna sosai ko banza
Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi.
Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi wata biyu ba Allah
ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa tana Kuma da irin Qualities din da yake
fatan Samu a gurin matarsa.
Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga.
Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi bikinsa da Rabi'a suka tare a
gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda
baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna.
Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara fuskanta na Rashn
zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi
BARDA.
Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina gida Mai kyau sunje
makka shida Nanna.
Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa.
Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin hausa za'a fata
nemawa Rabi'a ne.
Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani idan ba wani cigaba
sai ayi na hausan.
A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara bunkasa gashi Allah yayi
shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai
Suma mutane suna tausaya Masa akan rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba
magaji.
Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI.
Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya shigo cikin tawagar vice
president.
Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na gwamnatin tarayya sanan
an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da
Ardon filanin Yana Karayi Masa bayanin abinda ya faru.
Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri Ardon ya juya Yama
fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?"
Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin shiga take ta Kamala Riga
da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da mayafinta farare.
Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji Jafar yake ta gaishe shi.
Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai ya kammala".
Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi ko me"
❤
❤️️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️
🔷PEGE TEN🔷
Story
&
Written
By
MAMAN FATIMAH
******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana fadin "Duba ka gani
Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa aka Gama wannan karatun ba domin na saka
auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi
karatun Nan shi ya fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa
Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura".
Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin.
"Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?"
Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan uwanta ta kaita aji
daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen nasa yaga tana da kokari shine yace Mata
idan ta Gama makarantar tana son taci gaba da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti,
to tunda sukayi haka ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan
maganar aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze barta tayi
karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu".
"Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna karatu barin ma na
bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke yiwa mutane allura ba da sauran
abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi
auren ta Kamar kowa".
Ardo ya amsa da "Allahumma Amin".
Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a hankali in yasa said dawo
Miki dashi".
Kai ta gyada alamar Eh.
Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja.
Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma kafa gwanatinsa cikin
ikon Allah suka yarjewa juna.
Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta da kalamai masu
kwantar da hankali.
Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a da Asma'u ya kasance
Zama Mai tsabta.
Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna sosai a lokacin ne Alhaji
Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take
tayi addu'a sosai akan matsalar ta.
A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun so Ma'un to koma
gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in dai sai Asma'u ta koma gida.
Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan da Nan suka nufi
asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa lafiya ta haifi takwaye mace da namiji.
Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai su Hassan da
Hasana aka daka musu.
Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka yayesu a lokacin Allah
ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya
zauna kusan lokaci daya suka haihu Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem.
Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan Rabi'a ta haifi mace
Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi
Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu
na waje suce Hajiya Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah.
Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya tun sassafe zu Zahra
suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma ta girmesu Amma yawan yi Mata
repeating yasa suka taddo ta.
Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta nufi cikin gida Sulaiman
Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta
kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu tafi na tuna".
Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar tare da fadar "Maza kada
ku makara mana".
Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci jarabawar saboda
Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu"
"To naji maza Allah ya bada sa'a"
A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu barki ba Dan Abba ya
fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan".
Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan.
Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako.
A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha.
Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra passport da visa Saida ya
Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin
da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da
Koda Hasana ko Hassan ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar
kudin Kamar yayi yawa".
Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da Alhajin yace.
Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har Jordan na kwanta a gida
hanakli kwance ko?"
Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe".
Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na daukesu yada zan yiwa
abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike maganar cacar kudi idan zan jera shekara
Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze girgaiza a cikin abinda na mallaka".
Ku tashi kuje.
Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai yawa na tsaraba.
Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya.
Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato suka gansu, sun Kuma
Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko
a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai address dai daya taba tambaya can wani lokaci.
A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan uwa aka dasa sabon
kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin
yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin turanci suka ringa magana dasu.
Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk yanda yaso zillewa kin
yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya
dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai
yasan hadin Allah ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin
su.
Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu hadu a Saudiyyar
tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a cikin garin Madinatul Munawwara.
Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty Nawwara.
A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan kanwar Ummee Hanifa
sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria
ba.
Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki Dan cewa yayi idan irin
haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda
Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi.
Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l Sayyaya dai Zahra ta shata
Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su.
Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai kala goma duk dai
dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta
Arziki.
Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya Basu suka tafi ba
sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala.
Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho ba sai Balan kawai,
sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya kwanciya har sai ya iso.
Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana fadin "Ammah!!! mun
dawo".
Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna Sai jikin zahra
Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi.
Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa ba notice?"
Alhajin ne ya Bata amsa.
"Surprised din ki mukayi ko Zahra na?.
Kai ta gyada masa.
Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part dinsa na cikin gidan yayin
da Ammah ta rufa Masa baya.
Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina Rabi'a ? Tace Masa tana
ciki watakila ko barci take.
Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda sukaje a Jordan da
saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin
wuri biyu da rabi na dare, leko tace su kwanta basu san dare yayi sosai ba.
Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado.
Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar.
Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu F.G.G.C KAZAURE yayin da
Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma ce kawai bata samu ba a cikinsu.
Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su Abban Kuma da ya
Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan
Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman.
Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne suka kaisu.
Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da wata prefect yasa su
Kai Zahra room din 'yan j.s one.
A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo ki zauna a kwana ta
tunda ni daya ce saman gadona ba kowa".
Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya.
Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE daga kukan da tsaha
sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar Gwammaja kefa ya sunanki?".
Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai nasu ya Zama
daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C.
Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga kyau ga ilimi Nan da
Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya
santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin nata ba A'a farin jini ne daga Allah.
Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri malam Bala yazo
lokacin har ya dauko Sulaiman.
Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan Sulaiman har da kuka,
Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana.
Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third term ne akayi auren
Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa a Rasha.
Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC AZAREN itama a ss1.
A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida.
Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai.
Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba namiji ba itace komai
nasa.
Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan daura gidan Nanna
da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara
kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah sai komai ya daidaita.
Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan majalissarsu Mai
wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta
haka dinki ma ya Dace da material din, simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na
kamfanin Al haramaini.
Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura kafin Hameedar ta fito.
A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara lafiyar kasancewar breast
lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane.
Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune ne da a falonta
kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya shigo falon da sallama ya Dan jefa
car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya Kama jikinsa.
Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a Kai wadda ke facing
dinsu Hameedar.
Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban ganki ba gaskiya Ina
ga tun kafin na tafi Colombia fa".
Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai bakwa ganuwa Kuna uwa
duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu".
Ta fada tana dariya.
Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma haka mukayi da Kai?"
Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu yanzu zanje na kawo
Miki in Sha Allah."
Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya Sahal ka tafi dasu tunda
cikin garin kayi.
Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal wadda mommyn
ta Basu.
Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki bani aron sister din take
Mana Kona ten minutes ne Mana".
Dan murmushi tayi tana fadar.
"Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi"
Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani irin kallo har a cikin mota
ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya
hankalinsa yana kan Zahra.
Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta wuce dakin su.
Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne baki sukazo gurin
Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne dayan Kuma kanin Babansu.
Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa yaron gurin Dan
uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa ya turosu ya gabatar da maganar
Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira.
Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa kenan, ya Kuma nemi
Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya amince musu da addu'ar Allah ya hada
kawunan su.
Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi Basu Dade sosai ba sukayi
wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal
yakewa zahra kusan Kullum da yamma Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka
tsaida lokaci wata shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata
degree din.
Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi Kamar ba'a San zafinsu
ba.
Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata -kwata Sahal ya rage
zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba, duk wani zazzari da yake na bikin su events din
da yake ta faman damun zahra da maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai
kirata ba, da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar saita hakura da
Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta tsareta da tambayar ko wani Abu ya
hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a
kwanaki idan ta Kira shi.
Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta umarceta da kada ta Kara
kiransa a wayar ta zuba ido kawai.
Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan ma sunce suna
Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin.
Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka Nigeria daga Istanbul
kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din gado har hudu kujeru set uku bayan
electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba sai dai idan an duba manual din.
Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi Masa haka toshi meye
amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba.
Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya kamata suyiwa diyar
Najwa kenan.
Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan dakin da duk abinda
ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya nutsa saita Fara business na abinda take
son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar.
Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take dawainya da wannan
marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba.
Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya tace bakinta yaki
rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani tunani na daban, Nan da Nan ta Kori
shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata.
Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra, yanzu ta Kai kwata-
kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a Fara biki Wanda yayi daidai da saura
kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa
zasu tafi daga baya su Ummeen sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske
Ummee ta shiryawa bikin sosai.
Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane ba Kuma halayyarta
bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi duk kasala ta baibayeta jinta take
Kamar ma zazzabi na neman rufata...
❤
❤️️
AUREN HUCE HAUSHIN
❤️
❤️
🔷PEGE TEN🔷
Story
&
Written
By
MAMAN FATIMAH
******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana fadin "Duba ka gani
Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa aka Gama wannan karatun ba domin na saka
auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi
karatun Nan shi ya fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa
Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura".
Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin.
"Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?"
Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan uwanta ta kaita aji
daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen nasa yaga tana da kokari shine yace Mata
idan ta Gama makarantar tana son taci gaba da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti,
to tunda sukayi haka ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan
maganar aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze barta tayi
karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu".
"Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna karatu barin ma na
bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke yiwa mutane allura ba da sauran
abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi
auren ta Kamar kowa".
Ardo ya amsa da "Allahumma Amin".
Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a hankali in yasa said dawo
Miki dashi".
Kai ta gyada alamar Eh.
Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja.
Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma kafa gwanatinsa cikin
ikon Allah suka yarjewa juna.
Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta da kalamai masu
kwantar da hankali.
Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a da Asma'u ya kasance
Zama Mai tsabta.
Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna sosai a lokacin ne Alhaji
Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take
tayi addu'a sosai akan matsalar ta.
A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun so Ma'un to koma
gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in dai sai Asma'u ta koma gida.
Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan da Nan suka nufi
asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa lafiya ta haifi takwaye mace da namiji.
Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai su Hassan da
Hasana aka daka musu.
Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka yayesu a lokacin Allah
ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya
zauna kusan lokaci daya suka haihu Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem.
Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan Rabi'a ta haifi mace
Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi
Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu
na waje suce Hajiya Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah.
Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya tun sassafe zu Zahra
suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma ta girmesu Amma yawan yi Mata
repeating yasa suka taddo ta.
Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta nufi cikin gida Sulaiman
Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta
kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu tafi na tuna".
Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar tare da fadar "Maza kada
ku makara mana".
Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci jarabawar saboda
Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu"
"To naji maza Allah ya bada sa'a"
A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu barki ba Dan Abba ya
fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan".
Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan.
Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako.
A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha.
Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra passport da visa Saida ya
Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin
da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da
Koda Hasana ko Hassan ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar
kudin Kamar yayi yawa".
Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da Alhajin yace.
Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har Jordan na kwanta a gida
hanakli kwance ko?"
Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe".
Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na daukesu yada zan yiwa
abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike maganar cacar kudi idan zan jera shekara
Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze girgaiza a cikin abinda na mallaka".
Ku tashi kuje.
Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai yawa na tsaraba.
Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya.
Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato suka gansu, sun Kuma
Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko
a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai address dai daya taba tambaya can wani lokaci.
A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan uwa aka dasa sabon
kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin
yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin turanci suka ringa magana dasu.
Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk yanda yaso zillewa kin
yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya
dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai
yasan hadin Allah ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin
su.
Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu hadu a Saudiyyar
tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a cikin garin Madinatul Munawwara.
Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty Nawwara.
A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan kanwar Ummee Hanifa
sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria
ba.
Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki Dan cewa yayi idan irin
haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda
Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi.
Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l Sayyaya dai Zahra ta shata
Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su.
Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai kala goma duk dai
dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta
Arziki.
Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya Basu suka tafi ba
sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala.
Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho ba sai Balan kawai,
sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya kwanciya har sai ya iso.
Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana fadin "Ammah!!! mun
dawo".
Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna Sai jikin zahra
Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi.
Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa ba notice?"
Alhajin ne ya Bata amsa.
"Surprised din ki mukayi ko Zahra na?.
Kai ta gyada masa.
Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part dinsa na cikin gidan yayin
da Ammah ta rufa Masa baya.
Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina Rabi'a ? Tace Masa tana
ciki watakila ko barci take.
Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda sukaje a Jordan da
saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin
wuri biyu da rabi na dare, leko tace su kwanta basu san dare yayi sosai ba.
Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado.
Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar.
Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu F.G.G.C KAZAURE yayin da
Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma ce kawai bata samu ba a cikinsu.
Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su Abban Kuma da ya
Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan
Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman.
Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne suka kaisu.
Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da wata prefect yasa su
Kai Zahra room din 'yan j.s one.
A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo ki zauna a kwana ta
tunda ni daya ce saman gadona ba kowa".
Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya.
Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE daga kukan da tsaha
sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar Gwammaja kefa ya sunanki?".
Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai nasu ya Zama
daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C.
Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga kyau ga ilimi Nan da
Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya
santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin nata ba A'a farin jini ne daga Allah.
Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri malam Bala yazo
lokacin har ya dauko Sulaiman.
Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan Sulaiman har da kuka,
Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana.
Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third term ne akayi auren
Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa a Rasha.
Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC AZAREN itama a ss1.
A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida.
Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai.
Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba namiji ba itace komai
nasa.
Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan daura gidan Nanna
da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara
kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah sai komai ya daidaita.
Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan majalissarsu Mai
wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta
haka dinki ma ya Dace da material din, simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na
kamfanin Al haramaini.
Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura kafin Hameedar ta fito.
A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara lafiyar kasancewar breast
lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane.
Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune ne da a falonta
kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya shigo falon da sallama ya Dan jefa
car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya Kama jikinsa.
Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a Kai wadda ke facing
dinsu Hameedar.
Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban ganki ba gaskiya Ina
ga tun kafin na tafi Colombia fa".
Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai bakwa ganuwa Kuna uwa
duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu".
Ta fada tana dariya.
Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma haka mukayi da Kai?"
Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu yanzu zanje na kawo
Miki in Sha Allah."
Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya Sahal ka tafi dasu tunda
cikin garin kayi.
Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal wadda mommyn
ta Basu.
Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki bani aron sister din take
Mana Kona ten minutes ne Mana".
Dan murmushi tayi tana fadar.
"Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi"
Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani irin kallo har a cikin mota
ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya
hankalinsa yana kan Zahra.
Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta wuce dakin su.
Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne baki sukazo gurin
Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne dayan Kuma kanin Babansu.
Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa yaron gurin Dan
uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa ya turosu ya gabatar da maganar
Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira.
Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa kenan, ya Kuma nemi
Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya amince musu da addu'ar Allah ya hada
kawunan su.
Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi Basu Dade sosai ba sukayi
wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal
yakewa zahra kusan Kullum da yamma Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka
tsaida lokaci wata shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata
degree din.
Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi Kamar ba'a San zafinsu
ba.
Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata -kwata Sahal ya rage
zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba, duk wani zazzari da yake na bikin su events din
da yake ta faman damun zahra da maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai
kirata ba, da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar saita hakura da
Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta tsareta da tambayar ko wani Abu ya
hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a
kwanaki idan ta Kira shi.
Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta umarceta da kada ta Kara
kiransa a wayar ta zuba ido kawai.
Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan ma sunce suna
Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin.
Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka Nigeria daga Istanbul
kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din gado har hudu kujeru set uku bayan
electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba sai dai idan an duba manual din.
Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi Masa haka toshi meye
amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba.
Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya kamata suyiwa diyar
Najwa kenan.
Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan dakin da duk abinda
ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya nutsa saita Fara business na abinda take
son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar.
Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take dawainya da wannan
marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba.
Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya tace bakinta yaki
rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani tunani na daban, Nan da Nan ta Kori
shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata.
Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra, yanzu ta Kai kwata-
kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a Fara biki Wanda yayi daidai da saura
kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa
zasu tafi daga baya su Ummeen sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske
Ummee ta shiryawa bikin sosai.
Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane ba Kuma halayyarta
bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi duk kasala ta baibayeta jinta take
Kamar ma zazzabi na neman rufata...
❤
❤️
AUREN
✨️ HUCE HAUSHIN
❤️
❤️
STORY
&
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH.
__________A cikin qanqanin lokaci aka Gama yiwa su Hameeda shirye - shiryen tafiya makaranta Dan sau
biyu suna Zuwa jigawar akan registration din. Sai wannan ciccira kai salma keyi tana sakin maganganu bare
idan suna dakinsu su kadai ta dinga fadin magana kenan, ko ci kanki zahra Bata ce Mata sai ma wani
lokacin Hameeda ke kwabawa Nan da Nan Kuma su hau sama da ita.
Ranar da zasu tafi harda ZAHRA a 'yan rakiyar, Mama ma taso zuwa Abba ne ya hanata ya Kama fadan me
zatayo.
Har hostel Zahra ta rakasu Lokacin da zasu taho ne Hameeda ta Fara share hawaye itama zahra ta Kama,
Saida ya Hamza yayi musu Jan Ido suka daina kukan, Yayin da Ya Abdul Hakeem yake musu dariya Yana
fadar "Banda tsabar shagwaba ta lalacewa har wani kuka kuke Kamar wasu 'yan J's one".
Wani kallo ya ai kawa zahra na Baki Fara kuka ba.sai kin ganki a tsakiyar masu jajayen kunne tukunna Dan
ma dai kema samman kalne ya gada a zuciyar sa.
Sai bayan magariba suka dawo gidan.
Ba'a fi sati biyu da tafiyar su Hameeda ba visa din su Zahra ta fito ita da Abdul Hakeem.
Sai ana ya gobe zasu tafi Ammah ta fadawa Mama. Ai Kuma tayi korafin abin Dan har Alhajn ta fadawa
yace shima jiya yake Jin labarin tunda Saida komai ya kankama sannan suka Kira suka fada Masa Dan kada
ya Hana.
Da safe Bala dureba ta dauke sai kano inda zasu tashi.
Satin Abdul Hakeem hudu a can Dan Bai taho ba Saida ya raka Zahra har syprus din a gabansa komai ya
kammala ranar da ze tafi Zahra tayi kuka Kamar idonta ze fita sai a sannan taga ba karamar wauta tayi ba
data yarda da wannan karatun, dadin ta daya da uncle Haisam a kasar ko banza tana da gurin zuwa a debe
Mata kewar gida.
Ta Fara karatu cikin nasara Bata da wata matsala ta zahiri saidai sau da yawa tana shiga dogon tunani akan
al'amuranta ta rasa Gane daga Ina ne ake samun irin wannan akasin? matsalar dai iri daya ce, Kuma salon
tafiyar iri daya ce sai Dan banbancin da baza'a rasa ba.
Suna yawan waya dasu Ammah da mutanen Jordan, lokacin data Kira Hameeda mita ta ringa yi Mata akan
tana boye Mata wani Abu tunda gashi Saida ta bar kasar kana ta Kira ta. Da kyar ta fashimtar da ita abun
ne yazo da gaggawa itama Bata sani ba Saida komai ya Zama ready, Kuma tayi ta try din ta sameta Bata
Samu ba lokacin ana fama da matsalar network a area dinsu.
Zahra najin dadin Zama a kasar duk karshen sati a gidan uncle Haisam take yin weekend din ta, sai Monday
da safe motar Embassy take dawo da ita.
Tsakanin syprus science University din wadda take kyrenia city a arewacin syrups din da capital city din
dake Nicosia tafiyar kilometers talatin ne, kawai daga Baya ma da uncle din cewa yayi ta baro cikin
makarantar ta dawo gidansa kawai da Zama sai a ringa kaita kullum itace taqi tana ganin Kamar abun da
wahala yau da gobe sai Allah daga nesa nesa dai.
Yau ma Monday da wuri motar Embassy din ta kawo ta, tayi gaba da wasu daliban zuwa mabanbantan
makarantu inda suke karatunsu.Ganin da saura Kamar awa aya da rabi kafin su shiga lectures yasa ta wuce
hostel Dan ta aje kayan da tazo dasu.
Tana cikin tafiya tazo gota wani hostel Kamar a mafarki sai taji Kamar ana hausa a dakin abin ya Bata
mamaki tayi Kamar ta koma ta duba sai dai tayi gaba tunda bin kwakwkwafi haramun ne.
Lokacin da suka Gama lectures din Bata koma hostel ba, karatu suka zauna sunayi da wata course mate
dinta 'yar kasar Lebanon Asseyeh tasu tazo daya sosai saboda itama akwai nacin karatu ga Kuma kwanyar
Allah ya hore itama, uwa uba ga rikon addini tunda su dai kasar sai a hankali kawai culture din ta rinjayi
addinin, Dan wasu Ma sai kaga suna sallah zaka Gane musulmi ne.
Yamma likis su Zahra suka nufi hostel, haka nan Zahra taji tana son karabi ta wurin inda taji ana magana da
Hausar nan, can ta nufa bayan sun rabu da Aseeyeh.
Very lockly kuwa tayi Dace da wata daga ciki ta fito tana waya bahaushiya sosai.A shape ce a jikinta ta
atamfa sai karamin hijabi a jikinta da alama Kamar fita zatayi.Dan tsayawa zahra tayi har ta karasa wayar,
cikin nuna zallar farin ciki zahra ta nufeta tayi Mata sallama.
Da sauri ta juyo Jin an Mata magana da Hausa cikakkiya.
"Wa'alaiki Salam" yarinyar ta amsa Mata tana kallon zahrar da murmushi itama a fuskarta.
"Masha Allah wallahi naji dadin ganinki kema daga Nigeria kike".
Zahra ta tambaye ta.
"Eh daga Nigeria muke muna da Dan yawa zamu Kai goma".
Mamaki ne ya Kama zahra ganin Bata taba ganinsu ba Koda wasa.
"Ikon Allah! Amman dai baku Dade ba ko?"
Kai ta gyada "Mata gaskiya Kam ai ba school daya muke ba mu a Nan mu hudu ne, sauran suna different
Universities ne on transfer mukazo nan daga Sudan tunda can rikici ya d'ai d'aita Qasar. Zo mu shiga ciki ki
gaisa da sisters Dina kafin na dawo zan fita na samo Ko fizza ne yau bamuyi girki ba".
Ta fada tana juyawa ciki, bayan ta zahra tabi suka nufi ciki.
"Khadijah ! Fatima,! Sajida! Kuna Ina ku fito gashi mun Samu qaruwa".
Kowacce barin abinda take tayi ta nufo kofar tana fadin "Anisa menene?".
Ai kafin tayi magana Zahra tayi Arba da sajida Musa, sajidar ta ta FGGC KAZAURE.
Cikin wani irin farin ciki suka rungume juna Zahra sai kuka Dan wani abune da Bata taba zata ba robonta da
sajidar tun suna cikin bala'in Sudan kafin wayar sajidar ta salwanta shi kenan suka daina Jin juma Amma
kullum zahra da fargaba take kwana har zuwa lokacin da ta Samu labarin dawowar su sajidar a bakin
Maryam Suraj wata kawarsu.
Kallo saiya koma sama Wai shaho ya dauki giwa ita Mai kawo bakuwa sai duk suka Zama 'yan kallo.
Hannun zahra sajidar ta Kama ta nufi bed in ta da ita tana fadin "wannan wace irin ranar farin ciki ce bestie
wallahi ranar nan tana daga cikin ranekun da bazan taba mantawa dasu ba cikin tarishin zamana a syprus,
pls bestie talk ya akayi haka ta faru Dan Allah kece ko gizo idona yake mini ne Dan Allah kiyi magana".
Ita dai zahra ba baka sai kunne, ai ita nata mamakin yafi na sajidar sau dari idan da Wanda Allah ya yiwa
gyadar dogo ai ita ce, ba zato ba tsammani Allah yayi Mata irin wannan suturar bama 'yan Nigeria ba A'a
aminiyar ta sukutun ya kawo Mata kasar, ba abinda zata cewa mahalicci sai godiya take a Nan tayin
sujudushshukur ga Allah. Sai da ta goge hawayenta sannan ta Samu damar magana suka gaisa da sauran
yayin da Anisar ta cire hijabin tana fadin "Ai Kuma saidai kowa ya hakura da cin fizzar Dan na fasa fitar
kawai ayi abinci tunda Naga bakuwar tamu ce ko sister" ta fada tana kallon sajida.
"Kwarai kuwa ai dukkanku kowa ya kwana da sanin Zahra Muhammad sani ko?".
Gaba daya suka zubawa Zahra idanu suna fadin sosai ma kuwa, niba har gaisawa munayi ba some times
idan Kuna vedio call lokacin muna Sudan" inji Khadijah.
"To ai ita ce gata a gabanki zahiri"
Khadijah ta Dade tana mamakin abun ita sai taga Kamar canza Zahra akayi tasan dai yesss ba karya zahra
Mai kyauce na a bugi kirji a fada, amma sai taga wannan Kamar ma Bata taba hada dangantaka da 9ja
tamu ba, komai nata classic ne.
Nan suka baje hajar hirar yaushe gamo, har kusan karfe goma na agogon kasar suna tare anan su sajida
suka fada Mata gwamnatin tarayya ce ta dawo dasu Nan tunda suna under scholarship ne shine aka
rarrabasu kasa kasa su Allah yasa suka shigo cikin daliban da aka kawo Nan din.
Har daki suka raka Zahra a Nan ta Basu fizzar tunda Daman tazo da ita daga gidan uncle Nan ma sun jima
kafin su koma.
Ai tun daga ranar wata nutsuwa da kwanciyar hankali suka Samu kyakykyawan muhalli a zuciyar Zahra,
haka itama sajidar duk da Daman ita tana da masu dauke Mata kewar gida, Suma su sajidar sau da yawa
suna bin Zahra a wasu weekend din zuwa gidan uncle Haisam din Amma su basa kwana duk da irin nacin
da zahrar ke musu.
A haka karatunsu ya Mika har sukayi exams, Mama Hanifa taso Zahra taje Mata tayi hutu Amma Haisam
yace tayi hakuri sai hutun karshe session.
A haka suka Kare hutunsu suka Dora da karatu, ba Sajida ba hatta su Khadijah suna Jin dadin Zama da
zahra gashi Sam abin duniya Bai rufe Mata ido ba, Dan ta ko'ina kudi ne ke sauka a Account din ta ba daga
9ja din ba, ba daga Jordan ba, ba daga turkey ba, kowa kokarin farantawa zahra yake zuwa lokacin tayi
wani irin mahaukacin kyau na ban mamaki ga wayewa da wayon zaman duniya ta Kara Zama 'yar gayu
Kamar me Dan ba karya matar Uncle Haisam Yar gayu ce sosai kamar Auntyn ta Hasana tasan yanda ake
tattalin jiki matuka.
Har zuwa lokacin ba ruwan Zahra da saurayi bil hasal ko aboki namiji Bata dashi, akwai wani Dan Syria
Omer yaso Zahra Kamar kaddara Amma ta shafawa idanunta toka tace ba wannan maganar yace to su
Zama friends Nan ma tace lah lah.
Dole ya hakura saindai duk inda zasu hadu sai yayi Mata magana idan abu ta saya duk yawan kudin shi ze
biya.
Lokacin hutun karshen shekara Zahra taso zuwa Nigeria tunda taga su sajida nata Shirin tafiya, ta kwallafa
Rai sosai akan zuwan Amman sai Ammah ta hanata zuwan tace taje Jordan idan hutun ya kusa karewa ta
dawo Nan gurin Mama Hanifa ta karasa Abdul Hakeem zezo ya ganta. Ba haka taso ba da har tayi niyyar
Kiran Abban ta fada Masa sai Kuma tayi tunanin kada Ammah tace ta Kai Kara dole ta hakura tunda Bata
San nufin Ammah din ba data hanata zuwan.
Taji dadin zuwa Jordan din sosai, dan Ummee na Shirin zuwa Saudi Arabia ne ma zuwan Zahrar ne ya kawo
Mata tsaiko, tare suka tafi bayan ta huta, a can suka tarar da Aunty Nawwara wadda taje zuwa na
musamman tunda lokacin ana daf da bikin aurenta inda za'a kaita Bagdad (Iraq).
Sunyi sati daya zuwa suka nufi makka sukayi Umara, sosai Zahra ta mayar da hankali gurin addu'a akan
matsalolinta na yanda rayuwa ke walankekuwa da ita Bata rasa komai ba Amma aure Yana neman yafi
karfinta dah kudi ko kyau ke sawa mace ta auru tasan da yanzu ba wannan zancen ake ba, sai dai tasan duk
Dan Adam baya wuce tasa kaddarar sai dai neman sauki gurin Allah s.w.a.
Madina suka koma da suka Gama umarar,basu Dade ba suka koma Jordan.
Lokacin da hutunsu ya taho garewa zahra ta koma syprus. Gidan uncle ta Fara Zama kafin daliban su dawo
tunda ana saura one week ayi resuming ta dawo. Karatu suke ka'in da na'in ba Kama hannun yaro, amincin
ta da Sajida ya Kara karfi tamkar uwa daya uba daya suke, Dan lokacin da sukaje hutu sajidar har Azare taje
ta gaishe da Ammah ta karbowa Zahra sako.
Duk lokacin da za'a yaye dalibai makarantar tana hada gagarimin taro tana baiwa best student na kowane
department award.
A karshe semester din ne aka hada taron Wanda ya Tara al'umma daban daban daga kasashen duniya
masu Taya 'ya'yan su da 'yan uwa murnar gama karatu, celebration ne ake na gasken gaske, su zahra dai
suna kallon abubuwan tunda wannan shine na farko da akayi suna Nan lokacin da akazo bada award ne ba
zato ba tsammani aka Kira zahra Muhammad sani daga Nigeria aka Bata award na overall a department
dinsu akan kowane subject.
Wayyo murna gurinsu ba'a magana Dan Zahra kuwa har mukan Dadi tayi data duba taga yawan daliban da
suke a department din nasu Amma ace ita ta karbi best ai abin murna ne Kam. Sun Sha hotuna da
mutanen mu na africa more especially 'yan Nigeria.
A ranar Zahra tayi takaicin karatun nesa da ace a gida ne da Abbanta ko Ammah ko wani daga cikin yayinta
zata danqawa kyautar su sharing happiness din tare Amma Nan kuwa fa sai da friends da wasu tsirarun
mutane Wanda ma ba saninsu tayi ba sukayi farin cikin, ga Uncle Haisam ma a matarsa da yaran duka sun
tafi turkey.
Sai ta waya sukayi murnarsu da jama'ar gida ta tura musu hoton award din ta waya hotunan da suka
dauka.
-----------------
AZAREN KATAGUM
Alhaji Jafar ne da Malam Bukar sai Habibu dan kanwar malam Bukar dake aure a suleja malam din yake
rikonsa tun yana karami mahaifinsa ya rabu da mahaifiyar sa acan gida Yobe da tayi auren a suleja din ne
baban Habibun yace baza'a tafi Masa da yaro gidan wani ba yayi agolanci, rigima sosai aka kwasa da shi
saboda itama tace bazata bar danta a inda za'a kashe Mata shi ba. Shine mafarin malam din ya dauko shi
tunda ba wasu 'ya'ya yake dasu da yawa ba, a hannun malam ya girma shi yayi karatun boko har matakin
HND.
Jikamshi malumfashj zasuje Daurin Auren 'yar abokin Alhaji Jafar din sannan zasu shiga Jikamshi dubiyar
malamin malam Bukar din daya kwanta kwanakin baya a Asibitin Ibadan nisa yasa shi majiyyacin ya Hana
masu zuwa dubiya sai yanzu daya dawo gida ne malam zeyi amfani da wannan damar yaje dubiyar.
Tafiya ce mikakkiya Dan tsakanin Azare da malumfashi tafiya ce ba kadan ba Dan haka sukayi sakko
Habibun ne ze tukasu malam Bala anyi Masa Rashi acen garinsu Itas gadau Yana can.
Cikin ikon Allah Basu rasa Daurin auren ba Dan Sha buying Mai kyau suna cikin garin malumfashin.
Basu Bata lokaci ba suka dauko hanya sun biya jikamshin sun duba malamin Alhaji yayi masa kyau ta girma.
Suka dauki hanya sosai Alhaji Jafar ya yaba da tukin Habib Dan baiyi zaton ya kware irin haka ba.
Sunzo kachako lokacin sallar la'asar yayi guri suka Sami inda akayi wani Dan masallaci dan matafiya.
Suka firfito Dan gabatar da sallar, malam ne ya Fara gewayawa yayi dahara sannan Shima Alhajin yayo
sukayi alwala suka shiga sallah Saida suka Gama suka fito sannan Habib Shima ya nufi gurin you daharar
Amma shi saiya nufi wani bangaren daban, Bai jima da tafiya ba sai gashi da sauri Yana Kiran" Baba malam!
Kuzo ku gani". Da sauri suka nufi inda yake harma da wani mutum da suka Sami a gurin Kamar Mai kula da
gurin ne Dan daga gefe da 'yar tiredar shi suka rankaya Habib na gaba suna bin shi tun kafin su karasa suka
hango mutum a kwance Kamar marar Rai.
"Subhanallahi "abinda suka gada kenan suna karasawa kusa dashi sai da suka matsa sosai suka Gane da
ransa Amma Yana cikin wani yanayi, dako dako sukayi aka rasa ya za'ayi dashi matashi ne ba zefi sana'an
Habibun ba saidai a yanayin yanda jikinsa yake ba alamar wahala a tare dashi. Habib ne ya matsa kusa
dashi sosai ya tsuguna Yana dudduba jikinsa ko akwai alamun duka ko makamancinsa amma babu komai,
shawara sukayi su daukeshi kodan ceton Rai su tafi dashi idan yaso sai su dauki hotonsa a Dora a social
media wata kila a Dace.
Lokacin da suka shigo Azare ana sallar insha'i directly asibiti suka nufa dashi ma'aikatan nan da Nan suka
duqufa a kansa, sai gurin Sha daya Allah ya taimaka ya kawa kwakwkwaran numfashi.
Sai lokacin suka nufi gida malam ya turo dalibansa guda biyu ya fada musu dakin da aka kwantar da Wanda
suka tsinta din, ya basu kudi saboda abun bukata.
Haka su Abubakar suka kwana da shi sai gurin hudu da rabi na Asuba ya bude idanunsa Yana kallon bakon
gurin da yake ciki ga bakin mutane a gurinsa, yukurawa yayi ze tashi yqji ya kasa kansa Kamar an Dora
Masa dutse, bakinsa ya bude zeyi magana yaji kwata kwata ya kasa yayi yayi Amma Sam maganar taki
yuwuwa sai hakuri yayi ya zuwa bawa sarautar Allah ido.
,❤️
❤️
❤️
❤️
✨ MAMAN FATIMAH ✨
__________Washe gari daga gidan Alhaji Jafar Abdul Hakeem da magaji suka kawowa su Abubakar abinci
Asibiti, sun tausaya bawan Allah nan sosai Dan zuwa lokacin sun fuskanci baya magana Kuma jikin ma baya
motsuwa yanda ya kamata, toilet ma sai da sukayi Kama Kama suka kaishi, a haka su malam suka shigo
Asibitin tare dasu Malam Mudi, Basu Dade da zuwa ba likitoci suka shigo round sun tambayi menene
Asalin ciwon to su dai sun fada musu Yan suka hadu dashi Dan Basu da masaniyar komai akai.
Gwaje -gwaje suka rubuta ayi Masa Dan binciken lafiyarsa.
Basu Dade ba suka koma gida saboda a ranar Alhaji Jafar ze shiga Bauchi suna da meeting da gwamna
Amma ya bar kudade a hannun Abubakar saboda magani da sauran hidimar Asibitin.
Da yamma Habib ma ya shigo ya duba marar lafiyar nasu, Wanda har lokacin baya magana.
Likitoci sunyi iya nasu binciken basuga komai ba a tare dashi, sai dai rashin maganar kawai Amma Kuma
Yana Jin komai da ake fada.
Bayan sun Gama bashi taimakon daya kamata suyi Masa suka sallame shi, Magaji ne ya dawo dasu gidan
malam, Nan dakin malam na waje aka ajeshi tunda aka dawo dashi gida malam ya dukufa da Yi Masa
addu'a Dan yayi bincike akan lamarin ya fashimci inda matsalar take, har Taraba ya tafi gurin malaminsa da
yayi karatu a gurinsa ya fada Masa matsalar yaron, kwanansa biyu ya dawo Azare aka dukufa da rokon
Allah da maganin hausa, haka zalika Alhaji Jafar ma Yana taho Masa dashi daga wani Islamic chemist da
yayi musu bayanin matsalar yaron a can Abuja.
Cikin ikon Allah ba'a rufe wata hudu ba ya Fara magana sai dai idan yayi sau daya sai a wuni bai sake wata
ba.
A haka aka dunga bashi taimakon har Allah yasa ya dawo normal Yana magana. A lokacin ne malam ya
zauna dashi da Habib suka fada Masa inda suka same shi da halin da yake ciki a lokacin shiru yayi kafin
yace musu shi dai yasan wata Rana Yana gida ciwon Kai ya takura masa har ya kasa fita, jzuwa dare yasha
magani ya kwanta, to tun daga lokacin bazece ga yanda akayi ba shi dai ya farka ne ya ganshi a Asibiti tare
dasu a hankali Kuma ya Gane a wani garin ma yake daban ba garinsu ba. Lokacin da Alhaji Jafar yazo garin
malam ya fada Masa komai yanda sukayi da Mahmud din, Alhajin yasa aka Kira shi ya Kara jajanta Masa
sannan ya nemi ya fadi garin nasu a mayar dashi Dan da gani Dan manyan mutanene.
Nan fa ake yinta Dan kekashe kasa yayi yace shifa ya manta sunan garin nasu akayi juyin duniya yace sai dai
ko Nan gaba idan Allah ya nufa ya tuna, abinda ya tuna ma daga baya tunanin yazo Masa, haka suka
hakura badan sun amince ba bayan ya tafi sun tattauna da Malam din akan lamarin inda Suke hasashen ko
bacin Raine ya baro shi da gidan ya gwwmmace yayi zaman sa a Nan kafin ya huce ya nemi komawa gidan.
Nan yaci bada da Zama da Malam Yana kwasar ilimi kala kala.
Nan da Nan ya Zama Dan gida suka dinke da Habib duk da ze iya girmar Habib din da Kamar shekara biyu
dan yayi Kamar sa'an Abdul Hakeem.
Bai cika wata shida ba Allah ya kawo aikin NGOs din Nan Wanda aka sakewa makarantar fasali da tsari suka
sayi wani katon fili na makudan da sunan makarantar akayi gine ginen hostel din Yara suka dauki ma'aikata
suka gyara tsarin karatun saboda kwazon Mahmud har co-ordinator din Shirin Muhammad Sameer ya
dauke shi aika a shiyyar Katagum local government din ya Zama shine idon su a Nan, tunda ya iya rubutu
da karatu. Habib ma Yana bada gudunmawa sosai a aikin duk da Shima nasa aikin da ma'aikatar ruwa ta
Nan local government din tasu.
Wannan kenan.
____
Syprus.
Zuwa lokacin su zahra karatu ya Mika, tun tana saka Rai da zuwa Nigeria har ta hakura Kuma abinda ya
Kara Bata mamaki sau biyu Abba da Abdul Hakeem suna zuwa ganinta idan harkar kasuwanci ya kawo sun
Istanbul.Amma Koda wasa Basu taba ce Mata ga lokacin da zataje gida hutu ba.
A haka har suka hada shekara biyu a kasar, da gaske gida take son zuwa shi yasa lokacin da hutunsu ya
gabato batayi shawara da kowa ba ta kama shirin barin qasar, online tayi komai Kamar su Sajida sai da
komai ya Zama daidai sannan ta fadawa Uncle Haisam Shima bai hanata ba yasan tayi hakuri, Mama
Hanifa ma ta waya ta fada Mata Nigeria zata wuce kawai, haka Ummee ma ta wayar itama ta fada Mata
taso ta hanata Amma sai tayi wani tunani kawai tayi shiru kudade dai to tura Mata masu yawa Wanda har
saida Zahrar ta Kara kiranta tana tambayar kudin ma meye haka da yawa? Tace ta turo Mata ne kawai ko
idan take zatayi wani abun, godiya tayi Mata sosai hakan Kuma dabi'ar Zahrar ne komai kankantar Abu
idan akayi Mata alherinsa zatayi godiya Kuma ko waye ta Bata Bata duba ai iyayene.
Kwana biyu suka Kara da akayi hutun shima visa din su Khadijah ne Bata Zama ready ba.
Lokacin da jirginsu ya dauka a Aminu Kano international airport taji ta sauko ta shaqi iskar Nigeria ji taji
Kamar a Aljanna take lallai kowa yabar gida gida ya bar shi, saukar safe sukayi wurin karfe Sha daya ba
yanda su zahra da Khadijah Basu da zahra ba akan ta zauna ta Dan huta kona awa daya ne a gurin sajida
Amma tace A'a Azare tayi Kira su Anisa ne da Fatima suka bi Sajida Su dan huta kafin driver dinsu ya karaso
tunda ba nisa tsakanin kazaure da kano, Kuma Gwammaja kan hanya ne.
Shatar taxi Zahra ta dauka ta kaita Kano line Dan direban taxi din ta tambaya Ina zata samu motar zuwa
Azare ya fada Mata akwai gurare Amma ita Kano line yafi Mata kusa.
Har cikin Tasha Mai taxi din ya shiga da ita gurin motocin arear Bauchi, tayi Masa godiya sosai ta kuma Kara
Masa kudi akan yanda ya bukata.
Away biyu da rabi Mai kyau matarsu zahra ta shiga Azare tun shigowa su ta Fara ganin 'yan canje canje a
garin Kamar sabbin titina street light na solar sai gine gine masu kyau. Masha Allah ya dunga fada a zuciyar
ta, Mai adai daita ta Sami ta fada Masa inda ze kaita, tunda suka tinkaro unguwar naji want irin nishadi ya
mamaye ilahirin zuciyar ta, unguwar tasu ma an Sami cigqba sosai ga wasu gine gine sabbi masu kamar
makarantar kwana har da gate a gurin gidan malam Baba gidansu ma gaba daya ya canza anyi Masa
mahaukacin gyara tamkar sake sabo akayi.
Lokacin da Mai adaidatan ya sauke ta dai dai lokacin ya Hamza ya fito da alama wani gurinzeje Nan kusa.
Da madaukakin mamaki yake kallon zahrar shi dai Koda Wasa baiji ance zatazo ba Kuma yasan da ansan da
zuwanta ai Bala driver ko su suje su daukota a kanon. Da sauri ya karasa Yana Mata sannu da hanya ita
Kuma tana gaishe shi, shi ya biya Mai Dan sahun yace ta shiga ciki za'a shigo mata da kayan.
Tunda ta shigo gate din tasan eh lallai gidan ya lashe makudan kudin Dan gaba daya an canza fasalin gidan,
tunda ta shigo gidan Mai gadin ke kallon zahra Dan shi dai sabo ne Bai Dade ba ta dai gaishe shi tayi gaba
Nan ma wani mamakin ya rufe shi Jin tayi hausa radau Dan shi dai ze iya rantsuwa da abinda ze kashe shi
wannan ko zo Bata sani ba da Hausa.
Ai mamakinta Bai karu ba Saida ta shiga cikin Nan dai ko rantsuwa tayi ba kaffara sabbin gine gine ne dam
kwata kwata inda parts din su na da yake gurin ba komai sai filing da shuke shuken flowers.
Lokacin data shigo gidan ba motsin kowa kamar ba mutane a gidan kowa ne kofar part Yana rufe Ido ta
lumshe tana shakar iska Mai Dadi ta gidan. Idonta na nufen Nan tana tsaye Dan ita batasan wane dakin
zata nufa ba tunda da gaske ta Zama bakuwa a gidan, maganar Ibrahim taji Mai bin magaji Yana fadar
"kai!" Da karfi ya juya a guje Yana fadin Ammah! Ammah! Kizo ga Aunty Zahra a tsaye a kofar part din
Mama".
Magaji ne dake zaune a falon yana kallon wani series na 'yan Lebanon ya dago Kai da sauri daga kallon T.V
Yana tsaki Yana fadin Amma Kai ba karamin soko bane dallah Banda tsabar hauka zaka wani ware murya
Kama kwala Mata akan shashancin Kawai Wai zahra A'a wat......"
Maganar ce ta makale Masa lokacin da zahrar ta kunno Kai ciki da sallama a bakinta, dan a bude yabar
kofar saboda zumudin ya kawo labari.
Ammah ce ta fito da sauri tana fadin Wai Kai har abada Ibrahim bazaka giirm..."
Idonta ya sauka akan Zahra wadda tayi tsaye ta langabar da Kai tana kallonsu,kafin Ammah ta dawo daga
duniyar mamaki sai Jin zahrar tayi ta rugumeta ta saki shashhshekar Kuka.
"Ikon Allah!" "Ikon Allah!"
Abinda bakin Ammah ke fada kenan, ita Kuma zahra ta riketa kamar zata bace Mata.
Mamace ta shigo dakin da sauri tana fadin "Ina zahrar yanzu sahura ta shiga ta fada min taga Zahra ta
shigo yanzu".
Ta fada tana kokarin Zama idanunta suna kan Zahrar.
"Wallahi kuwa Mama kin ganta Nan yanzu Ina daki Ibrahim ya shigo a guje Yana fadin gata Nan a waje nayi
zaton shashancinsa ne Saida na fito na ganta kwatsam ba zato ba tsammani ba wani bayani".
Ammar ta saki da Dago kanta tana goge hawayenta tana fadin. "Haba Ammah an kaini wata uwa duniya an
manta Dani idan nace zanzo ace A'a ni Kuma wallahi na gaji gida nake so shi yasa naki fadawa kowa na
tasho kawai na gaji da ganinku a waya ni zahiri nakeso". Ta fada tana maida kanta jikin kafadar Ammar.
Tunda ta Fara magana Mama ta kureta da ido dan wani irin mahaukacin kyau taga Zahrar ta kara, ga wata
irin gogewa da wayewa tamkar ba Zahrar data sani ba komai nata ya canza har ma salon yanda take
magana.
"Ai kodai ki daina irin wannan kasadar ta tahowa daga uwa duniya irin wannan ke kadai sai ki fada ko
addu'a ayi Miki sannan aje a daukoki daga Kano, Amma fa Ina tunanin a motar haya kikazo garin Nan ko?"
Mama ta fada.
Kai Zahra ta gyada alamar eh, dai dai lokacin Yara suka shigo da jakunkuna ta guda biyu.
zaunawa tayi tana gaishe dasu Ammah, sannan magaji yayi Mata sannu da hanya Yana fadin "irin wannan
surprised haka uktiy? kin ganki kuwa kin juye Balarabiyar ki sak kodan kina cikin 'yan uwa dangi farare
irinki"
Dariya Zahra tayi Masa kawai.
Ibrahim ne ya shigarwa da Zahra jakunkunan ta dayan bed room din Ammah, ya fito ya nufi kitchen ya
kawo Mata ruwa da lemo, ya koma ya dauko warmmers din abinci sai Ina yaka saka yake da zahra har
Mama na Masa Dan biki.
Saida tayi wanka taci abinci sannan suka zauna da Ammah bayan sallar insha'i, hira sosai Suke Amma duk
yawanci korafin Zahra ne na hanata zuwa.da Ammah tayi, a haka Abdul Hakeem ya samesu Shima yayi
mamakin ganin.zahra kamar a mafarki Dan lokacin da ta dawo baya nan yaje Darazo ganin ganin wasu
gonaki da Ya Hassan ya saya a can.
Sun raba dare suna Hira da 'yan uwanta a falon Mama sunyi waya ma da Abban tunda lokacin Yana aAbuja,
Shima yayi fada sosai lokacin da Ammah ta Kira shi ta fada Masa ga zahra tazo.
Sai da ta kwana biyu tana huce gajiyarta, tana jikin Ammah kullum kamar kamar wata 'yar yaye, duk 'yan
uwan kowa nan nan yake da ita, kowa kokarin kyautata Mata yake yi.
Sunyi waya da Aunty Hasana tace Mata tana nan tafe Jos zatayi Mata sati Amma sai Abba ya dawo, haka
kusan Kullum sai sunyi waya da Hameeda.
Ranar data kwana biyar ne Ammah ta takura Mata akan ta leka makwabta ta gaishe wasu da yawansu sun
shigo, wasu Kuma sun turo yaransu suyi Mata sannu da zuwa harda abin hassafinsu.
A waya Zahra ta Kira mujiba akan ta Shirya ta rakata Nan gidajen su shishhiga a gaisa.
Doguwar Riga ta saka kirar Dubai blue black Mai duwatsu tun daga sama har kasa ta saka plat she dinta fari
tas ba wani makeup da tayi powder kawai ta saka sai lipsglow turarenta na Alkawari ta fesa Mai sanyi
kamshi, Kota sa ko Bata Saba komai na sutarata kamshin yake.
Ta fito Kamar wani dawisu Dan da gaske zahra mai kyauce komai nata Kamar ita ta zabarma kanta. Tunda
ta shiga bedroom din Ammah ke kallonta data ita sai halicinta suka San abinda zuciyar ta ke ayyana Mata a
fili Kuma sai tace "Masha Allah! Har kin shirya?"
Kai ta gyada Mata tare da fadin "Eh Allah Dan dai kin matsabe Ammah Allah da Babu inda zani sai nayi sati
biyu ko gate ba leka ba".
Wata leda Ammah ta Miko Mata tasa hannu ta karba tana tambayar "na waye?"
" Idan kunje gaida Baba malam saiki bashi tasa tsarabar turarika ne".
Murmushi Zahra tayi har fararen hakoranta suka bayyana tana fadar "wace irin tsaraba Kuma Ammah nida
ba Hajji naje ko Umara ba daga makaranta fa na dawo hutu".
"To Miko min kije hannu sake ki gaisa ki taso tunda Zama da turawa ze saka ki koyi rowa" ta Mika Mata
hannu alamum ta Bata ledar.
Dariya tayi Zahrar tana fadin "Allah ya Baki hakuri Ammah Ina ni Ina koyo rowa a garin wasu alhalin na gaji
kyauta gaba da baya Allah qara lfy". Ta nufi kofa tana fadin "saina dawo"
"Allah ya tsare Kya gaishe da Malam din.
Gidan su mujibar Zahra ta Fara shiga suka gaisa da Mamanta sannan suka shishhiga gidajen suka gaisa,
gidan Malam ne na karshe, a hanya Zahra ke tambayar Mujiba ginin da taga anyiwa Almajiran Baba
Malam? nan ta fada Mata iya abinda ta sani akai.
A cikin rumfar canopy din da Malam yake bada karatu Zahra suka tarar da Malam din suna magana da
wani matashi sukayi sallama a bakin rumfar a tare malam da Wanda Suke magana suka amsa sallamar,
Yana fadin Bari naje na karbo yanzu in Sha Allah. Juyowar da zeyi sukayi ido hudu da Zahra wallahi ita dai
batasan lokacin data rufe idanunta ba Dan wallahi wani Abu ta gani a idonsa Wanda Bata taba gani a idon
kowa ba take zuciyarta ta wani harba a cikin girjinta. Ga wani mayen kamshi daya cika Mata hanci ita dai
Bata San ya wuce ba Saida Mujiba ta tabata tana fadin ki bude idonki "Zahra menene?".
Ajiyar zuciya tayi a hankali tace "ba komai muje"
Cikin rumfar suka shiga suka zauna daga gefe suna gaida malam din.
Amsawa yayi Yana fadin Masha Allah da bakin turai ne Fatimah yaushe Kika shigo ban sani ba kodon Alhaji
Yana Abuje shi yasa bani da labari".
Sunkuyar da Kai zahra tayi tana fadin.
"Ban Dade ba Baba Malam yau kwanana biyar da dawowa, Saida na huta nace Bari nazo na gaisheka"
"To Masha Allah! Allah yayi Albarka ya bada sa'ar abinda akaje nema, ai ba'a Gama karatun ba ko?".
"Eh da sauran shekara daya karatun ne da banbanci da namu na nan tunda su basa yajin aiki".
"Wannan haka yake, Allah yayi jagora ya bada sa'a"
"Amin" suka amsa tashi zahrar tayi ta karasa gaban malam din ta aje Masa ledar turarikan dake hannunta
tana fadin "gashi Baba ba yawa"
Godiya yayi sosai kafin yace "ku shiga ku gaisa da zainabu batajin Dadi tana fama da masassara tun jiya".
"Allah ya sauwake"suka fada suna fita faga cikin rumfar.
Tunda suka shigo gidan suka sallama Amman gidan shiru a falon ma ba kowa uwar dakin Zahrar ta nufa
tunda gidan ba bakonta bane, can tsakiyar gado ta hango Iya Abun jikinta yana ta kadawa tana ta rawar
sanyi da sauri Zahra ta karasa kusa da ita tana Mata sannu Amman Sam ta kasa amsawa hannunta Zahrar
ta Mika ta taba jikinta sai taji Kamar wuta.
"Ya Salam".
Ta fada tana nufar falon inda tabar mujiba tana fadar "Bari na fadawa Baba Malam jikin Kamar ya matsa
gaskiya". Tayi waje ba tare data jira taji abinda mujibar zatace ba.
Tafiya take cikin sauri burinta ta Isa gurin malam ta fada Masa abinda kenan.
Ita dai Batasan yanda akayi ba sai ji tayi ta bugi kirjin mutum da kanta abinda yayi sanadiyyar ta tafi taga -
taga zata Fadi taji an fusgota da Dan qarfi kafin ta Kai kasa sai ganin ta tayi rungume kane kane a jikin
koma wannene an saka hannu biyu an zagaye bayanta.
Kici kicin kwace jikinta ta shiga yi data Samu ta Sami kanta coming fishing ta daga ido taga wane Mai tarar
aradu da fadin Kaine ya kwakumeta haka da yammcin Allah wata'ala ta sauke Masa zallar rashin mutunci
duk da ba halinta bane, tana daga Kai sukayi arba dashi ya kafeta da idanunsa masu wani irin kaifi da
mugun kwarjini a cikin nata idanuwan Wanda a ganinta dashi na farko ya yamutsa duniyar ta
"Allaumma amin ya Rabb". suka fada su duka. Magunguna ya rubuta Mata na ulcer da tayi masa complain
na ciwon girji da gefen kafadar ta, sannan yayi Mata Allah ya sawaqe suka fita.
Har magariba su zahra suna gidan Baba malam, tun bayan fitar su malam ba dadewa Iya Abu ta koma daki
ta kwanta Zahra ta rufeta da wani qaton blanket barci Mai nauyi ya dauketa.
Nan falon suka zauna suna Dan tattaunawa da junansu, da tafiya zasuyi Majiba tace su zauna zuwa wani
lokacin tunda ansan suna Nan Dan lokacin da zasu shigo mujibar taga kaninta Mubarak tace ya fadawa
Mama suna gidan Baba malam.
Duk hirar da Mujiba ke yiwa Zahra Sam hankalinta baya tare da ita ta tafi duniyar tunanin abinda ya faru
dazu da Wanda aka Kira da Mahmud wai ita Zahra ce kwance a kirjin wani namijin daba muharraminta ba,
Kuma ba wani mataki data dauka Koda kuwa na kad'a Masa warning ne yanda gobe baze Kara marmarin
rungumar wata ba, Amma Wai sai gata ta b'ige da shakkar idanunsa abinda kaf tarihin rayuwar ta hakan
Bai taba faruwa da ita ba, ga wata faduwar gaba ta ba gaira ba dalili data sameta yanzu, ganin nan biyu da
tayi Masa duk Abu daya takeji a kansa.
Wani wawan tsakin Zahrar tayi Wanda ya tabbatarwa Mujiba Bata tare da ita duk zubar da takeyi kamar
'ya'yan kanya.
"Keda waye kike tsaki haka kuma?".
Majiba ta fada.
"Kedai kawai bari kawai ba komai. Ta fadar tare da you kwafa ta tashi tsaye tana fadin
"Tashi mu wuce gida tunda Naga wannan barcin na Iya Abu bana Kare bane, inaga har da allaurar barci
yayi Mata gaskiya".
A kofar gida suka yiwa malam sallama Yana ta Sanya musu Albarka.
Tun daga ranar Zahra Bata sake fita ba tana gida saidai lokaci-lokaci Mujiba na shigowa, a ranar data cika
sati daya Abbansu ya dawo murna ba'a maganarta gurin Zahra, duk da tana ganin shi a can syprus din idan
yaje Amma hakan bai Hana sun Kai wani lokaci ba suna tattaunawa irin ta d'a da mahaifi.
Saida Zahra tayi sati biyu sannan ta nufi Jos gurin Aunty Hasana.
Taji matukar dadin zuwanta Jos din. Dan har gidan Aunty Jana sukaje da Yara tunda lokacin da akayi bikin
Bata Nan. Duk inda ya kamata taje taje har gidansu Mama taje haka ta kaiwa jannifer ziyara lokacin sunyi
hutu tana karatu a Nan University ta Jos.
Maganar samari da gaske ta sakata side idan ka ganta tana magana Mai tsawo da namiji to ka tabbatar dan
uwanta ne ko wani Mai qirma a idanunta.
Satinta daya a Jos suka taho tare da aunty Hasanar da Yara Wanda a satin sukayi hutu, bayan dawowar ta
daga Jos ne su Hameeda sukazo hutun semester.
A lokacin ne Salma ta fito mata a mutum sak, ta nuna da gaske Bata yin zahra abinda yaso ya kawo b'araka
Mai girma kenan tsakanin Mama da Ammah Dan da gaske an Kai hakurin Ammar karshe, maganganu
Salmar ta ringa saki kamar lokutan baya, sai dai a wannan karon Zahrar ta nuna Mata jiya fa ba yau bace,
idan da tayi tolerating na nonsense din ta a yanzu Kam dai dai take da ita tunda Bata Jan girmanta a
gurinta, abinda ya Kara harzika Salmar lokacin da Zahra ta kalleta tayi tsaki tace "Wai wannan ce
mace,kina duba mirror Kuma kina ganin kanki kuwa?gara ni da har kike min gorin ana saka aurena ana
fasawa, Ina laifi tunda har ana ganina ana sona, kaddarar Babu mijina a cikin su ce take rabani dasu, kefa
ko Kare Bai taba zuwa yace Yana sonki ba, baga kanwarki Nan ba Ina cewa har anzo tambayar aurenta?
kije kiji da abinda ya dameki Zaki zauna kina fada da kanwar bayanki".
Tana Gama fada Mata maganar ta nufi hanyar ficewa daga dakin. Cikin fushi salmar tayo kan Zahrar ta
fardota baya saura kadan ta Fadi dai dai lokacin Kuma sahura ta shigo zatayi musu sharar yamma ta tarar
da wannan badakalar, da sauri ta shiga tsakanin tana Basu hakuri ta Kama salmar ta fita da ita daga dakin
tana faman zagin Zahrar abinda ya janyo hankalin Amma dake main kitchen din gidan tana yiwa Abba gas
meat saboda Yana sonsa sosai yawanci idan Yana gida kusan duk dare sai anyi Masa shi.
Da sauri ta fito tana tambayar "me yake faruwa ne?"
Sahura ce ta fada Mata abinda ta shiga ta gani tsakanin Zahra da salmar, juyawa kawai Ammah tayi ta
koma taci gaba da aikinta Bata Kara lekowa ba tanaji Mama ta fito tana fadan daman ai ba tun yau ba ta
fuskanci Zahra ta Raina Salma, Kuma komai runtsi dai Salma ai gidan ubanta ne Nan ba Mai hanata
sakewa.
Zahra ce ta fito zata wuce zuwa part din Ammah,har ta gota Mamar batace komai ba, Mamar tace.
"To fiqe kafi qaya tsini da Kika Samu guri kina yanda kikeso a gidan wallahi duk rintsi bazaki Kai matsayin
'ya'yan gida ba, tunda har abada ba'a canzawa tuwo suna"
Har zahra tayi kamar ta maida Mata martani sai taji bazata iya ba babba babba ne, kawai ta shige part
dinsu.
Har Mama ta juya taji maganar Ammah daga bayanta, dan harga Allah batasan Ammah ta fito main
kitchen din ba, Sam duk da tana jiyo kamshi ta dauka a can part dinta take aikin.
Bata juyo ba Amman ta tsaya.
Ammar tace
"Haba Mama ban zaci haka daga gareki ba wallahi, cewa nake da Zahra da su Hameeda dauka daya ne a
gurinki, ai saiki tambayi meya hada fadan?kiyi musu fadan gaba daya ba wai ki nuna Salma itace taki ba,
kina fadin maganganu irin haka ai na dauka ni duk binda lauje ya yayo a gidan Nan ya kamata ki dauke shi
ciyawa ne na gode amman ki sani Banda komai nufin Allah ne Zahra tafi karfin ace Mata 'yar karere tunda
Mai gidan ne da kansa ya karbo rikon lokacin da aka nemi tafiya da ita kema Kuma sheda ce kinsan su
waye kakanninta ba bakinki bane, dukiya idan ana gadonta kinsa Zahra 'yar mun gada ce, ko shi Wanda
kike takama da dukiyar tasa yasan tazarar da nisa a tsakaninsu da kakanninta idan kina tunanin karya ne
idan yazo ki tambaye shi ze Baki cikakken bayani".
Bata jira taji abinda mamar ke kokarin fada Mata ba tayi gaba abunta ta nufi part dinta.
Tun daga ranar Ammah ta daukewa Mama wuta gaisuwa kawai ke hada su, a kwana na biyu da Mama ta
karbi girki ta kasa hakuri ita abin yafi damunta ta fadawa Abban Ammah Bata Mata magana, yayi mamaki
matuka da gasken gaske Dan wannan shine karo na farko da irin haka ta faru da matan nasa duk tsawon
shekarunsu. Bai taba rabasu akan sun Sami matsala ba Koda wasa, dan haka ya Kira Ammah a waya yace
tazo part dinsa Yana son ganinta.
Batayi mamakin ganin Mama a zaune ba tasan za'a Rina tunda kaf tasan halin Mama na zahiri.
Gaishe da Abban tayi suka Kuma gaisa da Mama, tambayar ta Abban yayi ko akwai abinda ya hadasu da
Ammah ne?.
Ba wani kwana kwana ita Daman tun can baya Bata da munafurci ko kadan. Dan haka ba wani ta fadawa
Abban duk abinda ya faru tunda Saida ta tutsiye Zahrar akan ta fada Mata abinda ya hadasu da Salma da
kuma abinda mamar ta fada, shi kanshi Abban yayi mamakin abinda Salma tayi sosai, itama Mamar ya
nuna Mata kuskurenta na fadar wannan maganar ya Kara da cewa.
Ban tabi yiwa zahra kallon ba nine na haifeta ba, bil hasal ma shine dalilin da yasa ban aura Mata Daya
daga cikin 'ya'yana ba, ita kadaice ba uwa ba uba tun batasan inda kanta yake ba, mu ta sani a matsayin
iyaye sauran yaran Kuma 'yan uwanta. Idan na aura Mata wani a cikinsu ba zata Zama feel free tare da ni
ba, idan damuwa ta shiga ba Wanda zata fadawa kinga ai anyi adoh badan kyau ba".
" Haka ne suka fada.
"To karna Kara Jin makamanciyar irin wannan maganar, ba Wanda ze kawo min rarraba kan iyalin gidana.
Zahra 'ya tace kawai na saka sunan mahaifinta ne Dan haka shari'ar musulunci tazo dashi, badan in
nunawa duniya bani na haifeta ba, a kiyaye kodon gaba".
"In Sha Allah".
Suka fada.
Bayan tafiyar iyayen yasa suka turo yaran yayi musu fada sosai sanan ya Kare da nasiha.
Tun daga lokacin abubuwa na zahiri sukayi sauki sosai.
Kusancin Zahra da Hameeda ba abinda ya taba shi saima Kara shakuwa sukeyi a kullum suna Jin dadin
butun, Zahra suna waya sosai da Ummee da Mama Hanifa harma da uncle Haisam a wasu lokutan.
Lokacin da hutunsu ya kusa karewa duk sai Zahra ta nemi walwalarta ta rasa ko da yaushe kamar marar
lafiya ana saura kwana biyu ta tafi Ammah ta matsa Mata taje Kiran da Baba malam yake Mata, dan sau
kusan uku yana turo Yara tana cewa gata Nan Amman sai tayi burus da zancen.
Har dai ta Kai Ammah karshe tayi magana. Hameeda tace ta rakata suje tare, yau gurin malam din ba kowa
ba Kuma rumfar karatu tunda ranar basa karatu. Gurin ganawa da mutane suka sameshi su Habib suna ta
gyaran Shirin kantar littafai.
Da sallama suka shiga suka gaishe da malam din sannan suka gaishe dasu Habib, sai sukayi shiru.
Malam ne yace "Zahra'u Ashe lokacin komawar taki har yayi ko?"
Kara risinawa tayi tana fadin "eh lokacin yayi yayi Baba gobe zan tafi in Sha Allahu amma a Istanbul zan
tsaya sai wani satin zan wuce syprus din".
"Masha Allah. Allah ya taimaka, ki Kara hakuri akan lamuranki duk wani bawan Allah na kwarai sai Allah ya
jarabce shi Dan ya gwada imaninsa ki dauki abinda yake faruwa dake Daman haka Allah ya rubuta Miki taki
kaddarar kada ki yanke kauna daga Rahamar Ubangiji. Ga addu'oi nan da littatafan addu'a ki tafi dasu ki
ringa yinsu Kuma kada a shagala da ambaton Allah a duk inda aka Sami kai, Allah yayi Albarka ya bada
nasara ya kiyaye hanya".
"Allahumma Amin suka fada a tare".
Habib malam ya yiwa magana ya Miko ledar da aka saka sakon nata, Hameeda ta karba suka Kara yiwa
malam godiya suka fito suka shiga cikin gidansa Zahra ta Kara duba jikin iya Abun ta Kuma yi Mata sallama.
Basu koma gida ba, gidan su mujiba suka shiga Bata Nan ma sai Maman ta suka barwa sallahun tafiyar
zahrar suka nufo gida, sunzo dai dai masallacin gidansu ne sukaga Ya Abdul Hakeem da Dodon Zahrar a
zauna a kan carpet karami a gefen masallacin suna hira Kai da gani da kyakykyawar alaqa a tsakanin su.
Gaishesu sukayi suka wuce, Hameeda ce ta kalli Zahra tana fadin "Kinga wancen Guy din yanda Salma ta
mutu kansa ba magana! lokacin data Fara ganinsa munzo hutu wallahi kamar zata zauce akansa sai da
Mama ta taka Mata burki taci Mata mutunci akan ta rasa Wanda zata so sai Almajira Wanda ba'a San
asalinsa ba, duk yanda taso ta nunawa mamar wannan da banbancin da irin Wanda ta sani amma Sam taki
fahimta Dan har so tayi tayi Mata duka tana fadin Dan lalacewa ta rasa Wanda zataso sai fakiri Mai
allaziwahidin Dan salon Abba yaji ya Goya Mata baya tunda Wai ance sune suka kawo shi garin bandai San
kan labarin ba gaskiya". Ita dai Zahra Bata tofa tataba daga uhm sai umh umu uhm, har suka karasa gida.
A Daren sun raba dare suna Hira da Ammah a Nan ta dunga yi Mata magiyar ta daure taje gurinta ko zuwa
karshen shekara ne ta ganota ba ta tura Mata Ya Abdul Hakeem ba.
Karfe shida Mai kyau sun dauki hanyar Kano ita da Ya Abdul Hakeem da Hameeda da magaji.
Nan suka zauna da zahra suna ta Hira kafin lokacin tashin su yayi, in da wani Abu da ya damu Zahra a gurin
Bai wuce kallon da wani matashi ya kureta da Shi ba, duk inda zata dago Kai sai sun hada Ido dashi, Sam ya
hanata sakat da idanunsa idan ba idanunta kemata gizo ba har wani lumshe ido yake da wani kankance su.
A haka har lokaci ya cika aka Fara shiga jirgin hand bag ce kawai a hannun Zahra tunda kayan an tafi dasu
tun zuwansu lokacin da ta juya ta Fara tafiya ba zato taji hawaye a idanunta abinda ta dunga kokarin kar
tayi kenan tun daga gida lokacin da Auta Musaddiq ya fasa Kuka da suka taso Amma sai gashi ta kasa
jurewa itama Saida suka zubu, juyawa tayi kadan lokacin da zata hau steps din sai taga Ya Abdul Hakeem ya
Kama hannun Hameeda sun juya sun Fara tafiya tana share hawaye da dayan hannun itama ta juyo hannu
Zahra ta dago Mata alamar bye sannan ta Haye zuwa ciki.
Kusa da wata Mata ta zauna da alamar kamar zatayi sa'ar Ammah, ta gaisheta.
Saida jirgin ze tashi ne taji na gefenta Yana fadin "duk tunanin gidan ne ya hanaki jin sanarwar a daura belt
da ake ne?" Ya fada in a soft voice. Dago Kai tayi ta dubi Mai maganar dake gefenta, wannan Wanda ya
dameta da kallo ne kafin su shigo, ita Sam batama San sanda ya zauna kusa da ita ba.
"Nagode" ta fadawa tana saka belt din lokacin da jirgin yayi balance a sama ne ta cire belt din ta bude
computer dake jikin kujerar dake gabanta tana kallon location din da Suke bi tun tana Gane garuruwan
data sani ko take jin sunansu har aka shigo Wanda sai dai ta karanta kawai. Jefi jefi suna Dan magana da
matar dake kusa da ita. Nan kusa da ita dai Bata Kara kallonsa ba tunda taga shi kallon mutane kamar
dabi'arsa ne.
Sanyi kamar tafiyar awa daya taji yana Mata magana da farko yi tayi kamar bataji ba, Saida matar dake
kusa da ita tace "bakyaji ba ana Miki magana, ko kina da aurene?".
Kai ta girgaiza alamar A'a.
"To meyasa kina Jin Yana Miki magana Kika kyale shi? ba Dadi irin haka baka wulakanta mutum ba kasan
gaba abinda Allah zeyi ba kinji".
A hankali take Mata maganar yanda ita kadai zata iya ji.
Bangaren Zahrar kuwa kusan Kullum suna tare da Musbahun a waya Dan har ya haddace lokacin agogon
kasar, tun tana daridari har ta sallama tare da karfafawar su Sajida kafin su gama semester din sun shaku
dashi sosai Bata rufe Masa matsalar data fuskanta a baya ba, nuna Mata ma yayi rabonsa ne ya kawo aka
ringa samun akasin na bayan ya Kuma yi Mata Alkawarin ruwa da iska ba abunda ze girgaiza tarensu bare
har akai ga rabuwa Koda kuwa Aljani ne ya aurata in sha Allah sai yaga bayansa, yayi Mata alkawura da
dama ya nuna Mata Babu wani abu da ze girgaiza shi koya bashi tsoro akan lamarin aurenta.
Magana tayi nisa Dan har iyaye sun shiga abinda yayiwa Ammah Dadi kenan Dan wannan karon Kam Zahra
tayi Dace da Dan manyan mutane sosai, dan basu bar garin ba Saida suka shaida lokacin aure idan ta gama
service da wata daya duk da sunso ayi bikin kafin tayi service din sai Alhajin ya nuna musu suyi hakuri tayi
idan ta gama saita zauna guri daya ba daga kaita ba ba dadewa ta Fara fita kullum, Kuma ya Hana kayan
lefe Dan Alkawari yayi ankawo biyu an karbe to kuwa ko waye zata aura sai dai ya aje Mata kayan idan taje
gidan ya Bata.
Lokacin dasu Zahra suka Gama karatunsu har da Ammah da Hameeda akaje bikin graduation dinsu
mutanen Jordan ma sunje har Mama Hanifa.
Bayan kammala taron sun Kara kwanaki a kasar, Zahra ta raka Hameeda kuraren shakatawa da yawa tayi
kallo tayi santin inama Abba ya dawo dasu Nan Suma gashi ita har ta Gama Amma su Kullum karatunsu ba
cigaba ana faman strike tunda a yanzu ma shine ya dawo dasu gida har ta samu damar zuwa itama.
Ranar da zasu taho sun Sha kukan rabuwa dasu Sajida tunda su saura shekara daya su gama.
Murna gurin Zahra ba magana ji take kamar ta sauke wani abu Mai nauyi daga kanta.
Musbahu yaso zuwa graduation dinsu Zahrar Amma lokacin Yana busy yaje wani special assignment a
Kenya dole sai hakuri yayi, Amma Yana dawowa ya yiwa Azare dirar mikiya a ranar Zahra taga zallar so a
gurinsa Dan ji yake kamar ya dauke ta yayi gaba da ita, itama ta bashi kulawa kamar me,Hameeda tazo sun
gaisa sun Dade suna Hira dashi tambakar sun shekara da sanin juna, sunan mujiba ma ta shigo suka gaisa
ba shi yabar Azare ba sai kusan magariba Dan ma Zahrar nata Masa magiyar ya tafi saboda rashin tsaro irin
na kasar.
Tun daga lokacin hanya ta aure shi tsakanin kano da Azare. Mushahu na mutane ne kusan duk Wanda ya
kwana ya tashi a Nan kukkuken unguwarsu Zahra yasa shi Koda kuwa ba gaisawa suke ba, wata kila ya taba
yiwa wani alheri a cikin yaran gidanku Dan da gaske hannunsa a sake yake gurin Alkhairi.
Sunyi sabo sosai da jama'a a Nan har gurin malam Bukar Yana zuwa sauda dama idan ya shigo garin, wasu
ma daga cikin samarin gidan malam din sunyi sabo sosai.
Lokacin da results dinsu Zahra ya fita Sam bataje ba Auncle Haisam ne yayi Mata komai Allah ya taimakeka
ta fito da first class degree a akan anatomy.
Allah ya taikata da taimakon Ya Hassan aka kawota bauchi service, bayan zaman camp sukayi posting dinta
Dr Sulaiman Adamu memorial college of Hygiene and Environmental health science Azare.
Ammah taji dadin hakan sosai haka shima Mushahun yaso hakan kwarai da gaske.
Zahrar najin dadin aikin sosai da sosai domin teaching Yana cikin hobbies dinta.
Bayan sun Gama ne da wata daya kamar yanda akayi Alkawari aka Fara kokarin Fara shidimar bikin ta dai
dai lokacin Kuma akayiwa su Ummee rasuwa a saudiyya abinda ya Hana su zuwa kenan da har Ammah
tace a daga bikin tunda rasuwar ta jikinsu ce kanin Baban Ummeen ne ya rasu,Amman sai sukace Dan me
ayi idan komai ya lafa zasuzo suga daki kawaii.
A satin da za'a Fara bikin kusan Kullum Mushahu da Abokansa shakikai su Deeni da Aliyu Wanda Suke
cussings suke ta zirga-zirgar ganin abubuwa sunyi yanda ake so duk wasu programs a nan za'ayi dinner ce
kawai zasuyi a Kano, sun Kama dakuna uku a hotel idan zasu zauna har zuwa Daurin aure.
Saura kwana biyar Daurin auren ne wani abun al'ajabi ya faru da Hajiya Nafisa Maman Mushahu wadda
suke Kira da Ammi.
Cikin dare tana barci ta farka a matukar razane saboda wani mugun mafarkin da tayi da Musbahun akan
auren, addu'a tayi ta koma ta kwanta ai kamar jira ake barcin ya dauketa sai abunda ta gani a wannan
mafarkin yafi wancen muni, wasa-wasa barci ya gagareta a wannan Daren kafin safe duk ta wani hargize ga
wasu irin tunane tunane sun cika Mata zuciya na rashin kwanciyar hankali kafin yamma gaba daya ta Zama
wata marar nutsuwa ba shiri ta Nemo kanwarta Aunty Jamila a waya Nan da Nan tazo tunda ba aure
gareta ba, duk ta kwashe komai ta fada Mata akan Bata son auren Musbahun kwata kwata ita fa ko a cikin
ranta ta tuna da zeyi aure ji take kamar zata zauce, da farko Aunty Jamilar ta dauki abun Wasa Amma ganin
da gaske abin yake yasa ta Kira Babban yayansu Alhaji sulaiman da kanin Baban su Musbahun Alhaji
isma'il, Suma da farko sunyi zaton na Wasa ne Amma da suka matsa akan ta Fadi dalilinta na Hana
yuwuwar auren sai abun ya ta'azzara ya Zama kamar Mai tabin hankali, ganin abun Yana neman ya Zama
wani iri ne yasa Alhaji sulaiman ya kirawo Aliyu tare da tambayar suna ina?.
Aliyun yace gasu Nan a hanya sunje Azare ne Amma har sun wuce wudil sun kusa kano ya fada Masa lallai
direct su nufo sokoto road su duka.
Haka suka shigo suka tarar da wannan dambarwar ana ta fama da Ammi.
Ai tana arba da Mushahu ta Kara tuburewa tana fama fadar wallahi matukar ya kafe sai auri Zahra Bata
yafe Masa nononta da yasha.
Su dai Basu ankara ba sai ganin Mushahu sukayi ya sulale ya zube a sume, da sauri Aliyu ya kawo ruwa aka
zuba Masa Amma a banza ganin haka yasa suka nufi Asibitin Nasarawa dashi. Haka aka dunga juyawa da
Ammi Amma ta kafe kamar kafiran farko duk Wanda ake tunanin ze kawo gyara a lamarin an fada Masa
Kuma yayi bakin iyawarsa Amma ba wani ci gaba da aka nemi a Zafafa sai lamarin yaso ya koma Mata tabin
hankali abinda daya tada hankalin Babarsu kenan Hajiya Yaya tace dole a hakura da auren tunda abin yazo
da irin wannan lamarin marar Dadi daman tun farko ita bataso lamarin ba sai dai yaran yanzu ne baka
hanasu abinda suke so, tunda Daman fa ance shine na uku a Wanda zasu auri yarinyar ana fasawa to shima
gashi tun ba'aje ko Ina ba lamarin ya Zama haka.
Tashin hankali iya tashin hankali Musbahu ya shiga Dan dakyar aka Sami nutsuwarsa dan kwata kwata ya
daina magana da kowa ya rufe duka wayoyinsa shima Deeni ganin kiran Zahra yasa ya rufe layin da suke
wayar da ita, Aliyu ne kawai Bai rufe wayar ba Amma baya picking idan ta Kira a halin hake ne su Alhaji
sulaiman sukaje Azaren da labari marar Dadi Wanda ya kawo karshen 'yar Wala walar da akeyi da Zahra
akan aure ta kawo karshen duk wani makirci da bita da kulli da ake Mata na rushe aurenta idan ya taso
abinda ya girgaiza duniyar Wanda suke fake suna tsula ta'addanci ta karkashin kasa.
✨
✨
✨
✨
MAMAN FATIMAH
Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu. Dan Allah ayi hakuri da matsalar da aka samu
gurin turo page fourteen sau biyu hakan ya faru ne saboda wasu dalilai Amma na karshen Wanda na turo
shine cikakken fourteen din yanzu kuma na hade fifteen & sixteen guri daya na gode.
Page
Fifteen
&
Sixteen
BACK TO STORY.
________ Gurin Zahra su Sajida suka shiga tana kwance a gado idanunta a rufe tayi zurfi cikin tunanin,
Sam bataji shigowar su Sajida ba Saida mujiba ta Dan zungure ta bude ido ta yunkura ta tashi zaune tana
dafe kanta dake Sara Mata.
Sajida ce ta zauna kusa da ita ta Kama hannun Zahrar tana fadin "bestie Dan Allah ki rage tunani kada
wani ciwon ya kamaki, ki yawaita addu'a komai yayi zafi maganinsa Allah. Kuma wani hanin ga Allah baiwa
ne, ke kanki Baki taba tunanin abun ze Zama haka ba, Kuma Allah ya juya lamarin yanda yaso, to saiki gode
Masa bisa ni'imar da yayi miki, Kuma nifa mujiba Ina doubting akan wannan da aka daura musu aure,
Kuma ki rubuta ki aje zakice na fada Miki kije kiga gidan da za'a Kai bestie, Kuma ki duba kiga irin kayan da
aka kawo yanzu kinsan duk Wanda ya hadasu first class ne a gurin gayu wallahi komai bana banza Amma
Kuma Wai almajiran malam ne gaskiya I doubt much".
Ta fada tana kallon mujibar.
Ita dai Zahra ta rasa inda zata Kama komai ya kwance Mata, su damuwarsu kaya da gida, ita Kuma tata
damuwar ta yanda za'ayi zaman ne, har yanzu gani take kamar a mafarki Wai wannan karon ma Saida aka
samu akasi,ta rasa daga Ina matsalar take, shi kuma auren da aka daura meye ze biyo baya tasan idan ba
wani nufi ba na Allah shima sai an Sami wani kalubalen a cikinsa.
A hankali ta furta "Ya Salam! Allah ka shiga cikin lamarina, wallahi bestie komai ya kwance min bani da
sauran dabara,kwakwalwata ta daina aiki yanda ya kamata kinsan Allah nifa kamar ma tsoronsa nakiyi Dan
tunda na Fara ganinsa naji wani irin Abu a jikina wanda ban tabaji ba a kan ko wane namiji sai shi, Kuma
yayi min abinda ya kamata na dauki mataki Mai karfi amman wallahi ko magana kasayi Masa nayi, yanzu
kuma a haka zan rayu dashi? Ni wallahi bana sonsa Sam Kuma fa Shima yace baya son abin yake ba kawai
dai baze iya watsawa su Abba kasa a ido bane". Ta karasa fada hawaye na zubo Mata a fauska.
Lallashinta sukayi da kyar tayi shiru kafin mujiba tace "haba Zahrar ki daina kuka idan kina daga hankalin
ki na Ammah ma baze kwanta ba, Kinga irin haka ba Dadi duk da an aura miki Wanda babu soyayya da
shakuwa a tsaninku, ita a hakan ma yayi Mata da ace wannan karon ma an fasa aure gara hakan tunda
naga alama da ita ake fadan ke kin ratso ne kawai ake fakewa da lamarin ki Dan a Hana duniyar ta zaman
lafiya da kwanciyar hànkali, Kuma Baki san dalilin da yasa Abba yayi hakan ba, kinsan dai Abba baze taba
aura Miki baragurbi ba kedai kiyi ta addu'a muma muna tayaki, Bari na tambaye ki Mana idan kina addu'a
bakya cewa Allah ya Baki miji na gari?"
Hannu tasa tana share guntun hayenta kafin ta harari mujibar tana fadin "Ina yi Mana kuma kawai saina
yi sallah na kasa wannan addu'ar dan na Zama abinda na zama ko?"
"A'a ba haka nake nufi ba bayani zan miki shi yasa nayi Miki tambayar dai, Allah ya huci zuciyar Amarya".
"Kina jina mu 'yan adam muna rokon Allah ya zaba mana abinda yafi Mana Alkhairi Amma wani lokacin
inda kake zaton alherin ne to sai kaga ba'a Nan yake ba, idan yazo ta inda baka zata ba tunda bakasan
gaibu ba, sai kayi watsi dashi idan bakayi sa'a ba haka abun ze kwaranye baka mori komai ba, alhalin Kai ka
roka aka baka sai kuma ka Raina abinda aka baka ba tare da kasan shine alherin ba. To Dan haka nake so ki
yiwa Allah da manzonsa ki rike abinda Allah ya Baki tunda shi Kika roka Kuma ga abinda ya Baki sai kiyi ta
Tahamidi ga Allah kawai, ki nemi Allah ya saka muku kaunar junanku da soyayya da jinkai. Dan kinsan dai
idan ba wata kaddarar Ubangiji ba Babu abinda zesa ya rabu dake tunda ya karbi auren Nan wallahi ko
rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba yana so, dan haka ki daure kiyi Masa biyayya shi arziki nufin Allah ne, naji
ana ta 'yan kananun magamganu ki toshe kunnenki kada ki bada barakar da wani ze kushe Miki miji dan
bashi da kudi, Allah ne Mai azurtawa lokacin daya so sai kiga wata Rana sai dai a tada labarin abun".
Sun Dade suna kawo Mata misalai da yawa na irin wannan auren nata daga baya Kuma ya Zama Alkhairi.
********** A matukar gajiye Mahmud ya shigo cikin gidan misalin karfe biyar na yamma tun safe ya kebe
kansa a dakin daya Kama na hotel yake ta faman aiki yaso kwarai ya Gama da wuri kafin yamma amma
abun ya gagara Dan da gaske aikin ya dauki hankalinsa sosai ga tafiyar dake gabansa Banda Allah yasa wasu
abubuwan sun daidaita a jiya da dole tsakanin gobe da jibi dole yabar garin ko baya so. Amma cikin
taimakon Ubangiji sai komai ya Fara daidaita, shi kanshi Yana Jin idan ya tsallake ya tafi daidaita wanna
gabar Bai kyauta ba Sam, dan jama'a zasuga kamar ya gujewa auren gatan da akayi Masa ne ya watsa
musu kasa a idon an Masa gata irin wannan sun dauki yarinyar su Mai tsada sun bashi ba tare da sun San
ko waye shi ba, ko la'akari da karancin samunsa suka aura Masa.
Su Habib ya tarar a falon Yana karatun Alqur'ani, Abubakar Kuma Yana ta faman hada Nile sat.
Su duka suka amsa Masa sallamar Nan falon ya aje jakar laptop dinsa abinda bai taba kwatanta zuwa da ita
ba kenan Dan duk aikin da zeyi sai dai yayi acan hotel din ya barota, amma yau dole tasa ya taho da ita nan
saboda so yake ya raba dare Yana aiki shi yasa ma Kai tsaye ya nufo gidan da ita yasan bashi da matsala
dasu duka biyun.
Abubakar ne ya tsaya da aikin Yana kallon Mahmud Yana fadin "Dan Allah Ina ka shiga Wai bakasan kana
dagawa Baba malam hankali ba? shifa yafi son daya juya ya ganka, gashi ka Kama ka rufe wayar ana ta Kira
a rufe".
Girarsa ta daman ya dan shafa kadan kafin ya zauna Yana fadin "cool down Mana my man Ina kake tunanin
zan tafi? Wallahi aikine yayi yawa na wannan NGOs din bakaga har kayan aiki suka bani ba tun zuwan da
sukayi wancan karon, yanzu haka ana koya min yanda zanyi amfani da ita laptop din ne yanda zanji dadin
aikin, Bari nayi wanka sai muje gurin Baba malam din nayi Masa bayani yanda ze fashimta, sunce ma nan
da sati daya ko biyu zasu kiramu zuwa babban taro da za'ayi".
Tunda ya Fara magana Habib ya dakata da karatun da yakeyi yana bin Mahmud da kallo haka nan kawai
yaji Kamar ba gaskiya Mahmud din ya fada musu ba, Kamar yana boye wani Abu, shifa tun lokacin daurin
aurensa ya lura da yanda Kamar yake baiwa Sameer umarni a wasu lokutan sai idan ya farga ne yakan yi
maza ya canza taku, sannan a watannin baya ya taba jin yana waya a kusa da dakin da suke taron abinda ya
shafi makaranta lokacin yana duba wasu sabbin forms da aka kawo na Enterprinuership da za'ay a gurin
Sam baisan Yana ciki ba tunda kofar a rufe take ji yayi sosai Yana bada umarnin yanda abin ze kasance
harda makudan kudin da za'a kashe gurin sawo kayan sana'ar da za'a koyar harda kudin da za'a
participants din tunda program din harda matasan unguwa a cikinsa duk za'a Kuma bada kayan sana'ar da
mutum ya koya kyauta, tun lokaci yayi masa alamar tambaya sai dai ba wata kafa daya Bari wadda za'a
fashimci komai. Bai tabbatar da abinda yaji ba Saida akayi komai Kamar yanda ya bada umarnin, ga Kuma
lokuta yawa sai yayi batan dabo ka nemeshi ka rasa Kuma har yanzu baisan takamaiamai Ina yake zuwa ba
duk kuwa iya kwakwarsa.
Jakar ya dauka yayi gaba Yana fadin Bari na Dan watsa ruwa na fito. Da ido suka bishi har ya shige corridor
din daze kaishi bedroom dinsu,kowa Yana ayyana wani Abu a zuciyarsa.
Ya dauki Kamar minti hamsin kafin ya fito cikin Riga da wando na shadda Fara tas, a gaggauce ya fito ganin
lokacin sallar magriba ya kawo jiki.
***
Da dare Zahra tana dakin Ammah suna Hira da Inna maimuna tana Kara nusar da ita yanayin rayuwa Sajida
ta shigo da waya a kunnenta ta gaishe da innar ta Mikawa Zahra wayar tana fadin "Baffan Rimi ne yake son
magana dake"
Amsa tayi tare da sallama, cikin daki Inna ta nuna Mata da hannu ma'ana ta shiga ciki tayi wayar, Dan
sajidar tana Mika Mata ta juya ta koma, haka Nan ta tashi duk da Bata San nufin innar na hanata waya a
falon ba.
Gaishe da Baffan tayi tunda Daman ya Santa tun suna makarantar kazaure sunje masa ita da Sajida
lokacin da Zahrar ta zauna a kano gidansu sajidar sanda akayi musu hutun midtrem break maimakon taje
Azare sai umman sajidar ta nemi Alfarmar Ammah ta barta tayi hutun a gurinta,to kafin su koma ne sukaje
Rimin sumailar gurin kakan sajidar, tun lokacin ya baiwa Zahra magunguna sosai yace tayi amfani dasu har
Sajida na mita ita Bai Bata irin na Zahra ba, a lokacin murmushinsu manya yayi Yana fadin "yanda aka saka
rayuwarta a gaba ke ba Wanda ya damu da taki rayuwar ita akwai tarnaki Mai yawa a kanta Kuma Naga
jikin nata ba wani abun azo a gani na tsarin jiki.
Gaisuwar Baffa ya amsa Yana fadin "Ashe haka lamura sukayita faruwa ko Fadima? Dazu Babar taku tazo
min da bayanin abinda ya ringa faruwa dake akan aurenki, yanzu haka tana Nan zata kwana saboda akwai
abinda nasa ayi Miki gobe in sha Allah zatazo Miki dasu da yanda zakiyi amfani dasu in sha Allah ba abinda
ze Kara faruwa dake, lallai akwai shedancin mutane akan lamarin Amma mu dauka Daman haka Allah yayi
nufi, wanin Allah Bai Isa yayi maka komai ba face da izinin Ubangiji, ga Uwar taki ku gaisa".
Ya mikawa Maman Sajida wayar.
Bayan ta gaisheta ta Kara da yi Mata nasiha sosai itama, sannan ta fada mata gobe in Sha Allah daga Rimin
Nan zasuyo ita da Babban danta Wanda some times shine direban ta idan zatayi doguwar tafiya, kafin
sukayi sallama.
Dakin Ammah Zahra ta shiga ta fada Mata yanda sukayi da kakan Sajida, godiya sosai Ammah ta ringa yi
tana Kara jinjina kaunar da bayin Allah nan.suke yiwa Zahra dalilin 'yarsu gashi saboda matsalar Zahrar zata
taso tazo har Azare.
Washe gari tunda wuri Zahra da Sajida suka Gama gyaran dakin Ammah sukayi wanka sannan sukayi
breakfast gurin karfe Sha daya Maman su Sajida da yayanta Ya Abba suka karaso murna gurin Sajida ba
magana, dakin Ammah suka nufa da Maman Zahra tasonsu Fara shiga gurin Mama su gaisa Amma Sajida
ta Hana tana fadin "A'a ki Bari mu shiga inda ya kamata idan min Gama abinda ya kawo ta sun gaisa da
kowa so kike azo a zaune Mana a hana ruwa gudu".
Tarba ta girma Ammah tayiwa Maman Sajida itama ba wata babba bace Dan Bata Kai sa'ar Ammah ba, an
sauki Ya Abba a dakin da suke sauke bakinsu yayin da magaji ya shiga shidima dashi.
Bayan Maman su sajidar ta Gama cin abubuwan da aka kawo Mata suka sake gaisawa dasu Ammah da
Inna maimuna ta jajantawa Ammar abubuwan da suka ringa faruwa, ta Kuma Dora musu da bayanin da
mahaifinta yayi Mata akan matsalar Zahrar inda ya bada tabbacin ko waye yake wannan shegantakar a
kusa dasu yake sosai, Kuma dashi ake faduwa da tashi, kuma yace kada Wanda ya kawo wani Abu da
sunan naci kona Sha yace a baiwa Zahra da sunan tsarin jiki ko na gyaran aure a barta taci sannan a kula da
Koda abincin cikin gidan ne in dai ba ita Ammar ta dafa da hannunta ta Bata ba daga Nan har tabar gidan.
Wata babbar leda ta dauko wadda sukazo da ita ta bude ta Ciro jarka da ruwa a cikin Mai kalar yellow na
za'afaran ta dauko wani garin magani Mai laushi ta hadasu da jarkar ta mikawa Inna maimuna tana fadar.
"Ga wanna ruwan addu'a ne da garin magarya zata dibi ruwan addu'ar ta zuba garin magaryar ta Sha ta
shafe jikinta safe da yamma,wannan Kuma kafa da hannu kawai zata Riga turarawa sai Addu'oi da ya bada
a Bata zata ringa karantawa safe da yamma".
Godiya sosai su Ammah suka shiga jerawa Maman Sajida Kamar ba gobe har sai da ta ringa fadin "Haba
Hajiya meye amfanin taren abinda ya shafi Zahra ai ya shafi sajida wallahi shekaranjiya data Kira ta fada
min hankalina ba karamin tashi yayi ba wallahi na dauka abin ya kwaranye tunda an dauki dogon lokaci
kafin a Kara maganar Auren".
"Wallahi kuwa muma mun dauka na bayan da aka fasa ko matsalar namijin Aljani ne ya aureta Amma duk
inda akaje da ita sai a ce ba wani iska a jikinta".
Inna maimuna ta fada.
Sun tattauna sosai da Maman Sajida Saida akayi sallar Azahar Sajida ta raka mamanta dakin Mama su
gaisa, sun Sami kawar Mama Asabe sun hada Kai suna kus-kus bazaka taba cewa da mutane ba.
Sun gaisa sajida ta fadawa Mama mamanta ce, Basu jima ba suka fito Mama ta biyosu har kofar part dinta
Nan godiyar ziyarar.
Sai kusan karfe uku su Maman Sajida suka juya Kano Sajida tace ita saita raka Zahra gidanta zata dawo.
Tun da Mahmud ya Kira Zahra sau daya Bai sake kiranta ba, yau yaji ya kamata ya Kira yaji lafiyar ta ko
banza fa yanzu tana karkashin ikonsa ne cinta da Shanta da duk lamuranta suna wuyans Kuma ai Bai
kyauta ba gaskiya ace yayi burus da lamarin ta abun sai yayi Mata yawa.
Sai gurin Tara na dare ya lalubo numbarta ya Kira, harta gama ringing ba'a dauka ba sai kawai ya share ya
tura Mata text massage ya fada Mata Daman ya kirane yaji lafiyar ta.
Tun bayan tafiyar Maman Sajida Ammah da Inna maimuna suka shiga hasashen abinda kakan Sajida ya
fada na hasashen Mai yiwa Zahra bita da Killin nan duk iya nazarain su Basu gano ba sai suka.barwa Allah
amma dai innar ta soke kwanan Zahra a can gurinsu tace su dawo dayan bedroom din Ammah suna wanna
ita da Sajida da ita innar ya ishesu ita ko katifa sai a saka Mata a kasa ta kwanta.
Hakan akayi su Zahrar suka tattaro suka duk wani Abu na amfaninsu suka dawo dakin.
Kafin su kwanta Saida Inna maimuna ta saka Zahra tayi amfani da duk magungunan da Maman Sajida ta
kawo Mata, wanna ne dalilin dayasa innar tace su dawo nan tunda komai na duniya Yana son sirri, duk da
Hameeda ce kawai ke kwana a tare dasu Zahra Dan Salma tunda suka dawo ma Bata taba kwana a part din
nasu ba.
Tun Hameeda na jiransu Zahra su shigo har tayi barci.
Saida Zahra ta Gama amfani da duk abubuwan da aka kawo Mata sannan ta dauko wayarta rabon data
dauko ta tun bayan sallar Azahar data hau online ta duba sakonnin whatapps.
Sajida da Inna maimuna Kuma sunta hirar duniya abunsu.
Missed calls ta gani har hudu uku na mujiba ne sai Kuma wani daya number ce amma kallo daya tayi Mata
ta gane ta waye, ji tayi gabanta ya fadi to neman me yake Mata da wanna tsohon Daren haka kawai ya
dagula Mata sauran lissafinta. Fita tayi daga call history din sai Kuma taga envelope alama massage ya
shigo budewa tayi sakonsa ta gani a hankali ta furta ta "Ya salam".
Allah da gaske fa take jin wani irin lamari a tare da shi.
Da safe ma innar ta saka Zahrar gaba Saida tayi duk abinda ya kamata kafin ta fice tabar dakin dan tun
kafin ta Fara Sajida tayi waje ta Basu guri. Saida tayi wanka kafin ta fito yin break bayan sun gama ne
Ammah tace Zahra taje Abbansu na kira, gyalen rigar ta yafa a kanta ta nufi gurin Abban, lokacin data shiga
ya Gama break Shima, guri ta Sami ta zauna kusa da kujerar da yake Kai tana fadin "Abbana Ina kwana?"
Jaridar dake hannunsa ya aje Yana fadin "lafiya kalau uwata, Ina fatan ba wata damuwa ko?"
Kai ta gyada kafin tace "ba komai"
"Masha Allah ya fada.
Kafin yayi gyaran murya ya Fara fadin "Uwa inaga in sha Allahu jibi da yamma Zaki tafi gidanki Dan dazu ne
malam Bukar ya roki wannan alfarmar saboda shi Mahmud din ne zeje wani taron da kunyar da suke aiki
dashi suka shirya to Kuma yace baya son ya tafi Baki tare acan gidan ba kada abin ya Zama na magana ace
ko ya gudu ne ya barki a nan, to Nima din na karbi nasa hanzarin tunda Masha Allah jikin naki yayi sauki
sosai Kuma Baki bani kunya ba kin kwantar da hankalinki".
"To Abba"abinda ta fada kenan tayi shiru, Mamace ta shigo dakin itama Tasha wanka sai baza kanshi take
Kamar Kullum. Da barkwwnci ta shigo tana fadin "A'a bamu Gane ba, irin wannan kebewa tsakanin 'ya da
uba mu ba'a neman ayi shawara damu".
Ta fada tana fadada murmushinta.
Gaisheta Zahra tayi kafin mamar ta gaisheta da Abban tunda ba itace da girki ba.
Bayan sun gaisa ne yake fadawa mamar "Ba wani shawara muke ba wadda Bata shafeku ba Ina fada Mata
ne jibi in Sha Allah zata tafi dakinta tinda Allah yasa ta warrare Kuma shi mijin nata ne zeyi tafiya shi yasa
nake son ta tafi dakinta".
Nisawa Mama tayi kafin tayi magana.
"Kamar Yaya zeyi tafiya daga Kai masa yarinya basai ya tafi da ita ba salon ya cuci yar mutane ya lallaba ya
budu ya barta tunda tsintacciyar mage ai Bata mage, gaskiya Abban Yara ka tsaya ka duba lamarin nan
Mana kada fa azo ana Dana sani kaga masu iya magana na cewa keyace".
Abban ne yace "ba abinda ze faru sai Alkhairi Amma Jibi da izinin Allah uwata zata tafi dakinta, tashi kije
Uwata Allah yayi Miki Albarka yanda Kika yi min biyayya Ubangiji ya Baki 'ya 'yan da zasu yi Miki biyayya
kema".
A zuciyarta ta amsa da "Amin"
Saida Abbai yaga ta fice gaba daya sannan ya dawo da dubansa gurin Mama yace "haba Rabi'a har yaushe
Zaki dinga magama irin wannan a gaban kankanuwar yarinya Kamar Zahra ai Bai kamata ba ki duba kiga
yanda aka dunga walagigi akan auren yarinyar nan a baya yanzu Kuma anyi aure Zaki ringa fito da
maganganun da zasu iya sakata a wani Hali ai kwantar da hankali uwata take bukata ba irin haka ba, mu
bita da addu'a in sha Allahu Alkhairi na hada Wanda a gaba duka sai sun gode min koda kuwa bana duniyar
ne".
Tunda Zahra ta shigo ta kwanta a kan sofa a nan falon Ammah na kallonta tasan kan zance dan tunda Abba
ya dawo daga masallaci ya fada Mata, zancen da suke da Inna ma kenan ta shigo suka bar zancen.
Da hantsin Ammah ta Kira Aunty Hasana ta fada mata.
Zuwa Sha biyu tana gidan suna zaune a falon Ammah Mama ta shigo ita da kawarta ta amana Asabe
wadda kwanan Nan ta mayar da gidan gurin zuwanta sabanin baya da sai a share watanni Bata zoba, Nan
suka zauna akaci gaba da tattaunawa akan tarewar Zahra har Asabe ke fadin zata saka wata 'yar gusau da
suke makwaftaka ta yiwa Zahra hadin kazar amare da daka shine nata Gudunmawar.
Da yamma Aunty Hasana ta umarci Sajida da Hameeda da zilai Mai aiki suzo suje gidan Zahrar a gyara
abinda ya kamata tunda jeren ya dan jima da yi.
Sun fito zasu tafi ne Abdul Hakeem ya tsayar da Auntyn Yana fadin "sai Ina Kuma Aunty mu?"
"Gidan Zahra zamuje a Dan Kara gyarawa jibi Abba yace za'a kaita kaga kuwa ai dole a shiga a duba ayi
abinda ya kamata".
Komai tsab suka sameshi da gani ana gyarawa Kullum dan har wani hadaddan kamshin freshner ke tashi a
falon haka bedroom din Shima komai neat yake a toilet ne abin ya bawa Aunty Hasana mamaki an zuba
kayan wanka masu azabar tsaba Bata Kara tsinkewa da ta janyo locker ta jikin mirror taga wasu designers
din turaruka na Mata Kuma da yawa na kamfanin Al -haramain ne harda irin Wanda Zahra take amfani
dasu.
Ita dai Hameeda Yar kauye ta Zama a gidan Dan ko a mafarki Bata taba kawo Wanda aka aurawa Zahra, ze
Kama hayar gida irin wannan aljannar duniya haka ba.
A kitchen ma Nan Hameeda da zulai suka lalace komai na gurin saiya burge mutum, Nan ma Saida Auntyn
taga wani fregde ash colour a cikin Dan ack din jikin kitchen din irin Mai kofa Kamar ta wadroof ko ba'a
fada ba kasan kudi sunyi kuka a gurin.
Burner Auntyn tasa aka jona aka zuba turarikan wuta Wanda aka hadowa Zahra daga Saudi Arabia tun
wancen lokacin tunda basa komai saima Kara kamshi. Basu baro gidan ba sai kusan magariba.
Aunty Hasana taso ta wuce da Zahra gidanta amman Ammah tace A'a ba inda zata so suke ace Mata
tsohuwar banza idan so suke su tafi to ita zahrar ta Kira ta fadawa mijinta idan ya amince ita nata Mai sauki
ne ita kuma Zahra tace lahlah a barshi kawai.
Wajen goma saura aunty Hasana ta dauki yaranta suka wuce gida. Da safe Saiga Asabe da dahuwar kazar
amare da jarkar zumar Mata da ta tsimi tayiwa gidan tsinke, part din Ammah ta shigo direct, bayan sun
gaisa ne ta mikiwa Ammah babbar ledar data zubo kayan tana fadin "Ina Amarya tazo gashi na cika
Alkawari tazo ta cinye ta bani kashin tace a koma Mata dashi zata hada Mata wani Abu dashi. Inna
maimuna ce tace "ai kuwa yanzu taci abinci ta shga daki saidai a aje zuwa anjima sai taci ko gida ne sai a
aika Miki da Qashin, mun gode kwarai madallah Allah yabar zaman tare". Asaben ta amsa da "Amin ai
bama sai an tashi mutum ya kaiba Nima saina jira taci din ko Nan da yamma ne" ta fada tana mikewa tayi
musu sallama ta nufi dakin Mama.
Bayan fitarta ne Ammah ta dubi Inna maimuna tana fadin "nifa jikina Bai bani ba akan taci wanna abun
Dan ni tunda ta fada jiya naji abin Bai kwanta min ba,mutuniyar da gaisawa ma sai ta kure akeyi da ita
Amma fa ki duba sai wani rawar jiki take akan abinda Bai shafe ta ba ko alama, Kuma kar nice wani abun
arziku sukeyi da zahrar Dan ko gaisawa saita kure, Amman ki duba ki gani yanzu sai haba haba take da
Zahra.
Dakin Ammah aka shiga da kayan ammar tace zata cire tsokar tabar musu kashin, hakan ne ya kasance tayi
komai ta baiwa auta ya kaiwa Asaben dakin Mamar.
Saida Asaben ta tabbatar auta ya fito ta kwashe da dariya tana fadin "wallahi Maman yara kinsan ta kan
mugumta, yarinya har yarinya amma ta Kare a auren marar asali Wanda ko danginsa ba'a sani ba"
Kwafa Maman tayi "barni kawai Asabe wallahi tun lokacin da aka dauko yarinyar nan hankalina ya kasa
kwanciya, saboda babu ta inda Allah ya rageta duk abinda ake so jikin 'ya mace to Allah yayi Mata ga uwa
uba yanda mazan zamanin nan suka jarabtu da son Mata irinta nasan ba karamin mutum ne ze dauke taba
Ina zaune sai dai na Zama 'yar kallo ga nawa 'ya'yan a gabana, wallahi baze yuwu ba ai hankalina Bai Kara
tashi ba Saida na raka Aunty Ladi gurin wani Mutum a can jos nayi Masa maganar Asma'u to cikin binciken
ne maganar yarinyar ya Fado yake fada min na kyale maganar Asma'u don ba yanda zanyi da ita jikinta a
shirye yake haka Shima Alhajin ba abinda zeyi tasirin da ze rabashi da ita, Amma ga wata yarinya Nan duk
gidan ba 'yar da zata wuceta a sa'ar rayuwa a gurin aure Dan mijin da zata aura ba karamin mutum bane
Kuma dai..... Sai kawai bawan Allahn Nan yayi shiru da bakinsa nayi nacin duniyar nan Amman yaki karasa
mana zance, haka muka tasho Aunty Ladi nata zugani kada na kuskura na Bari ta auri Mai maiko duk yanda
zanyi nayi Naga hakan Bata faru ba. Nayi ta fama duk Wanda zezo gidan Nan gurin yarinyar nan zezo duk
kuwa da Fadi tashin da nake akan su Salma amman a banza, maganar dai daya ce Zahra, ni Kuma nayi
Alkawarin badai Zahra tayi aure ta barmin Yara a gida ba,Kuma badai ta auri Mai rufin asiri ba, gashi kuwa
ta Kare a Wanda ko asalin kirki bashi dashi Abu daya ya tsaya min a Rai yanda Naga gidan da zata zauna da
abin yaso razani sosai Dan ba haka na zata ba, amman duk da hakan ma yayi tunda ai gidan ma Malaminsa
ne ya bashi aro su zauna, Kinga kuwa karshe sai dai a Kare a yawon haya cikin Yama yamar matan
alarammomi, Kuma wannan kayan da ake qafafar an saka a gidan karshen wasu kayan saidai a sayar Dan
Babu abinda za'aci dasu Dan an sawo da zimmar su tafi Abuja sai gasu sun Kare a gidan Alaramma".
Ta fada cikin izgilanci.
**
Duk yanda Zahra taso ta kwantar da hankalinta abin ya faskara dan da gaske zulumi takeyi na yanda zata
fuskanci wannan sauyin da yazo Mata a bazata Wanda Bata tab'a tunanin hakan ba ko cikin mafarki, lallai
tayi zaton daga kan Mushahu komai ya kwaranye Amma sai wata matsalar ta taso wadda tafi ta baya.
A kwance ta wuni duk ta tsangwami kanta Sajida sai tausarta take duk da itama tata zuciyar a kusa take
Dan da gaske tana tausayin zahrar ba kadan ba.
Gurin karfe biyu ne sukaji alamar Kamar anyi Baki a gidan da alama ma da dan damarsu.
Sajida ce ta fito ta gaishesu zata koma cikin ne Ammah tace taje ta Kira Mama tace tazo su gaisa da Baki
Iyayen Musbahu ne daga kano.
Ta fita tana mamakin to meya kawo su Kuma.
Tare suka shigo da mamar Dan sajidar na fada Mata ta nufo dakin cikin rawar jiki.
Ciki Sajida ta wuce yayin da mamar ta zauna tana gaishe da bakin nasu Kafin Inna maimuna ta Fara Mata
bayanin Maman Musbahu ce tazo da 'yan uwanta ta bada hakurin abinda ya faru Wanda ita kanta Bata San
yanda akayi ba sai daga baya ake fada Mata shine tazo taji ko da yanda za'ayi a gyara matsalar tunda ta
dawo hayyacinta take cikin damuwa domin kwata kwata Musbahun baya cikin nutsuwarsa tun bayan
samun labarin an Aurar da zahrar, ganin lamarin nasa ba sauki ne yasa suka nufo nan Ashe har da yaron
sukazo sun jima a gurin Alhaji ma kafin su shigo nan din, hakuri kawai ya basu akan aikin Gama ya Gama
tunda yanzu matar wani ce ita.
Kallonsu Mama ta karayi tana tambayar "Ina mamar tasa take"
Hajiya Nafisa kanwarta ita ta nuna Maman Musbahun tana fadin "gata nan"
"Ayya Allah sarki Hajiya sai hakuri Allah Bai nufa matarsa bace ba sai dai yazo ya duba wata tunda da
sauran yaran a gidan".
Mama ta fada tana kafe Hajiyar da ido.
"Kayya a yanzu dai bana tunanin haka zata yuwu sai ko a gaba tunda ban taba ganin abinda Musbahu ya
kwallafawa Rai ba Kamar auren yarinyar nan tunda kuwa ya rasa ta bansan Kuma lokacin da ze Kara
maganar wani auren ba".
Sun Dan Jima kafin Ammah ta tashi ta shiga gurin su zahra tace ta fito su gaisa da Baki zasu tafi.
Jiki ba kwari ta nufo kofa doguwa rigace a jikinta kirar Bahrain Mai duwatsu har kasa blue black gyqlenta
kwai ta Dora a kanta Dan Sam Zahra Bata fiye son saka hula ba a kanta Dan Sam santsin gashinta baya Bari
hular ta zauna ta dunga zamewa kenan.
Cikin takunta na nutsuwa ta shigo falon hade da sallama Kanta na kallon kasa ta karaso cikin nutsuwa ta
zauna gefen Ammah a kasa kan carpet, tunda ta shigo suka bita da idanun kowa da abinda yake ayyanawa
a zuciyarsa.
"Masha Allah! tubarakallah 'yata matso kusa dani dole my son yayi kamar ya zauce da labarin rasaki ya
riskeshi" abinda Aunty Nafisa ta fada kenan tana nunawa Zahra kusa da ida, jiki ba kwari ta karaso ta zauna
tana gaishesu.
Suka amsa jiki a sanyaye su kansu sun San dansu yayi wani babban rashin da maida shi sai nufin Allah,
tunda Daman shiya hada shi da Zahrar kuma shiya raba lokacin daya so.
Nan sukayi sallama suka fita cikin matukar jimami Dan da gaske sunyi rashin sirika.
A daki Zahra kwanciya bayi ta rufe fuskarta da hannu biyu Batasan lokacin da hawaye ya zubo Mata ba,
Wai shike nan komai ya Zama past tsakaninta da Musbahu duniya ba tabbas. sajida na kallonta Bata
hanata ba Dan itama Saida ta matse, lokacin zahra na falo Mushahun ya Kira wayar ta, sajidar ta dauka
yanda taji maganarsa ko rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba kuka yake shima da idanunsa Dan abinda ya fada
kawai ya karya Mata zuciya, kalamai ne na bankwana ga masoyi da da given off akan Abu, da kyar ta iya
fada Masa ba zahra bace itace magiya yayi Mata dan Allah ta fito Masa da zahra yayi Mata sallamar karshe
Amma hakuri kawai ta bashi tunda yanzu Zahra matar aure ce bashi da hurumin yin magana da ita.
Sun Dade a haka kowa da abinda yake sakawa a zuciyarsa nkafin su jiyo maganar Magaji Yana fadin
"Ammah ga Ya Mushahu zaku gaisa yazu tafi ne".
Su biyu suka shigo suka gaishe dasu Ammah a nan Inna maimuna ke fadin "kayi hakuri da hukuncin Allah
kaji kada kayi fushi da mahaifiyar ka itama bayin kanta bane duk uwa bataqi ace danta yafi kowa sa'ar
abokiyar Zama ba, irin wannan matsalar ta Jima tana bibiyar yarinyar Nan to munyi zaton daga kanka abun
ya Kare sai Kuma ya canza salo akan mahaifiyar ka, kayi hakuri ka fawwalawa Allah komai shi ze baka
wadda tafi Zahra daman Allah hukunta kai ba mijinta bane ayi hakuri".
Kansa Yana kasa tunda ta Fara maganar wani Abu ya tsaya masa a makogwaro yaji Sam ya kasa magana sai
Aliyu ne ya amasa da "ba komai Mama haka Allah ya nufa, Allah ya Basu zaman lafiya mu zamu koma".
"To Allah ya tsare ya baka mace ta gari wadda zata maye maka gurbin Zahara'u" Inna ta fada ita kuwa
Ammah kasa magana tayi dan da gaske yaran tausayi suke Bata sun kwallafa Rai da juna Amma akayi musu
karan tsaye, a zuciyarta ta ayyana "Allah ka biwa yaran Nan hakkinsu duk Mai hannu a cikin Bata lamarin
Nan kayi Mana sakayya da gaggawa Dan isar Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w."
Ta window zahra ta leka lokacin da suka fito daga falon kamar ance ya juyo sai ganin zahrar yayi tana
kallonsa da sauri ta juya ta rufe fuskarta da hannu ta saki wani marayan kuka ta zube a gado. Su Kuma suka
fita zuciyarsa Kamar zata Kama wuta dan ganinta ba karamin fami ya zamar Masa ba, har ji yayi Yana wani
layi Kamar ze fadi.
Magaji ne ya shigo falon Yana fadin "Sun tafi, wallahi Ammah naji tausayin Ya Musbahu sosai kinsan har
gurin Baba malam yaje Amma magana daya dai kowa yake fada masa yayi hakuri, bayan mun fito ne yace
na nuna Masa mijin Aunty zahrar na fada Masa ai shine suka Fara gaisawa dashi bayan sun gaisa da
malam, shiru yayi sai kawai Naga ya dafe kansa Yana girgizawa, yace na hakura da zahra nasan wannan
baze taba sakin zahra ba. wallahi Ammah sai Naga yana goge hawaye gaskiya Allah saiya saka musu
wannan ai zalunci ne Kullum idan Aunty zahra ta samu miji sai an samu matsala".
Ya fada Yana Jan tsakin takaicin.
"To magaji babu yanda za'ayi haka Allah ya hukunta sai hakuri".
Bayan tafiyarsu da Kamar awa daya Abdul Hakeem ya shigo ya fadawa Ammah tazo Abba Yana kiranta.
A bedroom dinsa ta sameshi Yana tsaye ya goya hannunsa a baya Yana Dan Kai kawo a tsakar dakin.
Sallam tayi Masa ya amsa sannan ya sauke hannunsa ya nufi gefen gadon inda Ammah ta zauna tana
tambayar "Lafiya kuwa Abba meya faru Naganka a haka?"
Ajiyar zuciya ya sauke Yana fadin.
"Da matsala gaskiya yaron nan ne yazo a rikice yana kuka Kamar yaro karami da kyar muka lallashe shi nida
Abdul Hakeem ga mahaifiyarsa da 'yan uwanta kingansu dai nasan mazan ne suka ce ba ruwansu shine ita
da kanta ta taso tazo wallahi hawaye bibiyu ta rinka yi min akan na rufa Mata asiri na warware wancan
auren a maida kan Musbahu abin har abin tausayin wallahi, shi yasa na turosu cikin Dan ku Basu hakuri
tunda wancen zance ya wuce Kuma ji nayi da nauyi na Kira malam wallahi tunda ganin Mahmud nake
Kamar Dan cikinsa Kinga na Kira shi akan maganar ai Bai kyautu ba, to bayan sun tafi ne Abdul Hakeem ya
Kira Hassan ya fada masa shine ya kirani Yana min magiyar Dan Allah a rakata dakinta yau basai gobe ba da
tun farko ma ankaita da hakan Bata faru ba yasan wasu ne daga nan zasu Gaya Masa tunda Yana da
mutane sosai suce ai tana gida ma yayi bata tare ba suyi tunanin ko Babu auren ne, Dan haka Nima nayi
na'am da maganar tasa, kuje kuyi duk abinda ya kamata da magariba zan mikata dakinta da kaina in Sha
Allah, na Kira malam ma na fada masa."
"To hakan yayi duk abinda ka yanke dai dai ne Allah ya nuna Mana lokacin".
"Amin ya amsa"....
✨✨
MAMAN FATIMAH.
_________ Karfe biyar mai kyau motar da Alhaji Jafar ya tuko da kansa daga shi sai Zahra a ciki daga
bayansa Kuma Abdul Hakeem ne a wata motar ya biyo Abban nasu bisa umarninsa,suka dira kofar gate din
gidan Zahra,sau biyu Abban yayi horn Mai gadin ya leko da yaga Alhaji ne da kansa tunda daman ya San
Alhajin farin sani yayi sauri ya bude kofar suka shigo gaba daya, da sauri Mai gadin ya karaso Yana budewa
Alhajin kofa Yana gaishe shi yayin da Abdul Hakeem ya budewa Zahra ta fito suka zagaya Gurin da Abban
yake, Abdul Hakeem suka gaisa da Mai gadin sannan Abban ya Kama hannun Zahrar ya nufi kofar main
falon da ita, tasha farar laffaya Mai adon kananan flowers pink, jikinta kamar an Mata barin turare sai
tashin kamshi take Mai Dadi. A bakin kofa suka Hadu da Mahmud din ya nufo kofar da sauri Dan Yana
bedroom dinsa yaji shigowarsu tun bayan anyi la'asar Baba malam yace Alhajin yace ya same shi a can
gidansa da yamma za'a kawo Masa iyalinsa.
Matsawa Mahmud din yayi daga bakin kofar Yana yiwa Abban sannu da zuwa sannan ya mikawa Abdul
Hakeem hannu suka gaisa, kan kujera Abban ya zaunar da Zahra sannan ya umarci Mahmud daya zauna
kusa da ita shi Kuma ya zauna a kujerar dake kallonsu, Abdul Hakeem Shima ya zauna, sai falon ya dauki
shiru, gyaran murya Abban yayi kafin yace "Abdul Hakeem yi Mana addu'a' bayan yayi doguwar addu'a
sun shafa Abban yace "To Mahmud ga matarka nan na kawo maka bani na baka ita ba Allah ne ya baka ni
nawa idawa ce, gata Nan amanace a gurinka kada ka zalunce ta duk inda yanayin rayuwa ya kaiku na baka
ita ne saboda na yaba da nagartarka na Dade Ina monitoring dinka ban tabaji ko ganin abun ashsha ba a
tare da kai, kullum addu'ata Allah ya bani ikon sauke nauyin marainiyar Allah dake hannuna, kuma
Alhamdulillahi na sauke gata nan marainiya ce Bata da uwa Bata da uba ba wa ba kani ita kenan iyayenta
duka suka rasu suka barta, kada ka zalunce ta Dan girman Allah ka tausaya Mata saboda Mai rauni ce, ka
zamar Mata uwa uba abokin Shawara kuyi dariya tare kuyi kuka tare ka jibinci lamarinta gwargwadon
iyawarka. Ina Kuma Kara gode maka bisa share min hawayena da kayi baka watsamin kasa a ido ba lokacin
Dana baka aurenta, na gode kwarai Allah ya saka maka da Alkhairi ya yaye maka damuwarka ya kawo maka
mafita a bisa lamuranka".
Suka amsa da "Amin"
Sannan yaci gaba da fadin "ke Kuma Uwata ga mijinki nan kiyi Masa biyayya abisa abinda Bai sabawa Allah
ba, ki girmamawa shi ki kiyaye bacin ransa ki kiyayie mutuncinsa da rike Masa sirrinsa kindaraja mas
iyayensa da 'yan uwansa lokacin da Allah ya hukunta ku hadu dasu,nkiji tsoron Allah a cikin zamanta
kewarku ki saka hannu ki Barbi duk abinda ya biyo bayan aurenki dashi Mai Dadi ko sabanin hakan. Dan
Allah ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da abinda Allah ya hukunta a kanki komai Kika gani rubutacce ne
daga Allah sai dai mu 'yan adam mu karasa shi, Amma tun ran gini tun ran Zane dama haka kaddarar take,
ko shi mijin naki idan yayi nazari zega wata kila wannan kaddarar auren ce ta rabo shi da asalin inda yake,
to Dan haka kowa ya rike tasa kaddarar wata Rana sai labari komai na duniya Yana da iyaka ikon Allah ne
kawai bashi da karshe, Allah yayi muku Albarka ya kauda fitina a tsakaninku ya tabbatar da Alkhairi a cikin
rayuwar aurenku, Mahmud sai anyi hakuri da Mata su masu rauni ne kwarai da gaske".
Tunda Abba ya Fara magana yaji kamar ya dauko wani gaigimemen dutse ya Dora Masa aka.
Cikin ladabin da baisan Yana dashi ba ya furta "in Sha Allah Abba ba wata damuwa Kuma amana na karba
na rike Allah ya bani ikon saukewa nike da godiya Allah ya saka da Alkhairi ya Kara Nissan kwanaki masu
Albarka"
"To Masha Allah, Abdul kayi Mana addu'a mu tafi kada almuru tayi Mana a nan, Uwata ki daina kukan Nan
haka bana sonsa kiyi hakuri kowa da haka ya girma Allah yayi Miki Albarka, ga makullin motarki wadda
mukazo da ita takice na sai miki, kudin dayar ta wajen Abbie suna gurin Alhaji muttaka tunda aka sayar da
ita nace ya juya Miki kudin zuwa lokacin da za'a bukaci wata motar Dan haka in Sha Allah cikin sati Mai
zuwa za'a kawo Miki dayar ma".
Suka tashi suka fita Mahmud yayi musu rakiya har gurin mota Saida suka tafi sannan ya dawo ciki, a inda ya
bar zahrar anan ya sameta ta kwantar da kanta a kan cinyoyinta tana kuka Mai tsuma zuciya a hankali ya
zauna kusa da ita yasa hannu ya dago kanta daga jikin cinyoyinta idanunta a rufe sai tsiyayara da ruwan
hawaye suke. Ba zato ba tsammani kawai taji ya sakata a girjinsa ya kwantar da kanta ya saka hankici Yana
share Mata hawaye, daya hannun Kuma Yana tapping din bayanta kamar yanda ake yiwa yaro idan ana so
yayi shiru Yana kuka, jikinta gaba daya ya dauki rawa ta taso da niyyar zare jikinta Dan wani Abu takeji duk
ilahirin jikinta Amma Dan bawan Allan nan yayi kememe yaki sakinta ba arziki ta hadiye kukanta, sai sauke
ajiyar zuciya kawai ba kakkautawa saida ya tabbatar ta Samu dan nutsuwa sannan ya saketa Yana fadin "
sorry Baby ki daina kuka bana son kuka Sam koda kuwa na karamin yaro ne".
Hannunta ya Kama ya mikar da ita ya nufi daya daga cikin bedrooms dinta guda biyu da suke mallakinta,
Saida ya zaunar da ita a gefen makeken gadon sannan ya juya ya nufi kofa Yana fadin " it's time for prayer"
Ya fice Yana ja mata kofa.
Sai ta dauki kusan minti biyar kafin ta Samu kuzarin warware Laffayar dake nannade a jikinta, doguwar
rigar material ce a jikinta anyi Mata dinkin fitted gown tayi Mata kyau sosai kofar data gani ta nufa tasan
toilet ne, lokacin data shiga abin ya girgizata irin kayan amfanin data gani a ciki ita ba bakuwar abin bace
tasan ba kananan kudin aka narkar ba a cikinsa, abin ya Bata mamaki sosai sai dai wa zata tambaya? ta
Jima a ciki kafin ta dauro alwala ta dawo dakin.
Ido ta ringa wurgawa ko zata ga sallaya tunda ita dai bakuwa ce a dakin can gefen sofa taga wani stool
kamar coffee table da sallayun akai ta shimfida ta Fara sallah.
Tana cikin sallah ne taji kamar karar door bell kamar sau biyu, Saida ta idar ta tashi ta fito har lokacin tana
share hawaye jefi- jefi, gurin kofar ta karasa ta bude Sajida da Hameeda da Mujiba ta gani ai batasa lokacin
data fada jikin Sajida ba tana dakin kuka Mai tsuma zuciya.
Ciki suka shigo Sajida na fadin "haba bestie wallahi Dana San har yanzu baki daina kukan Nan ba da
bazamu biyo bayanki ba, haba Ashe bazaki karbi kaddara yanda tazo Miki ba? ki Kuma godewa Allah a
kowane Hali Kika Samu kanki, bake Kika halicci kanki ba ballantana ki tsarawa kanki yanda Zaki rayu, kin
taho kina kuka duk kin dagawa Ammah hankali itama, kin kyau kenan? haba kiyi hakuri Dan Allah ki share
hawayenki wallahi nasan yanzu zuciyar masu binki da mugun nufi tana can kamar zata fashe Dan ba haka
suka soba duk da bansa daga Ina matsalarki take ba, ai kodan makiya kin kwantar da hankalinki ki rungumi
mijinki ki ba mara d'a kunya, Amma kin tsaya kina wani Abu kamar wata karamar yarinya"
Tayi tsaki tana kallon zahrar da tayi kozai kozai ido ya kode Mata abinka da farin mutum.
Suma su Hameedar ban baki suka dunga yi Mata, da kyar ta hadiye kukan ta kallesu tana fadin "wallahi
bazaku Gane bane ni kadai nasan me nakeji, komai ya kwance min Sam duniyar bata mun dadi".
"Hakurin dai zakiyi ki Kuma yawaita addu'a in sha Allah komai ze wuce kamar ba'ayi ba, muda muke son
next year by now mu dawo suna".
Sajida ta fada tana murmushi.
Wani kallo zahrar tayi Mata ta juya kanta gefe tana fadar "Allah ya kiyaye min wata haihuwa can".
Mujiba ce ta kwashe da dariya tana fadar "A'a Banda cika Baki dai 'yan Mata Nan da labari yasha banban
zamu tsinceki kina faman 'yan amaye amaye, lokacin ne Zaki gane Baki da wayo ko ba wata haihuwa can
ba?".
Zumburo Baki tayi tana fadin "sai kiyi Kuma haka kawai Zaki jaza min, wani ciki ko dadin fada ma Babu".
Saima zahrar ta zame ta kwanta, tana jinsu suna ta faman zolayar ta har aka Kira sallar insha'i a Nan sukayi
sallah kafin su shiga Kara gyara Mata Fallon da Kara masa freshner da turaren wuta Hameeda ta Kara karfin
A C a falon ta gyara cutains din, bedroom din data fito suka shiga Mujiba bakinta ya kasa shiru tunda dai
suka Samu zahrar ta daina 'yan koke koken sai ta balle da santin gidan Dan bayan sun idar da sallar ba inda
Bata shiga ba ta leka can ta shiga can bedroom din Mahmud ne kawai Bata shiga ba tunda a rufe yake, fada
take "wallahi zahra ki Kara godewa Allah, irin wannan haduwa haka wallahi ko makiyi Saida yaki fada
Amma dai duk wani gata kin same shi sai dai fatan zaman lafiya kawai".
Ita dai Zahra ba baka sai kunne.Dan ita kadai tasan abinda ke Kai komo a zuciyar ta, su inda suka dosa
daban ita inda ta dosa daban, ko tayi musu bayani ba ganewa zasuyi ba, domin su duka ba wadda ta tab'a
shiga irin gararin data shiga, rayuwa Rumi rumi saika Gama sakankancewa da mutum Rana tsaka Abu ya
lalace, uwa uba ganin da tayiwa Musbahu ba karamin famu yayi Mata ba, saboda da ta cire shi daga ranta
kwata kwata ta hakura, Amma tana ganinsa komai ya rikice Mata da tana zargin kamar da niyya mamansa
tayi haka saboda ya taba fada mata Maman nasa taso ya auri 'yar Yayarta shi Kuma ya ringa sharewa ana
haka ne Allah ya had'a shi da zahrar abinda ya kawo karshen wancan dambarwar kenan. Amman tasowar
mamansa da 'yan uwanta dashi kanshi takanas ta kano har Azaren don bada hakuri da neman gyara idan
lamarin Mai gyaruwa ne, sosai abin ya tashi hankalinta, wata sabuwar soyayyar sa ce ta sake bijiro Mata
idan tana tuna yanda yaci buri a irin wannan ranar da za'a kawo Masa ita a matsayin matarsa ta sunna
halalinsa, irin abinda yake fadin ya tanadar Mata ita a wancen lokacin idan Yana fada kamar zata nitse kasa
dan kunya Amma shi ko a jikinsa.
Wasu sabbin hawayene suka zubo Mata masu zafi tana ayyana shike nan komai ta Zama tarihi, ga inda
kaddara ta kawo ta gurin da ba'asan darajarta ba ko alama sai aukin taba Mata jiki da yake Wanda ta
fashimci hakan tun haduwarsu ta farko, ba kunya ya wani saka hannu ya rungumota Wama ya sani ko Dan
duniya ne aka hadata dashi, tunda ance ba Wanda yasan asalin sa kuma tasan yanda yake din nan ko bashi
da sisi mata zasu ringa kawo Masa rida tunda sun ganshi smart dashi.
Wani tsaki tayi tana ayyana to Ina ruwanki da wani smartness dinsa.
Mahmud Bai dawo gidan ba sai bayan sallar insha'i ganin takalma yasan akwai baki cikin gidan baya raba
daya biyu 'yan uwanta ne ko kawaye, dakinsa ya wuce yayi wanka ya canza kaya ya fito falo, bai shiga
dakinta ba daga inda yake yana jiyo mganganun bak'in, ita dai baiji tata maganarta ba Sam Zama yayi yana
daddana wayar hannunsa.
Acan Kuma dakin Zahra Ya Abdul Hakeem ne ya Kira wayar Sajida Yana fada Mata su fito su tafi ya dawo
daman lokacin daya basu kenan bayan sallar insha'i lokacin daya kawo su.
Sun fito falone suna zolayar Zahra Basu kula da mutum ba sai da suka sauko daga steps din da ze sada ka
da corridor din bedrooms din suka ganshi a zaune Yana ta faman Danna waya, kallo daya Zahra tayi Masa
ta kauda Kai haka kawai taji gabanta ya fadi, ta rasa wace irin masiface wannan.
Kansa ya dago yana amsa gaisuwar su Sajidar Yana fadin "har zaku koma ne?".
Hameeda ce tayi farat tace "To ba dole mu tafi ba yallabai tunda angon yaki zuwa ya sayi bakin amaryarsa
ba Yana ganin Mai araha ce bai Sha wahalar komai ba aka bashi ita".
Ba Zahra da aka ciwa fuska a fakaice ba hatta Sajida da Mujiba Saida sukaji kamar kasa ta nutsa dasu a
gurin Dan kunya, gaba daya suka zubawa Hameeda ido har shi uban gayyar, wani abune Wanda Zahra Bata
taba tunanin Hameeda zatayi Mata ba, dan wannan cin fuska ne qarara bako kawaici a cikin maganar ko
kad'an. Zahra kasa gaba ko baya tayi ta tsaya a gurin kawai, su sajida ma rasa ta cewa sukayi shi kuwa uban
gayyar wayar dake hannunsa ya aje Yana kallon Hameeda direct kafin yace " waya fada Miki Mai araha ce
bakiji sunanta ba? Zahra fa kinsa ma'anar sunan kuwa? tauraruwa fa a cikin taurari a gurinki take Mai
araha Amma ni a gurina tafi zinari daraja, bari na baku indai abin sayen Baki ne in dai shi ne abinda ke
shaida Kima da darajar mace a irin wannan ranar gurin kawayenta, ina zuwa". Ya fada Yana mikiwa ya nufi
hanyar bedrooms dinsu, tunda ya wuce zahra ta juya da sauri ta nufi daki Bata yi musu ko sallama ba.
Bai jima da shiga ba ya fito da wata katuwar leda da Kuma envelope guda uku a hannunsa. Yana zuwa
directly Hameeda ya nufa ya Mika Mata ledar da envelope daya sannan ya baiwa Sajida da Mujiba Suma
dai dai Yana fadar "ga kayan sayen bakin Nan a cikin wannan envelope din Kuma kunsha ruwa a hanya".
Ba kunya Hameeda tace yanzu naji magana ai shi tuwon girma miyarsa Nama mun gode".
Taja katuwar ledar tayi gaba abinta mujiba ma tabi bayanta har suka fita Sajida Bata motsa ba ita kollon
ikon Allah take akan Mahmud Wai wannan shine Almajirin da ake ta yayatawa a aurawa Zahra har Hajiya
Mama na yiwa Abba magiyar kada ya Fara wanna danyan aikin tab wallahi da sake ita tafa abinda ta gani
ga tare dashi ai da hasashe ne take yanzu be taga zahiri. Ganin sun fita yasa sajidar aje Masa envelope
dinsa a gefen shi tana fadin "kabar abinka na gode, ni fatana ka rike min bestie da mutunci da amana yafi
ka bani duk abinda ka mallaka, bansan Kai ko waye ba Amma jikina Yana bani kana boye wani Abu tun
lokacin Danazo gidan nan da Kuma irin kayan danaga an kawowa bestie nasan Kai ba kaskantanccen
mutum bane, Ina hadaka da girman Allah kada ka bautulcewa Iyayenta da suka baka ita kaji tausayinta
marainiya ce, Dan Allah nasan duk inda ka fito ba karamin guri bane ka Zama garkuwarta ka zamar Mata
bangon da zata jingina taji dadi duk rintsi. Dan Allah ka Bata kulawa Zahra 'yar gata ce kaddara ce ta
zaunar da ita a kasar nan da Kuma kawaicin kakanninta suka hakura suka barwa Ammah ita, Dan Allah ga
amana Nima na baka kamar yanda iyayenta suka baka kaji tsoron Allah a cikin zamantakewar ka da ita na
San Nan gaba zaka samu zabinka ko Kuma tuntuni kana dashi Dan Allah kada ka wulakanta ta.. na rokeka
ka Zama adalin shugaba a gurinta idan kaji yanda rayuwa ta dunga jujjuyata zaka tausaya Mata matuka,
Dan Allah badan niba...."
Da tayi gaba ta nufi kofa Bata taji me ze fada ba domin hawayene suka ciko Mata idonta idan tace zataci
gaba da magana kuka zata fasa masa ne. A bakin kofa sukayi kicibus da Mujiba wadda ta dawo kiranta
ganin shirun ya yi yawa.
✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
✨✨
💎PAGE EIGHTEEN💎
STORY
AND
WRITTEN
BY
MAMAN FATIMAH.
_________ Bayan wucewar Sajida Mahmud ya Dade Bai tashi ba, kwarai yarinyar ta burge shi matuka, da
gaske take son Zahra domin furucin da yarinyar can tayi yayi touching dinta sosai, lallai ya tabbatar son da
take yiwa Zahra bana Wasa bane shi tun lokacin da Magaji ya fada masa ta baro syprus Dan kawai ta
halarci bikin zahrar ya jinjina Mata duk da suna hutu Amma yasan irin wadannan daliban ba kowane hutu
suke zuwa gida ba sai dai idan iyayen sun sunci sun tada Kai.
Envelope din data aje masa ya kalla yayi wani killer smile ya zurata a aljihun Wando Yana Kara wani
murmushin Wanda shi kadai ya barwa kansa sani.
Yaso ya shiga dakinta sai ya share kawai Dan yasa baya raba daya biyu kuka take Dan da gaske koshi baiji
dadin furucin da akayi Mata ba Kai tsaye bako rusunawa a ciki.
Lokacin da Abdul Hakeem ya Parker motar a parking lot na gidan Sajida ce ta farkon ficewa daga motar
zuciyar ta na Mata wani zafi Dan da gaske idan ta tsaya zata shatawa Hameeda rashin mutunci ne na
karshe Wanda zata Dade Bata manta ba, dan da gaske an shirya ne kawai dan a tozarta Zahra a gabanta
mijinta, shi yasa kenan lokacin da zasu ltafi ta shiga part din Mama Kiran Hameedar akan ta fito suje, taji
Salma na fadin saura Kuma ki kasa fada ki dawo Mama ta tumurmushi banza, ita Sam Bata kawo komai ba
kawai dai ta dauka wani abune can tsakaninsu saida hakan ta faru ta Gane me ake nufi da waceccen
maganar. Tana jin Mujiba na kwala mata Kira lokacin data nufi karamin gate wanda ze sada ta da cikin
gidan, batabi ta Kanta ba tayi wucewarta ciki ta kyalesu.
Koda ta shigo part din Ammah directly bedroom din da suka kwana ta wuce tana yiwa su Aunty Hasana
sannu har ta shiga ta fito tana fadin "Aunty Dan Allah idan su Hameeda sun shigo kice su raba kayan su
biyu kwai Banda ni". Ta koma da sauri Dan tana jiyo maganar su a kusa alamar Nan suka nufo.
Tun shigar Zahra bedroom din Nan ta kwanta rub da ciki take risgar kuka Kamar ba gobe, Hameeda ta Bata
mamaki Bata taba zaton irin wannan ranar ba a tsaknainta da Hameeda cewa take ko kowa ya nuna Mata
naqi a bangaren Mama ita kadai zata tsaya a bayanta duk runtsi duk wuya saboda a baya ba Mai cin fuskar
ta a dakin Mama makukar tana gurin Koda kuwa mamar ce, Amma yau Hameeda da bakinta Kuma a gaban
idonta take fadar magana irin wannan, to meya canzata daga Hameedar data sani Mai sonta da kaunar ta
da Bata kariya da kulawa a kowane janibi. Saida tayi Mai isarta har ta baiwa uku lada, sannan ta hakurkurta
da Kanta ta tashi zaune. Kanta taji ya Sara Mata a hankali ta furta "Alhamdulillahi ala kulli halin. Allah na
gode Maka duk abinda kayi nufi a gareni na karba ka bani ikon cinye jarabawar Nan dan isar Annabi
Muhammad s.a.w.w".
Hannu tasa ta dafe Kanta dake matukar Sara Mata, wannan wace irin rana ce a gareta? ranar da duk wasu
masoya keda tarin burika a Kanta Amma ita ranar ta ta farko ta kasance ranar cin fuska daga inda Bata taba
zato ba, ba tarairaya duk burin da suka dade sunaci na irin wanna ranar ya tashi a banza. "Astagafirullah
Ubangiji ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan rayuwar Mai tarin qalubale a cikinta".
Ajiyar zuciya ta sauke tana Kara dafe Kanta da gaske jinsa take Kamar ze rabe gida biyu, ba zato ba
tsammani taji an bude kofa Bata daga Kai taga ko waye ba dan kamshinsa kadai ya Isa ya fada Mata Mai
shigowar, Kuma ma waye ze shigo haka Kai tsaye a irin wannan lokacin, sallama yayi Mata Amma Allah
baisa ta amsa Masa a fill ba ta dai amsa a zuciyar ta.
Takowa yayi a hankali har zuwa inda take zaune, har lokacin Kuma Bata daga Kai ta dube shi ba farar ledar
dake hannunsa ya aje kusa da ita ba tare daya tanka Mata ba ya juya ya nufi kofa yana juya baya ta dago da
sauri ta kalli bayansa kananan Kaya ne a jikinsa sabanin dazu da yake sanye da wani lallausan yadi fari tas
da hula, sai taga Kamar yafi kyau yanzu akan dazun, kananun kayan sunfi karbarsa akan manyan da yake
sakawa, hannun daya saka ya Kama handle din kofar idonta ya Kai taga hannun wani fresh dashi Kamar
Mai rayuwa a kasashen sanyi. Ganin Kamar ze juyo ne yasa tayi saurin kauda Kanta Dan kada ya kamata da
wadannan idanun nasa tana kallonsa. Kofar tabi da kallo bayan ya fice a hankali ta sauke ajiyar zuciya da
gaske fa mutumin Nan yana Mata wani irin kwarjini, ga wani tsare gida naba gaira ba dalili da yake saiya
karta Abu ya wani maze Yana Shan kamshi.
Karan bude kofar ne ya dawo da ita daga tunanin data shiga na wucin gadi, kusa da ita ya zauna daf da daf
dan ji tayi Kamar numfashi daya suke sharing dashi, a hanakli yasa hannu ya dago fuskarta data Kama idon
ta rufe, a zuciyar ta tace "na bani ni Fatima shi Kuma kome faskar Nan tawa tayi Masa? shi dai ya taba
jikina kawai ya sani, muryar shi ta jiyo cikin deep voice yana fadin "Pls open your eyes and look at me
mana".
Kai ta shiga girgiza Masa alamar a'a.
Shi abin nata ma mamaki yake bashi, a ranar da suka samu wannan arangamar da ita soron gidan Baba
malam yaga ta rufe idanu ya dauka ko tsabar razanar zata fadi ne. Amman sai yaga abin na neman ya
Zamar Mata jiki indai zata ganshi to kuwa sai ta rutse idanu Kamar taga wani abun tsoro, a haka zasu rayu
da ita ai baze yuwu ba gaskiya dole yayi wani abun daze cire koma meye yake haddasa Mata hakan a tare
dashi.
"Ok Ashe zamu kwana a haka kenan tunda bazaki bude idanun ba, ko Kuma wallahi na shayar dake
mamaki yazun nan".
Shiru tayi Masa kirjinta Yana fat, fat da sauri kusancin yayi yawa duk ya kanainaye ta.
Batayi zato ko tsammani ba taji harshensa akan fata idonta Yana lasa yana busa mata iskar bakinsa
kamshin Lister mint mouthwash Yana dukan fuskarta ciki Shirin fita hayyaci tayi baya da sauri ta fada kan
gadon da baya idanun nata tar akan fuskarsa da yana mata wani Yana Mata wani kallon kasa - kasa nan da
Nan taji tsikar jikinta tana tashi sai hawaye zurrr...
"Why! meyasa? Ai da sai ki barni na kwashe abinda yake hanawa kina kallon nawa Mana, oya tashi abinci
zakici bazaki kwanta da yunwa ba kisa na Fara karya Alkawarin dana daukar Iyayena na kula dake,dan
kowa amanarki yake bani da jaddadda min na rikeki da amana da gaskiya cikinsu harda bestien mu kuwa".
Ya fada a kasalance Yana kashe Mata ido.
Sai Kuma ya dan zamo kadan ya dauko plate Wanda ita Sam Bata San lokacin daya ajesu a gefenta ba, ledar
ya bude wani kamshi ne ya doki hancinta Mai shegen Dadi kaza ce wani irin gashi akayi Mata Kamar na
tsire da vegetables a ciki ya juye Yana fadin.
"Oya tashi kici kafin ki kwanta kinsan yunwar dare tana kawo ciwon ulcer,kada ta kamaki ace Ina barinki da
yunwa ni d'an malam gara na Kara kiwataki duk wanda ya ganki ace Masha Allah! Kamar ba matar
Almajirin Baba malam ba".
Ya fada da alamar zolaya a karshen maganar tasa. Itafa Yana Bata mamaki wallahi zata iya rantsewa idan
aka saka Masa hannu a Baki baze ciza ba amma dubi yanda ya wani zage yana magana Kamar bashi ba.
Ganin da gaske zata Bata Masa lokacin shi Kuma Yana da abinyi da yawa yasa ya matsa sosai kusa da ita
ganin Yana nema Kara mannata a jikinsa yasa tayi saurin tashi zauna tana kikkibta idanu tana kallonsa. Da
hannu ya nuna Mata plate din, cikin Rashi kuzari a maganar tata tace Masa "na koshi bazan iyaci ba kaina
ciwo yake".
Ta fada murya a shagwabe ga daman tasha kukanta.
Sai yaji ta Kara bashi tausayi abun ne yayi Mata goma da ashirin.
Cikin sigar lallashi yace.
"To kici ko kadan ne saina kawo Miki magani kisha kinji"
Ya fada yana Kara nuna Mata plate din da idonsa, kadan taci duk a takure shi har mamaki take bashi a
yanda yake ganinta ai ta wuce ace tana jin irin wannan kunyar ko tsoron irin haka, tunda da gani wayayya
ce ta ajin karshe, ga Kuma yanda ta ringa ta'ammali da samari kala kala, a yanda yaji labari fa sau uku ana
fasa aurenta Wanda ba Wanda yasan dalilin hakan, yasan kawai rainin hankaline irin na Mata, yanda
zamanin ya Zama abinda ya Zama Amma dai ai gaskiya zatayi halinta komai daren dadewa.
Ba laifi ta danci tace masa ta koshi tana kokarin fitar da kwalla. A zuciya yayi yana jinjina saurin kukanta
Kamar wata 'yar goye Sam yaga kuka ba wani wahala yake Mata ba, tana kuka tun abun kukan Bai Samu ba
to idan ya samu yaya za'ayi kenan?.
Kwashe kayan yayi ya fita dasu Bai jima ba ya dawo da p.c.m tablet a hannunsa da ruwa marar sanyi, farm
fresh yogurt ya Fara zuba Mata ta karba Tasha sosai dan tana sonta sosai lokacin tana Jos har kamfanin
take zuwa ta sawo musu, tayi Mata Dadi sosai sanyin moderate ba Mai cutarwa ba.
Saida ya tabbatar da tadan samu relief kafin yace Mata.
"Ki tashi ki canza kayan jikinki ki kwanta idan kikayi barci kan ze daina ciwon, in Sha Allah, Kuma na fada
Miki tun kina Asibiti ki rage damuwa Bata maganin komai sai Karin matsala Amma idan Kika hakura komai
Mai wucewa ne Zaki sameni fiye da yadda Kika tsammmata kiyi hakuri komai da Kika gani hukuncin Allah
ne ba Wanda ya Isa ya canza idan Ina tunani akan kaina na duba yanda connection din ya faru nasa ba
Wanda ya Isa ya tsara haka sai Allah Dan haka ki Barbi abinda ya Baki Koda bakya so kinda ance wani hanin
ga Allah baiwa ne tunda gashi ya Baki Dan malami sukutum ai tsakaninki da Allah sai godiya". Ya fada Yana
kafeta da idanunsa masu sakata ladabin dole.
Kai kawai ta gyada Masa, ba baka sai kunne, mikewa yayi da cup da robar farm fresh din a hannunsa ya
nufi kofa a hankali ya juya very lockly suka hada ido kashe Mata ido daya yayi Yana Dan murmushi Wanda
Batasan Kona menene ba, sannan yace Mata "good night".
Yaja kofar wasu sabbin hawayene taji Kuma ita harga Allah bada niyya ba jinsu kawai tayi hakika tana
tausayin kanta, da gaskiyar masu iya magana da suke cewa cusa Kai ba kwarjini yawa ne yau ta gani ganin
idonta Wai ita Amarya ce wadda zayati kwanan farko a gidan miji.
"Ya illahiy!!! Wannan wace irin ranace haka? Yanzu da Musba.... Astagafirullah".
Ta fada da sauri tasan tunanin wani irin haka haramun ne da aure a kanta.
Ta jima a gurin tana sakawa da kwancewa Amma dai duk inda ta juya amsar daya ce aikin Gama ya riga ya
gama sai hakuri da zubawa ikon Allah ido Dan shine alimil gaibi.
Tunda Mahmud ya shiga nasa bedroom din ya kasa samun nutsuwa Banda yayi namijin kokari ya kauda
kansa da lallai sai ya rage zafi gaskiya idan yayi haka baimata adalci ba. Dan shi a nasa bangaren kamai ya
gama zamar Masa daidai, saidai ita uwar gayyar batasan wainar da yake toyawa ba dan idan da abinda shi
Kuma Bai lamunta ba yayi Mata dole yafison komai Daren dadewa taso shi da muradin kanta yafi son ya
koyar da ita yanda zata soshi fiye da kowane da namiji data taba so a rayuwarta, ba Kuma ya son tasan
koshi waye bama ita ba kowa ma dake tare dashi a nan, yafi son ya Gina kanshi a gurinta a wannan
matsayin na yanzu.
Wanka yayi ya saka pyjamas dinsa farare sol nasu laushi, yana jinsa cikin watan irin nutsuwa, maimakon ya
kwanta sai ya dauko laptop dinsa ya dosa aiki sai gurin biyu da kwata ya ture computer din ya tashi ya nufi
kofa ya fita dakinta ya nufa dakin zahrar yana zuwa yana turawa yaji kofar a bude Kuma dakin da haske
yayi zaton ko barci ne ya dauketa tabar wutar Mai haske a kunne. Yana turawa ya ganta akan sallaya tayi
sujuda Amma shashhshekar kuka take Allah kadai yasan abinda take roko tsakaninta da mahalicci ya jima a
tsaye kafin yaja Mata kofar ya fita jikinsa a matukar sanyaye dan ba karamin qima ta kara a idonsa ba ya
Kuma Kara godewa Allah da yayi Masa kyauta da wannan yarinyar yasan Allah sami'uddu'ai ne yasha raba
dare Yana rokon Allah ya bashi mace ma'abociyar addini, sai gashi a inda Bai taba zato ba Dan gaskiya Bai
taba kallonta a wata mujahida ba yafi Mata zaton bokon ya rinjayi bangaren islamar ta.
Koda ya koma shima Bai kwanta ba Saida yayi nafilfili sannan ya kwanta da tunani kala-kala a zuciya.
Hudu da minti arba'in ya farka ka'idarsa kenan ta tashi sallar Asuba, wanka yayi ya saka jallabiya milk
colour ya bude kofa har ze wuce sai yaga Bai Dace ba gara ta tasheta ta.
Sanda ya tura kofar har ta Fara raka'atanul fajri ta Riga ta tashi, lallai ya jinnina Mata gurin ibada sai yaji ya
qara samun wata nutsuwa a tare da ita da sauri yaja Mata kofar ya nufi falon jin za'a tada sallah.l
✨✨
✨✨
✨✨
✨✨
MAMAN FATIMAH
_______________Mahmud tunda aka idar da sallah Bai shigo gidan ba sai kusan karfe shida da rabi, ya
Dan jima da Mai gadi kafin ya shiga ciki dakin Zahra ya nufa a kwance ya sameta akan sallaya da gani
batasan lokacin da barci ya dauketaba yasan kusan kwanan zaune tayi, a hankali ya matsa daf da ita Yana
karewa fuskarta kallo idanunta sun dan tasa alamun kukan da tasha da Kuma rashin barci, wayarta ce a
gabanta a kunne tsugunawa yayi ya dauka Qur'an ya gani tana karantawa barcin yayi gaba da ita, baiyi
tunanin tashin taba kada ya katse Mata barcinta.
Kan stool na madubi ya zauna da wayar a hannunsa Yana dubawa haka nan yaji Yana son ya shiga ya duba
received calls da missed calls nata, a hankali ya ringa bi Yana dubawa yawanci kawayenta ne sai Kuma
Ummee da ya gani har ze aje sai yaga Kamar number din guyn da zata aura Dan lokacin daya tafi da
wayarta ya canza mata wayar da sim card din a Nan ya haddace number din tasa sai Kuma yanzu daya ga
Kiran jiya dai dai lokacin suka bar gurin Baba malam, Nan da Nan yaji ransa ya sosu duk da Kiran daga
gurinsa ne ba daga gareta ba.
Tashi yayi tsam yabar dakin da wayar a hannunsa shima kwanciyar yayi, can cikin barci yaji alamun ana
Danna door bell da kyar ya tashi ya nufi kofa, Musaddiq ne da Faruq din Aunty Hasana suke kawo break
fast cikin ladabi suka gaishe dashi ya amsa yana Basu hanya suka shigo da basket din dake hannun
Musaddiq ya Dora akan dining table.
Musaddiq ne ya juya ya nufi kofa yayin da Faruq yayi tsaye, har Musaddiq yakai kofar fita daga falon ya
juyo Yana fadin "Faruq me kake jira ne ka tsaya? kasan driver Yana jiranmu fa"..
"Taya zamu tafi bamu gaishe da Aunty Zahra ba?".
Mahmud ne yace "Faruq Auntyn barci take sai dai zuwa anjima sai ku dawo kaji".
***
Cikin damuwa da matsanancin tashin hankali Mama ta tashi, tunda garin Allah ya waye ta tasa kayan da
Hameeda ta shigo dasu jiya a leda da envelope din kudin da mijin Zahra ya Basu a gaba ko bakasan kayan
kwalliyar Mata ba kaga wadan Nan kasan ba Karabiti bane ga uwa uba kudin daya lafta musu ita abin har
ya Fara Bata tsoro, dan a zahiri kowa yasan fakiri ne wanda Bai ajeba bai bada ajiya ba amma a badini
abubuwan da yakeyi suna da ban mamaki.
Wayar ta ta dauko tayi dealing din wata number ba'a Dade ba aka daga Bata koyi sallama ba ta Fara
magana "Asabe kome kike kizo anjima da matsala babba komai Yana neman ya dagule fa kizo kiga abinda
wancan tsintacciyar magen ya baiwa su Hameeda jiya harda fadin magana dan Hameeda ta fadin
maganganun danace ta fada wallahi Ina kokonto akan lamarin yaron nan Dan jiya da dare Dana Kira malam
na BANDE cewa yayi Wai mun kuskure wani abu shi yasa har Alhajin ya iya daura mata auren Kuma yayi
duk iya yinsa ya kasa ganin komai akan mijin nata sai wani haske kawai yake gani".
Daga can taji magansr mamar ta amsa da "hakane ba damuwa sai kinzo din ta aje wayar tana jan karamin
tsaki ta tashi ta shiga toilet.
A bangaren Ammah kuwa bayan Sajida da zulai sun Gama aikin break fast din da aka Kai gidan zahra,
sajidar wanka tayi ta Shirya kafin ta fito falo su karya, bayan sun Gama ne ta kalli Ammah tana fadin
"Ammah in Sha Allah yau an tafi gida Ina son na wuce school ne daman na jira ne saina raka Zahra gidanta
tun last week muka Fara lactures".
Ta fada a ladabce.
"To Babu laifi hakan Allah yayi Albarka, sai Magaji ko Malam Bala wani ya Kai ki mun gode madallah, kunyi
sallama da mutuniyar tun jiya kenan!" Ta tambaye ta.
Kai ta girgaiza tana fadar "A'a sai anjima zan shiga muyi sallamar".
___
Zahra Bata tashi ba sai wurin takwas da rabi tayi Mika gami da salati tana Kara ware idanu tana kallon
dakin da alama kamar ma ta manta inda take Sai a hankali ta dawo cikin nutsuwarta "ya Salam".
Ta furta hankali tana ware sexy eyes dinta, wallahi Sam ta Manta da waifa a dakin gidan aurenta take ba a
dakin Ammah ba, tashi tayi zaune kan sallayar tana Kara kallon Kanta har lokacin hijabin da tayi sallar ne a
jikinta.
Toilet ta shiga duk jikinta ya Mata wani irin nauyi Sam Bata jin dadin jikin nata ruwa Mai dumi ta hada ta
shige ciki tayi kwance tana shakar kamshin turen wanka data zuba ta jima sosai a cikin ruwan kafin tayi
wanka ta fito sabon towel ta dauko mai kalar purple Babba ta daura ta fito gurin mirror taje lotion ta
dauko ta shafa a jikinta, tashi tayi ta nufi gurin wata jaka kayan gyarab gashinta ta dauko, zuwa tayi ta
zubesu yanzu da a gida ne da Ammah ce zata gyara Mata tsab ta hade shi guri daya, tana kiciniyar daureshi
taji alamun bude kofa da sauri ta kalli gurin, Mahmud ne cikin shigar kananan Kaya yayi wani irin
fitinannan kyau, hannunsa ya nade a kirji ya jingina da kofar ya zuba Mata idon dake figitata, shi be shigo
ba shi be koma ba ya kafeta da idanunsa.
Tunda suka hada ido dashi tayi saurin sunkuyar da Kanta jikinta na wata irin rawa duk ji tayi ta rasa yanda
zatayi daga ita sai towel din Nan a jikinta, gashin ta saki ya bazu har gadon bayanta ta matse hannunta a
kijinta, sun Kai kamar minti uku a haka Yana Kare Mata kallo son ransa a cikin zuciyar sa Yana tsarkake
sunayen Allah da yayi Masa kyautar bazata da wannan kyakykyawar halittar dake gabansa a matsayin
matarsa ta sunna halaliyarsa wadda ba wani shamaki a tsakanin su.
Cikin takunsa Mai Cike da karsashi Amma a nutse, ya doso inda take tsaye Yana zuwa ba zato ba tsammani
taji ya saka hannu Yana tattaro gashin daya bazu a kafadarta yana fadar "Bari na gyara Miki tunda Naga
yana neman gagararki".
Bata iya ce Masa komai sai jikinta daya cigaba da tsuma, tsab ya hade ya saka ribom din daya gani a kusa
mayukan gashin brush comb ya saka ya Kara gyara shi sannan yayi baya a hankali ya zauna akan sofa Yana
fadar "ki shirya kizo muje ki bamu break fast gashi can Ammah ta aiko tun wurin 7:30 su Musaddiq suka
kawo".
Bata amsa ba Kuma ta dago kalle shi ba, d'an gunguni ta fara kasa kasa "kawai ka zauna mun a daki kana
kalleni kaki fita a gabanka kake son na saka kayan ko me?".
Yana kallonta gefen ido tana magana a ciki baya raba daya biyu yasan complain take akan zamansa. Tashi
yayi Yana fadin "idan kin Gama kiyi min magana Ina aiki ne".
Ya juya ya fice.
Wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadar "innalillahi ni Fatima Naga ta kaina Wai shi wannan waye shi? Nifa
wallahi lamarinsa sun fara bani tsoro gaskiya" ta fada tana cuno Baki, sai Kuma tayi sauri har towel din
jikinta na neman faduwa key ta sawa kofar, a gurguje ta saka doguwar rigar lace peach colour Mai touching
din flowers green Bata daura Dan kwalin kayan ba saita rufa gyale green,Sam batayi wani make up ba
powder kawai ta shafa sai lips glow turarenta ta fesa ta nufi kofa ta bude ta fice tsaye tayi a cikin corridor
din saita rasa a wane bedroom din yake.
Ta jima a tsaye tana saka yanda zata tunkari dakinsa Kai tsaye, cikin yin shahada ta nufi inda take zaton nan
ne bedroom din nasa a hankali ta murda handle din ta tura kamar wadda za'a cewa ket ta ruga, wani sanyi
da kamshin turensa Dana freshner ya shiga hancinta dakin ba wadataccen haske duk curtains din windows
a sake suke can kan sofa ta hango shi da laptop a gefen sa yana ta faman daddanabawa tsaye tayi ita Bata
shiga ba ita Bata koma ba, yana kallonta ta gefen ido Amma sai ya basar kamar bai ganta ba.
"Assalamu Alaikum".
Ta fada a darare, Bai kalleta ba Amma ya amsa sallamar.
Dan Jim tayi kafin tayi karfin halin cewa "na gama shiryawar".
Kansa ya dago ya kafeta da idanunsa da yake razanata dasu kafin yace "idan bazaki shigo kije kawai an fada
min Ina cinye mutane ne da Kika tsaye a nan".
Dan cuno Baki tayi ta saki handle din ta shigo a nutse Amma fa Babu nutsuwa Kota sisin kwabo a zuciyarta
ta ayyana "waya sani ko mayen ne tunda abune a duhu".
A tsakiyar dakin ta zauna an carpet Kanta na kallon tace Masa "barka da Asuba".
Shiru yayi kamar Bai jiba Saida ya Mula dan kansa yace "Lafiya ya kwanan bakunta I hope ba wani damuwa
ko?".
Kai ta gyada masa alamar eh.
Yace "good Bari na karasa wani dan aiki muje muyi break ko?"
Ya fada Yana kallonta.
Ganin tayi shiru yasa yaci gaba da aikinsa ita Kuma tana zaune duk sanyin dakinsa ya Mata yawa, tana son
sanyi amma sai taji na dakin yana neman ya sakata rawar jiki.
Baifi minti biyar ba ya rufe laptop din ya Miki, gurin da take zaune ya nufo yana zuwa ya Dan tsuguna kusa
da ita Yana fadin "taso muje kada nabar 'yar amanata da yunwa na amsa query a gurin su bestie ko?"
Ya fada Yana murmushi.
Hannunta ya kama ya dagota tsaye suna shakar numfashin juna Amma ita kanta yana duban kasa, dayan
Hannun yasa ya dago fuskarta as usual yanda ya saba.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali Amma bata rufe idon ba kamar yanda ya hanata a jiya Bata manta ba
amma ta kauda Kai gefe dan da gaske Bata iya had a ido dashi.
Dan kwanto da ita yayi jikinsa Yana juyo da fuskarta yana fadin.
"Wallahi kada ki rusa min budget dina kisa na kwashe kunyar nan daga idanunki tun banyi niyya ba
matukar zakici gaba da irin wannan dabi'ar".
Das das girjinta ya kara bugawa akan wadda yake, tana fadin "oh ni Zahra tawa ta sameni shi Wai wane iri
ne haka? sai yayi ta sakin magana ko kunya babu".
Saida ya matsa mata taci abincin kirki bayan sun Gama ne suka dawo parlor suka zauna Sam Babu sabo ko
kalilan a tsakaninsu kallo ya kunna a Nile sat ya kamo super support suna kwallo live.
Ganin ita ba wani gane kan ball din take ba yasa ta Mike zata koma daki ta kira Sajida taji ya maganar
tafiyar Dan tun jiya da Abba yace a jiya zata tafi gidanta sajidar tace itama sai gida ta.
Takunta biyu taji ya janyo ta ta fada jikinsa ba Shiri ta zaro ido waje hura kata iskar bakinsa yayi a fuskarta
dalilin yasa ta rufe idonta kenan a hankali yace "Ina Zaki ki barni a zaune alhalin saboda na tayaki Zama
yasa naki fita ko ina".
✨✨
✨✨
✨✨
✨✨
_______"ya Salam". Zahra ta fada a hankali jin yanda yake hura mata iskar bakinsa a fuskarta, yasa
hannuwansa duka biyun ya tallabo fuskarta yana kallon face din very cute da ita, shifa baya gajiya da
kallonta komai nata burgeshi yake yi Dan bakinta ya kalli 'yan kyawawan lips din ta pink, gdy yake yiwa
buwayi Gagara misali daya mallaka masa ita a lokacin da bai taba zato ba, tunda ya kafeta da ido Bata
yarda sun hada ido ba, ba Kuma tayi gigin dogowa ba.
Qaran da door bell din tayi shiya kawo karshen 'yar tutsiyen da yayi Mata wani soft kiss ya yiwa gefen
wuyanta Wanda har Sai da ta zabura tana fadin "wayyo Allah!".
A shagwabe ta janye jikinta daga rikon da yayi mata, shi Kuma ya tashi ya nufi kofa, Bata jira taga waye ba
tayi wuf ta nufi ciki jikinta kamar mazari.
Tana shiga ta zube a gado tana fitar da numfashi da sauri da sauri kamar wadda tasha gudu, jin alamun
bude kofar yasa tayi saurin duba gurin Sajida ta gani tsaye ta tsura Mata ido tana Mata wani kallo cikin
mutukar tsantsar farin ciki zahrar ta taso tana fadin "haba bestie kin wani tsareni da ido kina min kallon
qurillah irin wannan ko Kinga wani abu a jikina ne?".
Ta qarasa fada tana karasowa kusa da ita 'yar madaidaiciyar ledar hannunta tana fadar "Wai meye Kika
wani yi shiru kina kallona ne Dan Allah talk to me Mana pls".
Biyo bayan zahrar tayi har gefen gadon kafin ta samu kuzarin fadin "Bestie Kinganki kuwa just one day
Amma har kin Fara canzawa, Fadi min meye sirrin gaskiya, na tafi jiya da zulumin ki a Raina yau kuma nazo
na sameki haka kin wani Kara Zama fresh dake".
"Bestie tsakanin mu harda 'yar zolaya zakice Wai na Kara zama fresh?"
Zama tayi gefen zahrar tana fadin "wallahi I am serious kin canza a idona gaskiya Kinga ai dole na fada
ko?".
"To shikenan kin fada bazan hanaki ba, wai da gasken yau Zaki wuce?"
Kai ta gyada Mana kafin tace "In Sha Allah meya rage kuma ai gara naje na fuskanci karatun ko tunda na
samu nutsuwa kin shigo gidan ki. Alhamdulillahi, ga sauran abubuwanki na wajen Baffan rimi kici baga da
amfani dasu dazuma munyi waya da safe yace na bawa Ammah abinda ya Aiko dai ya Kara jardada Mata
na a fada Miki kada wani ya kawo Miki abu kici Kuma yace a tura a karbo Miki sako Nan da sati daya".
Dan langabar da Kai tayi tana Kara ganin kimar Sajida ta dauki matsalar nan tata bada wasa ba.
Godiya sosai Zahra ta yiwa Sajida akan abinda suke mata, sun Dade sajidar na yiwa Zahra nasiha akan ta
rike aurenta da kyau ita bataga wani abun ashsha ba gurin Mahmud idan. Nan da Nan idon Zahra ya kawo
ruwa ta shiga sharewa da hannunta tana fadar "wallahi bestie na rasa dalilin da yasa nake jin wani abu a
tare dashi tun ranar Dana Fara ganin shi naji abun ko kallonsa fa nayi sai naji gabana Yana faduwa heart
beat Dina Yana karuwa, kinsan ma inda matsalar take?"
Kai sajidar ta girgaiza tana fadar "sai kin fada".
"Kinsan haduwar mu ta farko rungumeni fa yayi a cikin jirjinsa tsam kamar.wata baby amman Kamar an
dinke min Baki na kasa ko fada Masa magana ne saima wani azababben kwarjini da yayi min harda fadar
na ringa kula kada nayi musu asara'.
Ai Sajida Bata San lokacin da wata dariya ta kubce Mata ba tana fadar.
"Babbar magana kice da wata tsumammiya a tsakani ku tun tuni har kika dauki alhakina gurin hanani
kwanciyar hankali tun jiya Allah barci ma ban samu na kirki ba Ina zulumin abinda kaje yazo, Dan ba kowa
bane za'a aje masa mace kamar ke ya iya kauda Kai gaskiya"
Wani duba zahrar tayi Mata tana fadin "ban Gane ba me kike nufi da maganganunki?.
Wata dariyar tayi tana fadin "A'a ba mefa nake nufi kawai dai...... "
Sai tayi shiru.
Wani zancen ta dauko Tana fadin "Zahra ki tsaya ki nutsu a gidan aurenki ki gyale kowa duk wanda ze raina
Miki miji kada ki amince ko waye kuwa Koda ni da nake Miki wannan maganar, Kuma game da Hameeda ki
kula sosai Dan a jiya ta nuna Miki jiya ba yau bace, jini kuma yafi ruwa kauri, Koda ta dawo tana neman
Kara shiga jikin ki da wata manufar tazo, Dan Allah kiba marada kunya duk yanda ake son ganin lapses dinki
kada ki bada damar hakan".
In Sha Allah zan kula nagode Bestie Allah yabar zumunci. Zahra ta fada
"Ameen" sajidar na ta fada, suna cikin hira akayi knocking din kofar ba'a bude ba Zahra ce Mike tana fadin
"ina zuwa, tana kokarin yafa gyale ta rufe gashinta Sajida ta warce ta aje gefen ta tana fadin "haba ke
kamar matar liman a daki na da Bata ja ba tayi gaba saboda an Kara buga kofar, budewa tayi Mahmud ta
gani Yana tsaye ya canza kaya ya saka Riga da wando na wani yadi light brown dinkin buda yana baza
kanshi sa na ibada.
Matsawa tayi daga jikin kyauren ganin alamar shigowa zeyi Amma fa Saida yadan shafi fuskarta kadan
sannan ya ida ahigewa ciki, tsaye tayi tana binsa da ido tana ayyana "Wai meye ne yake faman shafa mata
fuska har a gaban mutane ko kunya bayaji tasan wlh sarai Sajida ta gani sai dai ta basar kawai gashi ta wani
rike mata gyale ta wani barta tsurarta".
Direct gurin mirror ya nufa ya zauna a Kan stool, Yana fadin "Bestien mu zuwa nayi muyi sallama naji
Abdul Hakeem yana maganar Zaki wuce yau ko".
Ya fada Yana murmushi, itama murmushin tayi masa tana fadar.
",In Sha Allah yau sai kano tunda Allah ya cika min burina Zahra ta shigo gidanta fine".
"To mun gode kwarai Allah ya saka da Alkhairi sai munzo visiting idan madam zata dauki nauyin zuwan mu
Kinga Nima sai Naga duniya ko madam?" Ya zubawa Zahra narkakkun idanunsa Yana Mata wani kallon qasa
qasa.
Shiru Zahra tayi tana yafa gyaren a kanta, Sajida ce tace "gaskiya Kam haka za'ayi".
Tashi yayi ya Dan tako kadan zuwa gaban Zahra kamar ze hadeta da jikinsa da sauri tayi baya tana turo Baki
yi yayi kamar Bai gani ba, envelope ya Mika mata Yana fadin ki Bata sskonta ne na jiya data Bari nayi niyya
bazan canza ba sai dai idan bataso ta bayar, nizan shiga gurin su malam".
A hankali tace "an gode madallah a dawo lfy".
"Jiya Mana lokacin da zamu tafi sanda wannan jikar marokan ta zubar da darajarta ta rokeshi, yanzu Dan
Allah me Hameeda ke nema? wane irin rufin asiri ne Allah Bai mata ba. Amma ta lalace gurin roko? shi
yasa na aje masa kudin sa nayi gaba kayan ma nace bana so su rike".
Dan murmushi Zahra tayi tana fadin "Saji danger wato halin na Nan ko? To nidai gashi nan tunda a gaban ki
ya bayar saiki karba".
"Bude mu gani to"
Sajidar ta fada.
Stalling founds ne na ingila musu yawa a ciki kallon kallo sukayiwa juna kafin Sajida tace wallahi bestie
akwai kukus a shinkafa zakice na fada Miki, Wai kuwa kin tsaya kin Kare guyn nan kallo kuwa?". Kinga ya
Miki Kama da Wanda baida abinyi ko wanda ya tashi a cikin rashin wadataccen ilimi da mugu? Dubi
muhallin daya ajeki, ance malam ya bashi gidan sai kungiyar da yakewa aiki sukayi renovation din gidan ki
kiyasta nawa yaci gurin aikin kinsan da an kashe abinda yafi kudin ginin duk yi Masa akayi? Ki tuna Nan fa
ba garinsu bane ance bako ne kuma yaki fadin garinsu anyi magana ance yace ya manta komai sai a hankali
idan ya tuna hankali ze yarda da hakan? Kuma kina tunanin Abba ze daukeki ya bashi ba tare da yasan
wani Abu a tare dashi ba? Kiyi nazarin abin Mana ni dai ina fada Miki kibi komai a hankali kuma yanda na
fashimci wani Abu a maganar da Kika fada min kinfa kamu da son guyn Nan tun sanda kuka hadu ba tare
da kin sani ba, Kuma Shima Naga yanda yake shige Miki ko kunya ta Bai jiba kinsan sai a hankali kawai
kwanan Nan labarin ze sauya irinsu basayi da wasa fa".
Ta garasa fada tana dariya kasa-kasa.
Suna cikin tattaunawa Kira ya shigo wayar sajida "Ya Abdul Hakeem ne" ta fadawa Zahra kafin ta daga.
"To"
Kawai tace ta kashe Kiran tana fadin.
"To bestie ya Abdul Hakeem Yana jirana Wai a she shine ze Kaini nifa daya fada na dauka da Wasa yake
lokacin da Ammah tace Magaji ko Malam Bala dureba zasu kaini sai kawai yace su Bari Shima Yana son yaje
kanon Sai ya tafi Dani".
Dariya Zahra tayi tana fadin "idan tayi wari munji batun, yanzu ba fa Naga Ya Abdul Hakeem Yana dama
dama dake ba bai fada min ba Amma zakice na fada Miki Ina ga target dinsa kenan yau yake son ya yad'a
manufarsa shi yasa yayi Riga malam masallaci yace Wai daman kanon zaya".
Kin magana sajidar tayi sai murmushi kawai. Zahra tace "bestie ko dai komai ma ya kankama ne ban sani
ba Ina shirme?".
Kafin sajidar ta Bata amsa wani Kiran ya shigo da sauri ta dauki jakarta tana fadin "To bestie sai gani na
gaba Allah ya bada zaman lafiya ya kade fitina, sai anyi ta hakuri kafin komai ya dai daita ki kwantar da
hankalin ki zakiji dadin Zama dashi in Sha Allah".
Har gate ta rakata babbar ledar dake hannunta ta Mika mata tana Mata addu'ar sauka lfy. Amsa tayi tana
Mata godiya ta bude gate din ta fita, ya Abdul Hakeem Zahra ta gani a mota a zaune cikin mamaki tace.
"Ya Abdul Hakeem daman kana Nan waje Amma baka shigo ba?".
Fitowa yayi ya karaso gurinsu Zahrar ta gaishe shi, sannan ta juya ta koma ciki duk zuciyarta ba Dadi Kamar
ta Hana sajidar tafiya amma ba hali.
*********
Mahmud Yana fitowa direct Famfon shanu ya nufa tunda lifan din Habib a gurinsa ya kwana, tun jiya daya
karba da yamma Bai koma unguwar ba.
Lokacin daya karasa yayi arba da motar Sameer wani murmushi yayi Yana fadin. "magulmaci kawai".
Kafin ya shiga Saida suka dinga gaisawa da jama'a anata Allah sanya Alkhairi, Binya ya tambaya Ina Habib
yace yaje Kai wani sako da malam ya tura shi ya Kai gidan sarki.
Gurin Malam din ya shiga shi dasu Sameer ya samu suna magana da malam din Yana shigowa da sallama
mlm din yace.
"Yauwa Dan halak yanzu nake cewa bazaka jima ba zaka shigo, mutanen ku ne sukazo da wasu ayyuka gasu
nan dai zasuyi maka bayani. Ya wajen iyalin naka!?"
Dan sosa kansa yayi Yana Dan sadda shi qasa yace "Lafiya kalau tace a gaisheka" .
"Masha Allah. Allah yayi Albarka"
Gurin su Sameer ya juya suka gaisa, kafin suka fita zuwa inda suke meeting.
Stepdown training zasuyi da school base management committee Basu tunda tsarinsu ya koma sun bin
tsarin makarantun government ne sai kuma officially da suka gayyaci Mahmud zuwa gurin taron da zasuyi
a Lagos nan da kwanaki biyar masu zuwa. Bayan Gama taron Sameer ya dauki Mahmud a mota suka fita
hotel din suka nufa a hanya Sameer ya kalli Mahmud Yana fadin "yallabai meye labari naga text dinka
komai an sawo zuwa anjima motar zata karaso amma sai nake ganin kamar kayi tafiyar nan da ita tunda
zaka jima a can Kuma kaga duka kwanan ta nawa zaka tafin baka ganin abin ze iya Zama na surutu ko ace
ma guduwa kayi amma dai ya kake gani?".
Dan Jim yayi kafin yace.
Tafiya da ita ba shine solution ba na dauketa na kaita Ina ko Kuma nace Mata wanene ni Nan nace Lagos
zani can Kuma taga sabanin hakan ya kake tunani ka tuna fa she's educated, zatayi saurin gane komai ni
kuma nafi son na Gina soyayya ta a zuciyarta ba tare da tasan who I am ba, I hope you understand?".
Kai ya gyada Masa alamar eh.
Sun Dade suna tsaya yanda program din ze kasance da abinda za'a batar da abinda za'a kashe a
makarantar zuwa lokacin da zasu dawo suna cikin aikin direban daya dauko kayan ya Kira Sameer ya fada
Masa ya shigo Azaren ya fada Masa inda yake tattara komai sukayi suka wuce gurin da direban yake,
Sameer din ne ya shiga gaba direban na binsa a baya har zuwa gidan Mahmud din.
Mai gadi ya taya direban sauke kayan, kayan abinci ne da sauran tarkacen girki hatta nama da kifi daga can
aka kawo kayane masu matukar yawa.
Ciki Mahmud din ya shiga tararwa ya yi tayi Baki har su zulai da sahura, a tsaitsaye suka gaisa yayi gaba
zuwa bedroom dinsa.
Ganin idon su zilan yasa zahra mikewa tabi bayansa dai dai lokacin Kuma Yara suka Fara shigon kayan
masarufin da aka kawo, ganin zahrar Bata Nan yasa su sahura shiga dasu store din kayan abincin suka hada
da wanda Abba yasa suka kawo dazu da kayan gara su gireba dasu dublan da alkaki.
Sunyi mamakin yanda yara ke shigo da kayan abincin basu Kara Shan mamaki ba Saida aka Fara shigo dasu
Nama da kifi ga drinks Nan ko ba'a fada ba Wai ance ido ba mudu ba amma yasan kima sun San kayan na
manyan kudi ne, ko wacce da magana a bakinta Amma bata furta ba.
Zahrar na shiga corridorn ta waske zuwa nata dakin.
✨✨
✨✨
✨✨
✨✨
...............…... Sai da su zulai suka gyara Mata komai yanda ya kamata sannan suka gyara parlourn,lokacin
da Mahmud ya fito bedroom dinta ya nufa baiyi wani knocking ba ya tura kofar a gaban gado ya ganta ta
cire bedsheet din ta zubo da pillows din da alama wani Abu take nema sallama yayi mata cikin muryarsa
Mai nutsuwa yana kallon ta, cikin takunsa na cikakken namiji ya karaso Yana tambayarta "lfy me kike nema
ne haka Kika birkita gurin haka?".
Jiki sanyaye tace Masa "wayata nake nema tun safe banganta".
Dan matsowa yayi kamar ze tayata dubawar Yana fadin "Kuma tun safe Baki ganta ba Kuma Baki nema ba
sai yanzu, to su waye suka shigo dakin ne?".
"Shiru tayi kawai tunda tasan daga ita sai sajida ne a dakin Kuma tun bayan tafiyar ta ko Baki ne 'yan ganin
daki Bata ahigo dasu Nan Dan gani take yaushe za'a dinga shigo da jama'a har dakin barcin mutum su dai
dayan tunda ba a ciki take ba.
Dagowa tayi ta Dan kalli gefen shi da gani wanka yayi ya canza kananun Kaya tana mamakin sa ita tunda
take ganinsa Bata taba ganinsa da shiga irin wannan ba Kullum manyan kaya ne Amma daga jiya zuwa yau
ya zamar Mata wani daban, Sam ba wancen bane take gani.
Kamar ze wuce ta bayanta sai Jin Hannun Mutum tayi ya zagayo ta cikinta ya manna bayanta a kirjinsa ya
kwanto da kansa dai dai saitin kunnenta iska yadan hura Mata kadan tare da hucin numfashinsa kafin yace.
"Ki daina wahalar da kanki tana gurina tun safe na dauka, nayi mamakin da baki nemeta ba sai yanzu? Na
cire sim din saboda Naga wani sakarai ya kiraki da number din to nasan ze iya bibiyarki tunda naga bashi
da taushidi ko kankani Bai hakura ba da hukuncin Allah so yake da karfi saiya kwato abinda ya kubce
masa".
Kasa ko kwakwkwaran motsi tayi sanda yake jero Mata maganganun. Amma jin ya Kira Musbahu da sakarai
marar taushidi yasa taji Zuciyarta ta wani baci, idan beji tausayinsa na abinda ya faru ba ai baze Masa bita
da kullin irin wannan maganar ba, shida ya tsunci dami a kala har ya samu bakin magana irin haka. Nan da
Nan taji ta samu wani courage wanda Bata San tana da shi ba, cikin muna bacin rai ta fara kokowar raba
jikinta da nasa tana fadin.
"Wallahi Musbahu ba sakarai bane, ba Kuma marar tauhidi bane,dan ya biyo abinda yake halalinsa amma
kasan dai Banda qaddara ba abinda ze rabani dashi, dashi muka tsara planning na rayuwarmu Amma
lokaci daya ka rusa Mana budget din mu ka yarda da aurena da aka baka Kuma wallahi tunda nake dashi
bai ko taba rike ko hannuna ba, amma Kai kuwa fa ranar Dana fara ganinka a duniya dame ka Fara min
bada rugumata ba?" Kai kenan baka da aikin yi sai tabawa mutane jiki ......
Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji ya hade bakinsa da nata cikin zafin nama Yana ladabtar da bakin
nata da harshensa, dayan hannun Kuma yayi Mata wani irin riko bana Wasa ba dayan Kuma yana yawo
dashi a ilahirin jikinta cikin wani irin sarrafawa Mai zafi.
Wata irin tsuma jikinta ya kama ga hawaye kamar na lalataccen famfo sai zuba suke ba bakin kuka sai
mutsu mutsu take Amma ko a jikinsa wajen sau uku ana Kiran wayarsa tana tsinkewa, yayi biris da Kiran
Kumar baya ji, sai da ya tabbatar da ya ladabtar da ita yanda yake so ya saketa, kan bed ta fada tana
shashhshekar kuka hannunta daya yana Kan lebenta dake Mata zafi haka ma kirjinta zafi yake Mata ga
gaban rigar ya farke Mata ita.
Kafarsa daya ya doro Kan gadon dayar tana kasa ya Fara fadar maganarsa hankali kwance kamar bashi
bane ya Gama yamutsa Mata jam'iyya yanzu ba cikin mugunta.
"Wallahi na Kara Jin wannan sunan a bakinki ko magana makamanciyar irinta saina shayar dake ruwan
mamakina, an fada Miki ni lusari ne da har Zaki tasani gaba kina fada min rubbish ne? an rusa muku
budget din sai kuyi duk abinda zakuyi, an fada Miki Nima son abin nakeyi ne? da har Zaki tsaya kina min
rashin kunya akan wannan lusarin Mai karairaya kamar mace,ke yanzu wannan har wani namijin arziki ne
da ze iya dake? wallahi da kinyi tsautsayin aurensa da kin Gane Baki da wayo, idan Kika Kara gigin fada min
magana makamanciyar irinta zan Baki mamaki wallahi, , har kike wani zakewa kina fadawa mutane
magana, kice tak akansa billahil Azeem sai kin Raina kanki a dakin Nan saina banbance Miki tsakanin namiji
da muna maza".
Yayi tsaki ya juya abinsa cikin takunsa na ingarman namiji ya fice daga dakin zuciyarsa kamar zatayi
bombing.
A yanda su zulai sukaga ya fito Saida abin ya Basu tsoro kallon kallo suka shiga yiwa juna, sahura ce tace.
"Zulai bakiga yanda Mai gidan nan ya fito bane? Allah yasa ba mutuniyar taki bace ta taboshi Kinga ai ba
haka ya shiga ba".
Zama zilan tayi tana fadin "waya sani sahura muna Nan tare dake, nifa shi yasa nace ba zanzo ba yau
amman Ammah ta matsa akan sai nazo na Gane mata lafiyar ta,tun safe wayarta idan an Kira Bata shiga".
"To Kinga kuwa dole ki dubota ki gani ko Lafiya ya fito a haka kofa a dawo lfyr mu bai amsa Mana ba".
Jiki ba kwari zulai ta nufi bedroom din Zahra ganin zilan ta shige cikin corridor sahura ta Ciro wayarta Nokia
ta Kira Mama. Ba bata lokaci ta dauka kamar jira takeyi ta shiga labarta mata abinda ta gani tun daga kan
kayan da suka Zuba store har fitowar Mai gidan yayi da alamun bacin Rai a tare dashi, to kawai sahurar ke
fada alamun wani Abu mamar take fad'a Mata sannan sukayi sallama.
Sai da ya fice harabar gidan ya Ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin Sameer ne yasa ya Maida wayar ya
nufi inda Sameer din yake zaune cikin mota, Bai Masa magana ba, zagaya yayi ya shiga motar yana fadin
"let's go"
Ganin yanayin daya fito ya hana Sameer din korafin barinsa a waje baice ya shigo ba, dan kwantar da
kujera Mahmud din yayi ya kwanta yasa hannu ya dafe kansa da gaske Sara Masa yakeyi lokaci lokaci Yana
Dan Jan tsaki, Sameer dai be tanka Masa ba yasan a kusa yake, sai da sukayi nisa da gidan Sameer din ya
Dan juyo yana tambayar.
"Ina muka nufa yanzu nifa na gaji ga yunwa Ina ji kace muzo gida muci abinci Kuma ka watsar dani a mota
inaga ma sai da ka rage zafi ni in Nan Ina hamma ka shanyani".
Ya fada Yana Maida hankalinsa a titi.
Tsakin ya Kara yi Yana dagowa daga kishingidar da yayi Yana duban Sameer din "Allah ya shiryeka ka dauka
kowa ma irinka ne Wanda baya iya kauda Kai a Kan Mata? Muje can hotel din kayi order abinci kaci tunda
bani na gayyato ka ba cewa nayi ka dorowa mota kayan Kai Kuma sai gurin jibi kazo, to bansan wane
kinibibin ya kawo ka ba ka bar yarinyar mutane da ciki kana gantali".
Ya karasa maganar Yana hararar Sameer din.
Dariya yayi Yana "fad'in easy man bani na kar zomon ba rataya aka bani, waya fada maka lamarin su da
sauki? bakaji abinda Abbanta ya fada maka ba? ai da yace sai ana hakurin da gaske ne Zama dasu Saida
hakuri".
Wani sakaran kallo Mahmud din ya aikawa Sameer da shi.
"Ka wani zaqe kana ta zuba wani Abu nace maka tayi min ne? da kaketa faman fadin maganganu haka
tsabar saka ido kawai, gobe ka tattara ka koma inda ka fito tunda ba gayyato ka nayi ba da zaka dameni da
kananun maganganu zan shigo da kaina kanon ba ai ba bakuwa ta bace ba".
Ya fad'a da gaske Yana Bata rai.
Shiru Sameer din yayi ganin da gasken koma Nene yayi touching dinsa sosai.
Suna shiga harabar hotel din kafin Sameer ya Gama parking a parking lot Mahmud ya bude ya fice abinsa
Yana picking din wayarsa da aka Kira.
******Tunda zulai ta doshi kofar bedroom din Zahra take jiyo Kamar shashhshekar kuka, hannunta har
rawa yake gurin bude kofar Dan ba maganar knocking, rubda ciki ta sameta tana faman shashhshekar da
sauri ta mayar da kofar ta rufe ta karasa gurin zahrar da sauri tana Fadin.
"Subhanallahi uwar dakina me zan gani haka me kikayi masa? Dukanki yayi? Dan Allah kiyi magana Kona
Kira Aunty Hasana ne sai ki fad'a mata ko na Kira Miki Ammah".
Kai ta girgaiza mata alamun a'a, "to ki fad'a min ko zan iya yi Miki wani abun Mana".
Saida kukan ya lafa Mata sannan ta yunkura ta tashi zaune ido zulai ta zuba Mata ita ba yarinya bace kallo
daya tayi Mata tasan da wata a kasa ganin yanda take a yamutsa ga labbanta sunyi jajir abinka ga farin
Mutum ga gashin kanta duk gyaran ya turje. Zama tayi kusa da ita sai a lokacin taga gaban rigarta a yage
Hannun bra dinta guda a tsinke.
Kai kawai zulai ta dafa tana Fadin "mezan gani haka ni zulaihatu! Haba Zahra'u me yayi zafi haka ai sai kisa
ya illataki a banza, gardama kika yi Masa yayi Miki haka?"
Cikin shashhshekar kuka tace "A'a maganar Musbahu yake min shine ya Fadi Abu marar Dadi a kansa shine
kawai Dan na mayar Masa da amsa Nima yayi min haka". Ta karasa fad'a tana kuka.
Cikin karfin Hali ta Mike ta nufi toilet da gaske ya tsumama mata jiki ta jima a toilet din tana kuka
maganganunsa sun Mata ciwo matuka har wani gori yake Mata Shima ba sonta yake ba, to an fada masa
ita son nasa take har yake wani Mata wulakanci, ita ta rasa a Ina ta kuskuro ne take haduwa da fitintinu
daga wannan sai wancan? "Astagafirullah".
Ta fada a zuciyarta, alwala ta dauro ta fito ba wani kwalliyar azo a gani tayi ba duk ranta a cunkushe ga 'yar
wayar da zata debe mata kewa ma ya dauke, a ranta tace "mugu kawai wani sumumu kasam dashi Kamar
na Allah Nan kuwa dan duniya ne Mai lasisi".
Tana cikin saka kaya taji karan bell alamun Baki a gurguje ta ida yafe gyalen rigar ta dan fesa turare tayi
gaba.
*****
Sai Bayan sallar magriba su zilai suka karasa gida dai dai lokacin Magaji ya fito da manya warmers a
hannunsa sai Autan Ammah da basket a hannunsa Shima, zasu kaiwa zahra abincin dare.
Suna shiga zilai ta wuce part din Ammah ta fada Mata sun dawo ita Kuma sahura ta nufi nasu bangaren sai
da zulan ta shige part din sannan sahura tayi wuf ta shige sashen Mama.
Salma kawai ta samu a falon tana kallon series na India ko arzikin amsa sallamar sahurar Bata samu ba sai
wani kallon banza tayi mata tana Fadin "lafiya Kika wani shigo afujajun haka?".
Kafin sahura ta samu zarafin Bata amsa Mama ta fito daga bedroom din ta tana Fadin Kamar maganar
sahura nakeji?"
Cikin azarbabi tace "nice Mama mun dawo".
Ta fada tana Zama a kasa kan carpet.
Cikin kwarewa da munafurci ta shiga korawa mamar bayanin abinda ta gani harta Kara da cewa.
"Anya Mama yaron Nan kuwa Babu abinda yake boyewa kin ganshi kuwa? Gaskiya wallahi baiyi kama da
fakiri Mai neman abincin yau da gobe ba, kayan abincin da muka zuba a store din wallahi ni wani abin ma
ban taba gani ba hatta madara wannan manyan gwangwwnaye sunfi ashirin Nama kuwa na kaji kawai sun
Kai hamsin Banda na rago Banda na shanu Banda kifi Allah Mama Saida muka cika freezer din cikin kitchen
din ga lemuka da ruwa Kamar banza ga......
Bata Bari ta garasa ba ta daga mata hannu "bar shi kawai jeki zan nemeki".
Mikewa tayi tana Fadin "a huta lafiya Bari naje nayi sallah naji ana Kiran insha'i". Ta fice.
Tunda ta fita Mama ke jijjiga Kai tana kwafa, Sam hankalin salma na can gurin kallon ta Bata damu da
abinda su mamar suke ba, Saida mamar ta Kira sunanta sannan hankalinta ya dawo Kan mamar tasowa
bayi ta dawo kusa da ita tana fadin.
"Mana menene Naga kamar ranki a bace,?".
Tsaki tayi tana fadin.
"Anya Abbanku da Asma'u ba ninkeni sukayi a baibai ba kan auren yarinyar Nan? ni daman tunda naga
daga b'angaren Asma'u da 'ya'yan ta da 'yan uwa ba wata turjiya nasan da abinda suka taka bakiji labarin
da sahura tazo min Rashi ba?".
Kai salmar ta girgaiza alamar bataji ba, Nan Mamar ta shiga fad'a mata abinda sahurar ta fada Mata, Nan
da Nan hankalin salma ya tashi ta shiga fadar "ai laifinki ne Mama Nan nazo na fada Miki naga wani inaso a
gurin Baba Malam Kika dinga zagina duk yanda naso ki fashimceni shi ba irin wanda kike tunani bane ni
naga abinda na gani Amma Kika shafawa idanunki toka kikaki saurarena ai gashi nan duk fafutukar ki ta
tashi a banza ko yanda kika fada min gidan yake ai kinsan da wata a kasa".
Ta fad'a tana share hawaye, Nan da nan hankalin Mamar ya Kara tashi idanunta sukayi jajur, cikin kaushin
murya ta Fara fadar.
"Ni za'a yiwa haka wallahi sai dai kowa ya rasa Dan wannan auren sunansa matacce dole ya saketa ko baya
kaunar Allah ai indai Ina raye yarinyar Nan sai dai kyanta ya Kare a banza ba dai tayi aure inda zata huta ba
ita da hutu sai dai tayi nata gaji da aiki, duk wani haske na rayuwarta saina dusashe shi Bari ma ki gani".
Ta yunkura ta Miki ta nufi bed room dinta tana lalubar wayarta.
Ayi hakuri ba editing Naga kwanaki wata na fadar kada a karanta rubutun ba kyau.
✨
✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨
✨
Story
&
Written
By
Maman Fatimah.
Godiya da yabo sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Amincin su tabbata ga shugaban mu
Annabi MUHAMMAD s.a.w.w.
________Mahmud Bai bar cikin hotel din ba Saida yayi sallar insha'i, cikin gari ya koma gurin malam
lokacin sun Fara karatun dare da maza manya Kamar Yanda suka Saba, shima littafin ya dauko na
Riyadussalihinp ya zauna daukar karatun sai gurin takwas, bayan jama'ar sun watse ya rage daga malam
din sai Mahmud da Habib.
Ganin Mahmud din ya zauna malam yasan da magana, Saida Habib ya gama gyara littatafan kusan aikinsa
ne shida Abubakar, bayan fitar Habib din kusa da malam din Mahmud ya matso Yana Fadin Baba barka da
dare".
Cikin sakin fuska malam ya amsa Masa Yana Fadin.
"Ya akayi ka zauna har wannan lokacin baka koma ba kasan ba sabawa tayu ba itama ya kamata a ringa
kula". Kai yadan Sosa Yana Fadin in Sha Allah yanzu zan tafi daman na tsaya ne Ina son muyi magana".
"To Babu laifi ina saurarenka".
Qara sadda Kansa yayi Yana Fadin.
"Daman game da maganar tafiyar da zamuyi ne nace ko za'a samu wadda zata zauna da yarinyar Nan ne?".
Gyaran murya malam din yayi kafin yace
"Eh hakan yayi dai dai saidai ka tuntubeta kaji nata ra'ayin tunda Naga gidan nasu da wadatar juma'a ko
wata zata tayata zaman tunda kasan sha'anin yau sai a hankali kada a Kai Mata wadda za'a samu matsala".
Tunda baba malam ya fara Kora bayani Mahmud ke gyada Kai sai da ya Kai Aya sannan Mahmud din yace.
"haka ne in Sha Allah zan nemi shawarar tata duk yanda mukayi zan fad'a maka, na gode" Ya fada kafin su
fad'a wata hirar akan wani sabon project da suka samu daga usaid karshi gwamnatin jihar Bauchi da
sukazo musu aikin plane na shekara bakwai. Bashi ya bar gurin malam ba sai wurin Tara da rabi, daya fito
ma majalissar su ya nufa gurin su salisu Nan suka dunga yi masa chari akan ya zagaye ya tafi gidansa bai
nemi rakiyar kowa ba ko rowar ganin Amarya yake musu, shi kuma ya Kare kansa da hujjar Shima be San
da zuwenta ba kawai da yamma Baba malam yace yaje can gidan ya jira Alhaji Jafar Yana son ganinsa, Yana
zuwa kuma ya ganshi da zahrar ya kawota da kansa, to wa zaya Kira Kuma ihu bayan hari.
Sunyi masa Allah Sanya Alkhairi da Alkawarin zuwa su gaida amarya sai goma ya karbi lifan din Habib ya
nufi hayin banki.
Lokacin daya shiga falon shiru ba motsin komai sai ni'imtaccen kamshin turarukan wuta 'yan asali da kuma
na roomfreshner masu dadin kamshi lumshe ido yayi Yana shakar kamshin.Nan da Nan yaji wata irin kasala
ta rufe shi ga wani mahaukacin feeling yana bijiro masa tun bayan barinsa gidan yake fama da wani irin
tunanin ta duk motsin da zeyi sai ta fado Masa,moment din yake tunawa duk da ba cikin dadin Rai yayi ba
Amma ya tsaya Masa a zuciya sosai Kamar magnet haka ya d'afe Masa.
A hankali ya taka zuwa tsakiyar falon komai tsab Kamar wani mahaluki Bai shiga falon ba, harya Fara Hawa
steps din da zasu sada shi da bedrooms nasu hankalin sa ya Kai wurin dining din manyan warmers ya gani a
hankali ya sauko ya nufi gurin abinci ne mai rai da lafiya sai Kuma pepper soup na cow tail da hadin salad
da alama na ba'a taba ba yasan aikin Ammarta ne kada kai yayi Yana fadin "wato abincin ne bazataci ba ko
me take nufi? baiwar Allah ta Bata lokacinta ta bada a kawo Amma ba za'aci ba"
Dakinta ya nufa Yana zuwa ya kama handle din yaji ta a rufe, shiru yayi wata zuciyar na cewa yayi knocking
wata Kuma na kwabarsa, juyawa yayi ya koma gurin dining din shi dai baze iya cin abinci Mai nauyi ba,
abincin ya dauka yabar pepper soup da hadin salad din tinda bashi da yawa.
Gurin Mai gadi ya nufa yana Fadin "Ga abincin nan a samu ayi amfani dashi yayi yawa".
Da hanzari ya taso Yana fadin "To yallabai ai dazu ma Mai gidan ta Aiko dashi har Saida na bawa wasu Yara
ma sauran, wannan kuma Bari na kira Mustapha yazo ya kai musu can gida madallah dai an gode da
dawainya".
"Haba ba komai gashi idan yazo sai ya biya mashin dasu". Ya aje Masa 5k akan warmer din ya juya yabar
Mai gadin Yana sheka Masa addu'a da fatan Alkhairi.
Saida yayi wanka sannan ya dawo dining din yaci iya Yanda yake ganin ya isheshi sauran ya Kara kaiwa Mai
gadin sannan ya koma daki.
Kan kujerar desktop computer ya zauna Yana kunnawa da ita akayi masa connecting din CCTV din dake
gidan, a hankali ya fara watching Yana kallon duk wani abinda ya faru a gidan wani irin murmushi yakeyi
lokacin daya ke kallon dabin su da ita da yadda tasha kukanta, wani Abu daya ja hankalinsa shine yadda
yaga su zilai da yadda yaga sahura tayiwa zilai dabara ta turata ciki gurin zahra, ita Kuma tana waya bayan
ta gama Kuma yaga ta shiga store ta fito tana kudundune Abu a cikin hijabinta wanda be San ko menene
ba, take a Nan ya Dora mata question mark.
Saida ya Gama ganin komai Dan yanzu ma littafi ne take karantawa har lokacin daya murda handle din
kofar da Yanda ta wani zaro sexy eyes din ta Kamar zasu Fado kasa saboda razana, murmushi yayi Yana
fadin "matsoraciya kawai wannan za'a Sha drama da ita Dan Naga alama shagwaba tabi jikinta Bata San
wahala".
Zahra kuwa tunda ta shige ta rufe kofarta tayi duk abinda zatayi na al'adun kwanciyar ta, sai ta dauko
littafin ta du'aul mustajaba tana karanta addu'ar barci, bayan ta Gama ta shafa shiru kawai tayi tana
tunane tunanen zuci ba, memories na abinda ya faru tsakanin ta da Mahmud ya shiga dawo Mata, Dan
guntun tsaki tayi tasa hannu a kirjinta data wuni suna Mata zugi, a hankali ta Fara magana Kamar Mai
gudun kada wani yaji ta.
"Jarababbe kamar maye duk ya cinye min labba da harshe ya shafeni tas yana wani gurnani kamar na zaki,
da wasu idanunsa da gani na fitinannu ne! Ni Zahra na gamu da gamona na shiga Tara bama uku ba,
shikenan na Zama nama sai Yanda hali yayi". Hawaye ne sharrr suka zubo Mata duk lamarin ya cud'e Mata
ta rasa mafita, alwala ta shige ta dauro tana ayyana gara ta kaiwa Wanda baya barci wani abu Kuma Bai
taba boyuwa ba a gurinsa kukanta tasan shine sami'uddu'a.
Sallah tayi raka'a hudu ta zauna tayi istigifari da hailala da salati ga fiyayyan halitta Annabin Rahama
Muhammad s.a.w.w har Saida taji zuciyarta ta samu nutsuwa kafin daga karshen ta daga hannuwanta
sama tana Fadi cikin raunin murya da Qasqantar da Kai ga Allah s.w.a
"Ya Ubangiji Kaine mafi sani ga abinda yake faruwa Dani, wani Abu Bai sameni ba sai da izininka na gode
maka a duk halin dana samu kaina a ciki, ka zama gata na,ka lullubeni da bargon Rahamarka, ka suturtani
da suturarka, ka rufa min asiri da rufin asirinka, kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka,
Ubangijina ga wannan bawan naka Nan kasan ko waye shi lamarinsa Ubangiji ka sani ba boyayye bane a
gurina Idan Yana da wani kaidi kada ka Bari yayi tasiri a kaina Dan isar Annabi MUHAMMAD a gurinka.
Ubangiji kajikaina ka duba raunina ka tausaya min kada ka Bari makiya suga wallena ka bani rinjaye a kan
dukkan al'amurana".
Duka hannuwanta tasa ta rufe fuskarta kamar me shafa addu'a Amma kuka ta saki Mai tsuma zuciya tana
ayyana "Wai fa ita Amarya ce wadda ya kamata ace a irin wannan time din ana can ana riritata kamar a
hadiyeta dan so da kauna da tarairaya da kulawa. Amman nata da haka yazo Mata, Astagafirullah Ubangiji
ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan gararin rayuwar".
Ta dauki dogon lokaci tana shashhsheka a haka barci yaci karfinta ta sulale a gurin yayi awon Gaga da ita.
Bata farka ba sai kusan biyar da rabi cikin sauri ta tashi tana fadin "subahanallahi!"
Da sauri ta nufi toilet tana addu'ar tashi daga barci, a gurguje tayi uzurinta tayi alwala ta fito sallah tayi ta
zauna yin Azkar da karatun qur'ani har gurin takwas na safe.
Mahmud Bai dawo gida ba daga sallar asuba gurin Sameer ya wuce, so yake yi suyi duk abinda ya kamata a
Nan tunda kwaso jiki ya taho, shi yasa jiya yaqi yin komai yayi kwanciyarsa kawai.
Ba karamin mamaki Sameer yayi ba ganinsa da yayi a irin wannan lokacin to ai ko lokacin da taye single
baya Masa sakko haka. Amma sai gashi shida yake expecting dinsa gurin one-two haka shine ya ganshi
haka kamar an koroshi.
Cikin zolaya yace "My man ya naga haka ka duba time kuwa? Ka fito kabar 'yar mutane ko dai da matsala
ne na fadawa Babanka manya su shiga ciki, sun baka yarinya girma -girma kana neman ka bada musu yaji a
ido duk Wanda ya ganka a irin wannan lokacin daya Kamata ace kana can kana Shan kafi tea, ai sai mutane
su dauka fanko aka kawo maka, gaskiya ka yiwa Allah ka koma ni zan shigo mu karasa aikin a gidanka
daman meke kawo mu Nan? ba bukatar privacy ba? to yanzu muna dashi kaga no need sai munzo Nan
Kuma kasan yanzu ba da bane ".
Ya fada ba alamar zolayar yanzu, ikon Allah Mahmud ya tsaya yana kallo kafin yace "ka Gama Alhaji
muhammadu tunda Naga alamar roll din tsohona kake playing, to Wai Ina ruwanka da harkar Nan Ina
cewa Mata dai tawa ce yanda nayi ra'ayi haka zan tafiyar da abina, ai dalilin daya kawoni kenan kazo mu
ida duk Wani aikin da zamuyi kaje kayi sallama da malam ka kama gabanka".
Ya zauna Yana dauko laptop din Sameer Yana operatin dinta.
Kusa dashi Sameer din ya zauna Yana fadin "Allah ya huci zuciyarka angon Zahra da Safnah....." wani kallo
Mahmud ya watsa Masa wanda yasa Sameer yayi shiru ba Shiri, shi kansa baisan sanda bakinsa ya furta
sunan safna ba ko alama.✨✨
✨✨
✨✨
✨✨
Story
&
Written by
Maman Fatimah.
________Zahra ba ita ta farka b sai gurin bakwai da rabi, sai lokacin ta tuna ta cewa Musaddiq ya fadawa
Ammah ta bar kawo abinci zata dafa tunda ba komai take ba, toilet ta fad'a ta Dan sakarwa kanta ruwa
Bata jima ba ta fito Riga da Wanda na Pakistan ta saka tayi rolling da gyalen ta saka plat shoes na daki ta
nufi falo Amma zuciyar ta tana ta dar- dar kada suyi arangama da Dodon nata, falon ta shigo shiru sai
sanyin A/C da daddad'an kamshin da yake ga curtains din duk a sake ga fitilu masu qarancin haske a kunne
saiya bada wani irin yanayi Mai saka nutsuwa.
Dan waige-waige ta Fara Kamar tana neman wani Abu gurin sai Kuma ta nufi gurin tv ta tsuguna tana hada
socket din adapter din tv ta kunna ta kamo tashar Almajid, kokacin sun saka Qira'ar Muhammad Saddiqul
minshawi a cikin suratul ISRA'I sai da ta dai daita volume din sannan ta nufi kitchen din a nutse da takunta
Wanda da yawa suke ganin yangace da jiji da Kai alhalin ba haka bane naturally haka Allah yayi ta.
Kitchen din ta shiga Kusan shigowarta ta uku Kennan, lokar da taga kayayyakin aikin ta bude ta dauko roba
mai Dan Fadi ta nufi store ta debo Irish ta fito wanke shi tayi ta fere ta zuba a tukunya ta kunna gas, sai
kuma ta dauko kaza guda ta yanka ta wanke ta zuba seasoning da spices ta rufe, ta jona egg boiler ta zuba
kwai hudu a ciki.
A gefe kuma ta dauko attarugu da Albasa ta yanka kananu ta aje a gefe Irish din ta Fara dubawa taga yayi ta
sauke ta zuba a container Mai zurfi tasa fork ta murje ta dora frying pan ta zuba Mai kadan ta saya
attarugu da albasar ta zuba a Kan irish din ta zuba magi da curry ta fasa ta yanka dafaffen kwan a ciki
sannan ta fasa danye ta zuga ta juya ta aje ta duba kazar itama tayi Nan da Nan ta hada pepper chicken
sannan ta jona tanda electric ta Fara zuba hadin Irish din Nan tana soyawa Kamar masa, tana gamawa tayi
pepper chicken. Dora ruwa tayi a karamar tunya kafin ya tafasa ta dauko madara ta bude ta diba a wani
bowl ta dama sannan ta dama corn flour a cup, jikin kitchen cabinets din ta tsaya tana bin karatun da yake
shigowa daga parlour har sun kai suratul D'AHA.
Madarar ta zuba taci gaba da tafasa sannan ta zuba corn flour din ta daure da yayi dai dai yanda takeso ta
sauke ta Kara Masa condensed milk a cikin ta juye, hadesu tayi a babban tray tayi ta nufi falon, Nan akan
dining table ta jero komai sannan ta koma ta dauko sauran tarkacen su cups.
Kitchen din ta koma ta gyara gurin tas, sannan ta koma daki wanka ta shiga, tana fitowa ta shafa lotion
dinta tayi simple makeup ta saka saka turarikanta na jiki dasu humra Nan da Nan jikinta ya shiga fitar da
wani fitinan Nan kanshi, doguwar rigar Dubai Mai kananun stones pink mai duhu ta saka rolling tayi dan
Vail din
rigar milk colour sai ta fito balarabiyarta sak Dan idan ba kaji tayi maka Hausa ba bazaka taba cewa tasan
ko zo da Hausa ba, tayi kyau matuka yarintarta ta fito sosai idan ka kalli fuskarta very cute sai wani annuri
take fitarwa.
Parlour ta fito gurin dining din ta nufa cikin takunta das das. Tana mamakin Ina ya shiga Dan ko motsinsa
babu har yanzu ita kuma bazataje bedroom dinsa ba, idan ya gaji da zaman dakin ya tunda ba yaro bane
yunwar cikinsa ta fito dashi. Kunun madarar ta zuba da masar Irish din kwara biyu kawai ta dawo main
parlourn ta zauna tana ci tana sauraren karatun, sai da ta gama ta Kai kayan kitchen ta wanke sannan ta
dauko Wanda ta zubawa baba Mai gadi ta nufi kofa a hankali take tafiya a cikin harabar gidan iskar
bishiyoyin da sauran shuke shuken suna kadawa gwanin sanyi can gurin gate taga baba Mai gadin ya nufa
da sauri da alama budewa zeyi.Dan tsayawa tayi daga gefe idonta Yana kan gate din Dan taji dirin mota
zata shigo cikin kankanin lokaci motar ta shigo ido cikin ido sukayi da shi shine yake driving din gabanta ne
ya bada ras ras Kuma ya kafeta da fitinannun idanunsa cikin gwaninta ya nufi parking lot, Sameer kuwa
Kamar wani sakarai haka yake kallon zahrar Yana tsarkake suna Allah a zuciyarsa ya ganta har kusan hudu
Amma da alama ganin tsoro yake Mata sai yau yaga zahirin zahrar, da sauri baba Mai gadin ya karaso yana
gaisheta ta Mika Masa Dan Karamin basket din ta juya da sauri ta nufi kofar falon har Kamar tana dan
sassarfa ta shige ciki, harta wuce idanun Mahmud suna binta Nan da Nan yayi kicin-kicin da fuska daman
ga Sameer ya tabo shi ga itama da kalar nata shirmen, cikin zafin nama ya kashe motar ya Kama kofar ze
bude Sameer ya kamo hannunsa ya rike Yana girgiza masa Kai kafin ya dungule dayan hannunsa irin na
roko din nan yace.
"Pls Dan Allah cool your temper kada kaje mata a haka kayi Mata uzuri Batasan Kai ko waye ba, Kuma
infact ma laifinka ne ka tafi ka barta a gida har zuwa wannan lokacin Kuma tana ganin hakan da tayi shine
dai dai koni nayi supporting dinta hakan shine dai dai ta nuna maka tasan haqqin abinda ka bar mata
amana" .
A Dan fusace ya kalli Sameer.
"Nine na Bata amanarsa da izuninwa ta fito nan wato. ya kalleta yanda yakeso ko? Matata take kaiwa Mai
gadi abinci wannan wane irin zubewar aji ne a gurina? Dubi fa yanda ta fito? Ko baka gani ba?"
Ya fada yana kallon Sameer.
"Ni banga wani Abu na rashin kyautatawa ba a shigarta, kawai dai idonka wani Abu ya nuna maka na
daban gaskiya".
Hannunsa ya zare daga cikin na Sameer din ya bude kofar a hankali ba Kamar dazu ba zagayowa Sameer
yayi ya rufe motar yabi bayansa Dan Idan ya Bari ya shige irin na jiya ze masa ya ajeshi a waje, kofar ya
bude wani sanyi da kanshin girki Dana turarikan daki sukayiwa Sameer sallama Bata Nan sai tv a kunne ana
karatun har lokacin.
Direct gurin dining Sameer ya wuce yana fadin Bari na Fara da Nan Idan na gama ma gaisa tunda ba bako
nake ba ya Fara budewa Yana kallon Mahmud Yana fadin.
"Tab da alama Allah ya tarfawa garinki nono irin wannan delicious".
Gaba Mahmud yayi Bai tanka Masa ba ya shige ciki.
Kofar bedroom dinta ya kalla har dariya take bashi bilhaqqi da gaske tsoransa takeji bare Kuma da jiya ya
Dan motsa mata Jamiyya.
Ta Dan Dade a bedroom din nata daga baya ta bawa kanta kwarin Gwiwar ta fita ko banza bazata bada
kofar da wani na waje ze gane da 'yar tsama a tsakaninsu ba Kar a Raina Mata wayo, fuskarta ta Dan Kara
shafawa powder kadan ta Dan Kara fesa mouth freshner Mai kamshi apricot ta nufi kofa tana budewa
saura kadan yau ma suyi karon, da sauri taja Baya. Shigar kananun Kaya yayi as usual dan zaman da sukayi
ta fashimci kamat ya samu wani freedom ne na sakewa, trouser black da milk T-shirt ne a jikinsa hannunsa
daure da agogo sai waya a hannunsa. Baya tayi da sauri tana Dan zare idanu Dan ba Karamin tsoro taji ba,
Shima kallon ta yake Kamar ya rungumota ko yaji relief na abinda yakeji a zuciyarsa, amma sai ya share ya
Mika hannunsa ya kamo nata ya natso da ita kusa dashi Sosai Yana Fadin "kin tashi lfy?".
Ya shafi gefen fuskantar, cikin siririyar murya tace masa
"Ina kwana? Shiru yayi Kamar beji ta ba, ya janyo ta suka Fara tafiya a cikin corridorn, sai da suka Fara
gangara steps din taji yace waya Baki izinin fita gurin watchman din can?"
Ya Dan matse hannunta dake cikin nasa.
"Wash!!! Allah ta fad'a ba tare data shirya ba. Dan da gaske matsewar ta shigeta dago Kai tayi cikin narke
fuska Kamar zatayi kuka dai dai lokacin Sameer ya dago Kansa daga daddana wayar da yakeyi Jin
maganarta Sam beji tahowarsu ba wani irin perfect match couples ya gani sun masifar dacewa da juna ya
Dade bega ma'auratan da suka burge shi kamar su ba, a zuciyarsa yake Fadin.
"Masha Allah".
Zahrar Tace masa.
"Ba kowa, Dan Allah ka sakar min hannu wlh zafi...."
Ta fada cikin shagwabar da Bata San tayi ba.
Murmushi Sameer yake ta saki daga inda yake Dan ba karya yasan muhmud yayi dacen da Basu zata ba
abun kamar a film yake ganinsa. Dan lokacin da suka Fara ganinta da Kuma furucin da shi Mahmud din
yayi ashe Allah ya karbi addu'ar.
Dan gyaran murya Sameer yayi Yana kallon Mahmud din tare da fadar.
"Yallabai a bar madam ta karaso mu gaisa Mana ni ba mazauni babe gaba nayi daga Nan"
Ya fada da sigar zolaya duk yaga har yanzu kamar Yana Jin zafinsa tun maganar da yayi masa na Safnah.
Sassauta rikon hannaun yayi suka ida gangarowa directly dining area ya nufa yana zuwa ya ja Mata kujera
ya zaunar da ita sannan Shima ya janyo ya zauna.
Gurinsu Sameer ya karaso daga inda yake zaune Yana fadin.
"Madam barka da Asuba kingan ni sai yau ki?".
Ya fad'a yana Zama kusa da Mahmud.
A kunyace ta amsa da "lfy kalau Ya Sameer ya kaje gida? Ina madam?"
"Komai lfy ya hakuri damu?".
'yar dariya tayi kafin ta Mike ta Fara bude abincin Wani daddad'an kamshin ne ya doki hancin Mahmud har
Saida ya lumshe idonsa, Dan kallonsa tayi sannan ta kalli Sameer tace "me za'a zuba?".
Kai Sameer ya girgaiza Yana fadin "ai ni na riga ku ci tun shigowarmu naji bazan iya jiran masu gidan ba
saina shide Ina jin kamshin delicious Amma ace saina jira".
Ya fad'a Yana dariya.Dan murmushi Mahmud din yayi.
"Wato ko Ina saika nuna halinka ko?".
"Pls zuba min kawai".
Kallonsa tayi kasa-kasa, tace "Toh"
Masar dankwalin turawan ta zuba sannan ta zuba pepper chicken din ta tura Masa sannan ta zuba kunun
Madarar sannan ta koma ta zauna a darare.
Wani cup din ya zuba kunun Madarar ya dauko da fork ya matso kusa da ita da plates din abincin yace.
"Oya saka hannu muci".
Ya wani hade gabas da yamma alamun ba wargi Kai ta shiga girgaizawa alamar ta koshi Shima ture abincin
yayi Yana duban Sameer.
"Muje kawai"
Ya fad'a yan Jan kujerar baya.
"Zanci".
Ta fada a gajarce.
Komawa yayi ya zauna Yana fadin "fine tunda zakiçi gara Idan mutuwar zamuyi mu mutu tare Dan naga
abinda Mata suke yayi kenan Idan aka Basu Wanda ba shine zabinsu ba su kashe shi su auri wanda
sukeso".
Tunda ya Fara Kora bayani Zahra tayi masa kur da ido tana Mai maita.
Kai Sameer ya shiga girgaizawa Yana mamakin wani sabon hali da Mahmud din ya tsira, yaga alama nema
yake ta Hana yarinyar Nan sakat.
Ita Kuma tunda ta furta zanci Bata Kara tofa ko kalma daya ba, sai kawai ta dauki fork ta cako Irish din ta
Kai bakinta ta tauna ta hadiye, pepper chicken din ta dauka taci ta dauki kunun Madarar ma ta Sha duk
Yana kallon ta shi kuwa Sameer Yi yayi Kamar Allah Bai halicce shi a gurina ba.
Tana gamawa ta tura kujerar da take Kai baya sannan ta dubi shi ido cikin ido tace.
"Gashi naci idan kana tunanin zan zuba maka poison a abinci kayi kuskure lalacewar tawa Bata Kai haka ba,
Idan na kasheka wace riba zanci? wato ka tafi lahira free ko? duk lodin zunuban daka dauka niga sakarai na
lodawa kaina, to Bari na fad'a maka ba saina aikata zunubi irin haka zan rabu da Kai ba A'a salin alin kowa
ze kama gabansa ni da Kai tunda daman masu iya magana na cewa tsintacciyar magen Bata mage nasan
komai Daren dadewa zaka koma inda ka fito".
Ta fad'a Tana wurga masa harara ta wuce ta kyalesu batabi ko takan Sameer da yake fadin "Allah ya huci
zuciyar amaryarmu".
Da ido Mahmud yabi Zahra har ta bacewa ganinsa "Wai shi yarinya kamar wannan zata saka shi gaba ta
fada Masa son ranta amma yayi shiru Yana kallon ta".
Sameer ne ya katse Masa tunanin da yake.
"Dan Allah kada ka koya matsa tsiwa wlh da gani Bata Saba ba, bakaga jikinta har rawa-rawa yake ba".
Ya fad'a Yana kallonsa.
"Jikinta na rawa kenan Kare mata kallo kayi har kaga jikinta na rawa ni ban gani ba?".
"Subhanallahi! Wace irin magana ce haka wlh ba haka nake nufi ba, Bari naje kawai sai munyi waya".
Ya Mike Yana aje rafar dari biyar guda biyu Yana fadin "A bawa madam ace Mata na wuce tunda ka Hana
muyi sallama".
Ya biya Kan center table ya dauki keys dinsa yayi gaba tunda yasan ba magana Mahmud ze Masa ba Dan da
gaske yazo wuya yanda yanayin fuskarsa ta nuna.
Bayan fitar Sameer, Mahmud kasa ko motsin kirki yayi wai shine tsintacciyar magen? Da gasken gaske
maganar ta dokeshi kwafa yayi Yana fadin zakiga tsintacciyar mage iya ganinki sai kin gane bakin rijiya ba
gurin wasan makaho babe".
Ji yayi kwata kwata abincin ya fice masa raga Rai duk yanda yake jin yunwa ture abincin yayi ya Mike ya
nufi bedroom dinsa Bai jima ba ya fito cikin shigar yari filtex fari dinkin boda da farar hula a Kansa Yana
baza qamshinsa na Ibada, yayi waje.
Tunda Zahra ta Fadi maganar dake ranta taji zuciyarta wasai, gefen bed dinta ta zauna tana mita.
"Haka kawai saika wani ringa sakarmin magana ba control duk abinda yazo bakinka saika fad'a mini, Wai na
saka wani Abu girkinma ba saina Kara yo da Kai ba sannan na Zama suspect daman saboda A kashedin
Ammah ne yasa nayi, kwana biyu amma kamar na shekara duk ka matsa min ka karbe min waya nayi Shiru
na Zuba maka ido Naga gudun ruwanka, na fita mikawa bawan Allan Nan abinci kace da izininwa? Haka
kawai ka zamar min karfen kafa".
Ta fad'a Tana kwafa.
Tunda gari ya waye Ammah Bata zauna ba shirye-shiryen tafiyar Inna maimuna take wadda zata tafi yau,
cikin Shirin fita unguwa Mama ta shigo lokacin Ammar na zubawa innar kilishin da Abba yasa akayi Mata
zaunawa tayi tana Fadin "Inna yau zakiyi Mana ta Baki wlh ba dadi".
"Kayya Hajiya Rabi banda abun yazo da sammazi Aida na jima da tafiya gida daga zuwa biki na share our na
zauna kinsan da Ardo Yana Raye hakan ba zata faru ba yaushe ze Bari".
"Haka ne Kam Allah yayi musu Rahama".
"Amin" su Inna suka amsa.
Leda mamar ta aje kusa da innar tana Fadin.
"Gashi Inna ba yawa Allah ya kiyaye hanya ni fita zanyi unguwa nasan kafin na dawo kin tafi".
Gdy innar da Ammah sukayi Mata ta tashi tana yiwa innar fatan sauka lafiya.
Sai bayan ta wuce ne innar ke tambayar Ammah ina Hameeda ne Naga tun she jiya da safe bata qara
ganinta ba.
"Jiya kina barci tazo Nan Wai ta tafi Jos gurin yayar mamansu larai".
"To ba laifi hakan ba laifi daman shekaranjiya ne da dare na fita zanje can inda na baza ganyen yandi Dana
shanya naji uwar tana surfa Mata zagi ban dai San dalili ba Amma naji ita yayar tata tana Fadin sai kije kiba
Zahra hakuri Mana tunda kanwar uwarta ce ni dai Nan na barsu Dana dauko shanya ta".
"Allah ya rufa asiri kowa yayi nagari Kansa ya yiwa kuma sharri Dan aike ne duk inda ka tura shi ze dawo,
bansan abinda yarinyar Nan ta tsare musu ba, bana raba day biyu da abinda sukasa Hameedar tayi inaga
daga baya ta gane Bata kyauta ba shine tayi magana uwar ke zaginta".
Sun Dade suna tattaunawa.
Gurin Sha Sha daya da rabi magaji yazo ya dauki Inna maimunar zuwa gidan Zahra.
Zahra na barci Dan batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba, cikin barcin taji alamar bell din kofa
ta yunkura ta tashi ta yafa Veil din rigar saman gashinta.
Tana budewa taga Inna maimuna da magaji, jikin innar ta fada kawai sai ta saki kuka Wanda ita kanta bata
San kona menene ba.
" Ke matsa can da Baki rabuwa da shiririta saboda Allah menene abin kuka magidanciya dake, Dan Allah
duba min Nan Mai sunan malam wannan ai rashin wayo ne koba haka ba?"
Ta fad'a Tana kallon magaji, duriya yayi Yana fadin "kumfi kusa Inna na bankwana ne tunda Idan Kika shige
wannan lungun Sai baba ta gani, ni Naga ma kinyi Rana gaskiya har yanzu Baki tafi ba".
"Ai a Gombe zanyi kwana biyu gidan Dan aminiyata da nayi rainonsa to nayi Masa Alkawarin zuwa idan zan
tafi".
Ita dai Zahra tunda ta kwantar da kanta a cinyar Inna maimuna Bata Kara dagowa ba, jinta a jikin innar sai
takejin wani sauki da nutsuwa suna saukar mata.
Gashin Kanta innar ta Dan shafa inda gashin ya fito tana Fadin shi dai wannan gashin baisan kitso ba
Kullum Yana Nan a nannade kamar gammo".
Dan turo Baki tayi tana Fadin
"Ya zanyi kinsan ba kitsuwa yake ba ko anyi idan ya Dade kwana biyu ne kawai ga zafi".
"Allah ya kyauta kawai dai 'ya'yan zamani Amma har yaushe za'a yita Zama da Kai haka? Yau Wai uwar taku
tace meya samu wayarki ko an Kira Bata shiga? tasan ba rashin caji bane tunda ance Kuna da wannan abar
Mai amfani da hasken Rana"
Dan Jim Zahra tayi tace ya karbe wayar ai hakan be dace ba, Sai kawai tace.
"Nima bansan meye matsalar ba kawai rufewa tayi taqi kunnuwa".
Magaji ne Wanda yaketa faman cakular waya dago Yana fadin dauko mugani ko abun minor ne".
"Bata gurina tana gurinsa ban sani ba ko dubawa ze bada ayi".
"Shu wa?"
Ya fad'a da sigar zolaya, banza tayi masa kamar bataji ba.
Tashi daga jikin innar Zahra tayi tana Fadin Bari na dawo wlh murnar ganinki ta mantar Dani ko ruwa ban
kawo Miki ba". Tayi gaba innar na Fadin "dawo Zahra'u nida ba bakuwa ba".
Gaba tayi abunta.
Saida ta ciko tray babba da dangin Zaki da sanyi har sauran pepper chicken din ta zubo musu, tunda ta aje
innar ke binta da kallo tana jinjina abin wannan cimakar bata mai Karamin kafin bace ko ance gida tallafin
qungiya ya samu har abinci ci susuka dauki nauyin bashi?"
Ita dai shiru tayi Bata tofa ba Amma a kasan zuciyarta da maganganu fal Wanda zasu tattaunawa da 'yarta.
Ware ciki magaji yayi ya kwashi gara har Inna na Masa Dan biki.
Wayarsa Zahra ta barba ta Kira Ammah ta gaisheta itama abinda ta fadawa innar ta fada Mata game da
wayar lokacin data sauke wayar harda share 'yan hawayenta, magaji Yana Mata tsiyar shatwabarta tayi
yawa ita Batasan ta kusa Zama uwa ba,Inna na Taya shi.
Sai da Innar ta Gama sannan ta tambayi Zahra.
"Wai Ina Mai gidan nawa ne banji motsinsa ba tunda nazo?"
Kafin Zahra ta lalubo abin fad'a magaji ya rigata Yana fadin.
"Ai kin baroshi can a unguwar mu gashi nan suna magana da Ya Abdul Hakeem a kusa da masallaci har
suka daga Mana hannu".
"Awoh to ai kasan ban waye dashi ba sai a hankali".
Nasiha Sosai da ban baki Inna maimuna ta Kara yiwa Zahra tare da kara jaddada Mata mashinmancin
biyayya ga miji.
Kaya Zahra ta zubawa inna a wata babbar leda harda atamfa dasu turaruka taba Magajin ya rike mata.
******
Tafiya ce miqqqqiya daga Azare zuwa Babban mutum ta Babura jihar jigawa, direban daya dauko Mama da
Asabe ya Dan juyo yana kallon Asabe wadda ta maida hankali gurin cin doyarta da kwai da suka saya a
kanya babba yace ",munzo Babban mutum fa Ina zamuyi kinyi shiru alhalin kece idona tunda wannan ba
yanyata bace".
"To na manta wallahi kasan da Dan Habu muke zuwa na zata shine ita dai Mama Bata cewa komai Dan
niqab nema a fuskarta badan ta matsu da son ganin malam na bande din ba da ba yanda za'ayi tayi
wannan kasadar Dan yanda ta fadawa Abban Itas/gadau zasu wata dubiya Alhajin yaso Bala direba ya Kaita
ta nuna Masa da kawarta matar tshon Ambassador zasuyi tafiyar abinda ya Hana Bala direba kaita kenan,
hanyar tinkin ta nuna Masa alamar Niger zasu shiga.
"Yanzu ke Asabe a she Niger zamu shiga shi ne kikace min kauyen Babban mutum wlh da bani da takardar
ecowas da Saida na zubeku ku nemi wadda zata karasa daku kinsan kuwa yanda suke da doka da order?".
Tafiya ce miqqqqiya daga Babban mutum zuwa bande, sun Sami tarba Mai kyau daga yaran malam na ciki
suna fitowa su Asabe suka shiga malam din yana zaune akan buzu da wani zabgegen carbi a hannunsa ya
amsa musu sallamar su suka zauna suna gaishe shi.
Asabe ya dago kai kalla.
"Baki fad'awa Hajiya sakona ba?"
"Allah ya taimaki malam na fad'a Mata cewa tayi na kawota gurinka tazo taji Koda yanda za'ayi lamuran ne
suke neman canza fasali".
Carbinsa ya Fara ja yana girgiza Kai yayi hakan kusan say uku kafi ya sauke wani dogon numfashi yana Kara
girgiza Kai.
Mama cikin kidimewa ta furta.
"Da matsala ko malam?".
"To da matsalar Amma Abu mafi ban mamaki shi yaron har yanzu bana ganin komai akan Lamarinsa kwata-
kwata sai yau Naga wasu mutane a Kan lamarinsa da Kuma itama yarinyar an tasa ta gaba da dafa'i shiri
Kuma na gasken gaske sai dai naga wata tafiya a gaban mijin nata da alama Kuma tafiyar da Alkhairi q a
cikinta sai dai idan dauke hankalinsa za'ayi daga garin kwata kwata, idan ya tafi ya kasa ko tunanin garin
bare ya dawo, idan ba haka akayi musu ba ba makawa sai kin Zama 'yar kallo a gidan dan duk yaran gidan
Mata ba wadda tauraruwarta ta kama kafar tata da gaske haka Allah ya yita da madaukakin Alkhairi".
Zuru Mana tayi ta kasa magana, maganar dai ita kenan Zahra tafi nata 'ya'yan.
"Malam ayi duk abinda ya Kanata inda hali ma ya rattaba Mata saki kafin yabar garin".
""Abinda ban gani ba kenan a cikin auren nasu Dan Idan shi ne ze saketa to inaga sai dai ta mutu da auren
Dan Banga hakan ba a tare dashi,ni a yanda na gani a istiharata ma ya Santa batun a Nan garin naku ba
Kuma da soyayyar ta Mai karfi a zuciyarsa wadda har abada baze iya rabuwa da ita ba, ayi dai hakan yanda
Idan iyayenta suka gaji da jiran dawowarsa Bai dawo ba su raba auren da Kansu". Bayanin ya kwantawa da
Mama hankali, ya kawo abubuwa ya bata har Wanda za'a hada da tuaren wuta a bawa zahrar Idan harta
turara Mahmud ya shaqa shida Azare har abada.
Kudi masu kauri Mama t✨✨
✨✨
✨✨
✨✨
MAMAN FATEEMAH
"Hakan ma na gode tunda an karbi Auntyn ai shike nan tunda ita ta gari batayi laifi ba saini da nake can
kauyen mu".
Ta fad'a Tana Zama a cikin one seat dake kusa da ita.
"Eh wlh Aunty tana da excuse a gurina tunda nasan Bata Nan taje gida sokoto Amma ke kuwa ko waya fa
Baki Kira kinji ya ake ciki ba".
"Kice dai ban Kira ba. Amma tambayi Sajida kiji na kirata yafi sau ashirin ma ke dince lokacin Kiran baze
yuwu ba Sai ki qara narkewa".
Dariya suka saka su duka harda Aunty safiyyar.
"Wlh Amah saina rama kinci bashi, Wai na narke kamar wani danyan tuwo".
"To da mecece? mutuniyar dake somewa Kikayi fa dif kika dauke wuta".
Kyale Amatu Zahra tayi ta karasa kusa da Aunty safiyya ta zauna ta Dora Shureem a Kan cinyarta tana
Fadin.
"Aunty sannu da zuwa Ina yini?"
Parlour suka dawo sukaci gaba da Hira, rabi duk ban Baki ne Aunty safiyyar kewa Zahra da nuna Mata ribar
hakuri a cikin hirar ne Amatu take fadawa Zahra sakon Sajida na tana kiran wayata Amma Koda yaushe
switch off.
Dan lumshe ido tayi sannan ta bude tana kallon Amatun.
"Matsala wayar ta samu shi yasa ba'a samuna Amma in Sha Allah soon zan sayi wata, yanzu bani taki na
kirata".
Wayar Amah ta Mika Mata tana dialing din number ta.
Tana dauka ta Fara mata tsugudidi.
"Yau wacce Rana Amatu ta kirani".
"Assalamu Alaikum ayi sallama Mana bestie".
Ta fad'a tana murmushi.
"Kai!!! wa nakeji haka bestie, haba Dan Allah kin kyauta kenan ba waya ba wasika kin barni a tunani kala-
kala Sam na kasa samun nutsuwa". Tashi Zahra tayi ta shige ciki tana Fadin "Bari kawai bestie guy din nan
ya fa karbe wayar tun ranar da Kika tafi ya dauketa da safe daya shigo, shine fa daya shigo ya tarar duk na
hargitse gado ina neman ta yace tana gurinsa, ya kama min wasu zantika akan Kiran da Musbahu yayi
ranar ni kuma na kasa hakuri shine yayi min Rashin mutunci Kuma ya hanani wayar".
Ta fada kamar zata fashe Mata da kuka, tambayar ta tayi yanda abun ya faru Bata rufe Mata komai ba ta
fada Mata. Bata katse Mata hanzari ba har ta gama.
"Amma ban taba sanin Baki da wayo ba sai yau, Gaskiya Baki kyauta ba ko alama Ina hankalinki ya tafi kada
ki Kara Koda Wasa saboda wani ki ciwa mijin aurenki fuska ai wallahi jarimi ne daya iya hadiye fushinsa
bakiji a jikinki ba".
Ta fada a kufule, kit ta kashe Kiran.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana kallon wayar a zuciyarta tana fadin ji a jiki na nawa Kuma ba ze fadu bane
shi yasa.
Lokacin da zahrar ta fito wasu bakin ta tarar sun shigo su biyu har Amatu ta kawo musu ruwa da drinks
suna hira dasu Aunty safiyya, sallama tayi musu sannan suka gaisa Nan Amatu tace musu "ga matar gidan
nan".
"Masha Allah"
Suka fada a tare sannan babbar wadda zatayi kamar sa'ar Aunty safiyya tace "mune makotanki da hannun
dama sunana Hafsat Amma ana kirana maman junior, wannan Kuma kanwata ce Nuratu da take karatu a
Nan Abubakar Tatari Ali polytechnic (ATAP) aiki ne ya kawo Mai gidana mu 'yan Taraba ne".
"Masha Allah! Allah ya taimaka ya bada sa'a".
Suka fada.
Sun Dan jima ana hira dasu sannan suka tafi har gate Amatu ta rakasu da ledar kayan garar biki.
Suma mikewa Aunty safiyya tana goya Shureem da yayi barci, Dan langabar da Kai Zahra.
"Wai har zaku wuce ne Kuma Aunty?".
"Eh mana zan shiga gidan fachalata data haihu bana Nan".
"Amman Banda ke dai Amah gaskiya tunda nasan kina garin Nan sai karshen wata keda jama'are".
Aunty safiyya ce ta tari numfashin zahra
"Ai ita ke driving dinmu ya zan barta a Nan ta dawo Miki special ko weekend ne".
Alamar bude kofar da akayi ne yaja hankalinsu, Mahmud ne ya shigo Yana musu sallama da katuwar leda a
hannunsa, tunda ya shigo Aunty safiyya ke kallonsa ita dai tasan wannan fuskar amma ta Yaya za'ayi haka
ko Kuma kama ce kawai.
A cikin takunsa na cikakken namiji ya shigo, da sauri Zahra ta nufo gurinsa tana Fadin.
"Sannu da zuwa". Tana Mika hannu zata karbi ledar.
"Da nauyi bazaki iya dauka ba".
Ya fada Yana kallon ta.
Har cikin kitchen ya shiga da ita sannan ya wuce bedroom.
Amatu ce ta zunguri zahra.
"Ke! meye hakan Kuma? Kika wani sharesa Kada dai kice min sokoncin da kike bazawa a gidan kenan ko
Kuma Dan kin gammu ne kikayi wani biris dashi".
"Gaskiya Kam ki dage ki Kama mijinki irinsu tsada suke".
Aunty safiyya ta fada tana nunawa Zahra hanyar daya bi.
"Kai! Aunty Kuma ......"
Bata karasa ba Amatu ta Kama hannunta ta nufi steps din tana Fadin "kije kawai tunda daman tafiya
zamuyi saina shigo Saturday in Sha Allah".
Dan raurau tayi tana kallon Aunty safiyyar.
"Na gode Aunty ku gaida gida saina zo har gida ban gajiya".
Dariya Auntyn tayi.
'Haba dai sai dai mun dawo, wannan turaren kada kiyi Wasa dashi tun daga besse na taho Miki dashi
kakata ta wurin Babana take haduwa da Kanta Yana da matukar kyau sosai ba sai fada Miki ba da kanki Zaki
nema".
Dawowa tayi Saida ta rakasu har gurin mota duk da mitar da Amatu ke mata, ta hadasu da kayan garar fal
ledoji biyu dasu bokitan roba da mug masu kyau da plates Wanda Aunty Hasana ta bada aka kawo mata
saboda Baki masu zuwa.
Saida suka fice daga gidan sannan ta dawo ciki.
Bata shiga ciki ba a parlourn ta zauna tana mitar. "Idan na shiga me zan Masa wanda yake ganina a wata
Mai neman rayuwarsa".
***
Saida Amatu ta dai daita a titi sannan da Dan dubi gurin da Aunty safiyyar ke zaune tana rungume da
Shureem.
"Aunty nifa wani Abu ya bani mamaki da daure Kai"
"Kamar me fa?".
"Duk gari ya dauka an aurawa zahra Almajiri k'olo saboda ita ba 'yar Alhajin bace, surutu dai gashi nan, ni
Kuma yanzu Naga sabanin abinda ake fada, yaushe Zaki kalli wannan kice Yana Qasqantacciyar rayuwa irin
wadda ake fada?".
"Ni Nama fiki mamaki Dan ni dai Idan ba gizo idona yayi min ba ko Kuma kama ce ta halitta tunda ance
kowa Yana da Mai Kama dashi a wani gurin, da sai nace Miki M.M DANGE na gani".
"Waye hakan?".
Amatu ta tambaya.
"Bazaki gane ba Amatu wasu Family ne a sokoto masu mahaukanta kudi Nima fa sau daya na taba ganin
M.M DANGEN a bikin wata cussing Dina zainab data auri Dan Family din, Kai gaskiya bashi bane inaga
Kama ce kawai, amma Kuma kamar harta baci sai dai ba yanda za'ayi DANGE ya iya rayuwa a nan".
"Kamar Yaya Aunty?"
"Tab kinsan kuwa waye shi? ai inaga kaf ba Wanda ya mallaki abunda ya mallaka a duk Family din, gashi
yaro matashi Kinga gidansa na sokoto ma kuwa? Banda na Abuja da sauran garuruwa, to in kuwa shine me
zeyi da Dan wannan gidan ai ji zeyi kamar Yana rayuwa a kurkuku ne, bama shi bane shifa ko bodyguard
dinsa abin kallon ne Suma sun Zama done fa"
Ido Amatu ta zaro.
"Kikace wannan gidan kamar kurkuku? Duk yanda na ganshi Aljannar duniya".
"Naki wasane Amatu. Allah ya kawo dalilin da Zaki shiga ko gidan daya daga cikin families din DANGE ne
kiyo kallon duniya me Kika gani a Nan kedai Allah ya Kai damo ga garawa kawai, Dan dai a wannan zuwan
da nayi sokoto naje yiwa zainab din barka naji wasu a cikin family din sunata hirar MM DANGEN Wai ko ya
bar kasar ya koma turai tun bayan samun wata matsala Mai zafi a cikin family din wadda ta tada kura har
rayuka suka baci".
Da ire-iren hirarrakin suka karasa gidan barkar.
...
Tana zaune a Nan parlourn ya fito cikin kananun kaya da karamar leda a hannunsa direct inda take ya nufo
ji tayi gabanta ya Fadi.
"Ya Ilahiy" ta fada a zuciyarta.
Gefenta ya zauna Yana Fadin
✨✨
✨✨
Page 25
Ta fada a shagwabe.
"Ki tashi ki bani kada lissafin ya canza fa"
Ya fada yana matsowa jikinta sosai, da sauri ta Mike ta nufi dining inda ta jera abinci.
Table mat ta shimfida a Kan carpet din sannan ta dauko abincin ta aje.
Plate biyu ta dauko dayan ya janye.
"Ki Zuba Mana a plate daya ya Isa ai Kuma indai Ina gida plate din mu daya tunda Kika yimin horon yunwa
yau daga Wasa Dan kawai kewar Hajiya ta ta kamani shine Kika horani duk ranar dana kaiki gabanta saina
fada Mata tasan irin zaman da zatayi dake, ni Dan gata ne a gurinta bana laifi zakiga yanda take sona".
"Ko?" Ta fada tana zuba abincin a plate, Dan tura Masa plate din tayi kusa dashi "Gashi Nan ni bana Jin
yunwa".
"Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike da karfi sai kin koya min surutu
ne? Kin iya kalato abin magana da wani bakinki chut".
Ya fada yana shafo pink din lips dinta.
Taci Amman ba wani na kirki ba da gaske abinci Bai dameta ba barta dai da 'yan ciye-ciye.
Bayan sun gama ne ta kwshe kayan ta gyara gurin duk Yana kallonta komai tayi kyau yake mata gata ba
wata babba ba sai dai akwai Sama da kasa masha Allah.
Lokacin data gama ne ya yafito ta da hannu,a hankali ta nufo shi kamar me counting steps sai rausaya take,
wani yawu ya hadiye, Dan risinawa tayi a gabansa duka hannuwanta ya kamo ya zaunar da it kusa dashi.
"Zaki rakani unguwa?"
Ya fada Yana zame Mata veil din da tayi rolling gashinta ne ya bayyana biki sidik dashi sai walqiya yake
yasha gyara ga kamshin hair spray Yana tashi.
"Eh zani Bari naje na shirya".
ta fada Tana kokarin zare jikinta daga nasa. Duka hannuwansa yasa ya riko kugunta ya hade ta da jikinsa.
"Ina zaki?wane irin Shiri zakiyi kinsan inda zamu ne kike sauri?".
Lakwas tayi a jikinsa da karfi da yaji so yake ya Saba mata da Zama a jikinsa gashi baya ko Jin jauyin taba
Mata jikin sai dai idan Bai soba.
"Bazaki tambayi inda zamu ba, kina Neman sake canza Kaya".
"Nasan gida zamuje Mana".
"Ai kece gidan, kinaji da so nake muje gidan da gaske mu roki alfarmar a bamu aron me aiki daya Wadda
zata zauna min dake kafin na dawo".
"Kafin ka dawo? Ina zakuje?".
"Au Ashe ban fada Miki ba, aikin NGOS din Nan ne ya taso suka gayyace mu zuwa meeting da zasuyi a UK
Kinga ai bazan zauna ba da dollars ko stalling founds suke biyan mu, idan Allah yasa na samu da Dan auki
Kinga na Kara jarina tunda Naga Nima Ina sha'awar siyar da materials har munyi magana da Abba yace ze
bani rumfa daya a Muda lawal market na gwada ko ina da nasibi a cikin sana'ar, sannan Habib ma munyi
magana zamu Fara siyar da spare parts na motoci a nan Muda lawal market din dai".
"Allah ya bada sa'a, Kuma idan ka tafi sai yaushe zaka dawo? Ko kaima shike Nan abinda yake faruwa Dani
ze faru a kanka kaima, kada ka tafi ka barni Dan Allah tunda nasan ba Sona kake ba baka ni akayi sadaka,
Dan Allah ka taimaka ka kaini Jordan tunda Ina kudin flight kawai ka taimaka ka fitar Dani daga kasar da
sunan Kai zaka tafi dani, bana son Ammah ta qara shiga cikin damuwa a kaina wlh Batasan tashin hankali
ba Sai Dana isa aure Kullum idan kaga Ammah a cikin tashin hankali to a kan lamarina ne ni Kuma yanzu
bana fatan na qara ganinta cikin bacin rai ta dalilina, kaje ka fada musu zaka tafi Dani ko Kano ne ka Kaini
na zauna gidan su bestie kafin na samu visa, nagaji da Kasar nan wlh Ina da gata Amma sai walagigi rayuwa
ta takeyi anan Dan Allah kayi min wannan alfarmar Koda ita kadai zakayi min ta karshe a zamana da Kai".
Ta kifa kanta a jikin kafad'arsa ta saki wani kuka Mai tsuma zuciya.
Bai hanata ba ya dai Kara matseta a jikinsa Yana shafa bayanta yasan abin Yana cin zuciyarta ne bata rasa
komai ba amma an dabaibaye Mata Jin dadin rayuwa kamar yanda Baba malam ya fada masa. Sai da tayi
Mai isarta ya dago kanta daga jikin kafadar tasa.
"Kiyi hakuri kowa da irin tasa jarabawar ke taki a haka tazo, Kuma waya fad'a Miki zan tafi na barki bazan
dawo ba? Waye kuma yace Miki bana sonki? Kinsan tun tsawon lokacin da nake dakon soyayyarki kuwa?
Tun Baki san meye son bama yarinya share hawayen ki Mahmud naki ne har abada, dole kije Jordan ke me
gida sukutum a can.Amma yanzu kiyi hakuri nema zani idan Kuma na zauna bakya son tafiyar saina fasa
Sameer yayi komai kawai nace madam ta Hana".
"Kaje kawai idan baka dawo ba nasan abinda zanyi".
"Keh! kina da hankali kuwa me zakiyi wlh zan turaki gurin Hajiya Inna duk da ban shirya zuwa yanzu ba
kawai ki Kira min ruwa, zaman Allah nakeyi zamanki nakeyi badan ke ba Dana Dade da barin garin Nan".
" Ni Kuma?"
"Off course"
Ya fada da karfin gwiwa.
"As how?"
Share ta yayi kamar bai jita ba.
"Tashi ki rakani kada dare yayi, dauko Mana key din motarki na dana kada na tafi ban Sanya albarka ba, ki
canza shiga kada a kalle min kayana" fada Yana mikar da ita daga jikinsa.
Duk kin haye min cinya kinsa sai ciwo take min".
Ya fada Yana Mata wani smile.
Bata kula shi ba tayi gaba abinta duk zuciyarta ba Dadi sannan tana jujjuya maganganunsa a zuciyarta,
kinsan tun lokacin da nake sonki? Danke nake zaune a garin Nan gasu Nan dai da yawa.
Saida ta sakarwa Kanta ruwa sannan ta shirya agurguje ta saka wata Riga da siket na atamfa super dinkin
ya zauna das a jikinta ta saka mayafin da yayi matching da atamfar ba tayi amfani da turaren kaya ba body
mist kawai tayi amfani dasu a jikinta kusan kala uku, sai ya bada wani sansanyan kanshi Mai dadi. Tana
gyara gyalen ya shigo dakin tsayawa tayi tana kallonsa shida yace unguwa zata raka shi sai gashi da Riga
armless da wandon ta farare tas na kamfanin Adidas sai taga kwata kwata ya canza Mata ya koma irin
'ya'yan hutu din Nan na gaske wadanda Jin Dadi ya gama ratsa su yayi wani irin fresh da shi.
Matsowa yayi kusa da ita Yana Dan watsa hannu irin dai na isassun yaran. Mayafin ya kama ya ida rufa
Mata a kanta.
"Kallon fa na menene? Kona canza Miki ne?".
Kai ta girgiza Masa.
"Baba son body language fa ki bude Baki kiyi min magana".
Yana janyo ta jikinsa.
"A'a kawai dai da naji kace unguwa zan rakaka kuma na ganka da......"
Sai tayi shiru.
"Karasa Mana sai Kika ganni da shigar nigas ko?"
Shirun dai tayi.
"Idan Ina tare da iyalin dole na sake, kema da nace ki canza ai na Shan iska nake nufi ba Wai irin wannan
ba, zo muje ki canza yawon Shan iska zamu ki min hira ki bani labarin ki tunda ke bakya bukatar nawa ki
bani happiness a wannan Daren yanda duk inda nake na rinqa Tino da abubuwan su zamar min kamar kina
kusa Dani".
"Ni dai Dan Allah ka barni haka muje kawai"
"Dauko key din to muje dare nayi Kuma Ina son ganin Baba malam da Abban mu, ko ba namu bane?"
Ya fada Yana kallon ta, an samu cigaba, tunda ko banza tunda ya mamnatse ta take iya kallon idanunsa ba
kamar da ba da Bata yarda ta kalleshi.
"Namu ne". Ta fada a hankali, badan Yana very closer to her ba da ba lallai yaji me take fada ba.
"Oya let's go".
Ya fada Yana nufar kofa, saida ya kashe electronics na gidan sannan suka fito Yana time da karamar luggage
a hannunsa,Kati ya curo daga cikin wallet dinsa ya saka a kofar ya rufe, daga nesa Mai gadi ya hangesu sun
nufi parking lot din gidan inda motar daya take ajiye, a ransa yake fadar "duk inda wannan Dan ya fito Dan
mafita ne ba irin yaran Nan bane lalatattu kamar yanda aketa surutun abun masu kushe da ganin rashin
kyautatawar su Alhaji nayi masu gani kyautatawar nayi".
Yana can Yana tunani Bai ankara ba yaji Karan Horn alamun har sun karaso Yana can Yana nashi zarafin.
Da gudu ya tashi Yana fadin Ayi hakuri nayi zurfi gurin tunani ne, a dawo lfy Allah ya tsare".
Horn ya yi Masa suka fice daga gidan.
Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan saida suka hada
turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan kanshi da mazubai Wanda dole yayi
attracting mutum.
Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai tambarin gurin Saida
turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin
gate din ya leko ya gane Mama tunda ya jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku".
Ta rusuna ya gaishe su.
'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa.
"Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau"
Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa suka fita da Mai
gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku shigo su Kuma sun fita".
Turus sukayi wannan ta kalli wannan.
"Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin rain a maganar ta ta.
"Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira ta a waya idan basuyi
nisa ba sai su dawo".
Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau.
"Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi Mata bayaninsa"
Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da sauri ta mikawa Mai gadin tana fadar "in Sha
Allah zan shigo Amma a fada Mata".
"In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida".
Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin tsayawa tana duban
kofar da Mai gadin ke kokarin turowa.
"Malam Bismillah".
Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta.
Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa.
"Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare"
"In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode madallah".
Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau.
"Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan su bugun Abuja ba
bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai dai in Baki nema ba, ai Nima goben da
sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman
kamar jira yake.
Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su.
******
Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin kwarewa lokaci lokaci Yana
Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin yasa Zahra ta Dan dube shi.
"Wai Ina zamu ne?".
"Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da naje haka nakeyi na
duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare na gudu nabar garin daman ba Wanda
yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki".
Ya fada Yana wani daure fuska.
Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta ya dauki rawa, duk
sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a
duniya.
Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara magana bakinta Yana
rawa.
Me nayi maka zaka cutar Dani?".
Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta tayi take hawaye suka
wanke mata kumatu.
✨✨
✨
AUREN HUCE HAUSHI
Maman Fateemah
Page 26.
________Sai da ya gangare sosai sannan ya kashe motar, chak ya daukota kamar 'yar Baby ya rungumeta,
dai dai kunnenta ya kai bakinsa ya hura Mata iska duka tsikar jikinta ta tashi duk da tana cikin halin rudu
bai Hana sakon zuwa ba.
"Ki rufa min asiri ada ace satoki nayi Nan da Nan kin rikice nayi Miki Kama da masu irin wannan d'abi'ar?
Wlh zolsyarki nakeyi haka Zaki shide min ki Kira min ruwa daga fita unguwa mu bige da kwanan Asibiti cool
down idan na sayar ai Nina kashe kaina".
Ba zato taji ya saka harshensa Yana lashe hawayen Yana Wasa da harshensa a saman idanunta,
qanqameshi tayi, "Dan Allah ka bari".
"Na bar me?"
"Hakan ba Dadi".
"To da cewa nayi kiji Dadi? Ni nasaka kukan Kinga ai shanye hawayen ya kamani kada muje inda zamu a
juya min baya".
Ya fada yana shinshinar gefen wuyanta.
" Kiyi hakuri bazan Kara ba tunda wannan idon naki Mai arahar kuka ne Ni zanga yanda za'ayi idan abin
kukan ya samu".
"Cewa fa kayi ka Saba halinka ne ka Saba yin hakan Kuma fa fuskar ka ba Rahama a ciki kamar Mai tsaron
gidan wuta".
"Kai innalillahi! Mai tsaron wuta ni din?" ya fada yana fiddo idanu waje
"A'a ba Kai nace ba kamar nace".
"Ba cinya ba kafar baya"
" Nifa nayi ne Dan Naga idonki, idan kina cikin halin tsorata yana sakani nishadi".
Wayar sa ce ta Fara vibration a jikinsa, Dan zameta yayi daga jikinsa ya dauko wayar ya duba tsaki ya d'an
Yi.
"Dan matsala kawai".
Ya fad'a yana saka wayar a handsfree.
"Ya akayi Hayatu".
Dariya ce ta kwacewa Sameer Wadda Bai shirya Mata ba.
"Wlh zan kashe, wato abin dariyarka na Zama ko?".
"Sorry sir wlh ji nayi gaba daya tazo min, Kuma ko sallamar da nayi baka amsa min ba".
"Ka Fadi abinda zaka Fadi Kona kashe da gaske Kuma sallama na amsa Kaine dai bakaji ba, duk safiyar Allah
baka tashi kirana ba sai yanzu da tsohon dare salon ka Hana mutum rawar gaban hantsi, na fada maka idan
Ina bukatar Abu ni zan nemeka Amma tsabar saka ido sai ka kirani ni, to fad'i meya faru? Ina jinka".
Ya fada Yana maido ta jikinsa.
"Game da maganar tafiyar Nan ce anya zanje kuwa wlh jiya danaje sokoto daukar wadannan hardcopy din
na shiga gurin Hajiya Inna muna cikin magana saiga uncle Mustapha ya shigo a sukwane bansan wane
minafikin bane ya fada Masa nazo garin ba tunda bana zuwa lokacin da suke gida, ya tasani gaba da
sababin nasan inda kake ina kallon su suna walaqiqin nemanka Amma nayi mirsisi naki fad'a musu komai,
Ni Ina ta faman lallaba mutuniyar taka amma Saida Uncle mustapha ya Bata lamarin Dan wlh kuka take da
hawayen ta bibiyu tana fadin Dan Allah na fada Mata idan mutuwa kayi saita hakurw tasan ita kadai zata
nesanta ka da ita, wlh yanda ta bani tausayi da bude aiki kawai zanyi sai Kuma na tuna da warning dinka
kawai na fasa, Kuma wlh yanda uncle yayi ba abinda ze Hana shi bibiyata ta karkashin kasa ban sani ba a
gida da waje amma ya kake ganin za'ayi? Numfashi ya sauke me karfi yana Kare matse zahrar a jikinsa har
Saida tayi 'yar karar Jin zafi.
"Karar me nakeji a kusa da Kai ne?".
"Ina ruwanka tsabar saka ido, to madam ce a kusa Kona baka ita kaji for confirmation, a'a Barta a
gaisheta".
Tana jinka a speaker wayar take, ka Bari kawai Zancen baze yuwu ta waya ba idan Allah yasa na shigo sai
mu tattaunawa Kuma ka tabbata komai ya kammala kafin na shigo goben in Sha Allah"
"Noted, in Sha Allah a gashe min da ita sosai a fada mata Batool tayi ta kiranta dazu ba'a dauka ba".
"Ina ga a gida ta baro wayar ka ganta Nan sai rigima take zabga min irin tasu ta shagwababbun 'ya'yan
larabawan" ya fada yana dan matse dantsen Hannunta kadan.
"Wash Allah na da zafi fa".
Ta fada tana Masa wani kallo Mai ma'anoni kala kala.
"Allah ya bamu Alkhairi"
Sameer ya fada Yana kashe wayar Bai jira yaji abinda Mahmud din ze fada ba.
"Kinga kinja ya katse Kiran bamu gama bayani ba irin wannan Abu haka ai sai ayi zaton muna hanyar shuga
wata nahiyar ne".
Harya rufe kofar Bata dauke idonta daga gurin ba, ita fa mutumin Nan ya Fara Bata tsoro mutane suna
daukarsa wani Abu daban ita Kuma tana ganinsa wani Abu daban.
Ta Dan jima Tana sakawa da kwancewa daga karshe ta watsar da komai ta dauki laptop din ta shige cikinki
bedroom din ta Haye lafiyayyan gadon ta bude ta shiga aikin inda Allah ya taimaketa yaci karfin aikin
karasa Masa zatayi.
*******
Lokacin da Mahmud ya fito Ibrahim da wani sulaiman ya Kira ya Basu aikin kula da dakin da Zahra ke ciki
duk da yasan suna da matakan tsaro sosai Amma hankalinsa Bai kwanta ba sai da ya Kara Mata da nasa,
gurin motar ya nufa bayan ya zauna ne ya Ciro wayarsa ya bude ta haka Nan ya shiga CCTV da akayi
connecting da wayarsa.
Hotunan ne suka fito rababa na dakinta yayi zooming qura Mata Ido yayi lokacin data fito daga wanka tana
daure da Karamin towel fararen cinyoyinta sunyi wani sambal dasu ta Kai ta kawo Yana kallonta harta
gama, tunda ya Fara kallon yake sakin wani Nishi kadan kadan Dan da gaske ta yamutsa Masa tunani ji
yake kamar ya zubar da Alkawarin daya daukarwa kansa a kanta, komawa yayi baya na kofar gate ya dauki
hankalinsa ganin wata mota mata sun fito sun dauko wani Abu a Leda sun nufi gate din gidan full screen
yayi da gurin da suke ya waye da mama amma Asaben çe bai ganeta ba yana kallon duk abinda sukayi har
Zuwa lokacin da Asabe tayiwa Mama rad'a a kunne ta Kira Mai gadin ta bashi kudi suka juya
da yanda suke kwasar dariya har da tabawa kamar yara sai abin ya bashi mamaki, meya kawo su gidan su
kadai ga Kuma motar da gani ta commercial ce, girgaiza Kai kawai yana tunanin abinyi.
Da gurin malam ya fara zuwa ya Dan jima tare dashi kafin ya aje Masa Alkhairi yayi Masa sallama, Yana
Kara yi Masa addu'ar samun nasara a tafiyar da godiyar Alkhairnin daya bashi, Habib ne ya Dan kalli
Mahmud din bayan sun fito Yana tambayarsa..
"Da gaske baka fad'awa Baba malam ba inda zakun kada fa yaji daga baya yayi fada yace ka tsallake kasa
baka fada Masa ba.
Kafadarsa ya dafa.
"Kada ka damu da kaina Zan fada Masa in sha Alllah".
Tare sukaje gidansu Zahra inda suka Dace suna kokarin yin knocking sai magaji ya fito, daga gani wani gurin
zaya yanda yayi Shar dashi.
Gaggaisawa sukayi kafin Magajin yayi musu jagora zuwan gurin Abban nasu. Anan falon ganawa da
bak'insa suka sameshi, sun gaisa Sosai a Nan Mahmud ya fada masa tafiyar da zeyi, Abban yasa Albarka
soshi.
.
✨✨
✨✨
MAMAN FATEEMAH
Page 27
_____Dan Jim Mahmud yayi kafin ya Dan muskuta kadan ya Kara sadda kansa kasa.
"Abba Dan Allah ko za'a taimaka a bamu Aron daya daga cikin masu aikin Nan Mata su tayata Zama kafin
Allah ya dawo damu". Ya fada a ladabce
Dan gyaran murya Abban yayi Yana fadin "Hakan babu laifi kayi tunani Mai kyau baza'a bar yarinya ita
kadai ba gara da babba, ba komai kome kenan da safe za'a turo wadda zata zauna da ita, Allah yayi Albarka
ya bada sa'a"
Sun jima suna Hira da Abban har suke fada Masa harkar kayan spares na kayan motocin da zasu ringa
saidawa, Albarka ya sanye musu sannan sukayi Masa sallama, har sun Kai kofa Abban yace Bari ya fadawa
Ammah ku shiga ku gaisa, a waya ya kirata ya fada Mata sannan yace su karasa ciki.
A kofar gate na shiga ciki suka samu Musaddiq Yana jiran su, cikin ladabi ya gaishe su Yana tambayar
Mahmud Aunty Zahra, hannunsa Mahmud din ya Kama Yana bashi amsa har suka shiga part din Ammar.
Sallama sukayi tana zaune a parlourn, sallamar ta amsa tana fadin. "Su Habib ne sannunku Bismillah".
Ta fada tana nuna musu gurin Zama.
Basu zauna a kujerar ba sai suka zauna a Kan carpet.
"Ina yini?"
Suka fada a tare, "lafiya kalau ya wajen malam?"
"Lafiya kalau yace a gaisheku".
"Masha Allah muna amsawa, Allah yayi Albarka, yayi muku jagoranci cikin dukkan lamuranku, ayi ta
hakurin Zama da yara".
Ta fada a kunyace Dan har ga Allah tana Jin nauyin yaron da kaunarsa saboda karamcinsa da halin fattako
daya nuna lokacin da aka bashi Auren zahra da Rana tsaka ya Kuma sa hannu biyu ya karba.
"Amin na gode ba komai, zahrar tace ma a gaisheku, kuma nazo ne nayi muku sallama zanyi tafiya ne
amma in Sha Allah bazan jima ba, na fadawa Abba a samu wadda zasu zauna tare kafin Allah yasa na
dawo".
"Masha Allah. Allah yayi taimako hakan baze gagara ba ko can gida Mubi Sai a samu wadda zatazo su zauna
tunda akwai yaran sosai ba sai an dauko bare ba tunda yau din ta Zama wata iri Amma kafin tazo sai su
Fara Zama da zulai tunda Bata da matsala"
"Godiya muke Allah ya kara sutura" Habib ya fada, suna mikewa har lokacin Autan Ammah Yana jikin
Mahmud a zaune. Addu'a Ammah take musu har suka fito Nan da nan wani rauni ya shigi Mahmud haka
tasa Umman take Masa a duk lokacin da ze shiga wurinta bakinta baya gajiyawa da Yi Masa addu'a, duk
kewarta sai ta rufe shi, "kaimu gurin Mama mu gaisa".
Mahmud ya cewa autan Ammah.
Part din Mamar suka nufa, Musaddiq ne yayi knocking har sau biyu ba'a bude ba Kuma suna jiyo
maganganu da sound din tv.
Habib ne yace "mu tafi Dan Allah yaushe zamu tsaya kamar wasu 'yan maula". Har sun sauka daga steps
din balcony din sannan aka bude kofar, Asabe ce ganin Autan Ammah da mutane yasa ta fito tana fadin ku
shigo Dan Allah wlh bamuji ba sai daga baya Salma ke fadin Kamar taji bugun kofa".
Habib ne yayi farat yayi magana "ai ba komai a gaishe da Hajiyar Daman mujin Zahra ne ya shigo ya gaishe
ta".
Sukayi gaba suka barta a tsaye.
Ciki ta koma jiki ba kwari.
Mama ce ta kalleta.
"Wai su waye Naga kin fita Kuna magana dasu ne Kuma Basu shigo ba?"
Zama tayi kusa da mamar, "sirikin ku ne inda mukaje basa Nan yazo gaishe ki da alama Kuma sauri suke
tunda sun jima a tsaye ba'a bude ba".
"Wai kina nufin Mahmud mijin Zahra?"
"Shifa sunce a gaishe ki, da alama sauri suke Dan har sun fice.
Baki Salma ta tab'e tana fadin. "saura kiris dai uban kowa ma ya rasa, ba dai kunce kun Kai turaren wutar
ba, yanda aka wayi gari aka ganshi da hakoransa talatin da shida haka za'a wayi gari yayi layar zana inga ta
qafafar da ake anyi aure, auren ma Dan jeka nayi ka da ba wani armashi yayi ba, Shima Abba Dan ya ganshi
handsome ne ya bashi ai ko banza ance mijin agolar gidansa ne".
Dakuwa Mama tayo Mata "Abban naki kike fadawa haka? Nima da farko nayi tunanin ko wani lashi yaga
yaron Yana dashi sai da na saka akayi min bincike aka tabbatar min da gidan da kayan da yake sakawa duk
Wanda yakewa aiki ne suka kawo Masa Dan wasu ma ance min wannan yaron shugaban aikin nasu ne ya
kawo Masa kwancensu Dan ya rinka fita kunya tunda matar tasa 'yar boko ce, shi Kuma almajiran soro
ance min ma iyakarsa secondary ya Dan iya rubutu da karatu ne yasa suka dauke shi aikin nasu, har kike
wani zaqewa kina sonsa ai da naji haka saina fad'i ba nauyi yo Dan kyau me ake da kyau bako sisi Allah
Banda nayi Alkawarin saina Maida Zahra karamar bazawara ba, da barinsa zanyi a garin to idan nayi
wannan saken kakanninta zasu iya bashi mahaukatan kudi ya nemi sana'ar da ze rike musu jika gara dai
yayi gaba tazo ta zauna na Dora daga inda na tsaya".
Dariya Salma da Asabe suka kwasa Asaben ce ke fadar "Aikinki Yana kyau uwar dakina ba Wanda ze taba
hasaso hakan daga bangaren ki kin kasa kin tsare duk wata kafa da wani ze fahimci da saka hannunki a
lamarin yarinyar nan".
Dariya mamar tayi itama "Au da sokike na ringa nuna adawata a fill ai Ni duk ranar da tazo gidan Nan da
bayanin mijin ya gudu sai nafi kowa kuka da tsine masa".
"Sai Maman mu". Salma ta fada tana kyalkyalewa da dariyar mugunta.
*********
A harabar gidan suka samu Abba Yana yiwa malam Bala direba magana, gurin suka nufa Abban na ganinsu
ya nufo inda suke.
"Har kun fito"
"Eh Abba zamu koma"
Suka fada tare, takarda Abban ya mikowa Mahmud.
Hannu yasa ya karba.
"Gashi Nan ka Kara guzuri Allah ya kaiku lfy ya bada sa'a".
Godiya sukayi Masa sosai har Saida yayi fada.
Tare suka fita da Auta har gurin mota ledoji biyu Mahmud ya dauko daga seat din baya ya mikawa
Musaddiq.
"Gashi naka daya na Faruq daya tukwaicin ku ne na kawo abinci".
Da murna Auta ya nufi gida Yana fadin "mun gode Uncle".
Cheque din kudi ne masu nauyi Abban ya bawa Mahmud saida abun ya Basu matukar mamaki.
Habib ya mikawa cheque din Yana fadin.
"Ka rike a gurinka kawai a sawo kayan shagon Nan dasu a Fara kasuwar tunda Allah ya kawo kawai".
"A'a baza'a yi haka ba ka tafi dasu kayi guzurin Kamar yanda yace idan Allah yasa kun dawo sai asan yanda
za'ayin".
"Kayi yanda nace ba wata damuwa acan komai Yi Mana za'ayi to me zanyi dasu? ga Kuma abun bukata a
gida ba gara ayi ba watakila kafin mu dawo ka koma sari na biyu".
Ya fada Yana murmushi.
Majalissar su sukaje Mahmud yayi musu sallama har salisu Yana zolayarsa akan barin Zahra da zeyi Yana
tsakiyar angwancewa. Bai Dade ba ya tafi duk hanlalinsa Yana kanta yasan har ta gaji da jiransa watakila
ma tayi barci.
Saida ya biya ya saya musu kaza da apple ya dauki hanya.
Lokacin Sha daya da minti ashirin da bakwai.
A hankali ya bude dakin abin mamaki Zahrar ya gani gurin fridge da glass cup a Hannunta tana Shan wani
abu, Sam bataji bude kofar ba saboda tv a kunne take sannan ta bawa kofar baya, Jin kamshin turarensa
yasa tayi saurin juyowa lokacin yazo daf da bayanta, juyowar da tayi sai a cikin kirjinsa.
Ledar ya saki qasa yayi Mata kyakykyawan masauki ya saka hannunsa ya talkafo bayan ta, yasa Bakinsa a
dai-dai kunnanta.
"Na dauka kin wuce Kano a barcinki Ashe dai jaruma na aura wadda take iya jiran mijinta komai dare". Ya
karasa fada Yana Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunnen.
"Dan Allah ka Bari".
Ta fada tana niyyar janye jikinta shi Kuma ya Hana hakan. Dan kwabe fuska tayi, "ka sakeni toilet zani".
"Ba wani toilet idan Kuma da gaske ne muje na rakaki".
Kai ta gigiza, shafa gefen ribs dinta yayi yaji yanda rigar ta matseta komai yayi tsan-tsan. Dan sakinta yayi
Yana Kare mata kallo daga sama har kasa, Dan sunan dinkin a tsokano fitina kawai, shi a dazu ai be karewa
dinkin kallo ba sai yanzu a kausashe ya jefa Mata tambayar.
"Waye telan da yake Miki dinki".
Hannu yasa ba zato ya shafo gaban rigar da sauri ta saka duka hannuwanta ta tsuguna sai Kuma kasan ya
baje. "Ya Salam" ya fada a hankali.
"Kinyi shiru Ina tambayarki".
"Makociyar Aunty Hasana ce take Mana dinki".
Ajiyar zuciya yayi yayi zaton namiji ne yaji ance sune ke gwada Mata idan hakan ta kasance ai an gama
dashi wani ya taba Masa wannan jikin. Tsugunawa yayi ya kamota ya dago jikinsa ya maidata "ki barni naji
duminki gobe ya wannan bana kusa dake Ina can na rungumi pillow, so muje muyi hirar yaushe gamo, ko
Kuma ban sani ba murna kike kina Jin dadin Zan tafi na Baki space ki sake ko?"
Ya fada Yana Wasa da Dan Karamin zoben dake 'yar karamar yatsarta.
"Oya talk kinyi shiru koba haka bane daman ba kince min me naci Kamar maye na tsotseki waya sani ko
maye ne ni ko Baki fada ba? Kawai Dan na koyawa bakinki ladabin magana da miji akan wannan yaron
shine na samu lambar maita daga gurinki".
Sexy eyes dinta ta zaro Masa, abinda yake burgeshi yake matukar so kenan yaga ta tsorata.
"Ni nace maka maye? Yaushe akayi hakan Wana fadawa?"
"Abar maganar kawai sai ranar Dana cinyeki danya Zaki gane Ni maye ne".
"Wlh Ni ban fada ba, Toni Wana na gani da Zan Fadi haka har a Gaya maka, a kwanakin Nan ko waya ban
rike ba fa".
"Naji shike Nan zo muje Naga aikin Allah yasa dai yayi kada aiki ya Koma baya"
Ledar tsarabarsa ya dauka ya jata suka nufi ciki. Gefen gadon ya zauna Yana janyo laptop din gefensa
Zahrar na tsaye a dayan gefen.
"Hayo ta Nan ki bude ki nuna min aikin in gani". Ba musu tayi yanda yace Kan cinyarta ya Dora laptop din
ya Dan kwanto jikinta yana ganin aikin har ta Gama nuna Masa, tab'a hannu yayi Yana fadin "inye kice idan
Allah ya hure mun na samu sakatariya ta a gida basai na nema a waje ba, yanzu jeki saman fridge akwai
plate biyu ki dauko kizo ki Zuba wannan" ya nuna Mata ledar daya shigo da ita.
Laptop din ta aje kusa dashi ta janyo gyalen da ta yafo zata yafa ya karbe Yana Mata wani kallo.
"Me zakiyi da shi ko akwai Wanda ba muharraminki ba a Nan da Zaki Kama rufe jiki, ok da bana Nan kin aje
har Dan kwalin kina watayawa yanzu Kuma na dawo Zaki wani saka gyale tunda idan na ganki kin dauki
zunubi ko?"
Shiru tayi Masa tasan idan ta magantu sai ta Kara laifi, juyawa tayi ta nufi kofa ya bita da idon Yana kistima
abubuwa da yawa a zuciyarsa.
Plates din ta dauko ta kawo ta koma ta dauko ruwa roba daya da fresh milk tunda taga Kamar yafi son
Shanta akan lemo.
"Dauki ki zuba" Nan ma ba musu ta bude kedar Naman wani kanshi ne ya doki hancinta har lokacin Kuma
da zafinta, daya ledar ta bude apple din ta Zuba a kai, gyara zama yayi Yana nuna Mata gefen shi, Kaita
girgaiza.
" Na koshi bana Jin yunwa".
"Naji ai ba abinci bane kizo kici ko nayi Miki dura da gaske nakeyi fa".
Narai narai tayi da ido, Allah bana cin Abu Mai yaji ko maiko da yawa da dare ulcer yake tada min".
Ture plate din yayi gefe ya janyota ya zaunar da ita a cinyarsa.
"Me Kika ce? Ulcer as how Kika kamu da ulcer, since when?"
"Bafa wani Abu bane tun Ina secondary ne Amma tunda aka fada min na rage cin wadannan abubuwan
more especially da dare idan Zan kwanta saina daina ciwon cikin".
Plate din ya ture gefe, "tashi ki Kai fridge ki dawo".
Kallonsa tayi da alamar tambya "to Kai bazakaci ba"
"Ni saboda ke na sawo coffee ko fruit kawai nake Sha a irin wannan time din, ki wanko Mana Apple kawai
ya Isa".
Saida ta wanko ta kawo sannan ta dauki kazar ta Kai fridge din ta dawo.
A Dan nesa dashi ta zauna taga alamar 'ya abun nasa Yau suna kusa.
Matsowa yayi jikinta da plate din Apple din Yana Danna waya da alama kamar Kira yakeyi Apple din ya
Mika Mata Yana ci gaba da trying Kiran, sau biyu Yana Kira ba'a daga ba ya hakura ya aje wayar.
"Labarin ki Zaki bani tun daga primary, secondary Zuwa Yau din Nan da muke tare Kuma ki fada min dalilin
da yasa ake fasa aurenki da dukkan Wanda sukaso aurenki laifin na waye? Ok kafin Nan Bari na tambaye ki
wani abu"
Wata wayar ya Ciro daga aljihun gefen hagu na rigarsa.
Jikinta ya matso sosai Kusan Rabin jikinsa Yana cikin nata ya kanainaye ta CCTV ya kunna ya Mika Mata ya
saka fullscreen gurin gate din gidansu ne Mama da Asabe ta gani tun tsayuwar motarsu har zuwa gurin
Mai gadi Saida ta gama ganin komai yace "Daman Kuna abin kirki da Mama ne? Kuma wacece wannan Dan
yanzu da Daren Nan da naje yiwa su Ammah sallama naganta a dakin mamar kenan daga Nan can sukayi"
Ya fada Yana tsareta da idanunsa masu razana ta.
"A'a ni bana wani good term da Mama ko kadan Dan da sam ita da Aunty salma basa yina Daman
Hameeda ce tawa idan tana gurin ba Wanda ya Isa ya Fadi marar Dadi a kaina, to ita dinma bansan meya
canzata ba lokaci daya tayi min cin fuska ba ko Kara gani a tsaye, ita Kuma wannan Asabe ce aminiyar
Mama ce komai tare sukeyi".
"Ok ba damuwa".
Wayarsa ce ta dauki wani slow music alamar shine ringtone din wayar, dauka yayi tare da sallama.
Magana ya Fara Bai jira Wanda yayiwa sallamar ya amsa ba.
"Kazo Azare katagum local government a cikin local government ne na Bauchi state ne a duba map zakaga
inda location din yake amma kada ka biyo ta jos Nissan yayi yawa ka shigo ta Kano kawai karfe bakwan
safe tayi maka a garin".
Abinda ya fada kenan ya katse Kiran.
Wani Kiran ya Karayi ringing daya aka dauka.
"Bilya a canzawa Mai gadin gidana gurin aiki ya Koma Sharar compound din makarantar yaran Nan kawai"
kit ya kashe Kiran duk tana binsa da ido.
Agogon jikin wayarsa ta kalla Sha biyu da Rabi.
A marairaice ta dube shi "yaushe zamu tafi nifa Ina Jin tsoron dare fa".
Kansa ya kwantar a cinyarta Yana facing din face dinta.
"A Nan zamu kwana bakiga harda jakar matafiya ba? jiranki nake ki bani labarin naki kinyi shiru kin
shareni".
Dan turo Baki tayi "Toni me zance maka ai kasan komai"
"Kamar Yaya nasan komai, harda labarin da aka turo min ta msm na duk Wanda kikayi tare dashi Saida ya
sanki 'ya mace yaji test din Bai Masa ba tunda kyawun iya jiki da fuska kawai ya tsaya" shima Hakan ne
tunda anfada min?"
Ruwan zafi ta hada ta zuba turarikan wankan data gani a gurin ajiye, shigewa tayi ciki tayi kwance ruwan
Yana ratsata kamar zatayi barci ta jima sosai sannan tayi wankan ta fito, sai da ta goge jikinta ta zura rigar
barcin cotton ce mai laushi ta sauko Mata har Kusan gwiwa sai da matsalar ta dayi zif akayi Mata har kasa
ga saman rigar wani net aka saka transparent komai a waje yake ba wani sirri Kai kawo da dinga yi a toilet
din daga karshe towel na wanka babba ta rufo a jikinta ta fito.
Dago ido yayi yana kallon ta sai Kuma ya janyesu yaci gaba da aikinsa cikin kware, idan yaci gaba da
kallonta wlh wata dariya zata kubce Masa, shi dai yasan duk wayon Amarya sai an Sha manta.
A darare tazo ta zauna a nesa dashi.
" Ki tashi ki kwanta ya nuna Mata tsakiyar gadon. Jinjina Masa Kai tayi ta Haye tana Jan blanket din tana
rufe jikinta. Kusan Rabin hankalinsa Yana Kanta Yana kallonta tayi Addu'ointa shafa a jiki, tun Tana Dan Jin
dar a jikinta har barci yayi awon gaba da ita.
Sai gurin daya ya kammala duk abinda ya kamata ace ya gama.
Wanka yayo tare da alwala pyjamas ya saka masu kalar off-white sannan ya tada nafila raka'a hudu yayi ya
sallame ya jima Yana addu'a kafin ya nufi gado dariya ta bashi blanket din daban ita daban sai barcinta
takeyi cikin nutsuwa face dinta ya kurawa ido "yes she's beautiful" ya fada a hankali kamar Mai tsoron
kada taji.
Kusa da ita ya kwanta kamshi turarensa Dana turaren wanka sai suka bada wani kamshin Mai dadin shaka,
madaurin jikin rigarsa ya since ya zare rigar daga jikinsa ya kwanta a jikinta Bata ko motsa ba a hankali ya
saka hannunsa ya zuge zif din jikin rigarta yayi mamakin nauyin barcinta blanket din ya janyo ya lullubesu
da shi sannan a hankali ya mannata da jikinsa yana sakin ajiyar zuciya, a cikin barci taji Kamar hannu na
yawo a jikinta a Dan tsorace ta bude idonta ga dakin ba haske so sai, Sam saita kasa gane takamaiamai a
Ina take ga ta Kuma a jikin mutum ko Riga Babu.
"Wayyo Allah na!!!" ta fada jikinta ya dauki rawa..
"Shittt, cool down nine kiyi barcinki Nima barcin nakeji..
.✨✨
✨✨
Page 28
____Hankalin Zahra be kwanta ba sai da taji Yana maida numfashi a hankali alamun barcin ya dauke shi
ajiyar zuciya ta sauke da farko Bata yarda ba da yace barci zasuyi Saida ta gani da gasken yayi barcin.
Kokarin zame kanta da yayi Mata pillow da gefen kafadarsa tayi, a cikin barcin ya kara janyo ta jikinsa
yana gyara Mata kwanciyar amman idonsa dai a rufe, shiru tayi lif a jikinsa Dan Bata son ya farka su hada
ido ai da kunya amma taga alama shi bashi da ita misqalazarratin idan wani ne ai zuwa yanzu Basu wani
sababa yanda abun yazo musu a hagunce, ko dan shifa yana ikirarin ya santa batun yanzu ba to a Ina?
Kuma waye shi?daga Ina yake? Waye sameer a zahiri shi yaron sameer ne ita Kuma a bad'ini shi yake bashi
directive abin da daure Kai Kuma yace ya manta garinsu da komai nasa Amma a gurinta yana fada Mata ya
tuno kakarsa har da 'yar tsamar da sukeyi.
Tunani barkatai ta dunga yi har barci yayi awon gaba da ita, karfe hudu da rabi na Asuba alarm din daya
saita ya tashe su kusan lokaci daya suka farka har lokacin tana jikin shi, shiru tayi Bata nuna ta tashi ba, so
take ya wuce toilet.
Addu'ar tashi daga barci yayi a hankali ya zare ta daga jikinsa kura Mata Ido yayi a cikin dimligh din dakin
face dinta sai glowing takeyi ko Ina a jikin fresh sai wani sansanyan kanshi ke fita daga jikinta wanda har ya
zauna a jikinta Dan duk jikinsa kamshin yakeyi, light kiss ya Bata a kumatu ya gyara Mata rufar saboda
sanyin AC ga sanyin Asuba. Duk abinda yake tana jinsa bakam tayi Dan ji tayi wani irin nauyinsa ya rufeta
Wai wane irin barci ne tayi har yayi sabgar rabata da rigarta amman Wai Bata sani ba, Jin karar ruwa yasa
tayi saurin tashi ta janyo rigarta tana cuno Baki.
"Haka kawai duk a kalleka waya sani ma ko Abu ya saka a cikin Apple din Dana Sha shike Nan na Kama
barcin asara sai yanda yayi Dani" da sauri ta ida janye blanket din tana duba jikinta Jin ba wani bakon Abu
yasa taji sanyi a cikin ranta, sai Kuma abun ya Bata dariya, Jin ze fito yasa ta koma ta kwanta jallabiya ya
zura ya saka tashi ka fiye naci, ya dauki tasbasha (counter( ya matso kusa da ita Dan guntun ruwan alwala
na fuskarsa ya yarfa Mata kadan a fuskar ta.
"Ki tashi kiyi alwala an kusa tada sallah nasan idonki biyu tun lokacin Dana tashi".
Ya fada Yana nufar kofa zuwa masallacin cikin hotel din.
Tashi tayi ta nufi toilet din a gurguje tayi wanka ta daro alwala lokacin data fito har an idar da sallar,
lotion din data gani ta shafa ta bude jakar duk wani abun da zata bukata ya sako a ciki ita mamaki take to a
Ina ya Sami kayan ita dai ba nata ya dauka ba, hatta bra ma size dinta ce doguwar Riga ta cire daga leda ta
saka baka Mai aikin stone, hijab ta saka ta tada sallah.
Har ta gama azkar Bai shigo ba sai gurin shida da rabi ya shigo directly inda take ya nufa.
"Barka da Asuba".
Zahra ta fada tana sadda Kai kasa, shiru yayi kamar Bai jita ba sake maiamaitawa tayi.
"Taso kiga yanda ake gaida Dear ba irin wannan local gaisuwar ba"
Sunne Kai tayi tana Dan murmushi, tsugunawa yayin daf da ita yana kallon 'yan yatsun Hannunta sumul
sumul dasu kamar Bata aikin komai da Hannun, dagota yayi gaba dayan ta ya mannata a jikinsa "ji nakeyi
kamar kada nayi tafiyar nan ko Kuma na daukeki mu tafi, idan na tuna zanyi nesa dake wlh wani irin rauni
ne yake kamani naji kamar idan bana Nan wani Abu ze faru".
Ya fada cikin muryar karaya da gaske a 'yan kwanakin Nan Yana Jin wani Abu daya fi na da a tare dashi.
Cikin 'yar siririyar muryarta tace "ba komai kaje kawai Allah Yana tare damu ba abun da ze faru sai abinda
ya hukunta a kaina, Allah ya bada nasara yasa a Dace, kawai dai Dan Allah kayi min wata alfarma kafin ka
tafi".
Hijabin ya zare a hankali daga kanta ya Dora a Kan bed side kafin ya zaunar da ita a jikinsa as usual.
"Fadi wace bukata gareki".
Dan shiru tayi kamar bazatayi magana ba.
Oya fell free with me, kiyi magana Mana kinsan eight thirty nake so na wuce".
"Daman so nake na ringa zuwa Dr.sulaimanu Adamu college of Hygiene inda nayi service na ringa yin
lectures ko sau biyu ne a sati".
Wani kallo yayi Mata na Amma Baki da lissafi.
"Ni matata da yawon aiki? Gaskiya A'a! Wannan bukatar Bata karbu ba, me kikeci na baka na Zuba indai
aiki ne wlh sai kin gaji da yinsa, tashi daga jikina kin wani samu cinya kin dane,kada na makara nayi missing
flight mu tsuguna duk dan burin bawa ya rushe".
"Yanzu Allah bazaka Bari na rinka Zuwa ba".
Ta fada a marairaice.
"Kinsan Allah wlh Zan hadaki da zayyan Dan nasan Yana daf da shigowa garin Nan ya juya min dake can
kauye gurin Hajiya Inna ko banza kin tuka mata tuwon dawa kin mata shara, kinga ita gaba ta kaita
balarabiya na mata aikatau ita kuwa bakar fata Kinga sai mu Dora a media muma 9ja munci gaba ana zuwa
daga middle East ana Mana aikatau".
Ya karasa fada Yana Jan Dan tsinin Karan hancinta.
Tana kokarin magana wayarsa dake Kan bedside ta dauki wani kidan larabawa Mai dadi.
"Dauko min wayata Dan tsabar na Zama mijin ......, Gashi Nan ringtone din ma kidan kune na saka". Wayar
ta dauko, Zayyan ta gani kwalalo idanu tayi Ashe da gaske yake da yace Shi wannan din zezo yanzu ko waye
shi kuma "oho" ta fada a zuciyarta.
Wayar ta Mika masa.
"Ka karaso?" Abinda taji ya fada kenan Bata San me yace Masa ba taji yace "ok, ka shigo ciki akwai
securities a kofa zasu zasu rakoka gurin da Zan ganka".
Ya kashe Kiran Yana nufar kofa, ki shirya kafin na dawo yanzu zamu wuce".
Yayi Gaga abinsa ya barta da Baki a sake "ikon Allah shi Kuma ko waye yake bada umarni cikin dare ya wayi
gari da abinda ya bukata tasan ko waye daga nesa yake Dan jiya tanaji Yana fadin kada a biyo ta jos a biyo
ta kano, ita duk ya Gama Dame Mata lissafi wlh.
******
A hankali yake tafiyar cikin nutsuwa Amma da gani kasan tafiyar ta ingarman namiji ce, tunda ya doso
gurin Zayyan ya kafe shi da ido, take ya shiga jinjina lamarin ogan nasa wato ana zaton wuta a maqera said
gata a masaqa, waze tab'a tunanin sa a irin nan yayi masifar bada kafa.
Bai Farga ya kureshi da ido ba Saida yazo daf dashi, "sorry sir" ya fada Yana sadda kai, baiyi magana ba ya
mika Masa hannu wannan d'abi'ar sa ce baka Masa irin gaisawar Nan sai dai kuyi musabihwa. "Barka da
Asuba ya Hanya?".
"Alhamdulillahi."
Ya fada sai da Mahmud ya zauna kafin Zayyan Shima ya koma ya zauna.
Kamar bazece komai ba gurin ya dauki shiru.
Saida yaja fasali sannan yace. "I hope ba Wanda ka fadawa munyi waya ga Kuma inda zaka sameni?"
Kai ya girgaiza "ko daya oga ba Wanda yasan inda na tafi kawai nace musu zanje gida ne na samu Kiran
gaggawa".
"Good, na kiraka ne zaka zauna gidan da wife Dina take zanyi tafiya, Wanda na saka gadin Naga alamar
gaskiya Bata isheshi ba, ko Kuma ze iya komai saboda kudi, zan turo maka pictures na wasu Mata koda
Wasa kada kabar kafarsu ta shigar min gida shi yasa na taso ka da tsohon dare ".
Zayyan jin magwnar yayi wani banbarakwai "wife Kuma? To ta ina Hakan ta faru? mutumin da ake tunanin
baya kasa sai Kuma ya ganshi a nan Yana wata irin rayuwa hankalinsa kwance, ga abubuwan tambaya
Amma ba Halin yinta.
"To in Sha Allah baza'a samu matsala ba".
"Yanzu zaka shiga cikin Ibrahim ze nuna maka dakin da zaka huta daga Nan zuwa sha daya Binyaminu ze
shigo kuje gidan".
Ya fada Yana mikewa.
Da kallo zayyan ya bishi har ya b'acewa ganinsa, ajiyar zuciya ya sauke Yana jinjina Lamarin ogan nasu wato
duk yanda kasan Shi idan yayi wata bada Qafar saika rasa gane wace alkiblar ya kalla. "Wife Dina". Yanda
yayi maganar kasan ba wasa cikin Yana wannan tunanin Ibrahim ya karaso Bai sani ba.
Da azama ya shiga falon a zaune ya sameta da luggage dinsa a kusa da ita tayi rolling da Veil din rigar sai
tayi masa wani irin kyau, a slow ya karasa inda take zaune ya saka hannu ya dagota tsaye ya sumbaci
saman goshinta.
"Nayi Miki irin gaisawar ku, Ina key din lokaci Yana ja kada da gaske nayi sakaci kija Mana, muna lallabawa,
kin hakura da Zuwa makarantar naji Baki ce komai ba?"
"Bani da say, sai yanda kace haka za'ayi".
"Nace A'a! in dai Ina raye da lafiya ta bazaki nemi komai ki rasa ba Koda kuwa faskare zanyi to zanyi na
samu abinda zankula dake".ya fada Yana daukar luggage din ita Kuma ta nufi kan fridge inda ya ajiye key
din jiya.
A jere suke tafiya sunyi wani irin dacewa wadda dole idan ka kallesu ka qara suna kokarin fita daga
reception su Zayyan suna kokarin shiga, Mahmud ya kalla da jakar matafiya a hannu Yana rike da Hannun
Zahra,.
"Kam bala'i"
Yaji Bakinsa ya subuce ya fada Yana matsawa baya Kamar yanda Ibrahim yayi.
"A sauka lfy" Ibrahim din ya fada shi kuwa Zayyan kamar an saka makulli an datse Masa baki.
"Ka bashi key din dakin ka biyoni mota Zan baka sako".
Ya fada Yana duban Ibrahim, mota Zahra ta shige ta barsu suna tattaunawa kafin ya shigo ya tada motar ya
nufi get din fita har yabar harabar hotel din, Zayyan na lekensa ta window sai dai yasan idan yayi magqnar
Nan da wani kwabarsa ce zatayi ruwa daya fesa labari, oga da rije jikar mace uwa uba yana tukata da kansa
Kai wannan abin surprised da yawa yake"Ga bikin zuwa ne babu zani.
Tafiya yake da hanzari Dan ma safiya ce sosai titin ba yawan jama'a cikin Kan kanin lokaci suka shigo
unguwar, Horn ya danna da karfi da gudu Mai gadin yazo ya bude yana fadin "barka da zuwa!"
Da gudu ya Koma ya dauko sakon dasu mama suka kawo jiya Yana fadin "barka da Asuba yallabai gashi jiya
bayan futarku su Hajiya Babba sukazo suka bada a ajewa Hajiya".
Ya fad'a Yana risinawa Yana mikawa Mahmud ledar.
Saida ya karewa shi da ledar kallo, sannan ya hade gabas da yamma yace ka rika idan kana so, Kuma
Ka hade kayanka in anjima kadan binyaminu ze zo da Wanda ze canjeka aikin Nan adalci daya nayi maka
ban koreka ba zaka koma share-sharen makarantar Yara kawai".
Jiki na tsuma Mai gadi ya durgusa Yana fadin "Yallabai me nayi haka da zafi Dan Allah kayi hakuri wlh
baza'a qara ba ka rufa min asiri".
"Iya Alfarmar kenan bana korar ma'aikaci sai lefinsa ya Kai uku to Kai daya kayi ba tare da kasan laifi bane
shi yasa nayi maka uzuri bazan rabaka da rufin asirinka ba dauki kaje yanzu Zan fito". Jiki ba kwari ya dauki
ledar ya juya Yana ta faman tunanin ta ina ya kuskuro yallabai jiya lafiya kalau suka rabu yau Kuma ya tashi
da canjin gurin aiki da Allah ma ya dube shi da Rahama daba Kora bace days shiga uku.
Suna shiga Mahmud yayi bed room dinsa ita Kuma ta nufi kitchen ta Fara hada abu marar wahala coffee ta
dafa Masa sai sandwich kawai tayi shaf-shaf a tray ta Dora direct bedroom dinsa ta nufa ya fito daga wanka
Yana goge jikinsa a ranta tace shi baya mura any time wanka kamar dangin kwadi.
Sallamar ta ya amsa Yana aje towel din dake hannunsa.
"Ke! Me kikayi daga zuwan mu ba dai abinci bane ko? Ni bana cin komai a irin wannan lokacin".
Langabe Kai tayi tana dubansa kasa-kasa har Zuwa lokacin wani nauyinsa takeji. Yana ankare da ita.
"Coffee ne fa da sandwich nayi maka Dan Allah kada ka tafi da yunwa,alhalin gani a tare da Kai ai da naji
kunya daga zuwa ka nemi abinci a kanon".
"Inye ashe dai ana son mamudan?".
Ya fada yana nufar inda ya aje kayan da ze saka kananun Kaya ne na kamfanin Armani ya saka bako kunya
ya cire rigar wankan ya tsaya daga shi sai boxer short, da sauri ta runtse idonta Dan Bata zata zeyi irin
wannan abunba Yana kallonta ya basar yaci gaba da shiryawarsa, Zama yayi Kan sofa Yana umartarta ta
kawo masa coffee din nan duka ta dauko ta aje gefensa ya dauka Yana sipping Yana kallonta tana Wasa da
gefen veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya watsa mata kasa a
ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin.
"Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota "Kinga gurin zamanki
Nan ya dorata inda ya Saba..
"Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa kona dawo ko ba na
dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan Nan ni dangatan iyayena ne da kakata
Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na
fadawa labarinki sai kakata ta sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira
ya zauna yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na, Dan Allah kiyi
min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena da Kima da daraja, idan Allah yasa na
dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada
min ba,
duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma nabar komai a
Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje mata su a akan cinyar ta.
Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai dai
hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki yaki kwanciya da ita"
"Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka tafi bazaka dawon
ba".
Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin ajiye Mana babies a ciki
idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin ki nema zani ki min addu'ar samun nasara".
✨✨✨
✨✨✨
Strory
&
Written
By
Maman Fateemah
Page 29
_____ Sun jima a haka Yana lallashinta kafin ya dagota su tashi tsaye tare " me za'a bani nayi guzuri
dashi?"
Ya tambaye ta, shiru tayi kafin ta Dan watsa hannu tana Dan kallonsa ta gefen ido.
"Ai kaga bamu kwana a gidan ba bare nayi maka wani Abu Saida idan biscuits din Nan Zan dauko maka sai
ka tafi dasu na bada a sawo min wani".
Dariya abin ya bashi ita bilhaqqi da gaske take fada Wai biscuits kamar wani yaro.
"A'a niba shi nake so ba tsarabar da zan rike Ina tunawa da ita har na dawo".
"Me Kenan?" Ta tambaye shi cikin nuna rashin sani.
Jikinta ya matso sosai ya riko ta Yana kallonta da wani yanayi mai wuyar fassarawa, Bakinsa ya Kai Kan nata
Dan bakin yasa Hannun ya talkafo kanta batayi zato ba tsammani taji harshensa na yawo cikin bakinta ya
lalubo nata harshen cikin gentle yake tafiyar da ita ba kamar ranar nan ba, sun dauko Kusan minti biyar
Yana Abu daya ji tayi kafafunta na neman gagarar daukar ta, jin jikinta na rawa yasa ya Kara mannata da
jikinsa wani Nishi tayi ba Halin magana, kokarin yanye harshenta take daga Bakinsa Kai ya girgaiza Mata sai
da yayi mai isarsa ya saurara Mata Kan gadonsa ta zube da gaske ya kashe Mata jiki ji take idan ta taka
kafarta faduwa zatayi.
Dan rankwafawa yayi saitin fuskar ta "Haba 'yan Mata be strong Mana me akayi da maza inji karya, taso
muje ki rakani idan na biye Miki labarin salo ze canza".
Ya kamo hannunta ya mikar da ita, jakar laptop dinsa kawai taga ya dauka, gyalenta wanda yake yashe a
kasa ya tsuguna ya dauko Mata Yana rufa Mata a kanta.
"Zaki bani Aron motar ki naje Kano da ita? amma fa saina dawo na dawo Miki da ita a airport Zan bada
ajiyarta yanda idan muka dawo saina karba kawai".
Kai ta gyada Masa alamar Eh.
*A'a magana zakiyi idan kin amince to idan Baki amince ba na nemi hanyar Tasha kawai".
"Ka dauka kaje da itan koka dawo ma na bar maka za'a kawo min wata ba kaji Abba ya fada ba".
"Ke! Kinsan kudin ta kuwa zakice kin barmin Dan ki hau Abba ya saya Miki, Aron ma Ina laifi".
Yaja hannun ta suka nufi kofar a falo ya tsaya Yana wasu 'yan dube duben da Batasan Kona menene ba
sannan suka nufi harabar gidan, kasa hakuri tayi ta jefa Masa tambayar.
"Wai haka zaka tafi ba kayan sakawa da takalma da sauran abun bukatu ne?" Dan shafa gefen fuskar sa
yayi ya Dan furzar da iska daga Bakinsa. "Bana tafiya da Kaya ai wahala ce nasan duk inda zani akwai na
sayarwa na saya kawai, aikin gane?"kallonsa kawai batace Masa komai ba.
Saida yaje gurin Mai gadi ya bashi wata envelope sukayi maganganu sannan ya dawo gurin da take tsaye.
"Zan tafi sai Allah ya dawo Dani, ki kula da kanki bana son yawo Amma idan gidan Ammah ne ko Aunty
Hasana idan Bata koma Jos ba kina iya Zuwa".
"To na gode, Allah ya tsare hanya ya bada sa'ar abinda akaje nema".
"Allahumma Amin. Allah ya tsare min ke daga sharrin mutum da Aljani da dukkan abinda yake cutarwa, ya
Ubangiji na bar maka amanar iyalina ka Zama gatan mu".
Ya fada yana nufar motar, a hankali ta biyo shi ya bude ze shiga ta riko hannunsa ta Manna masa kiss a
tsakiyar hannun. "Safe journey" ta fada da wata murya Mai rauni da gudu ta juya idonta fal hawaye. Tsaye
yayi Yana kallon ta har ta shige ciki, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya shiga ya tada motar jikin window ta
tsaya har Saida ya fice daga gidan.
________________________
Tunda Mahmud ya bar cikin gari ya saki motar, rabon da yayi tuqi irin wannan har ya manta, kyakykyawar
awa daya da minti arba'in da Tara ta kawo shi Kano, daga Hotoro NNPC sai ya shiga ta ring road ya fita 'yan
kaba haka ya dunga yayyankewa har Zuwa round about na sani Baban kwari Sannan ya nufi Malam Aminu
Kano international airport,Yana daf da shiga gate din ya saka face mask da glass sannan ya shiga, wayar
Sameer ya Kira tana daf da katsewa ya daga.
"Kana Ina? Na shigo yanzu ina fatan komai ya dai-daita?". Dan Jim ya yi yana sauraren sa. "Ok kazo ina
parking lot inda ake bada ajiyar motoci".
Ya sauke wayar Yana kalon masu Kai da kawowa.
Yana Nan tsaye har sameer din ya karaso ya gaishe da Mahmud cikin girmamawa, jakar laptop din Sameer
ya karba da key din motar ya nufi inda suke da alhakin karbar ajiyar, shi Kuma Mahmud ya nufi reception
din.
Sameer Bai jima ba ya dawo da takarda shedar bada ajiya, sun Dan tattauna kafin lokacin tashinsu yayi,
zasu shiga screening ne Mahmud ya Kira wayar zahra, tana kwance a gado rungume da pillow bayan tayi
kukanta Mai isarta ta lallashi kanta tunda Babu Mai lallashin gani takeyi shima kamar ya tafi kenan. Ringing
din waya taji da sauri ta tashi Dan ita Sam tama manta da wata waya tunda ya Bata Bata karabi takanta ba,
da sauri ta dauko tana duba waye ya Kira MM DANGE ta gani wani sanyi taji ya saukar mata,
Picking tayi tare da sallama, sai kuma tayi shiru.
"Zamu tafi ne nace bari na kira na fada Miki, ko zamu sake waya ze iya kaiwa jibi kada hankalinki ya tashi
idan komai ya dai-daita Zan kiraki in Sha Allah".
"Tom Allah ya saukeku lfy".
"Allahumma Amin my precious, please take care bye".
Ya katse Kiran yasan idan yaci gaba kuka zata saka Masa ya rasa wane irin idanu gareta masu saurin kuka.
Sha biyu da rabi jirginsu na kamfanin air Max ya daga.
Wayar tabi da kallo kafin ta aje kusa da ita, sai Kuma ta tashi kamar wadda aka zabura. Wayar ta dauko
dubawa tayi wata baguwar number ta gani batayi kasa a gwiwa ba tabi Kiran Dan missed call ne tunna jiya.
Cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga Bata jima Tana ringing ba aka daga muryar matashiyar macece daga ji
tana ji da ajinta sallama Zahra tayi Mata suka gaisa sannan zahrar tace Mata taga missed call dinta ne a
wayar ta.
"Missed call Dina gaskiya bani na Kira ba Amma Dan Allah wacece ke?.
Yar dariya Zahra tayi kafin tace "sunana Fatima Zahra Muhd sani Ni mazauniyar Azare ce ta jihar Bauchi".
Kit ta kashe wayar ta yunkura ta tashi, ta nufi kofa tana daf da fita taji wayar ta Kara daukar Kara ta dawo
number dazu ce yi tayi kamar zata share sai Kuma ta dauka taji me zata fada Mata.
Sallama tayi daga can ta amsa sannan ta Dora da fadin "Dan Allah kiyi hakuri da farko ban ganeki bane sai
da Kika fada min sunan ki wlh nice na Kira bansan yanda akayi banyi saving number din ba matar oga
Mahmud ko?"
"Eh nice ke wacece?"
"Sunana Fateeha matar Sameer Babban yaron oga jiya ne ya bani number yace na kiraki na gaisheka nayi
Miki Allah Sanya Alkhairi sai Kuma ba'a daga ba, an Sha sauga bamuzo mukaga daki ba gashi har sun wuce
China, amma in sha Allah idan suka dawo zamuzo indai ban haihu ba har lokacin"
"Nagode kwarai da gaske,Amma naji kince China ba UK zasu Fara Zuwa ba? To can din zasu tunda kune
masu tafiyar Amma na dauka da China zasu Fara tunda canne aka samu matsala sai Kuma Dubai, kinsan
ogan naki ne kamar computer yake baya gajiya da aiki danma yayi wannan hutun Mai yawa sai Habibi ne
yake wasu ayyukan".
"Hakane kam aiya huta yanzu sai a Dora daga inda aka tsaya".
"Ai gaskiya samun kamar oga Mahmud sai an tona".
Basu jima ba sukayi sallama. Ta Dade a zaune tana jujjuya hirar su da matar Sameer, zamewa tayi ta
kwanta tana duban sama a hankali ta furta. "Ubangji ga baiwar Mai rauni ka jibinci lamarina Kasan ko waye
ka hadani dashi ka Kuma sakamin nutsu a tare dashi ban tabaji bana sonsa ba Amma lamarinsa Yana bani
tsora na rasa alkiblar daya duba, Allah ka Zama gata na ka jibinci dukkan lamurana Dan Isar Manzon Allah s
.a.w.w.
Tashi tayi ta fita dakin nasa ta koma dauko tray din da Takai Masa break fast, duk wani Abu daya danganci
kayan electronic sai ta kashe sannan ta fito tana gangarowa daga steps din corridor ne taji door bell din
tana Kara alamar anyi Baki, a Kan dining table ta aje kayan ta gyara gyalenta ta nufi kofar.
Budewa tayi sai sukayi arba da zilai Mai aiki da 'yar jakar kayanta.
Cikin farin ciki Zahra ta karbi jikar kayan tana fadin "sannu da zuwa anti zilai"..
Suka shige ciki murnar Zahra taki boyuwa itama zilan ba Karamin murna tayi ba lokacin da Ammah ta fada
Mata zata zo ta Taya Zahrar Zama. Nan suka shantake suna Hira har Kusan karfe dayan Rana kafin Zahra ta
raka zilai dayan dakin da ba cikinsa take ba ta aje kayan ta.
Tambayar Zahra zilan tayi me zata dafa musu,
"Ki dafa komai na ni harna manta wlh ashe ko break banyi ba, ga sandwich can ki dauka kada ya lalace, Zan
shiga na Dan kwanta kafin karfe biyu"
"To Allah kaimu" zahra tace "Amin"harta fara tafiya zilan Kira sunan ta tsayawa tayi har zilan ta karaso.
"Uwar dakina Naga kamar wani mutum mun gaisa dashi ko Mai gadi kuka canza". ,"Eh Mai gidan ne ya
canza shi wlh jiya lfy muka fita Amma yau muna dawowa ya sallame shi, wani ya Kira ya zauna Dani kafin
ya dawo.
"Wani Kuma daga Ina,?. "Nima ban san daga Ina yazo ba" Tab Allah kyauta ya kamata asan asalinsa gaskiya
zamanin ne yazo da wata irin rayuwa sai godiyar Allah".
"Wannan gaskiya ne". zahrar ta fad'a. Ita nufi bed room ita kuma zilan tana nufar kitchen.
✨✨✨
✨✨✨
Written
By
Maman Fateemah.
This page is deducte to the Family of late Alhaji Isah Musa bakin kasuwa kazaure.
Innalilllahi wa Inna ilaihi raji'un! Ina Mika sakon jaje da ta'aziyya ga jama'ar garin MAJIA TAURA LG bisa
ibtila'in daya samesu na gobara Mai Muni sakamakon faduwar tankar man petrol, Wanda yayi sanadiyyar
rasa daruruwan rayuka Allah ya jikan wadanda suka rasu,wadanda Kuma suke gadajen Asibiti Allah ya tashi
kafadunsu ya Basu lafiya yasa ya zamar musu kaffara ya kiyaye faruwar haka a gaba dan darajar manzon
Allah s.a.w.w
Page 30
_______Misalin karfe daya da rabi Mai a dai daita sahu ya sauke Asabe a bakin gate din gidan Zahra Dan
yauma Saida taje can kauyen jama'are gurin wani mutum da wata kawarta ta tab'a fada mata shi, Nan ma
ta karbo abubuwa Wanda za'a binna a gidan Wanda har abada Mahmud baze kara waiwayo garin Azare ba
ko sunan jihar Bauchi ma Sai yaji ya tsane shi.
Cikin karfin gwiwa ta karaso bayan ta sallami Mai Dan sahun tunda tasan Mai gadin Dan hannu ne dubu
biyu ta Isa tasa yayi musu kowa ne irin aiki ne, iyakar ta tace masa na tsarin gida ne ze binna Mata saboda
yau da gobe.
Knocking tayi da Dan karfi tana mazurai ita ga uwar matar gida. Cikin takunsa na kakkarfa ya bude kofar
gate Dan da hanzari tayi baya Dan ji yayi Kamar ze bangaje ta, kallo daya yayi Mata ya gane face din Dan
hoton da oga ya nuna Masa yafi bada mahimmanci akanta Dan ita ce suspect dinsa ta farko, yasan da ita
za'a yi amfani gurin isar da ko wane irin sako ne.
Da hargagi Zayyan ya tunkaro ta.
"Wa kike nema?"
Duk daburcewa tayi nan da Nan jikinta ya dauki rawa.
A'a Daman gurin matar gidan nazo munzo jiya ne basa Nan shine na dawo yau".
Ta fada tana rawar murya.
"Kama gabanki Nan ba wata mace a ciki gidan maza ne, idan Kuma Zaki shiga Bismillah tsuntsu daga sama
gasashshe, Dan muna da kudajen da basa haram akan duk Mai tsautsayi, idan na Kara ganin giccinki a
wurin Nan saina hadaki da karena yayi min fata-fata dake, wuceeee min daga nan" yayo kanta,da gudu ta
kwasa ko waiwaye babu.
"Stupid! Da gani wannan tsohuwar kwarkwar ce wlh Banda oga ya hana da kinci na jaki banza wato kin
samu oga a araha shine kuka Neman zaku masa shegantaka akan matarsa ni na rasa yanda akayi ma oga ya
Fado garin Nan,? Kuma har ya iya Zama a haka ba wani damuwa, ko Dan meze dameshi Yana tare da
wannan danyan gold din".
Ya fada Yana komawa bakin aikinsa Amma zuciyarsa fal tunanin abinda ogan nasa ya sani game da wannan
matan daya turo Masa hutunan su ya Kuma shata musu dogon layi.
Asabe Bata samu zarafin tsayawa ba Saida ta dangana da wani gurin me suyar kifi a bakin titi shima gani
tayi gurin da jama'a ko cimmata yayi za'a ceceta, gefe ta koma tana mayar da numfashi sai lokacin ta dubi
hanyar data fito ko Mai Kama dashi Babu. Gefen wani dutse ta zauna tana tunanin to koba gidan da sukaje
jiyan bane tunda ba wannan basamuden suka tarar ba Amma daga Daren jiya Zuwa yau har lamarin ya
canza ita damuwarta daya shin sakon da suka bayar ya sameta ko kuma na jiyan ba shine asalin Mai gadin
ba yayi musu ta 'yan duniya ya barbe kayan da kudin ya wuce nasa gurin.
Tashi tayi Kamar wadda aka tsikara ta dauki 'yar ledar data sawowa Mai gadin Dan abun tohiyyar Baki sai
Kuma labarin ya canza salo. Harta dauko wayar ta Sai ta mayar idan tayi gigin fadawa Mama kwabarta
zatayi ruwa Dan a yauma Saida Mana ta karo kudi masu nauyi tace a bawa Mai gadin yanda duk abinda
za'a saka shi yaji baze iya gardama ba, to idan ta koma Mata da wannan labarin amshe kudin zatayi tasan
halinta kayan ta, data Bata naira dubu gara ta bawa Dan tsubbu dubu hamsin, Sam Bata karuwa da ita saita
wadannan hanyoyin idan ta aiketa tunda itace amintacciyarta ta Nan takeyin nata duk rintsi bazata so ta
rasa wannan mafakar ba Dan Kusan da ita ta dogara gurin kwaramniyar yau da Kullum nata.
*******
Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti ashirin da hudu, da sauri ta Mike
tana addu'ar tashi daga barci tayi mamaki ita fa gani tayi kamar barcin minti goma Sha biyar tayi Ashe
lokacin ya ja haka, alwala tayi tazo ta Fara sallah bayan ta idar wayar ta da dauko Ummee ta Kira cikin
shauki tun dazu ta nemeta network din na garin ba kyau sai hakura tayi, Bata jima ba tana ringing aka daga
ba Ummeen bace wata ce ta daga tana ta yi Mata larabcin gargal ita kuwa zahrar na language yafi kwarewa
a Dan daburce tayi Mata bayini ta gane Ummeen ta fita masallacin Annabi sallah tunda har lokacin suna
Madina basu tafi ba Kuma a yanda sukayi daga Saudi Arabia Nigeria zasuyo gurinta, sallama tayi wa matar
ta kashe.
Number sajida ta lalubo ta syprus tasan zata Sha mita tun ranar da sukayi ways da wayar Amatu tayi Mata
buyagi ta kashe Basu Kara waya ba, har tayi ringing ta katse Bata dauka ba, Bata hakura ba wani Kiran ta
karayi shima Yana daf da ze katse aka daga.
"Haba bestie Ina ta kira kin shareni ko har yanzu fishin ne?"
Mai makon taji bestien sai muryar Fatima taji tana kwallawa Sajidar kira tana fadin "ku taho ga Amarya
Zahra! Zahra" ta kirata da karfi tana murna kamar zata tsaga wayar, daya bayan daya suka dunga gaisawa
suna ta korafin amarci Dadi ta Kama waya ta rufe wato Bata so a shigar musu rayuwa ko? Hakuri ta Basu
tare da fada musu tayi missing din waccen wayar ne har sim din, sai daga karshe sajida ta karbi wayar.
"'yar duniya wato kinji dadin lamarin ko Kika wani shareni, ni yanzu ai yallabai Mahmud ya fiki kirki kinsan
ya kirani Kusan sau uku? Daman ko Baki kirani ba Zan kiraki dazu wurin Sha daya ya kirani Wai na kiraki na
lallasheki yayi tafiya ya baroki kina kuka?".
Ya fada tana kunshe dariyar ta.
"Malama ki fito kiyi dariyar ki sosai kada ta kume Miki a ciki,da kike wani kunsheta".
Dariyar tayi da gasken sai tayi Mai isarta tace. "Dan Allah bestie mekika bawa wannan guy din Kinga yanda
yayi masifar macewa a Kanki? Wlh har tausayi yake bani Ni har mamaki nake idan ya kirani Yana min
maganarki ranar Nan fa cewa yayi na bashi labarin zamanki a Nan syprus din wlh nayi zaton da Wasa yaki
tunda nasan ba Karamin cajin kudi za'ayi ba. Amma haka na ware na rinka bashi labarin har na Gama ko a
jikinsa, yanzu Ina aka tsaya da fatan komai ya dai daita? Dan nafi son dai dai lokacin ganawarmu muyi
murna biyu graduation da naming ceremony".
"Wlh Zan kashe yaushe Kika zama haka Mai bin kwakwkwafin jama'a? to bazakiji ba an fada Miki kowa ma
irinki ne ai wlh ya Abdul Hakeem ya debo ruwan dafa kansa Dan nasan Dan bawan Allah saiya rinqa
guduwa daga gidan"
Wata irin dariya ta saki tana fadin "billahil Azeem gara wata wainar data wake yarinya gyara zancen ki idan
ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma idan ana sallah ba'a magana".
"Wlh sharri zakiyi Masa Amma shi dai salihi ne".
"A inda salihai sukayi karanci ba".
"Mubar zance kawai tunda abun ya Zama haka".
Zahra ta fada tana cire hijabinta daga jikinta vest ce Fara Kal sai wando shima fari ai pink din kananun
flowers gashin tayi parking a tsakiyar Kan ta kashe da band shima pink, sai fito baby sak.
Gyara kwanciya tayi, tayi ringinnine da wayar a kunnenta Hira sukaci gaba da sajida yawanci duk akan
auren zahrar ne. Sun dauki lokaci Mai Dan tsawo suna tattaunawa akan bututuwa da dama kafin suyi
sallama, ta nufi toilet wanka take son yi kafin ta fita cin abinci.
********
Jirginsu Mahmud a Addis Ababa Bole international airport yayi landing, daki biyu Sameer ya kama musu
Nan kusa da airport din tunda a kalla zasuyi Kusan three hours.
Saida ya kaiwa Mahmud jakar laptop dinsa sannan ya nufi nasa dakin, bayan fitar Sameer Mahmud wanka
yayi sannan yayi sallah maimakon ya kwanta ya Dan huta sai kawai ya bude wayarsa so yake ya ganta duk
wani matsi da yayi tana manne da zuciyarsa so yake ya ganta kafin ya kirata. CCTV ya shiga ta wayarsa duk
abinda akeyi ya rinka bi Yana gani yasha dariyar karon Zayyan da wannan matar wadda ko sunanta Bai sani
ba, shi yasa ya dauko shi yasan shi kadai ne cikin amuntattunsa Wanda ze Masa wanna aikin ba tare da an
samu matsala ba.
Saida ya gama kallon ko ina na gidan yaga ba wata matsala, sannan yayi zooming din cikin bed room dinta
daga ita sai vest purple da wando skintight kanta tayi parking da purple din band sai tayi wani irin kyau na
musamman, kura Mata ido yayi Kamar ya warto ta yakeji, turare ta dauko tana fesawa a jikinta. Nan ya
shiriri ce Yana kallonta knocking din da akayi Masa ya katse Masa abinda yakeyi, umarni ya bada a shigo
Sameer ne sai ma'aikaciyar hotel din dauke da tray na abinci sai karairaya take shi har dariya abin nata ya
bashi, me Kamar zahra yaushe irin wadannan zasu burge shi, bayan ta wuce ne ya dago ya dubi Sameer
"kada ka qara zuwar min da irin wannan a rinqa bawa maza suna kawo min kawai".
"Noted sir"
Ledar dake hannunsa ya Mika Masa Mai tambarin wani boutique ne, sannan ya aje Laptop dinsa a kusa
dashi Yana nuna masa wasu ayyukan da ya Gama yanzu, sun jima suna aikin kafin sameer ya fita saboda
lokacin tashinsu ya kusa cika shi kuma Mahmud ya ciro kayan da nufin sakawa.
Saida Zahra ta Gama feffesa turarenta sannan ta dauko after dress ta zura ta yane kanta da gyalen sannan
ta nufo parlour, zalai ta samu tana 'yan goge goge duk da ba wani datti a gurin, gaishe da zilan tayi tana
Mata sannu, ajiye mofar tayi "Allah ya taimaki uwar dakina ga abincin can nayi Miki abinda kikeso faten
dankalin turawa da pepper soup din kifi"
Zama Zahra tayi tana fadin "Kai Amma wlh na gode kwarai da gaske shi yasa nake yinki kinsa favorite Dina
wlh".
"Ai shi yasa na cewa Ammah kada a wani dauko yarinya tun daga Mubi Nima na isa na zauna dake saina
kirawo Kanwata Alawiyya ta cigaba da yiwa Ammar kafin Allah yasa yallaban ya dawo, ai ni har zaman
wanka ni zanyi Miki Koda kuwa bakwa garin Nan ne".
Dan smile tayi kawai bata ce komai ba saima ta canza akalar zancen.
"Ni Kuma Aunty zilai kin mikawa mutumin Nan abinci kuwa?".
"Ai tunda na Gama na zuba na hada harda ruwa da lemo na mika Masa. Naga Dan gayu ne beyi kalar
masu gadi ba".
Dariya zahra tayi tana fadin "Aunty zilai kenan shi Mai gadi har Kama gareshi".
Yana da kama Mana Wai Kinga wannan din?"
Na ga wani dai dazu ban sani ko shine Wanda aka Kira jiya cikin dare".
" Cikin dare Kuma?"
Kai ta gyada "Mata kusan Hakan tunda Sha biyu ta wuce ya kirawo wani kawai umarni ya bashi yazo garin
Nan da safe kinsan bakwai a Nan tayi mass nifa mutumin Nan wlh tsoro yake bani na kasa gane kansa".
Dan murmushi zilan tayi tana kallon Zahra "kiyi hakuri uwar dakina a hankali Zaki San komai a kansa badai
Kuna tare ba da sannu Zaki gane shi din waye, kici abincin sai muci gaba da hirar idan kin gwma".
Bata k'i Shawarar zilan ba ta tashi ta nufi dining ita Kuma zilan ta nufi dauko Mata ruwa da mutuniyarta
farm fresh, sai da ta Gama cin abincin sannan ta dawo parlourn gurin da tabar Aunty zilan sukaci gaba da
hirar su, amma Kusan hankalin Zahra yana Kan Mahmud haka Nan sai taji ya fado Mata ta yarda da ake
cewa sabo turken Wawa, yanzu da baya Nan sai taji duk kewarsa ta kamata, tun dazu take duba waya ko
zataga kiransa Amma shiru tasan tsakanin Nigeria da inda zasu indai da gaske chinan zasu da nisa a kalla
jirgin zeyi landing a Ethiopia da India yaci ace ya kirata Amma shiru har Yanzu ko lfy? ta ayyana a cikin
zuciyar ta.
Ganin tunanin Zahra yayi zurfi yasa zilan ta tashi tana fadin Bari nayi wanke wanke tunda kin Gama da
kwanukan"
Tayi hanyar kitchen, ita kuma ganin tunanin ze dameta yasa ta kunna tv ta kamo MBC MAX tana son
finafinan su sosai,Aunty zilan ma data Gama Zama tayi sukaci gaba da hirar jefi jefi har aka Kira magariba
suka shiga sallah. Tana addu'oin yaumiyya na cikin du'aul mustajaba ne kira ya shigo wayarta da sauri ta
dauko tana duba Mai Kiran Ummee ta gani da sauri ta daga tana fadin "Ummeena"
Amsawa tayi suka gaisa Ummeen ke fadar an fada Mata ta kirane nan tayi Mata fadan rufe layi da tayi,nan
Zahra taji kuka yazo Mata, Nan da Nan Ummeen ta rude tana tambayar ta ko tana da damuwa ne ta fada
Mata cikin kukan tace "Ummee Shima fa wannan daga kawo ni gidansa ko sati daya ban rufa ba ya tafi ya
barni Wai aiki zejeyi uk" shiru Ummee tayi kafin ta shiga rarrashinta da kalamai na kwantar da hankali da
nuna Mata ba lallai ne hasashenta ya kasance gaskiya ba, kada ta damu saboda ita har Umara tayi bayan
auren tayi mata addu'oin samun nasara akan dukkan lamuranta, sannan ta yi mata fadan ta kiyayi yawan
kukan Nan bashi da ma"ana, daga karshe tayi Mata albishir zawan su next week harda Mama Hanifa da
Aunty Nawwara duk suna hanya Daman ko Bata sameta a waya ba zata kira Hajiya Asma'u tasa a fada
Mata. Murna ta shigayi Kamar tayi me har Ummee na Mata dariya Nan da Nan ta ware ta shiga lissafo
abinda takeso Wanda za"a taho Mata dashi.
Bayan maga wayarsu da Ummeen Ammah ta Kara kira lokacin tana tare da Abba.
Tana zubawa Abba Dan fruit salad wayar ta dauki ringing Abban ne ya dauko ya duba 'yar dariya yayi Yana
mikawa Ammar wayar tare da fadin.
"Uwata ce ke kira". Ganin Kiran ze yanke yasa Abban karbar fruit salad din yaci gaba da zubawa Yana fadin
"A dauki Kiran uwata kada ya yanke".
Daukar tayi tana amsa sallamarta da gaisuwar da take mata.
"Ammah yanzu Dan Allah bazakizo ba Kuma Aunty Hasana ma fa batazo ba fa Kuma Ni sonake na ganki".
"Ikon Allah yanzu ke saboda Allah sai a ganni a gidanki a irin wannan kwanakin ai sai a dauka ba lafiya
Auntyn taku dai zatazo Daman jiya take fad'a zata shigo ta ganki tunda mijin naki baya Nan, ai Mahmud
din ma ya turowa Abban ku da sako ba dadewa ta whatapp yace sun sauka lafiya, ke dai abinda nakeso ki
kwantar da kiyi Masa biyyayya kinji".
Ta fad'a tana rarrashinta.
"To Ammah, daman kira nayi na fada Miki Ummee tace next week zasu shigo Nigeria nasan zata fada
Miki".
"To Allah ya kaimu Daman munyi maganar shekaran jiya har take tambayar meya faru da taki wayar? Nace
ta Dan samu matsala ne, ga Abbanku yace a gaishe ki"
"Lah! Ammah Daman yana Nan amma ba'a fada min ba Bashi na gaishe shi"
Sun gaisa da Abban har Yana Dan tsokanar ta, tunda a wani bangaren kakace a gurinsa, Nan yake fada
Mata mijinta yace ya tafi da motarta Kano tana airport Dan haka daga nan Zuwa jibi za'a kawo Mata daya
motar ta gurin Muttaka, godiya ta yiwa Abban sannan sukayi sallama.
Ta jima Bata aje wayar ba, tana juya maganarsu da Ammah Wai ya fadawa Abba sun sauka wato ita da
bayaso Bata da matsayin da ze kirata ko sako ya fada Mata sun sauka, kenan Daman duk abinda yake Mata
a 'yan kwanakin Nan yaudara ce Dan ya lasa Mata Zuma a baki ya gudu ya barta da kewarsa inda ta
godewa Allah be lalata mata rayuwa ta gudu ya barta ba wlh duk rintsi sai ta bar Kasar Nan ta koma
Jordan, Dan tasan Allah kadai yasan halin da Ammah zata shiga idan bawan Allahn Nan yaqi dawowa....
✨✨✨
✨✨✨
✨✨✨
✨✨✨
Story
&
Written
by
Naman Fateemah.
page 31
______________Har aka Fara Kiran sallar insha'i tana zaune tana faman tunanin makomarta, tashi tayi tayi
sallah, nan Kan sallayar ta kwanta tana lazimi a haka har barci yayi awon gaba da ita.
Tun zilai na saka ran fitowa Zahra har ta hakura ta shige ciki duk da ba barci take ji ba, tun yamma take
ganin zahrar wani sukuku Kamar marar lfy.
Zahra ba ita ta farka ba sai Kusan daya da kwata, tashi tayi tana mik'a tare da salatin Annabi, duk jikinta
ciwo yake Mata hijabin ta cire tare da after dress din ya Zama daga ita sai vest da wandon toilet ta shiga
Bata Dade ba ta fito canja kayan jikinta tayi da rigar barci ta Kashe wutar Mai haske ta kunna bed side
camp tayi shiru tana istigifari ga Allah s.w.a da Salati ga fiyayyan halitta Annabin Rahama duk yanda tunani
yaso ya bijiro Mata saida ta kawar dashi kawai ta fawwalawa Allah lamarinta tasan duk rintsi Yana tare da
ita, a haka har barci yaci karfinta.
Da safe har zulai ta Gama share share da mofin Zahra bata fito ba ganin shirun tayi yawa yasa tayi tunanin
buga Mata kofa kada ta Zama babbar banza zuwanta ya Zama marar amfani rabonta da yarinyar nan tun
magaribar jiya Bata Kara sakata a idonta ba, kofar bedroom din ta nufa tayi knocking taji shiru lokacin
Zahra na Wanka, Kara bugawa tayi still dai shiru taji Nan da Nan hankalinta ya tashi kada fa wani abu ya
Sami yarinyar Nan ta shiga uku.
Tana Nan tana shawarwarin ta bude ta gani ko lafiya? taji alamun motsin tafiya daga ciki da sauri ta Kara
knocking din, Zahra da towel a jikinta ta nufo kofar ta bude.
"A'a Aunty zilai kece? Ina kwana?"
Ta fada tana goge gashinta daya jike gurin wanka.
"Lafiya kalau, naji ki shiru ne tun daga shiga sallah jiya harna gaji da zama Baki fito ba, gashi yanzu ma naji
shiru har Ina kokarin Kiran Ammah na sani koba lfy ba".
Ta fada tana kokarin barin gurin "na gode da kulawar ki Aunty zilai wlh jiya barci ne ya daukeni a nan Kan
sallaya bani na farka ba sai Kusan karfe biyu na dare".
"Ikon Allah kice kwanan kasa kikayi da sanyin tayis Bai Kama ki ba, tunda Naga gidan naku ko Ina sanyi
Kamar gidajen larabawa".
Sai Kuma ta rufe bakinta da hannu.
"Kin jini ba wlh na manta Ashe gidan nasu ne".
Dariya Zahra tayi "Kayya Ina wani balarabiya anan ai da uba ake ado Ni bafulatana ce kalarce dai na dauko
tasu Amma idan masu abun suna yarawa wani abun sai kallo Dan ma Allah ya hadani da jarimin uba da
yayi tsayin daka gurin ganin na iya yaren saboda na samu saukin mu'amala da dangin Mamana".
"Wannan gaskiya ne Allah ya sakawa Alhaji da Alkhairi ya biya Masa bukatunsa na Alkhairi"
"Allahumma Amin".
Zahra ta fada.
"Me za'a dafa miki? Mu dai nayi Mana nida bakon ku".
"Wai bakon mu wato dai bazaki ce Mai gadin ba ko?.
Dariya tayi. "Wlh baya Kama da masu gadi Kinga kuwa ai bana ce Masa ba".
"Haka ne ki dafa min indo mie da cooker oat kawai".
"To an gama sai kin fito".
Ta fada tana juyawa zuwa main parlour din yayin da Zahra ta koma ciki.
*************
DAMAGARAM NIGER REPUBLIC.
Cikin takun ta na nutsatstsiya kuma wayayyar mace 'yar gayu ajin karshe ta shigo parlourn tana sanye da
doguwar rigar madam gezber kalar peach sai gyalen kalar light yellow touching din flowers din dake jikin
kayan sai takalmi plat Mai azabar kyau shima light yellow din tun kafin ta karaso kamshinta ya hade gurin.
A hankali ya dago ya dubeta har ta karaso gurinsa, tattara aikin da yake yayi ya Maida hankali a kanta
lokacin da take Zama a kujerar dake gefen da yake.
"Sannu da aiki Yaya barka da Asuba".
Ta fada tana sadda kanta kasa Bai amsa ba Jin shirun yayi yawa yasa ta dago kanta ta dube shi, ita yake
kallo.
"Yanzu abinda Kika zaba kenan Zainab da girmanki da hankalinki ki zazzage jiki ki baro dakin mijinki kizo ki
nemi guri ki zauna mijinki yayi rarrashin duniyar Nan kinqi ki saurare shi daga karshen ma Kika zabi ki dawo
Nan Damagaram saboda a Yamai uncle Yousoufu ya nuna Miki rashin kyautatawar abinda kikayi shine
kikayo yajin Nan ko?.Ni tunda tubus ne Bari kizo ki zauna ki Mike kafa gashi nan har an Fara kawo Miki
caffar ana son aurenki idan kin Gama idda wannan arzikin ki ne?".
Ya fada Yana kureta da ido, da sauri ta cira Kai ta dube shi. "Ni Kuma Yaya ake jawo min zawarci kawai daga
ganin mace sai ace zawara ce".
"Kada kiga laifinsu sun ganki yau sun ganki gobe Baki da niyyar tafiya,idan Badi'a zata fita ki wanke jiki ku
kama tafiya ba dole ace Miki haka ba".
Idonta taf da hawaye ta dube shi "to Yaya ya akeso nayi kasan dai yanda abun Nan ya kasance duk yanda
naso a saurareni idanuwa suka rufe ba Wanda ya kula da abinda nakeso su gane Saida suka rabani da Dana
yabar gida cikin bacin Rai Wanda har gobe ba Wanda yasan inda yake, gaskiya Kuma tayi halinta yanzu za'a
matsamin da zarya na fada musu niba yaji nayi ba duk ranar da yarona ya dawo Zan dawo".
"Zainab a gabana kike fadar danki, Dan farin ba zakiyi min Kara ba".
"Kayi hakuri Yaya na Bari d'anka to" ta fada.
'yar dariya yayi na nawa Kuma sai dai a koki gaba, yanzu Dan Allah Alfarma zakiyi min kiyi hakuri ki koma
dakinki Suma sauran yaran suna bukatarki kusa dasu ko badan Babansu ba ki duba girman Hajiya Inna har
Yamai Saida tasa aka kaita ko a jirgine dai ai tanayi dake ne amma Kika kasheta da dadin Baki akan kina tafe
kikayi zaman ki karshe ma kikayo hijira daga can, duk laifin Hajja ne wlh ita an taba Mata dan 'yar so ba
zaman lfy, gobe nace aje Abuja a daukeki tunda ba jirgin sokoto direct, kije kiyi ta yi masa addu'a bakin
uwa Mai Albarka ne akan 'ya'yan ta muma muna tayaki nasan fushi yayi idan ya huce ze nemi gida".
Har ranta bataso wannan hukuncin ba Amma yata iya da Yaya ishaq uba ne sak tun bayan rasuwar
mahaifinsu bai barsu da kukan maraici ba, duk rintsi baya Bari su koka uwa uba yanda ya janyo gudan
jininta ya nuna Masa hanyar nema tun a kananun shekaru duk abinda yaronta ya zama shine sila gashi
Zuwa yanzu Allah yayi Masa karfin daya fi na Yayan. Hira sukaci gaba har Aunty Badi'a ta fito itama kamar
me Zuwa gasar sarauniyar kyau ita Fara ce tas buzuwa kallonta Yaya ishaq din yayi "wato ta wata fuskar
naji dadin zuwanki Zainab ko banza mutuniyar ta koyi gayu irin naki da dai sai a hankali".
"Kai Yaya wlh bani na koya Mata gayu ba Daman Aunty na me class ce ko Aunty?".
"Fada Masa dai,kawai nasan dai na koyi amfani da perfumes designers dani kowa ne ma saye nake Amma
yanzu tunda ta bani naji dadinsu nake amfani dasu". Dariya yayin Yana fadin .
"Ba cinya ba Wai 'yan magana sukace kafar baya, Wai yanzu Ina da kikace min zakuje? Bana son yawo har
an Fara min sallama idan ta Gama idda".
Ido Aunty Badi'a ta kwalalo "sallama Kuma?.
"Wlh kuwa shi yasa nace ta tattara tayi hakuri zanyi Mata booking ta tafi kawai muci gaba da addu'ar Allah
ya bayyana shi duk inda yake".
"Gaskiya kam shi yasa kenan ranar da mukaje gidan sarki kingmakers sun fito daga meeting da Mai
martaba Naga ana nuna ta har wani dogari Yana kokarin Zuwa gurin mu muka tafi".
"Kinsan kuwa sakon daga fada yake".
Baki Ammi ta rike "tab gara nasan inda dare yayi min kafin wannan labarin ya Isa kunnen general".
Ta fada suna nufar kofar fita daga falon.
"Da dai kin yiwa kanki gata"
Yaya Ishaq ya fada.
*********
Tun safe su Mahmud suka fita da Sameer su shiga can su fita can duk da Sameer Kusan Dan kallo ne an Kai
ruwa Rana kafin a samu ganawa da Wanda alhakin matsalar ke hannunsa Basu suka dawo ba sai dare a
gajiye suka dawo Jin dadinsu daya ba a hotel suka sauka ba gida ne. Sameer yayii musu order din abincin
Africa. Saida sukayi wanka sannan sukaci abincin inda Allah ya taimaka sunyi sallah a wani masallaci a
hanya. Bayan Mahmud ya shiga daki wayarsa ya Ciro ya shiga ciki gurin da akayi Masa connecting da CCTV
nan ya lalace gurin kallon Zahra yanda yake more kallonta yasan da ace tasan da CCTV a dakin bazata Bata
sakewa haka ba tana sabgoginta. Amma ganin ita kadai a dakin take zuba yanda takeso, amma yanda ya
fuskanceta kamar wani Abu Yana damunta ya Raina yanda take walwalarta, ya rasa aikin me suke ita da
Mai Taya ta zama Dan gani yayi ita Mai tayata zaman ta fita waje da alama wani Abu ta sawo Dan can baya
yaga ta hada wuta da gawayi akan wani Abu ta Dora tukunya Mai Dan girma, so yake yaga wace wainar
zasu toya.
Dayar wayar ya dauko Yana kokarin kiranta sai kuma Kiran Mr Lee ya shigo akan Yana fada Masa kome yake
ya fito bakin da zasuzo daga Thailand sun karaso shi kadai ake jira, tashi yayi Yana Kiran Sameer akan ya
zama ready zasu fita.
**
ZAHRA.
Tun bayan data gama break Basu zauna ba aiki Zahra ta dauko dambun Nama take son yi yau akwai
Naman da yawa sai kuma abinci shima Mai Dan yawa haka Nan taji tana son kaiwa Abban ta da Baba
Malam abincin juma'a zilai ce tace a sawo kufat ayi suyar dambun a Kai tunda da yawa za'ayi ta Bata kudin
aka sawo ta Dora, Basu suka Gama aikn ba sai bayan azzahar zilai ita ta mikawa zayyan bayan ta wuce ne
ya bude abincin yaga irin garar da aka kawo Masa yayi ta mamakin yanda matar oga ta iya girkin hausa
haka Mai shegen Dadi gashi ita Kuma ba bahaushiya bace ko Ina ya samo wannan da Kuma dalilinsa na
zabar wannan rayuwar shifa ko a mafarki baiyi tunanin ogan nasa ze iya sakewa har ya Mike kafa yayi
zamansa a irin wannan muhallin ba da iyalinsa, haka yayi ta sakawa Yana kwancewa.
Sai da su Zahra suka Gama Zuba komai a mazuban da suka Dace sannan Zahra ta wuce ta Kira magaji a
waya akan yazo tana nemansa sannan ta shige wanka sai bayan la'asar magajin yazo lokacin ita kadaice a
falon tana tulawar alqur'ani, Saida ya cika cikinsa Yana zuba Santi sannan ta bashi yace ta fito Masa na
Baba Malam Dana gurinsu Ammah har ya Kai kofar fita daga parlour ya juyo Yana fadin "inyeeh su Adda
Zahra an girma har an Fara aikin neman ladar tsaffi da fatan dai kin fadawa mijin naki kada garin neman
lada a kwaso zunubi". Ya karasa fada Yana dariya.
"Allah ya shiryeka magaji Kai Kullum baka girma ko?"
"A'a zancen gaskiya ne Dan bawan Allahn nan baki San yanda yayi ya Nemo kudin sayen kayan nan ba
Amma kin tashi kin zuba irin wannan garar Dan kawai Kinga baya gari ko?"
Harararsa tayi "To nayi kayan nan dai nawa ne mijina ya aje min Bai Kuma yi min iyaka ba duk abinda
nakeso zanyi dasu idan bazaka Kai ba dawo ka aje min sai Aunty zilai ta Kai ko naje da kaina". Ta taso ta
nufo inda yake da sauri yayi gaba Yana fadin.
"Allah ya huci zuciyar uwar gidan Mahmud tuba nake".
"Dan rainin hankali shi dai gurinsa ya saka mutane magana".
Aunty zilai ce ta Bata amsa Sam Bata lura da fitowarta ba.
"Kema uwar dakina Kamar kin manta halin Mai sunan Alhaji ai shi burinsa Ke nan yayi jan magana".
"Masha Allah kice wata Rana ku sai turai tunda Mai gida ya Fara irin wannan babbar harka ai ku hannu
sama chololo lallai mutuniyar kinzo da goshi".
Tsaki tayi wlh ki raba kanki da camfi Wai nazo da goshi to tun kafin nazo yake aikinsa Kuma tafiyar ma
dagawa sukayi tun ba labarina a rayuwarsa zasuyi abarsu Nima da abinsa na same shi sai yanzu ne dai ta
Kara tasowa.
Haka suka dunga Hira har Kusan magariba sannan suka tafi Zahra ta Basu kilishi da biscuits masu yawa.
Saida magaji ya Fara Kai sakon Baba Malam sannan ya karasa gida, yauma aikin Ammah ne lokacin daya
shiga parlourn ta ba kowa sai Alawiyya tana saka turaren wuta da freshner tambayarta yayi Ina Ammah?
Tace Masa taji dakin Abbansu can ya nufa da basket din da ledar knocking tare da sallama a kofar falon
Mamace ta amsa Masa ya bude ya shiga da alama wani Abu suke tattaunawa.
Gaishe da Abban yayi sannan ya gaishe dasu Ammah Yana aje basket din da ledar Naman da aka kunshe
cikin poil paper.
"Abba gashi inji Adda Zahra tace a kawo maka".
Mama ce ta taso tana fadin"Kai Masha Allah lallai wannan 'yar tana ji da Abbanta". warmers din ta Fara
cirowa tana bude miyar falon ya cika da kamshi Curry da spices.
"Abban ne yace "magaji sannunka Kaima lallai uwata ta haifu Allah ya yiwa wanna aure Albarka ya tsane
idon makiya wlh naji Dadi kwarai da gaske a Miko min nan Naga abinda uwata ta kawo min".
Ya fada Yana mik'awa magaji bugun Abuja biyar zuwet.
"Na gode Abba, Kuma ta bada an kaiwa Baba Malam ma ya fada Yana nufar kofa.
"Masha Allah nasan uwata zatayi abinda yafi haka".
Cikin rawar jiki mama ta kinkimi basket din ta Kai gurin da Abban yake zaune ta dora akan coffee table,
sannan ta dauko ledar, ledar yace ta bude lafiyyayan dambun naman rago ne yasha kayan Hadi ya sayu
jawur dashi sai Kamshi ke tashi, Dina yayi yakai Bakinsa ya tauna Yana fadin "Masha Allah uwata ta Gama
min komai wlh har Raina Ina son yarinyar Nan bilhaqqi uba ta daukeni sak duba ki gani Rabi'a ga Asma'u a
zaune amma Ni ta yowa wannan garar Kai madallah, Yau abincin ki sai dai yayi hakuri na uwata zanci".
Ya fada yana kallon Ammah. 'yar dariya tayi Ammah tana fadin "Ana ta sabon d'a wa yake ta tsohon da inji
barmani choge".
"Gaskiya kam, ai Babu Mai shafewa Zahra Zane a gurin Abba"
Mama ta fada.
"Ki Fadi ki Kara Zahra yarinya ce mai tsananin yi min biyayya ki duba yanda lamarin auren Nan ya kasance
Amma tunda tayi 'yan koke-kokenta ta hakura ba Wanda ya Kara Jin kanta, duk da mijin nata Mai Karamin
karfi ne akan wadanda suka nemi aurenta Allah be nufa ba da Kuna duba da inda ta fito da Kuma uwa uba
dangin mahaifiyar ta Amma tayi zaman ta Ni kuwa ba abinda bazan yi Mata ba matukar baifi karfin arzikina
ba".
"Wannan gaskiya ne duba da yanda ta waye tayi karatu Mai zurfi ai ba wata ce bijirewa zatayi ayi ta Kai
ruwa Rana"
Mama ta fada.
Yar dariya kawai Ammah tayi duk Dadi ya cikata Bata taba tunanin Zahra nada wayo haka ba tasan dai
abun duniya Bai rufe Mata ido ba.
✨✨✨
✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨✨
✨✨✨
Maman Fateemah.
Page 32
_______Qaran alarm din daya saita ne ya tashe Shi sallar Asuba, duk da bai kwanta da wuri ba Dan sai
Kusan karfe biyu na dare suka shigo gidan, meeting din nasu sun jima suna tattaunawa akan sabon kafanin
da zasu bude a jihar kebbi na shinkafa, masallacin da suke sallah da gidansu akwai tazara sosai shiyasa ya
saita kafin sallar Asuba da kamar hour daya, sai da yayi yaqi da Shaidan sannan ya samu ya sauko daga
gado Bai jima a toilet ba ya fito sanye da bathrobe Fara tas Mai jikin towel. Jallabiya ya saka yayi
raka'atanul fajri sannan yayi waje a Yana niyyar yiwa Sameer knocking ya bude ya fito.
"Barka da Asuba" Sameer ya fada yana mikiwa Mahmud hannu sukayi musabaha,
"Ashe ka tashi ai nayi tunanin saina shafa maka ruwa sannan ka mitsa".
'yar dariya Sameer yayi Yana fadin "irinku da kuka San inda kuka dosa Kuna dagewa da mujahada to mu ta
Yaya zamuyi kwance muna barcin asara ai sai lalacewa tayi yawan".
"Kayya Kai dai Allah ya datar damu kawai"
"Allahumma Amin"
Sameer ya fada lokacin da suka jero suna Kara tattaunawa akan harkokin yau da Kullum, Sameer ne yaja
musu motar suka fice daga gidan, bayan sunyi sallar zama sukayi akayi karatu Kusan masallacin mahadar
'yan Africa ne mazauna can Kusan duk Wanda yake a kukkuken gurin Baya Bari khamsu salawat ta wuce
shi, sai da gari ya waye sannan suka nufo gida.
A hanyar ne Sameer ke fadawa Mahmud sunyi waya da Habib jiya a kan training din da za'ayi na matasa
maza da Mata na koyon sana'a.
Har suka zo gida suna zancen, yaso yayi barci amma ya fasa, so yake ya Kira Nigeria baze iya mazewa ba
Kamar yanda yayi niyya Bai gane shi Mai rauni bane sai akan yarinyar nan,sai da yayi Mata nisa ya gane
shayi ruwa ne, duk da Bata shigo rayuwarsa da Wasa ba kafin ya hadu da ita shi jarimi ne sannan shi
baima fa San yanda kake kwana da Abu ka Kuma tashi dashi, shifa idan ya tunata har wani ji yake zuciyarsa
ta harba, yaso ya dan Bata iska, so yake ya fahimci shin ta karbeshi da zuciyarta da gangar jikinta ko Kuma
har yanzu tana zaune dashi ne by force na iyayenta, amma idan ya kalli kwayar idanunta Yana hango wani
Abu na daban a cikinsu Kuma uwa uba yanda sukayi rayuwa a Dan zaman da sukayi da ita.
Bayan sun shiga gida kowa nasa gurin ya dosa Dan shi dai Sameer barcin ya kama, shi kuma daya shiga
wanka ya sake, shifa idan ze wuni Yana zubawa jiki ruwa bashi da damuwa. Sai da ya gama komai ya Haye
gado daga shi sai singilet Fara sol da boxer short.
Wayar ya dauko dauko cikin ikon Allah yaga Zahra online ji yayi wani Dadi yaji ya rufe shi, vedio call ya Kira
daya wayar Kuma ya bude connection din CCTV.
Tana cikin charting da Aunty Nawwara kawai kiran nasa ya shigo Yana kallon yanda ta kwalalo Ido waje
abin har yaso bashi dariya, hijabin da tayi sallah ta dauko ta rufa kirjinta sannan ta daga Kiran suna hada
Ido taji gabanta ya Fadi ji tayi abun Nan na da ya dawo Mata.
Sallama yayi mata da husky voice dinsa wanda ya saukar Mata da wata muguwar kasala, a hankali ta daga
idonta ta kalleshi cikin murya Mai rauni da rashin karsashi ya amsa Masa sallamar, kuri yayi da idon Yana
kallonta yanda tayi Masa wani irin kyau Kamar shi gani yayi a tsakanin jiya da shekaranjiya Kamar an Kara
Mata kyau.
"Ki bude Ido ki kalleni ki bani labarin abinda ya faru daga tafiya ta Zuwa yau, kuma wlh ki cire hijabin nan
tunda ba sirikinki bane Ni da Zaki dauko hijabi ki Kama rufe jiki wato Ni ban cancanta Naga abinda yake
halalina ba ko?"
Kai ta girgiza tana masa kallonsa a shagwabe.
"Nifa tunda nayi sallah nake sanye da abuna bawai saboda Kai na saka ba nida bansan zaka tuna Dani
bama ballentana ka kirani, nifa na dauka Kama shafe babina tunda baka nemana wanda ka damu dasu
kake nema".
Ta fada tana juya sexy eyes dinta wanda Bai sani ba ze dauka da niyya tayi Hakan.
Ajiyar zuciya yayi Yana Hadiyar yawu shifa ganin Nan da yayi Mata ta jangwalo masa wata fitinar da sai
Allah kawai.
"Ki cire hijabin Nan Allah kona Baki mamaki". Kafada ta make tana kallon gefe Dan wani fitinan nan kallo
yake Mata.
"Dan Allah ka dena kallona".
"Ikon Allah wato naje nayi ta kallon Mata a titi kenan ba ruwanki ke ko irin 'yar kissar Nan ta Mata Ni
baza'ayi min ba tunda ni ba Mai aji bane banyi boko mai zurfi ba ko
"Ni kuma? Yaushe nace bakayi karatu Mai zufi ba?"
Yar dariya yayi irin ta kana cikin ?nishadi din nan.
"Wato wayo zakiyi min na bar maganar hijab wlh ki cire Kona biyo dare nazo Nigeria na....
"Dan Allah ka Bari wlh Zan cire kada ka fada".
"Ki Bari kiji mezance Mana my previous".
Ya fada Yana Kashe Mata ido.
Itafa mamaki yake Bata idan Yana fadar wasu kalmomin turanci sai taji Kamar zurfin iliminsa ya wuce
yanda ake fada, ta ko Ina a waye yake ga wata irin tsabta ta ban mamaki itafa idan ba karya idonta yayi
Mata ba sai tace Bata taba ganin ya Mai maimaita Kaya ba idan ya saka Bata qara ganinsu a jikinsa.
"Wlh kiyi abinda nace kona baro Miki aikin da Baki shirya Masa ba, 'yar yarinya dake kin hana zuciyarta
sakat tunda na Dora idona a kanki komai ya kwance min duk, akanki na iya tsayawa nayi doguwar magana
na iya ja in ja akan Abu duk soyayata da Hajiya Innata saida mukahau sama da ita mukayi uwar watsi nayi
Mata yaji Kuma haka kawai Allah ya dubi diminiya ta ya tausayawa Dan malam kiyi min rowar ganin
halalina, wlh Zan fadawa oga Sameer ayi min afuwa na dawo gida na fasa attending din meeting din a saka
wani na dawo na rungumi 'yan kayana".
" Wai Kai baka jin komai idan ka Fadi magana! Dan girman Allah kayi zamanka kayi abinda ya kawoka in
dan hijab bari ba cire. Amma Dan Allah ka Bari na saka riga Allah ba kaya a jikina sai vest".
Wani kallo ya jefeta dashi na Amma kin Raina ni.
"Dan Allah, wlh kunyarka nakeji da gaske"
Ta fada tana sunkuyar da Kai kasa.
"Kunyata ni Kuma wlh immediately kuwa Zan cire kunyar Nan aini cutuwa zanyi, To wai tsaya na tambaye ki
yaushe Hakan ta faru? Ko bayan na baro kasar ne ki? amman ai bakya jin kunyar kallon tsabar idona ki
tarewa wani Kato fada Dan nace masa lusari kika Kare min tas har kina fadin na Kama ki na runguma ko
kina min kallon Dan duniya ko? humm Ashe ma duka nine lucky din a cikinsu dama na San abin nawa ne
Aida saina dama daddawata da moda a lokacin Dan wlh a Ranar sai da na Raina kaina Banda mutum besan
gobensa ba Aida saina Yi wandaqata a lokacin" fuskarta ta rufe da tafin hannunta dayan, da gaske so yake
ya koya Mata fitsara taga alama shima ba kyalle bane cikakken zani ne. Idonsa ne ya sauka q gurin data cire
hijabin.
"wow!! Masha Allah! Koke fa Amma da kin zumbuda hijabi Kamar wata matar liman ai yanzu hirar zatafi
Dadin yi ki kawar min da tunani kowa daga zuciyata sai naki, Baki fada min abinda kukayi jiya ba Naga
harda spare girki a waje" .
Zaro ido tayi tana dubansa "waye fada maka nunyi wani Abu a gudan?
"Nina gani kinsan nabar idona daya a Nan na taho da daya, ga Kuma Dan gidana magaji shine yayi min
voice note ya bani labarin selfishness din da kikayi na kawai su Abba Kika garar arziki ta juma'a Kika ware
min iyayena Mata, shi yasa Kika saye zuciyar su Abba da Baba malam kenan,? Kullum maganar daya ce ga
amanar yarinyar Nan ka kula da ita Ashe dai tushiyar Baki kike bayarwa".
"Kai wlh ba haka bane ai gani nayi idan na kaiwa Abba Kamar na bawa Ammah ne, haka Baba malam ma ai
Iya Abula na bawa koba haka ba"
"Eh kusan Hakan ne amman dai da gyara, Kuma kike wani cewa Abula ko 'yar Karar Nan Babu nifa sunan
tsohuwata ne,amma kici gaba da fada wata Rana kunya zakiji idan Kika fada a gabanta tunda bakinki ya
Saba fada kinsan dai mu mutanen karkara bama Raina abun fada can zakiji zance ya zagaye cikin kauyen
mu ace Mamuda ya auro 'yar birni ko sunan Inna Bata sayawa gatsau take fada".
Kai ta Dade tana tadan turo Baki irin na sakatattun yaran Nan tana fadin "Nifa ban sani ba Ina janta ne
tunda sunan kakata ne babar su Ammah zakace min waye waye nima ai Mamana ce ba taka bace Kai kadai
yanda kayi kutse a gurin Amma Nima haka zanyi a gurin Mamana harda Hjy Inna".
"Kice nayi celebration ana son da Ammi, inye matar Mahmudun ba, fada min wace addu'ar kike min Dana
kasa kallon ko wace mace da sunan so tun bayan kin shigo rayuwata, da dai bana musu da kowa Amma a
kanki humm har bore Saida na koya, oya fada min sirrin inji?"
Shiru tayi saboda ji tajeyi kamar zir take a gabansa, Amma ta lura shi ko a jikinsa kamar ma be damu da
yanda take din ba.
"Kinyi shiru ko abun sirri ne baza"a fada min ba?"
"To me kake so na fada maka".
"Komai ma, me kike fadawa samarin ki idan sunzo zance? Nima yau zancen nazo Wanda ban samu damar
yi ba a baya shine yanzu nike qara'i".
Batasan sanda tayi dariya ba "Au dariya ma na baki ko? Shike nan wlh nifa a kanki na iya zance me yawa
da mace ada daga Ammi sai Hjy Inna kawai nake doguwar Hira sadu, nasan duk ranar da Hjy ta ta ganki sai
tayi Miki ciwon Baki tace dan kwali yaja hula kinsan meta fada lokacin Dana fada Mata mgnr ki?" Girgiza
kai tayi alamar A'a.
"Cewa tayi idan na cika cikakken namiji na shiga duniya na nemoki, Ni kuma nayi wani Alkawari daga ni sai
Allah saina bata mamaki wlh".
Kama Baki tayi tana Dan Zuba masa sexy eyes dinta wadan da ke rikita Masa lissafi.
"Kakar taka zaka bawa mamakin duk soyayyar da kake yi Mata kace za'a ganku a rana?".
Kai ya gyada Mata yana gyara kwanciyarsa.
"Yes ai kece mahadin aikin da zanyi na Bata mamakin ko bazaki tayani ba?".
"Ni kuma meya hadani da dabin ku?"
"Kina son sani na fada Miki?"
"Uhm".
Karan doorbell ne ya dakatar dashi daga kokarin bayanin da ze Fara mata.
"My precious Afuwan naji ana bukatar shigowa Bari naje I will call you later, take care by".
Ya tura mata wani hot kiss Yana kashe Mata ido ya sauka daga online din.
********
DAMAGARAM.
Waya ce a kunnenta tana magana cikin tsantsar ladabi kamar tana gaban Mai magabar, cikin ladabi ta Fara
fadin "wlh Hajiya ba haka na fada Masa ba cewa nayi kada ya tura kowa Abuja nayi booking din flight ne
daga Abuja Zuwa sokoto, tunda Yaya ishaq jirgin Abuja ya yi min booking Kuma nace masa ko nazo sokoto
bana son a turo min kowa yanda na fita Ni kadai haka bake bukatar dawowa ni kadai kinji yanda mukayi
dashi ai nace masa Zan dawo Amma gani yake kamar gaba zan karayi"
"To ai yanda Kika gindaya Masa dokar ne yake tantamar hucewar taki, kiyi hakuri Zainab anyi Miki ba dai
daiba Amma ki zama mai yafiya akan laifin da akayi Miki kema sai Allah ya yafe Miki naki kura kuran, ki
Kara godewa Allah kece karama ke Kuma Allah ya daukaki naki Dan fiye da kowa a dangi ki dauka abinda ya
faru jarabawarsa ce tazo a haka,Daman Allah swa yace shin bana jarabceku ba? to ki dauka hakan
rubutaccen al'amarine daga Allah idan aka daure wata Rana sai labari, shi ba yaro karami bane da za'ace ya
bata kawai yayi Mana fushi ne inaji a jikina Yana kusa da dawowa garemu da izinin Allah, ai kawunsa
mustapha yace min ba abinda ya tsaya a harkokinsa Dan yana bibiyar lamuransa a yanar gizo yaga komai
yana tafiya daidai".
"Nima Ina bibiyar lamarin nasa Hajiya Amma abinda yafi damuna koni bai taba kirana ba ko sau da har
zuwa Yau".
"A'a Zainab mu duka masu laifine lokacin daya kamata a saurare shi kowa baya ya juya masa, Banda Mai
biyaya bane yanda Allah ya daukaka shi ko ganinsa basai yayi Mana wahala ba? Amma yaro Mai ladabi da
biyyayya mun taru mun yi masa naqi ba dole yayi nesa damu ba".
Saita balle da kuka, da kyar Ammi ta lallasheta tayi shuru. Sannan tayi mata sallama tana Kara jaddada
Mata zuwan tare da fadin ta turo direbanta ya daukota Dan gidanta zata sauka tunda anan tabar motar
data zo gurin Hajiyar da ita a Ranar data wuce YAMAI.
Aunty Badi'a ce ta karaso kusa da Ammin tana fadin "ina ganin soyayyar uwar miji da matar d'a amma ban
taba ganin irin taku ba inaga yanda Hajiya Inna ke sonki ko Yallabai Bata so haka gashi ta kwallafa rai kan
Mahmud kamar me"
Tunda Aunty Badi'a ta Fara Kora bayani jikin Ammi yayi sanyi saboda suk abinda Aunty Badi'ar ta fada
gaskiya ne, nisawa Ammin tayi "haka ne Aunty wannan observation ne me kyau hakan zanyi Daman
fulanince ta Fara kawo maganar Naga Kuma ya dace na Bata goyon baya, Amman in Sha Allah zanbi
Shawarar ki...✨✨✨
✨✨✨
Page 33.
MAMAN FATEEMAH.
________Zahra ta Dade a kwance tana sakawa da kwancewa, wani irin yanayi takeji a jikinta ita abun har
mamaki yake Bata "Wai menene hakan" tayi tambayar da ba Mai Bata amsa. abinda takeji wani Abu ne na
daban Wanda Bata taba Jin irinsa ba akan kowane da namiji ba, cikin kankanin lokaci ya cika Mata zuciya
ita abun har kunya yake Bata,ta gama bore harda su somewa dasu wunin Asibiti Kuma yanzu a wayi gari a
ganta dumu dumu cikin soyayyarsa ai da kunya wlh.
Wani tunanin ta qarayi Bata San lokacin data rufe idonta ba tana ambaton "Ya Ilahiy wlh abun da matukar
Allah ka agajeni gaskiya idan hakan ta kasance naji kunya".
Ta fada tana qara qanqame jikinta.
Saida ta Kusan Bata minti talatin tana abu daya sannan ta yunqura da kyar ta tashi,wanka tayi ta shirya
cikin English wears yellow irin shaking material din Nan sai sukayi Mata wani irin kyau Karamin mayafi ta
rufe gashinta dashi black Mai shara shara ana kallon bakin gashinta Mai santsi da laushi ta cikin gyalen,
sama sama ta fesa turarenta ta fito parlourn ba kowa sai kamshin freshner da turaren wuta kawai sai Kuma
sanyin A/C daya ratsa ko Ina,cikin takunta na nutsuwa ta doshi kitchen inda take jiyo motsin zilai a cikinsa.
Sansanyan kanshi ta ya Fara shiga hancinta zilan kafin ta karasa shigowa.
"Masha Allah! Uwar dakina dawisu sarkin ado, Allah ya barki gidan Yallabai muhmudu, ubangji ya kawo
Mana kazantar daki Amma Bata shara ba".
Dan murmushi Zahra tayi tana Fadin kin jiki Aunty zilai ni kibar wannan maganar gaskiya, Ina kwana".
Ta fada tana komawa parlour biyota zilan tayi tana Fadin "yau fa abinda kikafi so nayi Miki" ta fada tana
kokarin bude warmers din abincin,waina ce manya irin tasu ta Bauchi sai Kuma pepper soup na cow leg da
kunun gyada Wanda yaji Madara.
"Wow! Amma aunty zilai kin gama min komai na gode" ta fada tana janyo plate din da zata Zuba, zilan ce
ta karba da sauri tana fadin "haba dai gani a tsaye Zaki Zuba abinci da kanki to meye amfanina".
Rike plate din Zahra tayi tana fadin "Dan Allah kada muyi haka dake Ina laifin dafawar ma ai dadin sai yayi
min yawa, Ina kwance Ina barci kina ta faman dawainya sannan Zuba abincin ma Sai anyi mini".
"To menene ai aikina ne".
"A'a wlh ba Aikinki bane a Nan cewa akayi ki tayani Zama kwarai".
Ta fada tana bude abinci akan dole zilan ta hakura ta koma kitchen inda take wanke waken alale zatayi
musu cikin abincin Rana.
Bayan ta Gama yin break din parlour ta dawo ta kunna tasharta mbc max tana kallon wani film da sukeyi,
tana Nan zaune taji karar door bell ta tashi ta nufi kofar ta bude yara ne kamar 'yan sheka sha uku haka
suna rike da manyan ledoji kowa guys biyu a hannunsa.
Cikin girmamawa suka gaishe da Zahra tare da fadin "gashi inji Baba Malam yace a kawo Miki Kuma Yana
gaishe ki".
Suka fada a tare, hanya ta Basu suka shigo da kayan ciki sai raba Ido suke suna kalle-kalle.
"Sannunku ku aje ku zauna, na gode kwarai da gaske Allah ya saka da Alkhairi, a me kukazo ne?". Dayan da
yafi magana yace "Yaya Habibu ne ya kawo mu Yana kofa gurin wancen mutumin" ya fada Mata.
"Masha Allah". Ta fada tana Kiran zilai, da sauri ta fito tana fadin. Gani uwar dakina".
"Kaya ne Baba Malam ya Aiko aka kawo min".
Gurin da kayan suke ta karasa tana fadin "Masha Allah 'yar gatan Baba malam, an gode madallah sai a
Basu tukwaici". Zilan ta fada tana kokarin bude ledar dake kusa da it's.
"To Bari na dauko musu ki shiga da kayan ciki sai ki zuba musu abinci a robobin nan na take away Wanda
aka kawo saboda zuba kayan gara Dan kada su zauna yau Ranar wanki da 'yan aikace aikacensu ne," ta
fada tana yin gaba.
Bedroom dinta ta shiga ta duba Sam ba kudi a gurinta, Dan Jim tayi sai Kuma ta bude bedside locker ta
dauko keys din dakin Mahmud daya Bata.
Kamar' Mai tsoron wani Abu kada ya kamata ta bude dakin, komai tsab hatta kamshinsa Yana dakin kamar
yanzu ya fesa yabar dakin,limshe ido tayi tana shakar kamshi, komai na dangin electronic a kashe yake a
dakin a hankali ta ratsa ta nufi inda ya nuna Mata yace idan bukatar wani Abu ya tashi ta dauka, locker din
ta janyo 'yan dari biyar ne da dubu dubu ko wanne rapper uku uku 5k kawai ta Ciro daga cikin 'yan 1k din
ta mayar ta rufe tana tunanin Kiran magaji yazo ya Ciro Mata kudin saboda irin haka Bata bukatar komai
tunda ba abinda ba'a aje Mata ba wani abun ma Sai a shekara Bata nema ba.
Bayan ta kawo musu sukayi gdy suka fita, gurin Aunty zilan Zahra ta shige.
***********
Karfe biyar na yamma jirginsu Ammi ya sauka a sokoto, lokacin data fito Harabar da masu jiran saukar 'yan
uwansu suke,Habu direban Hajiya Inna ne ya nufo Ammi da sauri Yana fadar "barka da sauka Hajiya, nine
Hajiya Inna ta turo nazo na tare ki".
Ya fada Yana karbar karamar luggage din dake hannunta .
"To sannu da kokari nagode kwarai".
Direct gidan Hajiy innar ya nufa da ita da yake unguwar mabera, duk yanda Abban su Mahmud yaso ta
zauna part dinta daya Gina Mata Amman ta nuna tafi son daga nesa dai.
Har kofar falon Hajiya Malam Habun ya kawo ta bisa umarnin Hajiya, lokacin da ze tafi dauko ta fada masa
ya kawo Mata ita har kofar parlour.
Kafin ta fito Yara qananu guda biyu suka fito da gudu daga parlour wanda yayi dai dai da fitowar Ammi
daga mota da gudu suka karaso, suna fadin ga Ammi! Ga Ammi" suka fada jikinta a tare suna fadin "Ina
kikaje Ammi Baki tafi damu ba mukayi ta kuka".
Kansu ta shafa tana fadin "sorry My babies ba gashi na dawo ba, ai kuka Kuma ya Kare"
Hannunsu ta rike ta nufi kofar da suka fito, sun riketa ram kamar zata gara guduwa ta barsu.
A zaune Ammi ta samu Hajiya inna tana lazumi, gurinta ta nufa cikin takunta na nutsuwa tana fadin "Hajiya
barkanmu da yamma".
.
Ajiye tasbahar dake hannunta tayi tana kallon Ammi wadda tayi wani tas da ita, bazaka taba cewa ta aje
kamar' Mahmud ba, idan aka jera su mafi yawan mutane zasu ce yayarsa ce. Gefen Hajiyar ta zauna daga
kasa wannan d'abi'ar ta ce Bata taba Zama a kujera matukar Hajiya na Kan kujera, cikin ladabi irin na D'a
da uwa Ammi ta gaishe da Hajiyar Tana fadin "Masha Allah zainabu kin cika Alkawarin da Kikayi min Koda
kuwa ba a lokacin bane nagode kwarai da gaske Allah ya Albarkaci zuciyar ki ya Baki rinjaye akan duk masu
son su tagayyara Miki zuri'a, ki Kara hakuri akan Wanda kike yi lallai duk Wanda akace yayi hakuri an Bata
masa ne, Allah yayi Albarka yanda kike min biyayya kema Allah ya Baki surukar da zatayi Miki fiye da yanda
like min, Wai kin samu yin magana da mutumina kuwa bayan munyi wayar nan?".
"A'a har yanzu be nemi kowa ba ina ganin ko ba lafiya ba dai shirun tayi yawa ya Kamata ace zuwa yanzu
yayi hakuri ya huce ya dawo gida".
Ammin ta fada cikin damuwa.
"Ba komai in Sha Allah lfy na fada Miki yanda mukayi da mustapha kema kince kina bibiyarsa ayi ta addu'a
Allah ya sassauto da fushinsa ya waiwayo gida wallahi ko cikin dare yaron Nan ya Fadi min a Rai to barcina
ya Kare Kullum ta Allah sai anyi mini saukar Alqur'ani akan Allah ya bashi kariya a duk inda yake wallahi
nayi Dana sanin fada masa maganar da nayi danasan maganar tawa ze dauketa da zafi wlh da bazan fada
masa ba yana cikin zafi".
Hawaye ne ya balle Mata kamar lalataccen famfo har da shashhshekar ta.
"Dan Allah Hajiya kiyi hakuri wlh ba maganar ki bace tasa yabar gida nakin dai yazo Kan gab'a ne kawai".
"A'a keda Baki Nan mukayi yazo Nan Yana ta huci Dan motar dazo a ciki ma ko kashe ta baiyi ba ya fado
min Kamar an jefo shi, Yana huci Yana Fadi wlh duk duniya ba Wanda ya Isa yasa ya auri safna Koda Matap
sun kare shi Daman koya aureta biyayya ne zeyi Yana da wadda yake da muradin aure, ni kuma a lokacin
bani da cikakken masaniyar abinda yake faruwa kinja layin kada a fada min gaskiyar maganar,Ina bude Baki
sai ce Masa nayi idan ya ciki shi d'ane na halali ya shiga duniya ya Nemo min yarinyar da yake maganar a
kanta Wanda take ganin darajarta tafi ta zuwairiyyar, wlh shiru yayi a inda yake tsaye kasa cemin komai
yayi Kusan tsawon minti biyar, kafin ya kalli idona yace min wlh zakiga cikakken Dana halak, ki rubuta ki aje
idan kin qara ganina a sokoto ba tare da ita ba to kuwa shege ne ni,idan Kuma ban sameta nida sokoto har
abada ya juya ya wuce ko motar Bai kalla ba Kuma tun daga Ranar har Rana Mai kamar ta yau ban Kara
saka mahmudu a idona ba, sai dai Babban yaronsa Yana zuwa ganina Yana kawo min duk abinda
Mahmudun yake kawo min ciki kuwa harda magungunan da nake sha na hawan jini".
Ammi tayi mamakin Jin Sameer na zuwa gurin Hajiyar koda Wasa Bata taba Jin haka ba, Kenan wato kafa
ya bawa mutane Yana cikin Nigeria din kenan bawai inda ake zaton zashi ba.
"Allah kyau Hajiya ki daina damun kanki, jikina Yana bani Yana cikin kasar Nan Kuma Yana da labarin komai
tunda kikace min Sameer na zuwa, duk inda yake ya sani ya hana shi ya fada ne kinsan halin kayanki dai".
Mardiyya da Urat Hajiyar ta kalla Tana fadin "yan nema kunki iyayenku sai uwar wasu tun barinki garin Nan
yaran Nan suka tare a Nan Wai saina kaisu Yamai gurinki tunda aka fada musu naje suka tada hankalin
iyayen sai su dawo Nan idan Zan koma na tafi dasu, Kinga mardiyya jiya da Iyayen sukazo daki ta gudu ta
rufe Dan ma kada su tafi da ita, ko makaranta sai dai direban ya biyo ya dauke su anan ya dawo min dasu
Nan".
Kansu Ammi ta shafa tana fadin rigima ta kare tunda ga Ammin ku ta dawo ko?".
Kai suka gyada Mata a tare.
Masu aikin Hajiya ne suka shigo ta kofar baya daga kitchen suna fadin "lale marhabin da Ammi barka da
zuwa".
Gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar su iyalansu.
Abinci na musamman masu aikin suka gabatarwa da Ammi Wanda Hajiya ta hanasu sakat tun safe ake
saukewa da dorawa da gaske Babu Mai shafewa Ammi Zane a gurin Hajiya tana sonta kamar me.
Sai bayan insha'i Ammi ta kwashi su Urat ta nufi gida cikin motar data Bari a gidan Hajiyar. So take ta bada
mamaki yanda ta fice batare da sanin kowa ba a wayi gari a ganta batare da kowa yasan sanda ta dawo ba,
duk gidan amintacciyar Mai aikinta kawai ta Kira ta fada Mata tana Nan Zuwa garin yay ko su Abeeda ba
Wanda ta fadawa tasan zumudin su ze saka kowa ya sani.
************
Safa da marwa take tun bayan gama wayarta da Aunty Ladi ranta idan yayi dubi a bace yake Wai shi
wannan yaron wane iri ne aiki akeyi a kansa Amma Kamar ana zubawa a teku wannan guri na uku ne da
Aunty Ladi taje Mata a Jos Amma amsar daya ce wannan yaron yafi karfinta, Mata ne guda biyu a teaye a
kansa da addu'a sannan yana da tsarin jiki na ban mamaki Nan kusa ba abinda zeyi tasiri a kansa sai ikon
Allah.
Wayarta ta dauko Asabe ta Kira cikin k"an k'anin lokaci ta daga Kiran "kizo ina jiranki yanzu". Ta kashe
wayar tayi wurgi da ita Kan gado.
Cikin abinda bai wuce minti Sha biyar ba Asabe ta shigo gidan ko part din Ammah Bata shiga ba kamar
yanda ta Saba direct ta wuce gurin Mama.
Parlourn ba kowa ganin haka yasa ta wuce bedroom dinta a tsaye ta sameta tana kaiwa da kawowa Ido
yayi Mata jawur kamar na tsohon mashayi.
Ko sallamar ta Mama Bata ba ta amsa ba ta, fara fadin "Ina ne garin da kikace min 'yar dago kawarki ta
fada Miki da wani shahararren mutum Mai aiki kamar yankan wuka?".
Shigowa tayi ta zauna tana kallon mamar "Wai lafiya na ganki haka?"
"Ina fa lafiya! Aunty Ladi ce ta tasheni daga barci take fada min taje har guri uku ba sa'a, Wai yanda suka
fada Mata yanzu ne ma Zahra ta gamu da Wanda ake ta fada Mana a baya bawai wadanda mukayi ta aiki a
kansu ba, Kuma Shi wannan din duk ya fisu Shirin jiki Dan da alama yanda sihiri baya tasiri a jikin ita
yarinyar shima baya yi a jikinsa, Wai wasu Mata ne guda uku a da maza biyu tsaye a kansa duk juyi sihirin
baya kaiwa inda yake, yanzu Kiran da nayi miki ina son Jin tabbacin kin koma kin tabbatar da Mai gadin ya
saka wannan abubuwan da Kika bashi?".
Dan murmushi tayi irin na kwararrun 'yan duniya din Nan kafin tace "Haba Hajiya shekara nawa muna tare
ban taba ha'intarki ba sai yau an aiwatar da komai sai jiran sakamako kawai ai wannan yaron bama Azare
ba Kasar Bauchin ma gaba daya shi da ita har abada, Kuma malamin da 'yar dagon ta fada min a wani gari
yake cikin kasar katsina ana ce Masa Bakiyawa tace idan na shirya zata rakani garin iyayen mijinta ne daya
rasu". Hake sukayi ta kullawa da kwancewa,Asabe nata Kara zugata akan ko nawa zata kashe kada ta Bari
Ammah da 'yar zumunta su fisu komai, tunda ta Nan take samun nata rabon a jikinta idan Bata
encouraging dinta itama zata rasa income nata.
**
Tun bayan ganawa da Bakinsa Mahmud ya shige bedroom ya Haye gado yaso ya Kira Zahra suci gaba da
Hira Amma saiya fasa Dan yasan yanzu gari ya waye sosai a 9ja Bari ya kyaleta sai dare hirar zatafi tafiya
yanda yake so. Bai tashi ba sai lokaci sallah, wanka yayo ya saka kananu Kaya yayi sallah yana cikin addu'a
yaji ana knocking din kofa umarnin shigowa ya bayar Sameer ne ya shigo Bakinsa yaki rifuwa.
"Barka da Rana". Sameer ya fada Yana mikawa Mahmud wayar hannunsa.
Hannu yasa ya karba yaga menene yasa shi irin wannan murmushin.
Wani fine Baby ya gani nade cikin farin towel na jarirai fari sol.
Kallon shi Mahmud yayi Yana neman Karin bayani.
"Takwaranka ne madam ta haihu jiya cikin dare".
Cikin madaukaikin mamaki Mahmud ya kalli Sameer "are you serious?"
Kai ya gyada Masa Yana Fadin " yes sir".
Mahmud sai juya wayar yake Yana Kara kallon babyn.
"Masha Allah, my friend Allah ya Raya mana, amma me yasa ka taho ka baro yarinyar mutane a watan
haihuwarta ai sai iyayenta suga rashin kyautatawar ka ga 'yarsu".
Shafa Kai yayi Yana Dan murmushi "ba wani Abu,idan na zauna me zanyi musu duk abinda ake bukata
nabar musu".
Wani kallon baka da lfy Mahmud yayi Masa "an fada maka Bata bukatar kulawar ka ne a irin wannan
lokacin?" wlh Dana San lokacin haihuwata yayi ba inda zakazo Kuma yanzu ka nemi visa ka koma gida
daman Nan anyi clearing din komai U A.E din naji da komai kawai, naji kace takwara na nayi zaton sunan
Abban koko za'a saka masa?".
"Ai umarninsa ne yace nayi masa huduba da sunan ka".
"To Masha Allah! Godiya ta har gida zanje na yiwa Abban tafi karfin ta waya Allah ya Raya Mana Mahmud
yayi Masa Albarka, kaje ka Fara shiri tun yanzu ka shiga kasuwa kayi musu abinda ya Dace".
"In Sha Allah".
Godiya Sameer yayi ya nufi kofa Yana fita alarm na shigo Masa Wanda Saida ya girgiza shi baya yayo yana
Murda kofar ze dawo ya jira yayi locking dinta, dariya yayi Yana Fadin "manya gatan Wasa, Allah ya biya
maka bukatunka na Alkhairi".
A Ranar cikin dare suka bar Kasar su duka Sameer yayi Nigeria shi Kuma Mahmud ya nufi U.A.E .
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page 34
______ Misalin karfe uku da rabi jirgin sun Mahmud ya sauka a DUBAI INTERNATIONAL AIRPORT (DXB)
cikin amincin Allah, yana cikin kusan rukunin mutanen karshe a fitowa, yana sanye da suit ash colour na
kamfanin Armani hannunsa sanye da ogogo Rolex, baya tare da komai sai jakar laptop dinsa a hankali yake
gangarowa cikin takunsa na cikakken namiji me ji da lafiya da karfi, direct gurin da taxin airport suke ya
nufa, baya bukatar asan yazo garin so yake ya tantance wata jimurda da aka hada, taxin ya shiga saida
sukayi balance a titi sannan ya fadawa direban ya kaishi JW moritte marquis hotel cikin harshen
larabci,sunyi tafiya mai tsayi kafin su karaso hotel din, bashi da matsalar kama daki dan tun yana china yayi
booking din dakin ta online, katin dakin kawai ya karba ya koma waje yin 'yan uzurirrika daga baya ya nufi
ciki, wanka ya fara kafin yayi order abinci, sai da ya gama komai sannan ya kwanta dan yayi matukar
gajiya, yaso kwarai ya kira 'yar gidansa amma yana son su tattauna sosai, sai yanzu yake jin haushin wani
ra'ayin nasa badan haka da suna tare da ita suna hutawarsu, yanzu kadaicin rashinta da be dameshi ba,
wlh da beyi alkawari ba da visa zesa ayi mata ta sameshi a nan saboda hotel din yayi masa, yana daga cikin
lattest hotels na duniya be taba sauka a wani hotel ba a dubai sai BURJ AL ARAB JUMAEIRAH dakinsa
parmanent ne duk mai hulda dashi a dubai nan suka sani, duk da yana da gidaje a kasar shi be fiye son
yakai abokanin bussiness dinsa gida ba. Wannan shigar ta sirri ce shi yasa ya canza sheka baya son asan ya
shigo kasar mamaya sake son yakai wasu gurare, yanda har ya gama abinda yake yabar kasar wani be sani
ba duk da abune mawuyaci hakan ta faru.
Barcinsa yasha sosai dan har akayi sallar magariba be sani ba, lokacin daya tashi ana gab da kiran sallar
insha'i, a gurguje yayi wanka ya zura sabuwar jallabiyar daya saya cikin kayansa a kasar, a cikin dakin yayi
sallar magariba ya fito yabi lifter zuwa masallaci,koda suka idar da sallah be dawo daki ba a nan harabar
hotel din ya Zauna da gaske yanayin gurin ya burge shi sosai, coffee yayi order ba'a jima ba wata
matashiyar balarabiyar yarinya ta kawo masa coffeen sai yaga kamar 'yar gidansa, nan da nan yaji duk
rintsi ita yake muradin gani number dinta ya lalubo ya kira duk ba baya son kira direct yafi son ta
Whatsapp.
Suna zaune a parlour ita da zilai tana Shan mutuniyar tata farm fresh, Kira ya shigo a wayarta dake kusa da
ita, tayi mamakin ganin code din Dubai har sai da ta kusa katsewa sannan ta dauka, batayi magana ba
Shima baice komai ba, ganin shirun yayi yawa yasa zilan Fadin "naji kinyi shiru koba Kira bane".
Karamin tsaki Zahra tayi "wlh na daga amma naji shiru inaga ko wrong number ne dan code din na Dubai
ne ni kuwa waye ze kirani daga Dubai da dai Aunty Nawwara Bata saudiyya da saina dauka ko sunje ne da
mijinta tunda business man ne, Bari na kashe wata kilama ba'asan an Kira ba"..
Kafin ta dauke wayar daga kunnen ta taji yayi magana cikin husky voice kada ki kashe min waya, ki bude
data zamuyi magana". kit ya kashe Kiran wayar tabi da kallo a zuciyar ta tana Fadin "ikon Allah shine
Kuma a Dubai ya illahiy, to Wai wannan Dan talikin waye shi lamarin fa Yana neman Zama abin tsoro fa,
yace Yana yiwa kungiyoyin waje aiki ita Kuma a gefe guda wani Abu yake yi irin na Mai bada umarni Kuma
bataga yanayi gaban kowa ba sai ita, kamar Ranar da taji yana Kiran zayyan da umarnin daya Bashi akan
lallai ya sameshi da safe Kuma Bai karya Umarnin ba"
Wayar ta kalla tana mikiwa zuwa bedroom dinta Saida ta shiga ta duba data idan Babu ta saka tunda Sam
Bata taba saka data ba tunda ta Fara amfani da wayar datar data gani tayi bala'in Bata mamaki 4.5 BT ta
gani sub din shekara daya ne.
Cikin sofa ta zauna Tana juya wayar Bata bude datar ba, wani Kiran ne ya sake shigowa still dai nashi ne,
dagawa tayi tana fadin Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
"Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, meya hanaki bude datar danace a bude?"
Shiru tayi ta kasa magana,.
"Wai ko sai nayi ramuwar sayen bakin da banyi bane ake min jan aji irin haka. Dan Allah kimin magana
kona samu nutsuwa wlh ji nakeyi Kamar na gudo tun ba'a gama ba duk kin mamaye ko Ina na kasa komai
sai tunanin ki, Ni danasanin zuwan ma nakeyi gashi sun rarraba mu wasu suna London mu kuma suka kawo
mu hadaddiyar daular larabawa, shine nace Bari na kira na fada Miki Koda abinda kike bukata na taho Miki
dashi tunda da kudinki a gurina"
"Kudina kuma? Name nene kuma yaushe na baka".
"Bake Kika bani ba ke aka bawa na manta na Baki Sai a Nan na tuna danaga Kaya irin naku na 'yan Mata".
Ya fada Yana dariya.
"Wai 'yan Mata".
Ta fada tana Dan turo Baki irin bataji dadin Nan ba.
"Au ashefa an wuce wannan stage din ko?"
Ya fada da alamun zolaya.
"Wato kinki bude data sai kin cinye min 'yan canjin da aka saka Mana kinsan dai ni ba iya saka Kati zanyi a
kasar Nan ba, pls Dan Allah ki bude datar na ganki kona samu nutsuwa nayi aikin daya kawoni, naso ace
kina gefena a wannan gurin Kinga dakina kuwa? da Hali gareni anan zamuyi honey moon irin Wanda naji
su Habib suna fada idan ana hira ko Zaki biya ki taho ki sameni?"
Ido ta ware kamar Yana kallonta.
"Na biyoka nayi maka menene?"
"Kiyi min abinda mace take yiwa mijinta ai kin gane?".
"Ya Salam haba Ya Mahmud menene haka kaifa yayana ne".
Wata dariya ce ta kubce Masa "A yaushe na zama Yayanki? Ki gyara zancen niba Yayanki bane, haka kawai
ki haramta min abinda Allah ya halasta min idan Zaki Ware ki Dan ina dawowa labarin ze canza salo gara
mu fuskanci juna ki tausaya min Kinga Sameer fa ya Zama Daddy madam dinsa ta haihu sunyi min
takwara,ai gara muma mu zage dantse ko?"
Dokin haihuwar da aka fada Mata ita ta Hana ta gane inda nasa zancen ya dosa, cikin nuna farin ciki tace
"Dan Allah da gaske yaushe Fateehar ta haihu? Masha Allah! Allah ya Raya kace mu sai Kano ko Yaya?".
"Allah bakinki ya kiyayi fada min yayan Nan tsabar kinibibi kawai yau Kika tashi dashi Wai wani Yaya kamar
a kauye, kibar 'yan garinmu su Fadi Amma Banda ke wato Ni da yake ba Dan bokon kirki bane ba baza'ace
min sweetie ba ko irin su my love ko Dear, saboda almajirin soro ne ni ko?"
"A'a wlh ni ban fada ba, kawai dai Naga abokin Ya Abdul Hakeem ne kai ai kaima yayan ne".
"To anki wayon, Kuma da kike cewa Zaki Kano ganin yaro keda wa zakuje kuma waye ze kaiki Kuma kice
Mata wacece ke".
"Address zata turo min Mana, Kuma maganar kaiwa sai Malam Bala direba kaimu nida mujiba wuni daya
dai, Kuma nace Mata matar yaron mijinta ce ko ba haka ba?
"Yayi Kam Amma saina dawo ki rakani muje tare anfi saurin ganeki ga kafarki ga tawa, kice na sawo Miki
kayan baby na zuwa barka kenan? ko kema a hado Miki kayan naki babyn? tunda da karfina Zan dawo
wata kilan ni double shoot ma zanyi tunda Nima Dan biyu ne Ina da twins sister Aishat".
"Twins sister da gaske?"
"Kin taba ganin nayi Miki karya? wlh mu biyu Ammin mu ta haifa first born dinta, mun B'ata ne da ita
shiyasa bakisanta ba. Amma nan gaba zaki santa ne Amma fa Zaki Sha surutu Dan sister Aishat parrot ce".
"Amman laifin me tayi maka da zafi haka? Mu namu twins din basa doguwar batawa gaskiya gashi kaima
Ammin irin na Ammah tayi mace da namiji".
"Ki Bari kawai labarin da tsawo sai na dawo ai nace Zaki San duk labarina kaf ba abinda Zan boye Miki
tunda kin sarkafo min zuciya tun kina free matured dinki Kika Hana duniyata zaman lfy,da farko na dauki
irin mutum ya burge ka ne Ashe diban Karan mahaukaciya Kikayi da gudan tsokar kirjina".
Dariya maganarsa ta bata.
"Au dariya ma kike min ko? bayani zakiyi da yarenki, yanda nayi ta fama da garari saina fanshe kayana tas
idan Zaki shirya ki shirya".
Cuno Baki tayi kamar tana gabansa ta Fara turza kafa tana fadin "Ni yaushe kaga Ina maka dariya kawai
dai... ni banyi maka dariya ba kaifa yayana ne koka manta my big bro....." Ta wani ja cikin salon da ita kanta
Bata San tayi ba.
"Ya salam" ya fada a hankali Dan yanda tayi magana har cikin bargonsa.
"Kinaso ki karya min budget ko?"
Ya jefa Mata tambayar.
"Wane irin budget Zan karya maka kana Nan Ina Nan".
"Idan kina min irin haka ai sai kisa na saki layin Dana hau na tattaro ya nawa ya nawa ko komo gida ko ba'a
gama ba".
MAMAN FATEEMAH
PAGE 35.
________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo ya shiga aiki sai kusan
karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa
yayi zance mata tana neman tikitawa kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi
wanka yayi nafila sannan ya kwanta.
*
Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu rage Masa dare
kenan neman Mata yajeyi?"
Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda karfin tuwo saiya nemi
wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin
zilai sukaci gaba da hirarsu sai kusan Sha daya suka shiga ciki.
Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata Jin Dadi wata irin
murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk karshen wata idan zatayi period Amma
wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice,
inda Allah ya taimaketa Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin ikon
Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah da sauki sosai sai Kuma yanzu
data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar
nauyi ta koma ta kwanta idan tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na
strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan yanayin.
Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta gani anya lafiya kuwa?
Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura kofar a can tsakiyar gadon ta
ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha
biyu ta gota Baki tashi ba abin Karin ki har ya Fara sanyi?"
Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin dadi tun cikin dare marata take
ciwo".
"Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan ace tun cikin dare
kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda
ance idan Kikayi aure ze dena, to na dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan
mu na karshen ko?".
Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji.
"Fada min Ina maganin yake na dauko Miki"
A hankali tace mata "Na sha".
"Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?"
"Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo.
Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta ta lalubo number Ammah,
lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar Imam Kiran zilan ya shigo.
"Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya".
"In Sha Allahu ma lfy".
Abban ya fada.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu"
Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta Dora da fadin "wlh
Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya tashi Tasha maganin Kuma a banza shine
nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam
Bala ya kaimu Asibiti taga likitar ta" .
"Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?".
"Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa".
"To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira".
Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya rigata.
"Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?"
Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare Tasha maganin da take
Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma suga likitar da take gani Dan munyi
expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi".
"Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk sauran basa Nan sai mu
bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?".
Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar da ita inda ta tashi dayan
Kuma Yana Kiran wayar magaji.
"Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti".
Ya kashe Kiran yana kallon Ammar.
"Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa Kika sani ko jika zamuyi
kwanan nan"
Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya.
Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa".
"Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida araha sai nayi aikin
bariki tilas ne".
Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma zasu samesu a can..
Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa tana fadin na hado
Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu".
Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba.
"Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan ne".
"Cornflakes".
Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta.
Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour zilai na rike da ita. Basu jima
ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda
zahrar ke kwance ya nufa akan two seater.
"Sannu Adda ya jikin naki?"
Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki".
"Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five minutes to one fa".
Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune Yana game a waya tunda
bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya
taimake kan jacket dinsa ta fada da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya
faru? Oga kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a rude yake.
Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin.
"Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu".
Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa".
"A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin wannan ma wani Bata
lokacin ne".
Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa Yana Kiran Mahmud.
Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya zauna yana mamakin
ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura ma yaga alama bayayi wata sabuwar
rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali.
Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga ciki shi Kuma magaji ya
nufi inda ze karbo file.
Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on call tayi Mata ta rubuta
Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da
masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido
ta kalli Abba tana kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?"
"Da sauri Abbana, Ina kwana?"
"Lafiya kalau".
Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?"
"Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu".
Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata.
"A'a uwata Banda kuka ai kin girma".
Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata ta.
Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward.
Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number Mahmud tafi cikin carbi
amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe
kawai number Bata tafiya take fada Masa.
A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana Asibiti Bata Jin Dadi.
Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma menene yake damun
diyar tawa?".
"Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta kita Asma'u ta fada
mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-
gwaje don su fadada bincike akan ciwon tunda ta jima tana fama da lalurar".
"Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an Nemo Mata taimakon
ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano wane irin ciwo ne a fada mini akwai
magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha
Allah zasu narke Koda na aikine zebi jinin al'ada ya narke ya zube".
"To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka".
Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama.
Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje Zahra tana barci sun gaisa
da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi.
****
Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar suka fice sun Kai
ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya dakatar da mutum hudu ya sallami mutane
biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin
tafiya tayi nisa Kuma baya bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki,
zuwan Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai takanas din ya
taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials da akayi Wanda suke zargin ba'a biya
kudin harajin kasa ba a tun farkon bude kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta
wibeside nasu Amma sunqi yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru.
Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi matukar gajiya sosai Koda
yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu
wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na
Zayyan da Habib su sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa.
Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake tare dashi Nan take
tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga,
Bai saurari gaisuwar da yake Masa ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da
nayi bashi da anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da tsohon
Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda throughout yau ban kirata ba nayi
busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make
text".
"Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?"
"Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani information akan komai ba".
Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya Kira shi.
"A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa.
"Wai meke fatuwa ne da Zahra?".
"Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam yace na kaishi
Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana
barci Amma idan an jima zan koma na qara dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka
naji Abban su Yana fadin Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har
hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan sanar da kai Allah
ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa.
Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka yasan wayar na gida
Basu dauka ba.
A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama da Asabe
Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje duniyar kanwar Babar su Asaben,
shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da
wayar Amman a.hannu Yana game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah,
batare da Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo Mahmud ze Kira ba.
Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar yasa Ammar fadin
"wa ake nema ne".
"Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude wayar ba muna aiki sai
yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti, Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata
fatuwa ba".
Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba.
Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci takeyi, ya akayi suka
fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan
ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din ta zasu bincike a Kai".
Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa.
"To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano zasu dubata sosai
tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira
Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka".
Sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita tamkar
mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau.
Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin yanayin ciwon nata gashi
abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya
barta da jangwam yanda aka Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi
Kuma yayi masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji ance harda
motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan".
Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana fada ne dan ta Bata
Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra tana gyara Mata hannunta da aka saka mata
drip, itama ko tari be kunce Mata ba bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace.
Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa.
"Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon Allah ba yaron Nan
guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin
gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake
Kar bashi da duhun jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya barta,
idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu jinjinan dangi kana ji a
sheganta yaro
ko yarinya".
Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo suka juyo tana kallon
Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da
iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini
har dakin mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin".
AUREN HUCE HAUSHI
MAMAN FATEEMAH
PAGE 35.
________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo ya shiga aiki sai kusan
karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa
yayi zance mata tana neman tikitawa kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi
wanka yayi nafila sannan ya kwanta.
*
Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu rage Masa dare
kenan neman Mata yajeyi?"
Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda karfin tuwo saiya nemi
wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin
zilai sukaci gaba da hirarsu sai kusan Sha daya suka shiga ciki.
Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata Jin Dadi wata irin
murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk karshen wata idan zatayi period Amma
wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice,
inda Allah ya taimaketa Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin ikon
Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah da sauki sosai sai Kuma yanzu
data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar
nauyi ta koma ta kwanta idan tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na
strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan yanayin.
Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta gani anya lafiya kuwa?
Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura kofar a can tsakiyar gadon ta
ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha
biyu ta gota Baki tashi ba abin Karin ki har ya Fara sanyi?"
Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin dadi tun cikin dare marata take
ciwo".
"Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan ace tun cikin dare
kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda
ance idan Kikayi aure ze dena, to na dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan
mu na karshen ko?".
Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji.
"Fada min Ina maganin yake na dauko Miki"
A hankali tace mata "Na sha".
"Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?"
"Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo.
Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta ta lalubo number Ammah,
lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar Imam Kiran zilan ya shigo.
"Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya".
"In Sha Allahu ma lfy".
Abban ya fada.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu"
Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta Dora da fadin "wlh
Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya tashi Tasha maganin Kuma a banza shine
nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam
Bala ya kaimu Asibiti taga likitar ta" .
"Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?".
"Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa".
"To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira".
Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya rigata.
"Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?"
Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare Tasha maganin da take
Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma suga likitar da take gani Dan munyi
expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi".
"Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk sauran basa Nan sai mu
bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?".
Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar da ita inda ta tashi dayan
Kuma Yana Kiran wayar magaji.
"Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti".
Ya kashe Kiran yana kallon Ammar.
"Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa Kika sani ko jika zamuyi
kwanan nan"
Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya.
Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa".
"Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida araha sai nayi aikin
bariki tilas ne".
Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma zasu samesu a can..
Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa tana fadin na hado
Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu".
Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba.
"Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan ne".
"Cornflakes".
Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta.
Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour zilai na rike da ita. Basu jima
ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda
zahrar ke kwance ya nufa akan two seater.
"Sannu Adda ya jikin naki?"
Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki".
"Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five minutes to one fa".
Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune Yana game a waya tunda
bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya
taimake kan jacket dinsa ta fada da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya
faru? Oga kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a rude yake.
Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin.
"Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu".
Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa".
"A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin wannan ma wani Bata
lokacin ne".
Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa Yana Kiran Mahmud.
Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya zauna yana mamakin
ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura ma yaga alama bayayi wata sabuwar
rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali.
Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga ciki shi Kuma magaji ya
nufi inda ze karbo file.
Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on call tayi Mata ta rubuta
Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da
masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido
ta kalli Abba tana kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?"
"Da sauri Abbana, Ina kwana?"
"Lafiya kalau".
Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?"
"Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu".
Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata.
"A'a uwata Banda kuka ai kin girma".
Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata ta.
Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward.
Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number Mahmud tafi cikin carbi
amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe
kawai number Bata tafiya take fada Masa.
A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana Asibiti Bata Jin Dadi.
Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma menene yake damun
diyar tawa?".
"Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta kita Asma'u ta fada
mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-
gwaje don su fadada bincike akan ciwon tunda ta jima tana fama da lalurar".
"Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an Nemo Mata taimakon
ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano wane irin ciwo ne a fada mini akwai
magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha
Allah zasu narke Koda na aikine zebi jinin al'ada ya narke ya zube".
"To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka".
Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama.
Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje Zahra tana barci sun gaisa
da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi.
****
Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar suka fice sun Kai
ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya dakatar da mutum hudu ya sallami mutane
biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin
tafiya tayi nisa Kuma baya bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki,
zuwan Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai takanas din ya
taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials da akayi Wanda suke zargin ba'a biya
kudin harajin kasa ba a tun farkon bude kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta
wibeside nasu Amma sunqi yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru.
Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi matukar gajiya sosai Koda
yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu
wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na
Zayyan da Habib su sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa.
Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake tare dashi Nan take
tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga,
Bai saurari gaisuwar da yake Masa ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da
nayi bashi da anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da tsohon
Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda throughout yau ban kirata ba nayi
busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make
text".
"Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?"
"Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani information akan komai ba".
Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya Kira shi.
"A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa.
"Wai meke fatuwa ne da Zahra?".
"Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam yace na kaishi
Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana
barci Amma idan an jima zan koma na qara dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka
naji Abban su Yana fadin Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har
hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan sanar da kai Allah
ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin".
Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa.
Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka yasan wayar na gida
Basu dauka ba.
A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama da Asabe
Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje duniyar kanwar Babar su Asaben,
shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da
wayar Amman a.hannu Yana game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah,
batare da Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo Mahmud ze Kira ba.
Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar yasa Ammar fadin
"wa ake nema ne".
"Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude wayar ba muna aiki sai
yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti, Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata
fatuwa ba".
Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba.
Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci takeyi, ya akayi suka
fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan
ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din ta zasu bincike a Kai".
Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa.
"To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano zasu dubata sosai
tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira
Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode Allah ya Bata lafiya".
"Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka".
Sukayi sallama.
Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita tamkar
mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau.
Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin yanayin ciwon nata gashi
abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya
barta da jangwam yanda aka Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi
Kuma yayi masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji ance harda
motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan".
Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana fada ne dan ta Bata
Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra tana gyara Mata hannunta da aka saka mata
drip, itama ko tari be kunce Mata ba bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace.
Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa.
"Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon Allah ba yaron Nan
guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin
gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake
Kar bashi da duhun jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya barta,
idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu jinjinan dangi kana ji a
sheganta yaro
ko yarinya".
Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo suka juyo tana kallon
Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da
iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini
har dakin mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin".
✨✨✨
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page 36
______Zahra tana Gama fadawa Asaben abinda ke cikinta ta juya musu baya, ko banza bazata kwana da
fushin zuciya ba, dan tasan idan ba ita tayi magana ba Babu abinda Ammah zata ce Dan sau da yawa idan
irin haka ta faru ko kallon Mama batayi sai dai ta bawa banza ajiyarta.
Daga Asaben har Mama ba Wanda ya Kara magana,haka Ammar ma da Zilai ba Wanda ko tari ya kuncewa,
Auta kuwa wayar mamar ya dauka yaci gaba da sha'aninsa.
Shiru dakin ya dauka kamar mutuwa ta ratsa, sallamar Abdul Hakeem da Abba ta katse shirun cikin nuna
tsantsar duniyanci Mama ta tashi da sauri tana fadin "Abba har kun karaso sannu da Zuwa" tana gyara
Masa kujerar kusa da gadon.
Sai da ya zauna sannan ya amsa gaisuwar dasu Zilai da Asabe ke Masa suna jajanta masa, suka gaisa da
Abdul Hakeem sannan suka fice daga dakin.
Mama ce ta Fara gaishe da Abban kafin Ammah ma ta gaishe shi, sannan Abdul Hakeem ya gaisu dasu
Ammar Yana tambayar Mai jikin.
Zahar ce ta juyo tana fadin. "Abbana sannu da Zuwa, ina yini?".
"Yauwa uwata lafiya kalau Alhamdulillahi jiki yayi kyau".
"Eh Abba Daman Kai nake jira kazo kayi musu magana su sallameni mu tafi Nina warke na gaji da Asibitin
tunda sunyi min hoton da gwajin da safe mun dawo mu karba bana son kwanan gurin Nan".
Ta fada tana hade rai.
"Eh Nima abinda ya taso ni Kenan maganar tafiyar taku gidan ne Dan yanzu haka daga office din doctor din
muke sun bamu referral Zuwa Aminu Kano kamar yanda mijinki ya bukata yace da safe zaku tafi kiga
gynecology doctor ayi bincke tunda ance kin jima kina fama da matsalar".
Kafin Ammah tayi magana Mama ta rigata.
"Wane irin Kano Kuma ana zaune lafiya, Wai ciwon har ya Kai haka ne idan Asibitin ake son canzawa aje
Bauchi Mana Amma har kano akan ciwon mara kawai".
Dan murmushi Ammah tayi Bata ce komai ba.
Abban ne yace. "Yanzu kina nufin na Kira shi nace masa abinda ya fada baze yuwu ba Kenan ko Kuma Yaya
kike son ayi?".
Shiru tayi Bata ce komai ba. Ammah ya kalla "kinyi Shiru ko kema hakan ne nufinki".
Kai ta girgaiza tana fadin "A'a tunda ga yanda ya fada ai shike da iko da matarsa ita da waye zasu tafi
kanon?".
"Yace Sameer ne zezo sai zilai ta rakata haka dai ya fada min yanzu da Daren nan"
" To Allah ya kaimu yanzu tafiya zamuyi ke Nan?".
"Eh haka ne, ku kuje Abdul Hakeem ya mayar daku gida kafin ya dawo ruwan ya Kare sai na raka uwata
gida" ya fada Yana murmushi.
Sororo Mama tayi Jin Abba da kansa ze maida su Zahra gida.
Badai ta tofa ba Amma a ranta taji ba dadi. Tun kafin Ammah ta dauko hand bag dinta Mama ta fice daga
dakin.
******
MAHMUD
Bayan sun gama waya dasu Abba, Sameer ya Kira harta katse ba'a dauka ba sake Kiran yayi tana Fara
ringing ta dauka.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Ya fada Yana Zama kusa da Fateeha tana shayar da jaririn su.
Daga can Mahmud ya amsa sallamar ya Dora da fadin "gobe in Allah ya kaimu ka shiga Azare ka taho da
madam zataga doctor a Nan kanon na Kira doctor Haseena za'a kawo patient dina".
"Doctor Haseena fa! ita zata duba maka madam din?".
"Eh Mana ko da matsala ne?".
"A'a gani nayi kada taga anyi Mata cin fuska".
"Ba wani damuwa kawai,do what I said".
"Ok. In Sha Allah".
"Kada ka kaisu gidanka a kaisu gidan dake Nan DAWAKI ROAD su zauna har su Gama abinda zasuyi su
koma".
"Kana ganin Bai musu girma ba kuwa? dana karkasara aka kaisu yafi kusa da Asibitin ma akan na
Nasarawa GRA".
"A Nan nake son ta zauna kake maganar girma har wani babban gida ne ka barta ta saba da Zama a irinsu
tun yanzu Kai dai kasan kuma abinda zaka fada Mata, a Kai musu duk abinda ya kamata sai dai na fada ba
kayi komai kawai, ka fadawa momi ta Basu house maid daya su hadu da tata sai su ringa aikin tare, kayan
sakawa dai nasan ba matsala ka Kira Rukayya ta duba abinda ya kamata sai taje ta sawo, ka Bata card din
master bedroom na kasa ta sauka a nan.
"Shike Nan za'ayi yanda kace, amma baka tunanin taga wata shaida data danganceka a gidan?"
"Gaskiya bana tunanin akwai wata alama dake alamtani da gidan".
"Anyway, Allah ya kaimu goben, takwaranka na gaisheka".
"Oh sorry a shafa kansa sai nazo ganinsa, kaina ne ya dauki zafi".
Dan murmushi Sameer ya kashe Kiran Yana kallon Fateeha dake Masa kallon Karin bayani.
"Oga ne, Kinga yanda ya shiga damuwa kuwa nifa Banga abinda oga ya damu dashi ba irin yarinyar Nan
idan Kika cire Iyayensa to ba na biyunta, ai ban Gama sarewa da lamarin sa ba saida ya nemi guri ya zauna
a dakin kofar gida na almajirai duk da gurin bashi da wani aibu". Baki bude Fateeha ta bi Sameer da kallo
"dakin Almajirai fa tace shi ogan da kansa? Tab lamarin Azimun ne, Allah ya bamu ko Rabin yanda tayi sa'ar
sace zuciyar jarimi kamarsa Wanda Mata ko kallo basu isheshi ba".
Lakuce Mata kumatu yayi Yana fadin.
"Waya fada miki ba'a Miki so irin Wanda ake mata?" 'yar dariya tayi kawai tasan zance ne inji 'yan magana
*******
Dariya yayi ya fice Yana mamakin Abba yanda yake nunawa Zahra soyayya fiye da kowa.
Ba zato ba tsammani Amma taga zilai ta shigo da Kaya a hannu Zahra na biye da ita.
"A'a ku kuma ya haka Naga Abba yace ze rakaki gida sai Kuma gaku a nan?"
Maganar Abban Ammah taji a bakin kofar parloun.
"Ni nace ta taho gida tunda batajin dadi Kuma gida su kadai, gashi Mai gidan nata yace goben zasu wuce
kanon gara su kwana a Nan kawai tunda ke dai ba can zaki bita ba gara su tafi a gaban ki".
"Ok, ai ban sani ba nayi tunanin ko gaban kanta tayi nasanta da kulafucin gida ganin ta samu dama zata iya
fakewa da haka ta taho kaima Abba kasan halinta"..
D'an Bata fuska tayi "Kai Ammah Dan Allah fa....."
"Kinga uwarta wuce ki kwanta ki huta Keda Baki da lafiya gida dai ai na danki ne, ba Mai hanaki shigowa
Zan Kira shi Mahmud din na fada masa ".
"To Abba na gode".
Ta fada tana shigewa cikin Zilai ta bita da ledar magungunan ta.
Abban Bai jima ba ya fice saboda ya baro mutane masu son ganinsa da yawa a kofa.
A bakin kofar bedroom din Ammah suka had'u da zilai tana kokarin fitowa.
"Ku kuma sai koyo gudun hijira bakwa tsoron maganar mutane masu jiran k'iris su karawa miya gishiri?".
"Kayya Ammah idan za'a biyewa maganar mutane ai ko ruwa ruwa ka shiga sunce ka tada k'ura, Kuma ma
waye ya ganta Kuma gobe da safe zamu wuce Kano idan Allah ya dawo damu ta wuce dakinta".
Zahra na shiga ta fada toilet Dan babu abinda take bukata sama da wanka du ji take jikinta na warin Asaibi.
Ta jima tana zubawa kanta ruwa kafin ta fito, sabuwar rigar barci ta dauko cikin kayan Ammah ta saka, ta
dauko zumbuelen hijabin Ammah ta Fara sallah.
Ammah ce ta shigo dakin lokacin Zahra ta Idar da sallah Tana addu'a, sai da ta shafa sannan ta juyo tana
fadin.
"Sannu da dawowa Ammah".
"A'a ke za'a yiwa sannu, ya jikin naki?".
"Da sauki sosai nifa da Abba ze fada Masa bama sai munje wani Kano ba, na warke tunda Daman na Saba
duk wata inayi wannan ne kawai ya matsa min sosai".
"Kamar Yaya Abba ya fada Masa shi wa za'a fadawa?".
Ammah ta fada tana kallon zahrar, Baki ta turo tana fadin. "kema Ammah kin sani fa kowa nake nufi".
Dan murmushi tayi kawai.
"Ki Kira ki fada Masa bazakije ba Mana sai Abba ne ze Miki tafinta, tunda yace ga yanda yake so ai haka
Zaki hakura kuje a duba ki tunda Naga alama Nan din be kwanta Masa ba, Kuma dazu naji kina maidawa
Asabe har da Mama magana tona Hana kada na k'ara Jin makamanciyar magana irinta daga bakinki, ki bar
mutum da halinsa kedai ki Zama me kauda Kai kawai ki Kuma rike Addu'a takobin mumuni ce kuma
hassada ga Mai rabo taki ce".
"Kiyi hakuri Ammah in Sha Allah bazan Kara tankawa kowa ba,gani nayi basuji kunyar maganar a gabanki
ba shi yasa na rama Nima".
Knockig da Sallamar Abdul Hakeem ce ta dakatar da abinda Ammah zata fada. Ammah ce ta amsa
sallamar ta bashi uzinin shigowa.
Sannu da dare ya Kara yiwa Ammah sannan ya mikawa Zahra wayarsa dake Hannunsa da alama vedio call
yakeyi, Yana fadar "gashi Mahmud zeyi magana dake".
A d'an kaikaice ta kalli gafen da Ammah take kafin ta Mika hannu ta karbi wayar.
Tana karba Ya Abdul Hakeem ya juya, Ammah tabi bayansa tana Masa maganar danyar Madarar da akace
ya Aiko da ita da yamma lokacin tana Asibiti.
Saida Zahra ta tabbatar sun fice gaba daya daga dakin sannan ta dubi
Screen din wayar fuskarsa ta gani Yana kallon ta sai taga yayi wani zuru-zuru kamar Wanda yayi ciwo sai
hancinsa ya Kara fitowa zuwat dashi hakensa ma ya qaru.
"A hankalin tayi masa sallama tana fadin "Ya M baka da lafiya ne Naga ka rame?".
Bushashshen lebensa ya da tura cikin Bakinsa ya lumshe idanunsa tun lokacin da aka fada Masa Bata da
lafiya bai samu peace of mind ba sai yanzu daya ganta. Dan ita ke ciwon Amma shi keda zulumin da ramar
Dan tun daga lokacin zuwa yanzu daya ganta Baya Jin yaci wani Abu na kirki a cikinsa.
A hankali ya bude idonsa ya Dora akan tata fuskar dake kallonsa, wani yarrrr taji da suka hada idon.
Cikin tsantsar kasala da jigata ya bude Bakinsa a hankali yace.
"My previous hankalina ya tashi, wallahi gani nakeyi kamar Zan rasaki, ya jikin naki? Kuma tun yaushe
ciwon ya kamaki Baki fada min ba? sai Zayyan ne yayi min text Wai an wuce dake Asibiti, kinsan kuwa
yanda hankalina ya tashi? Daman kina yin irin hakan ne ko yanzu ya Fara Miki?".
Dan walainiya tayi da idanunta tana fadin " Naji fa sauki Daman inayi kawai wannan ne yayi min tsanani
sosai, amman tunda akayi min allurai da drip na warke, kaga ai ba sai munje Asibtin Malam din ba ko?".
Wani kallon Baki da lissafi yayi Mata, shi Yana can ya kasa tsugun da ransa ita Kuma tana fada masa wani
shirme.
"Zuwa can ba fashi, kuma da izininwa Kika taho gida jinya kin tambayeni Zaki zo gida?" Narai narai tayi da
Ido abinda ke tsuma shi kenan yaji Yana neman sakin layi.
"Kai Yaya wallahi na fada maka Zanzo gurin Ammah Kuma ka amince kace nazo koka manta Ranar da zaka
tafi?" Ta fada a shagwabe tana zubawa Masa sexy eyes dinta da suka Kara wani hasken wahala data Sha.
"Kawai dai kin min wayo tunda kin fini sanin takan duniya kin fini ilimin boko me zurfi shine zakiyi min
education, haka ake cewa ko?".
Shiru tayi Masa.
"Kiyi magana Mana nifa bana son Shiru sai Naga kamar jikin ne"
"Nifa na fada maka na warke sai wani jikon Kuma".
Zaro Ido yayi Yana Mata kallon mamaki.
"Sai wani jikon kamar Yaya? Kenan har kina tunanin Zaki qara fuskantar wani ciwon bayan wannan?".
Kai ta gyada Masa alamar Eh.
"Pls talk ki bude Baki kiyi min bayani as how kike expecting Zaki Kara irin wannan ciwon?".
Sai da ta kauda kanta ta daina kallonsa sannan tace Masa.
"Nifa each and every month sai nayi wannan ciwon".
Ta fada tana Kara juyar da kai.
Cikin damuwa yace. "Pls juyo muyi magana Ina son sanin yanda ciwon yake ne Zan fadawa wani doctor
Kinga ai saina San komai kafin na fada Masa yanayin ciwon"
Cikin Jin kunya da nauyinsa tace. "Nifa idan zanyi period ne nake yin ciwon cikin Baya sauki sai anyi min
doclofenic injection yake denawa".
"Ok, to idan period din yazo Kuma shike nan baya Kara ciwon?".
Kai ta gyada masa. "Ki cire hijabin Naga yanda Kika rame tunda Nima daba ciwon nayi ba na rame lokaci
daya dubi yanda nayi Rama? a lokaci aiki ma zanyi amma na kasa tabuka komai".
Rufe bakinta tayi cikin mamaki tace.
"Dan Allah ka daina haka ka manta a dakin Ammah fa nake idan ta shigo fa ta ganni a yanda nake me kake
son na fada Mata?".
"To ya za'ayi Kenan Ranar data ganki da ciki Kuma a jikinki tunda kina kunyar taga muna video call ba
hijabi kamar Wanda ta aikata alfasha Allah idan na dawo dole asan abinyi na Fara gajiya gaskiya sai ragaita
nake kamar marayan da bashi da uwa, alhalin Allah ya Gama min sutura, koba haka ba?".
Shiru tayi Kamar ruwa ya cinyeta idan ta biye masa kunya ze Bata tunda taga alama Yana neman fitsare
idanunsa.
Jin tayi Shiru yasa Shima ya bar zancen ya koma Kan batun tafiyar su Asibiti.
"Goben idan Allah ya kaimu magaji ya kaiki ki dauko wayarki tunda tana gida ki dauko Yan abun bukata
tunda sai kun Gama komai kafin ku dawo wata Kila zaku dauki lokaci ba'a Gama gwaje-gwajen da zasuyi
Miki ba, itama wannan Matar ta dauki abinda ya Kanata nata saiki fada Mata".
Sun Dade suna wayar har Ammah ta wuce part din Abba Basu Gama ba, sai kusan Sha daya ya hakura
sukayi sallama.
Da safe tunda wuri Ammah ta saka magaji yakai Zilai gidan ta karkashe kayan electronics, ta cire duk
abinda ake ganin ze iya lalacewa ta Mika gidan maman junior bisa Umarnin Ammah.
Karfe bakwai da rabi Mai kyau su zilan sun koma gidan Ammah da kayan Zahra a jaka set biyar da sauran
tarkace na bukatar yau da Kullum.
Sam Mama Bata da labarin kwanan zahrar a gidan Sai da zilai ta shigo da Kaya a hannu magaji Kuma
karamar luggage a hannunsa da sauri ta aje bowl din dake hannunta ta nufo Zilai tana fadin "lafiya kuwa
daga Ina haka zilai?"
Gaishe ta zilan tayi tana fadin "munje mun daukowa Zahra kayan sawarta tunda Bata koma gidan ba Nan
muka kwana daga asibitin gida mukayo". Ikon Allah wallahi ban sani ba, Babu Wanda ya fada min tun
daren, Bari na shiga Naga jikin nata".
Suka nufi part din Ammah.
✨✨✨
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page 37.
_______Cikin wani irin takun Jin Dadi da karsashi Mama ta shiga parlourn Ammah tana fadin "Ina patient
din take? Ashe nan Kuka kwana jikin ne yaqi Dadi bayan mun taho? wlh ban sani ba sai yanzu da naga zilai
ta shigo da kaya ta fada min". Ammah ce ta fito faga kitchen din part din ta tana fafin "ko daya sangarta ce
kawai Wai kada ciwon ya tashi cikin dare, kamar an fada Mata a Nan din ciwon baze tashi ba".
Dan murmushi Mama tayi "ai kinsan yanda take da son gida ai inaga idan sun dawo ma saita zauna a nan
din tunda ba'a San ranar da mijin nata ze dawo ba gara tana kusa tunda Naga alama ba wani iya riqeta zeyi
ba da farawa da iyawa, Allah ma yasa Bata da juna biyu ai da abun yayi yawa ga zawarci ga goyo".Dan Jim
Ammah tayi Dan da gaske maganar ta doketa wane irin mugun fata ne haka bako kawaici gurin fadin
maganar.
"Allah ya rufa asiri, duk abinda Allah ya tsarawa zahra Zan karba da hannu biyu ba komai, idan Allah ya
hukunta Mata rabuwa dashi bani da tsimi bani da dabara,kinsan shi dare ga Mai rabo hantsi ne, fatan da
muke dai Allah ya rabata da wannan ciwon me bibiko".
Zahrar ce ta fito Shar da ita cikin doguwar Rigar material Baki da pink din flowers manya ta saka gyale
medium a kafadarta tana baza kanshi kamar anyi barin turare a jikinta a hankali ta shigo cikin takunta na
rausaya tana amsa wayar sajida wadda ta kirata tana dubata da jiki.
"Ke kuma waya fada miki bani da lafiya?" Zahra ta fada tana Zama kusa Auta da yake breakfast ze tafi
school.
Tunda zahrar ta shigo idanun mama ke bin zahrar da kallo.
Wayar taci gaba da amsawa tana fadin "jikin fa da sauki kawai shine yake ta bankama abun kema fa kinsan
ciwon tun Mana kazaure shi ne fa yaketa faman tsallen tsinka tsimma akansa".
Ta fada tana dariya kasa kasa.
"Amma Baki da kirki mijin naki ne me tsallen tsinka tsimman? Saura kadan nayi Miki tawaye bestie irin
wannan cin fuska haka?".
"Sai anjima Zan kira".
Ta fada a hankali duk da Daman idan ba Kuna kusa sisai ba bazakaji abinda take fada ba.
Sai da ta kashe wayar sannan da dubi inda Mama take zaune ta Dan rankwafa kada daga zaune tace
"Mama Ina kwana?"
Ba yabo ba fallasa ta amsa tana fadin "ya jikin duk da dai ba alamar ciwo a tare dake, Banda son yawo Ni
banga abin tafiya har Kano ba akan ciwon mara na Mata".
Badan Ammah ta jawa Zahra layi ba da Babu abinda ze Hana ta bawa Mama amsar maganarta ba to ba
Hali sai zilai ce ta magantu "To Mama tunda yace taje a duba lafiyar ta ai dole taje tunda da gaske Yana
cikin damuwa".
Dan tabe Baki tayi tana fadin. "Ai kam sai kuje nasan dai rabe-rabe zakuyi a gidan uban gidan nasa".
Duk abinda ake Ammah najin su amma ko kallon su batayi ba, haka zilan ma Bata Kara fadin komai ba ta
fice daga parlourn.
Hamza ne ya leko parlourn ya gaishe da Ammah tunda sun gaisa da Mama, Zahra ta gaishe shi Ya amsa
yana fadin "ya jikin naki? Ku fito inji Abba zaku wuce kanon".
Ta amsa da "to Yaya, jikin da sauki nafa ware wlh, kawai dai".
Ganin Abba a harabar gidan ya hana sahura garasowa gurin zahrar dole taci burki a gefen second gate din.
Zahra gurin Abban ta nufa Yana ganota ya Fara fadar "Masha Allah! Uwata jikin yayi kyau, ya kika kwana?".
"Da sauki Abba, Ina kwana?"
Ta fada tana tsugunnawa kusa dashi.
"Lafiya kalau Aina leka dana dawo daga masallaci akace Baki tashi ba".
"Eh Ammah ta fada min, nifa Abba dama hakuri akayi da zuwan Nan nafa warke ba inda yake min ciwo
yanzu".
Sameer ne ya shigo da alama daga wurin Baba Malam yake Dan harda Habib suka shigo, gurin Abba suka
nufo Habib ya gaishe da Abban sannan Zahra ta gaishe su shida Sameer din suka dubata, mikewa tayi suka
nufi inda Malam Bala direba yake jiran Auta su tafi makaranta, sai ya shiga ya zauna sannan Zahra ta bashi
1k, tace ga kudin chocolate Nan idan ka dawo Ammah zata baka wasu na saka Aunty zulai ta debo maka".
"Nagode Aunty Allah ya sauwaqe Miki Zan Miki addu'a idan nayi sallah, malam Bala ne ya karaso suka
gaisa da Zahra ya tada motar suka fice Musaddiq Yana daga Mata hannu.
Ta juyo kenan ta hango zilai da sahura sun nufi gurin su Abba suna gaishe su sannan Habib ya karbi key din
motar suka zuba kayan dake hannun su.
Sallama su Sameer sukayiwa Abban suka nufi gurin motar, zahrar ce ta dawo gurin Abban tana fadin "zamu
tafi Abbana ayi Mana addu'a"
"Allah ya tsare hanya uwata ya Baki lafiya yasa daga wannan zuwa Asibitin a samu warakar wannan
ciwon".
"Amin Abba nagode mun tafi sai nu dawo" ta juya ta nufi motar.
Har gurin motar Abban ya karaso Yana musu Addu'a da fatan sauka lafiya.
A hankali Sameer yayi kwana ya nufi gate din fita Abban Yana daga musu hannu, haka ma Ya Hamza shima
Saida yaga ficewarsu sannan ya koma side dinsu, sunzo fita Sameer ya dunkulo kudi yaba Mai gadi cikin
murna ya Fara jero Masa Addu'oi da fatan Alkhairi har yayi Dan nisa suna jiyo muryarsa.
A wurin gidan sarki Habib ya sauka, sukayi sallama da Sameer yayiwa zahra sallama da fatan samun lafiya
Mai dorewa, yayi gaba zuwa ina zaya.
Sun mika a tafiyar sosai Sameer ya Dan juyo kadan Yana fadin.
"Madam tun jiya nake Kiran wayar ki ba'a dauka".
Dan kwantar da Kai tayi jikin seat din tana fadin. "Wallahi rabona da wayar tun jiya da safe a gida na barta
lokacin Ina Zan iya tunawa da wata waya Ina tunanin ko ranar karshen ce tazo, sai dazu da Aunty zilai ta
dauko min nabi wasu missed calls din kafin na Kira taka number din ya Hamza ya shigo yace kazo mu fito,
na gode kwarai da kulawar ka Allah ya Raya Mana babyn mu". Ta fada tana Dan murmushi.
Shima murmushin yayi tana fadar "wato baby kadai Zaki tambaya Banda mamansa wato saboda sunan
mijinki ne son Kai ko?.
Hannunta ta saka ta rufe fuskarta.
Dariya zilai tayi tana fadin tuba muke Yallabai ai baza'a Fara haka ba, gani tayi baby shine bako".
"Kin Kare ta dai kawai Aunty".
Tafiyar awa biyu da minti Arba'in da biyar suka shigo Kano.
Suna area mariri Sameer ya lalubo Rukayya.
"Da fatan komai yayi yanda akeso ya zama ready ko?"
Sauraren amsar da take fada Masa yake, kafin yace "ok mun shigo ki Kira mommy tasa salmanu ya kawo
iya Rahane yanzu".
Bai jira abinda zata fada ba ya kashe Kiran.
Wani Kiran ne ya shigo masa, shima dai yana da alaqa da zuwan nasu duk dai zahrar naji tayi mamakin
Yanda Sameer yake magana cikin ladabi irin haka to shida waye yake wayar Wanda ya jibinci lamarinta
haka? Wata qila inda sukeyiwa aiki ne suka dauki nauyin zawa Asibitin nata, haka ta ringa sakawa da
kwancewa, shi Kuma Sameer shiga can kurda can har suka shigo Nasarawa G.R.A sultan road.
Tunda suka shigo Kano zilai ke baza idanu, Tana bawa idonta abinci, ita fa zilai duka zuwanta Kano baifi sau
uku ba,
Shima Ammah take yiwa rakiya idan wani uzurin ze kawota.
Gidaje ne na garari take gani da ban mamaki yinsu ake kamar baza'a mutu a barsu ba, tana ganin gidajen
da take mu'amala dasu sun Kai sun kawo Amma yanzu sai take ganin tamkar akurki ne kan wadan da take
gani Bata gara sarewa ba Saida taga gidan da Sameer ya dosa, take hantar cikinta ta kada, innalilllahi takeyi
a zuciyar ta, Nan da nan jibi ya Fara karyo Mata Daman tana mamakin gidan da zahrar ke ciki na can
Azaren to kuma saiga wani, duk da Bata San mamallakinsa ba, wata Kila karar kwanace tasa ta biyo zahrar
irin wannan gidan da sai ayi dambun Naman ka na waje baiji ba.
Kofar wani mahaukacin gate ya tsaya yayi horn sau biyu aka bude suka shige.
Ba zilan ba ita kanta Zahra ta sare da lamarin gidan Dan tasan yes Sameer masu kudi ne ko kungiyoyin su
suna sakin kudaden aiki kamar ba gobe amma Bata taba tunanin ya mallaki irin wannan mahaukacin gidan
ba. Dan da gani ba tambaya mamallakinsa yaci ya tada Kai. A kofar parlourn ginin da yafi ko wane tsaruwa
da kyawun gani ya tsaya yana hamdala ga Allah s.w.a.
Wata matashiyar buduruwa ce ta fito daga parlourn cikin rigar atamfa fitted tana takun yanga da gayu ta
nufo motar tana fadin "sannunku da zuwa, Amma wallahi I am very surprised Dana ganka yanzu".
"Rukayya Kenan kin dauka Ina Miki Wasa ne idan Kinga banyi driving ba nine bansa kaina ba".
Dariya tayi "ai na yarda Kuma nasan wannan assignment ne me mahimmanci a gurinka".
Fitowa yayi Yana fadin "yauwa sannunki da kokari, kuma haka ake tarar Baki a garin ku? kinzo kinata surutu
kin tare Mata kofar fita".
"Oh! Sorry" ta fada tana budewa Zahra kofa duk da Bata ganinta sosai saboda tintac glass ne a motar.
Dan matsawa tayi ta bude Mata kofar, kanshin da yayi Mata sallama ne yaja hankalin Rukayya ta kalli kofar
lokacin Zahra ta sako kafarta daya Kan fuskar zahrar idanun Rukayya suka sauka.
"Kam bala'i"
Rukayyar ta fada a zuciyar ta "wacece wannan din Kuma? Tun jiya lokacin da ya Sameer ya aiketa shopping
na abubuwan amfanin gida da kayan Mata ready made take Masa kwawar ya fada Mata na waye? sai dai
yace Mata wata ce Zaki ganta yarinya ce ko sa'ar ki Bata kai ba yayanta ne ya hada su ya kawota Asibiti, sai
oga yace a sauketa a gidansa har su gama da asibitin.
Rasa wane yare Rukayya zatayi Mata tayi saboda tasan wannan ko zo da hausa Bata sani ba duk da shigarta
ta hausawa ce. Aunty zulai ce tayi magana lokacin data fito "haba yallabai Ina laifinta gashi ta fito ta tarbe
mu".
Dan murmushi zahra tayi lokacin data fito daga motar gaba daya ta kalli Rukayyar tana wani smile Mai
daukar hankali tana fadin "sannu Aunty mun gode" ta fada tana mika Mata hannu, ba Karamin mamaki
Rukayya tayi ba Jin zahrar na zazzaga tsantsar hausa bako gargada. Bangaren Sameer zahrar ta kalla tana
fadin "Haba oga Ina laifin Aunty na ko wannan fitowar da tayi ai shima Yana cikin entertaining ne mun
gode".
Ta fada lokacin data rike hannun Rukayyar.
Sai lokacin zilai ta Dan samu Peace of mind ganin Rukayya tasan dai da alama gidan bana macuta bane duk
da ba tana zargin Sameer bane,yau din ce wata iri baka saurin amincewa da mutane.
"Sannunku da hanya".
Rukayyar ta fada tana kallon Zahra, yayin da Sameer ya shiga motar ya nufi parking lot ya ajeta.
"Yau Aunty mun gode"
Zulai kuwa sai kalle kalle take tana jinjina girman gidan Dan wasu gine - gine take hangowa na Alfarma ga
shuke-shuke Nan sai wani sanyin kamshi ke tashi a gidan ko Ina Kuma tas ba alamar datti a cikin, dukiya dai
Mai sunan dukiya an kasheta a gidan Nan.
Ita tunda uwarta ta kawo ta duniya Bata taba shiga irinsa ba, sai yau da dalilin uwar dakinta Zahra ya kawo
ta.
Maganar Rukayya ce ta dawo da ita cikin hankalin ta.
"Bismillah mu shiga daga ciki".
Rukayyar ta fada tana nufar kofar parlourn numbers ta daddanna ta bude musu kofa ita dai zilai yau jinta
take kamar ba cikin kasar take ba.
Lokacin da suka shiga parlourn ba zilai ba kifin rijiya ita kanta zahrar sai da wani shock ya shigeta na wucin
gadi, badan Zahra tana fita waje ba Kuma kakanninta masu dashi ne kuma tayi zaman syprus taga guraren
hutawa da yawa da gidajen Alfarma da Babu abinda ze Hana ta zabga kauyanci, dan Babu karya naira tayi
kuka a cikin parlourn Nan tamkar fadar sarauniyar ingila komai na ciki off-white ne da sirkin ash colour ba
tarkace da yawa sai dai an kawata shi da wasu irin cutains masu azabar kyau dan shi kadai abin kallo ne, sai
fremes masu kyau da tsari da wasu irin flowers, sai wani special kamshi daya hadu da sanyin A/C ya bada
yanayi Mai dadi, sai plasma kusan bango guda.
Zilai dai 'yar kauye sak ta koma ko Zama kasayi tayi sai da Rukayya ta juyo tace Mata Bismillah ki zauna
Mana ku Sha ruwa".
Ta fada tana yin gaba ta nufi wani steps gurin dining table ta shige wata kwana.
Zahra zilai ta kalla "Wai Ina ne Nan din Kuma gidan na wanene nifa duk a rude nake na kasa samun
nutsuwa ko kadan, irin wannan gidan ai sai sarki ko wani gagarimin Mai kudi".
Da watsa hannu Zahra tayi.
"Toni Ina nasan amsar tambayar taki, Nima duk daya muke dake bansan komai ba, nasan dai yace zamu
zauna a Nasarawa GRA kawai ba wani Karin bayani da yayi min". Rukayyar ce ta shigo dauke da babban
tray da robobin farmfresh dasu ruwa da Shani na gwangwani, sai fruit fresh ones.
"Bismillah kusha ruwan sai muje ku huta sai kuci abinci".
Sannu Zahra tayi Mata, itama zilan tayi mata, Sameer ne ya shigo da wani matashin saurayi da luggage din
Zahra da 'yar madaidaiciyar jakar zilai a hannunsa ya gaishe su ya aje ya koma.
Rukayya ce nufo inda Sameer din yake tana fadin "Ya Sameer Dan Allah ka jirani Zan bada sako gurin
mommy ka taho min dashi"
"Kefa Ruky kina da damuwa kiyi Abu Mai mahimmanci sai ki tsaya kina Wasa".
"Allah Yaya da gaske nakeyi ka taimaka min".
"Ok"
Gurin su Zahra ya duba Yana fadin "sannunku madam kun sha hanya ki huta zuwa dare zamu fita Asibitin
doctor tace mu hadu da ita a Nan Asibitin Nasarawa zataga patient yau a can da dare saita dubaki idan
yaso sai mu hadu da safe a malam din".
"To ba damuwa in Sha Allah Zan shirya da wuri nagode".
Ya juya ya fice daga parlourn.
Zahra tayi mamakin ganin favourite drinks dinta da aka kawo, more especially farm fresh Amma Bata kawo
komai ba ta dauki abin arashi ne kawai.
Bayan Sameer Rukayyar tabi suka fice daga parlourn.
Saida suka sauka daga steps din gurin sannan Rukayyar ta dubi Sameer tana fadin "big bro Dan Allah
wacece wannan din? Meye matsayinta a gurin Ya Mahmud nasan wlh ba banza ba yace a bude Mata
wannan apartment din nasa".
Tsaki Sameer yayi "na dauka want important Abu Zaki fada min Ashe tsabar gulma ce a cikinki, ba abinda
yayi Miki zafi a lamarin yarinyar Nan yanda Kika ganta haka Nima na ganta bansan ko wacece dinsa ba
tunda baiso in sani ba, Dan haka kada rawar kanki tasa ki fadawa Dr Haseena wani Abu Koda zata
tambayeki kice Baki San komai ba".
Tunda ya Fara magana Rukayya tayi zuru tana kallonsa yanda ya kiciccife yasa tayi masa alamar (?) Tasan
there's something behind.
Amma fadan dayafi karfinka sai ka mayar dashi Wasa.
Dan jinjina Kai tayi tana fadin shake Nan Bari na koma kada suga an barsu su kadai".
Ta juya ta koma Zuciyar ta fall da tambayoyin da Babu Mai Bata amsarsu.
MAMAN FATEEMAH.
Page 38.
A hankali ta ringa tafiya kamar wadda ke tsoron kada a kamata, abinda ta gani ne ya Bata matukar
mamaki wannan bed room din tamkar an dauko na can Azare na Mahmud an aje a Nan, hatta da curtains
din windows din iri daya ne ba banbanci, Abu daya wannan yafi wancen shine girma wannan yafi balance
akan wancan, Amma tamkar an dauko shi an aje, ita abin da farko tsoro ya bata hatta kamshin turarensa
taji a dakin jiki ba kwari ta dosana ta zauna a gefen bed din tana Kara karewa dakin kallo tabbas a gizo
idanunta ke Mata ba abinda ta gani haka yake, bata Kara tabbar da kamshin Mahmud takeji ba Saida ta
zauna kamar lokacin ya saka ya fita daga dakin.
Dan dam tayi Jin ta Fadi sunan Mahmud fatsal sai taji wani bambarakwai a bakinta duk sai wani irin Abu ya
darsu a zuciyar ta.
A shagwabe kamar tana magana da wani ta Fara fadin "to me ma zance masa ne? Kuma Wai Nan din dakin
waye da suke kamanceceniya da nasa har kanshin ba banbanci?.
Ba Mai Bata amsar tambayar Dan haka ta Dan zamo kadan tana janyo luggage dinta tana fito da abinda ke
ciki,wanka take sonyi duk jinta take a takure indai tana period sai a hankali sam Bata da sakewa ko
misqalazarratin, Banda dole Babu abinda ze sakata barin gida a irin wannan condition din.
Luggage dinta ta janyo a hankali ta Fara fito da abinda ke ciki, na Kan mirror ta Fara diba ta nufi inda yake
lokacin data karasa ba karamin mamaki tayi ba ganin irin kayan shafar da take amfani dasu har da wasu
daga cikin irin turarukanta ta gani Banda su freshner na fesawa.
Bata fasa aje na hannunta ba, gurin kayan ta dawo ta bude cloth set din data gani tana budewa tayi arba
da kayan Mata Babu abinda Babu, harsu shoes da bags, dasu inner wears.
Mayarwa tayi ta rufe ta dawo da kayan a hannu ta mayar inda ta dauko su.
Wanka ta shiga Nan ma wata duniya ce aka hada, ta jima tana gasa jikinta Dan idan Tana irin wannan
condition din Bata kaunar abinda ze hadata da ruwan sanyi ko kadan.
Bata wani Bata lokaci ba gurin shiryawar ta saka doguwar Rigar atamfa glitter purple, Rigar tayi Mata das a
jiki mayafi light brown ta saka touching din jikin atamfar sai takalma suma light brown din plat, haka nan
taji tana son saka turarensa Mai sanyin kamshin Nan dauka tayi ta fesa ta nufi hanyar ficewa daga dakin.
Saida ta fito yanzu ta karewa wannan parlourn kallo yafi duk Wanda ta gani a baya tsaruwa kunjerun dake
ciki ko rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba Bata taba ganin irinsu ba duk kuwa da gidajen Alfarma data shiga
ta bangaren Ummee.
"Iya aje a fito da sauran abincin sai muje kiyi lunch din tun, shigarki ciki ya Sameer ke kirana Wai kinci
abincin Baki da lafiya na tabbar kin Sha magani ni har mamakinsa nakeyi Bai dauki lamarinki da Wasa ba
gaskiya".
Iya Rahane ce tace "Haba Rukayya yaushe Alhaji karami Zeyi wasa da lamarin iyalin Mahmud, Nima da
Mommy ta kirani Saida ta Kira shi ta fada Masa nice zanzo ya amince kafin Nazo, ya jaddad min na kular
Masa da ita yanda ya kamata, Kinga kuwa ai baiyi laifi ba ko?".
Kai kawai Rukayyar ta iya gyadawa mamakin duniyar Nan ya gama kasheta a zaune "matar Mahmud? Haba
biri yayi Kama da mutum, tasan ba banza ba ya Sameer keta rawar kafa ya kasa tsaye ya kasa zaune akan
lamarin, Kuma da alama itama yarinyar ninketa sukayi ta bai-bai Dan da alama batasan waye hakikanin
mijin nata ba, gaskiya ta tayata murna dan ta zama Mai sa'a duk da shima Saida ya dauko diamond a cikin
zinarai, Dan Daman wannan irin matansu ne.
Gurin dining din Rukayya tayi Mata jagora suka nufa tana fadin "kice min matar big bro ce Amma nayi
mamaki gaskiya sun lullubeni Amma ki Bari kawai bazance naji ba Naga iya gudun ruwan ya Sameer sai
wani cewa yake kanwar abokinsa ce".
Ita da zahra Dan murmushi take tunda ba gane Kan zancen tayi ba.
Abinci ne yakai kala biyar Rukayya ce ta bubbude wa zahra tana fadin "Auntyn mu ki zabi Wanda kike so a
zuba miki".
"Kaji Aunty ni basai kin zuba min ba haba dadin sai yayi min yawa hakan ma na gode, ina Aunty zilai tazo
muyi lunch din".
"A'a nan naki ne ke kadai na Kai Mata nata dakin ta tun dazu".
********
Knocking din kofar akeyi a tana zaune ta Sha uban gayu kamar wadda zata wuri dinner ta biki sai kanshi ke
fita a jikinta Mai Dadi tana rike da wayar ta tana addu'oin yaumiyya na cikin du'aul mustajaba.
Umarnin shigowa ta bayar tana kallon kofar, Basira ce yarinyar dake aikin shara da goge-goge a bangaren
ta, tsugunnawa tayi tana fadin "barka da Asuba Ammi".
"Barka kadai Basira har kin fito da wuri haka, lafiya dai ko?"
"Lafiya kalau Ammi Daman Hajiya Inna ce tazo ita da Abie".
Littafin ta aje akan bed side tana fadin "Hajiya Inna kuma"?"
Kai Basira ta gyada alamar eh.
"Kije gani Nan fitowa in Sha Allah".
Ta nufi clothset dinta ta dauko gyale mahadin shaddar ta fito daga bedroom din.
A hankali take saukowa daga stairs din shar da ita tun kafin ta karasa saukowa kamshinta yayi musu
sallama, cikin takunta na nutsatstsiyar mace Mai aji da yarda da kanta ta da tarin ilimi Hadi da wayewa,
sallama tayi musu tana nufar gurin Hajiya Inna ko inda general yake Bata kalla ba.
Kusa da Hajiyar ta zauna lokacin da take amsa sallamar tata.
*******
A qalla sun dauki minti kusan Sha biyar kafin Zahra ta Gama. Parlour na biyu Rukayyar taja Zahra suka shiga
Bai Kai na farkon girma ba Amma ba karya Shima ya hadu kamar jira ake su zauna wayar zahrar ta dauki
sansanyan kidan ringtone din ta.
"Amma"
Ta fada tana picking din Kiran sallamar Ammar ta amsa tana fadin "kiyi hakuri Ammah wallahi yanzu na fito
daga wanka naci abinci, yanzu nake son kiranki na fada Miki mun sauka lafiya".
Daga can Ammar ta amsa Mata da "babu komai da fatan dai komai lafiya ba wata damuwa? zilai ce taso
daga min hankali Wai wani gida aka kawo ku gari guda bata taba shiga ko kwatankwacin irinsa ba kamar
Kuna wata kasar ita tsoro takeji".
Dariya sosai zahra tayi Jin yanda zilai ta nadi zance ta fesawa Ammah.
"Kai haba Ammah kyale Aunty zilai rudunta ne kawai, gidan Dan babba Kam babba ne Amma komai
normal Ina Jin gidan wani friend din oga Sameer ne aka kawo mu, Kuma momin su oga Sameer ma Saida ta
turo Mai aikinta daya da kanwarsa daya Aunty Rukayya gata ma nuna tare ku gaisa".
Wayar zahrar ta mikawa Rukayya suka gaisa da Amma, godiya Ammar ta dinga yiwa Rukayyar har kunya ta
kamata tace Kuma ta bawa Zahra number din mommy ta kirata tayi Mata godiya.
Sallama sukayi da Ammar suna kashewa Kiran ya shigo international tana gani tasan shine.
Dagawa tayi tana masa sallama Jin muryarta ba kamar jiya ba ya sauke ajiyar zuciya a hankali da Bai yarda
ba da Sameer ya fada masa kamar batayi ciwo ba sai yanzu da yaji muryarta tana fita ba kamar jiya ba.
Sallamar ya amsa Yana fadin "my previous...".
Wani deeply saida tsikar jikinta ta bada wani yarrr. "Wash" ta fada.
Kara Kiran sunan yayi a hankali ciki wata murya Mai tada zaune tsaye "me ya faru ne to jikin ne"?".
"A'a ba komai" ta fada a shagwabe.
Rukayya na ganin haka ta Miki tana nuna Mata tana zuwa Dan ta barta ta sake yanda ya kamata.
"Alhamdulillahi haka nake son ji, ya ciwon ya daina ko yanayi kadan kadan".
"Ya M na warke yanzu ba wani Abu da yake damuna dama mu koma gida kawai tunda ya wuce, kawai naje
Naga baby muje mu gaishe da mommy da Umman sajida zuwa jibi mu koma, Dan Allah kace to kaji Kuma
fa kaga gidan da oga Sameer ya kawo mu gaskiya ka fada Masa ya mayar damu gidansa ko gidan mommy
wallahi yayi girma Ni tsoron inda aka kaini nakeyi gurin yayi nisa da main parlour Kuma wani abin mamaki
kasan funitures din dake dakin irin na dakinka ne na Azare komai da komai".
Dan Jim yayi kafin yace irin nawa Kuma wace unguwa ya kaiku?".
Dan Jim itama tayi. "Ina ga ko Dawako Road Nasarawa G.R.A.
"Ok nasan gidan na wani friend dinsa ne, wane bedroom din aka Baki?".
" Bangaren dama daga can ciki sosai".
Shiru yayi wato Sameer be bude Mata master bedroom din ba kenan.
"Precious ki hakura a duba min ke kinsan kuwa tension din dana shiga akan ciwon nan naki? kiyi hakuri ayi
bincike akai kawai sai nafi samun kwanciyar hankali, gida Kuma nasan shi Baki da matsala dashi Dan cike
yake da tsaro ba wata kafa da za'a shigo cikinsa".
"Baka Gane ba nifa ni kadai ce bazan iya kwana a gurin ba sai dai Aunty Rukayya tazo mu kwana".
Ta fada kamar zatayi masa kukan shagwaba.
"A'a ban Amince ki kwana da kowa ba, ba abinda ze kamaki matsoraciya kawai kice na shirya nida nake
fatan Allah ya hore min nayi Miki Wanda yafi wannan girma yanda Zaki sake ki walwala keda yaran mu, to
kina tsoron wannan ma inaga Wanda nake fatan ajiye sarauniyar Mata a ciki Zahra fa kike ko cikin taurari
keta dabance, haka kawai ki janyo min wata ta hanani rawar gaban hantsi da dare so nake ki ragemin zafi
idan da wata a dakin ai kin sabautani ko baza'a taimawa dan malam ba?".
Ya fada cikin wata irin kasala wadda ta saka Zahra Jin wani irin Abu a jikinta. "Ya Ilahiy Ajib"
Ta fada cikin kasakalliyar murya.
"Yan Mata yaya dai Kona gudo ne kina bukatata a kusa"
Ya fada Yana huro Mata iskar Bakinsa ta cikin phone din, da sauri ta cire wayar daga kunnanta, Dan da
gaske sakon yaje inda aka aike shi kashe Kiran tayi bako sallama.
Page 39.
________Wurin karfe takwas Sameer ya shigo gidan, wayar Rukayya ya Kira yace su fito doctor tana
jiransu, lokacin suna bedroom din da zahrar take suna cakusawa da Zahra akan wata Rigar shadda 'yar Mali
da Rukayyar ta daukowa Zahra cikin kayan da Sameer ya bada ta sawo haka Nan Rukayyar taga zata Dace
da zahrar shi yasa ta nace akan ta sakata ita kuma tana ganin tayi Mata girma da yawa, Jin Kiran Sameer
yasa ta hakura ta saka sai gashi tayi Mata das kamar an gwadata aka Dinka.
Shar ta fito kamar ka dauke ka buye saboda kyau sai yarintarta ta Kara fitowa, dauri mai kyau Rukayya tayi
Mata tunda ta kware har makeup din amare takeyi, light makeup tayi a fuskar ta sai ta fito kamar amarya
ranar a yini.
"Masha Allah" kadai Rukayya ke fada ba karya kyau daban yake ko ita mace zahra ta tafi da imaninta to
yayi namiji Kuma? Bata yarda da kyau idan yayi yawa hadari bane sai yanzu da Zahra ke gaban ta Dan babu
namiji da ze ganta Bai Kara kallonta ba.
Kasa hakuri Rukayyar tayi Saida ta magantu.
"Allah yasa kiyi ta haifowa big bro Yara masu Kama dake gaskiya Ya Mahmud ya Dace ai shi wallahi gaba ta
kaishi gara da aka samu wannan incidence din da Bai faru ba yaushe ze gano Mana ke".
Ita dai zahra murmushi kawai takeyi, amma Kasan zuciyar ta tambayoyi ne fal, Ta Ina Mahmud ya zama big
bro din Rukayya da alama akwai wata dangantaka Mai karfi a tsakanin Sameer dashi bawai aikin NGOs din
Nan bane gaskiya.
A haka suka fito main parlour suka tarar da Iya Rahane da zilai suna kallon Arewa 24 suna program din
mata a yau.
"Masha Allah, Allah ya kade mugunji da mugun gani".
Iya Rahane ta fada tana kallon Zahra.
"Allahumma Amin. Allah ya tsare uwar dakina ya Baki lafiya yasa a dace".
Zalai ma ta fada, Rukayya tace "Allahumma Amin, sai mun dawo".
Suka nufi hanyar fita, a cikin mota suka iske Sameer, gaba Rukayyar ta shiga ita kuma zahra ta shiga back
seat.
Basuyi wata tafiya Mai nisa ba suka shiga cikin Asibitin, bayan sun fito daga motar number Dr. Haseenar
Sameer ya Kira, saiga wata sub-staff da wayar a hannunta tana fadin "sunnunku da zuwa doctor tace na
tafi daku office dinta tana zuwa suna wani aiki ne"
"Ok mun gode".
Rukayya ta fada.
Har cikin office din ta kaisu ta fita Nan Sameer yabar su yace zeje yaga wani friend dinsa Dr. Sulaiman.
Bai jima da fita ba aka turo kofar su duka suka juya suna kallon Mai shigowa macece wankan tarwada Mai
matsakaicin tsawo fuskarta doguwa ce da maidadaicin idanu da hanci tana sanye da doguwar Rigar
material coffee Mai haske tayi rolling da milk din veil fuskarta fal fara'a ta shigo tana fadin " wa nake gani
kamar Rukayya a office dina rabon daki tako Nan harna manta Sai dai a waya".
Dariya Rukayyar tayi tana fadin "Ina laifin Kiran wayar ma Shima zumunci ne yafi ace ba'ayin ko daya".
Direct gurin da suke zaune ta nufa " Kinga kin dauke min hankali Ina ta zuba ban yiwa bakuwa ta sannu da
zuwa ba, sorry na barku a zaune ta fada tana kallon zahra"
"Lah haba doctor ba komai yanayin aikinku ne hakan".
Zama tayi kusa da Rukayya tana maida hankalinta akan Zahra.
Patient din dangen ce?"
Ta jefawa Rukayya tambayar, da alamun mamaki a fuskar ta.
Kai Rukayyar ta gyada mata.
"Anyway Bismillah ta fada tana tashi daga gurin ta nufi table dinta.
Zahrar ta Mike tabi bayanta.
Tambayoyi sosai ta rinqa yiwa zahrar wasu har kunya take kamata ta kasa Bata amsa, tambayar data fi Bata
mamaki shine inda take tambayar ta meye tsakanin ta da Mahmud Dange?"
Kafin zahrar tayi magana Rukayya ta rigata "sister din abokinsa ce daga Bauchi, kuma matar aure ce Dan
naji Baki tambqyeta ba, ita Kuma Bata fada Miki ba".
Wata ajiyar zuciya ce ta kubcewa Dr Haseenar har Saida Zahra ta kalleta.
"Ai ban sani ba Ruky Naga DANGEN yayi matukar damuwa ne ko yanzu kafin na shigo saida ya kirani yana
fada min Kuna Nan Kuna jirana na dubata sosai".
Dan smile zahra tayi kawai ita Kuma Rukayya tace "kinsan halinsa baya Wasa da rashin lafiya komai
kankantar ta, kinsan suna China Aunty Fateeha ta haihu sending Ya Sameer yayo Nigeria shi ya wuce
Dubai".
Dan murmushin itama Dr din tayi "zeyi abinda yafi haka in dai Dange ne yanda ya damu Zaki dauka
matarsa ce wallahi duk yafa rikice kamar ba dangen da Mata ke fada a kansa ba ko kallo basu isheshi ba
Sanda muna school a UK da yawa mutane sunyi mamakin yanda muka Dade dashi ba wani matsalar data
faru fatana ya dawo su hadu da Daddy ayi a wuce gurin kawai, kinsan halinsa tunda aka samu matsala
Nima fa ta shafeni tunda lokacin da abun ya faru munje gida sokoto shiya Hana ayi abinda za'ayi ta fice
yabar kasar Kinga Banda case din Nan ta sister din friend nan tashi Bai Kara kirana ba wlh na tura Masa
sako ta email dinsa Amma ba reply".
Ita dai zahra ba baka sai kunne wata magana sukeyi wadda ta jefata a kogin tunani akan Mahmud abinda
kunnen ta keji daban abinda yake nuna mata daban.
"Hum lamarin big bro sai a hankali kin sanshi da zuciya kafin dai yayi fushin ana dadewa Amma idan yayi
jam'i yakeyi gurin yanke hukunci sai hakuri komai ze Zama normal".
Rukayyar ta fada.
Forms ta cikewa Zahra ta test-test Wanda za'ayi Mata ta Mike ta fito daga mazauninta tana fadin kuzo muje
ayi wannan testses din Sai Kuma muje ayi scanning mu gani akwai abinda nake tunanin yana kawo
matsalar Amma bazamu tambbatar ba sai mun duba.
"To Allah yasa a Dace" Rukayya ta fada.
Sai da suka Fara zuwa lab sannan suka nufi radiology department inda za'ayi hoton cikin.
Dr karima ce tayi mata scanning din tambayoyi ta Riga yiwa Zahrar harta gama.
Basu jira karbar result din ba, da safe doctor Haseena zata shiga dasu can Asibitin malam Aminu inda za'a
mata saura gwaje-gwajen Nan sun Dan rage ne saboda cunkoson can din.
Har gurin mota doctor ta rakasu suna 'yar tsama da Sameer, sannan sukayi sallama Sameer na Mata godiya
saboda taki yarda ya biya ko sisi tace patient din DANGE nata ne, itama Zahrar godiya tayi Mata Rukayyar
ma haka.
Har Sameer yayi ribas doctor Haseena ta daga Masa hannu alamun yazo gyara parking yayi ya fito ya nufo
inda take a gefen baranda.
"Yana zuwa Bata jira komai ba ta Fara tambayarsa cikin nuna damuwa Dan idanunta har Dan ruwa ya taru
a ciki da gani tana cikin damuwa da tashin hankali.
" Wannan yarinyar wacece a gurin DANGE?"
Iska ya Dan huro daga Bakinsa ya hade hannuwansa a kirji Yana kallonta kawai.
"Me yasa Kika yi min wannan tambayar?"
"Just pls answer me who's she?"
"Abinda ya fada Miki da farko yanzu ma dai shi zan maimaita Miki, kanwar friend dinsa ce daga Bauchi
sukazo Kuma matar aure ce abinda na sani kenan".
"To Amma me yasa ya shiga damuwa akan lamarin ta ya hanani sakat Ni Kuma nasan wannan ba d'abi'ar
DANGE bace".
"To ki Kira shi kiji gaskiyar magana daga Bakinsa Mana".
Ya fada Yana kokarin barin gurin.
"Kada kaji haushina na kasa samun nutsuwa ne"
Bai tsaya ba Dan da gaske nema take ta karya Masa gwiwa har yayi abinda baze musu Dadi ba, gara taji
daga baya a bakin wani ba shi ba, Daman yasan za'a Rina dole ta kawo wani Abu a ranta yanda ya nuna
damuwa akan lamarin Zahrar.
Jiki ba kwari ya dawo motar ya tada yabar gurin, har lokacin tana tsaye Bata bar gurin ba. Shi kansa yaji
Babu dadi a ransa yanda Haseena ta mace akan Mahmud tun suna UK yasan idan taji yayi aure ba Kara min
tashin hankali zata shiga ba.
Sai da sukayi nisa da Asibitin sannan Rukayya tayi magana "Dan Allah Yaya kaimu murtala Muhammad way
zanyi sayayya a Nameer Sale".
Tsaki yayi kadan da gani ranshi ba dadi, "nifa baba son yawo kinga ai saimun koma baya, me yasa Baki fada
min ba tun kafin mu fito nasan da zuwan".
"Kayi hakuri mantawa nayi Amma muje gobe in Sha Allah naje kawai".
Bai Kara kulata ba haka zahra Bata tofa tata ba.
Yana zuwa round yayi ya dawo ya nufi murtala Muhammad way din, tare suka shiga da Sameer din yace
zahra ta duba abinda take so, har Rukayya ta Gama daukar abinda tazo nema zahra Bata dauki komai ba,
ganin haka yasa Rukayyar ta daukar mata kayan shafa dasu turarikan gashi Dana wanka shi Kuma Sameer
ya daukar Mata dangin su wafer da ice cream, a hanya hira sosai Rukayya keyi musu Amma ita Zahra
hankalinta Yana Kan maganganun doctor ita fa abin yafi karfin tunanin ta ke nan da lauje cikin nadi, shin
waye uban gidan wani tsakanin Mahmud da Sameer idan ba kunnenta ne baiyi daidai ba taji Rukayya na
cewa Mahmud ya Turio Sameer gida daga China ya wuce Dubai zance yayi dai dai Dana Fateeha matar oga
Sameer lokaci tafiyar su.
Har suka shigo unguwar hankalin ta baya tare da ita tayi zurfi cikin tunanin makomarta kodai yanda ya taba
fada Mata Yana yaudarar matan ne ya gudu dasu tunda yanzu yasa an dauko su ba Wanda yasan inda ya
kawo su daga Rukayyar har Sameer din ba Wanda yasan takamaimai Ina ne asalinsu an kawo su ita da
baiwar Allah an killace su a wannan uban gidan kamar resident na matar shugaban kasa.
Sai da Rukayya ta Dan tabata lokacin da suka tsaya a kofar parlourn Dan da gaske tayi mugun zurfi a
tunanin Dan zabura tana Fadi. "wallahi har naji tsoro".
"Ai ke dince Ina ta magana Amma kinyi Zurfi a cikin tunanin, ki rage yawan tunani saboda lafiyarki kinsa
Yana shafar lafiyyar Dan Adam".
"In Sha Allah Zan Dena na gode".
Ta yungura ta fito Bata jira ba ta nufi kofar shiga tana fadin oga Sameer sai da safe kaina yake Dan Sara min
a shafa min Kan Abeed"
Dariya Sameer.
"Zeji in Sha Allah Banda mamansa ko?"
"Kaina bisa wuyana na Isa ayi min gaisuwa, zanzo muyi jegon tare".
Wani kallo Rukayya tayi Mata tayi wani killer smile ta matso daidai kunnen ta "saurin me kikeyi in dai jego
ne kamar yaune kinsan Yayana ba rago bane daina gaigaye zakiçi tumo".
Tayi gaba abinta kamar Bata Fadi komai ba. Ido Zahra ta zaro tabi bayanta da kallo, ta fuske kamar ba ita ta
Fadi maganar ba.
Ganin haka yasa Sameer ma ya basar ya dauko wasu ledojin yabi bayan Rukayya data dauko wasu.
A Nan parlour sukayi sallama da Sameer ya tafi, su zilan Basu tashi daga kallon ba suka Yi musu sannu da
zuwa tare Da tambayar ya jikin nata, bata jima ba ta dauki kedar cosmetic din da robar ice cream Daya da
biscuits da chocolates ta nufi hanyar masaukinta tunda yace Mata ba komai a gidan da tsaro sosai ta Sami
kwari gwiwa da kwanciyar hankali, tana barin gurin ta dauko wayarta ta kasheta gaba daya tana fadin.
Wallahi kwana kusa ba zasu gaisa ba tunda shi wani irin mutum ne marar Alqibla. Kuma tafiyar ta zatayi ta
koma inda ta fito haka kawai Kullum ita kenan cikin matsala gara ta koyi jajurcewa itama kowa ya samu
dama saiya ringa dokata kamar wata ball impossible wallahi".
Ta fada tana zura katin bude kofar ta shige ciki, a Kan sofa ta zube kayan ta shiga cire kayan jikinta Daman
duk sun dameta, wanka ta shiga Dan wallahi barci takeji, barcinta zatayi tasan mutum Bata wuce
kaddararsa.
******
A gajiye ya shigo masaukinsa yau throughout bai samu hutu ba, hankalinsa gaba Daya yayi gida so yake ya
ganta ra'ayal ain bawai ta wayar ba yaji dumin jikinta ya tarairaiyi kayarsa suyi barci tare su tashi tare ya
gaji da watangaririyar Nan gara ayi wadda za'ayi kawai game din ya Zama over.
Saida yayi wanka yayi order coffee sannan ya janyo wayar ya shiga nemanta da gaske yayi kewarta ba
kadan ba, shifa yana ganin yarinyar Nan itace weakness dinsa duk inda take tana manne a kirjinsa ko barci
yake itace a cikin barcin idan ba ganinta yayi ba ko yaji muryar da da akwai damuw, yaga alama any nan
gaba ze iya kulla wani abun arziki kuwa? tun yanzu da gishiri bai Sha Kan kazar ba yana jinsa haka Yaya idan
labarin ya sauya salo?
Abin mamaki wayar switch off.
Zuru yayi Yana kallon wayar "me kenan?"
Yasan dai ba matsalar charge bane, Sameer ya Kira, duk da basu Dade da Gama waya ba.
Sameer yayi mamakin ganin wani Kiran nasa.
Kafin Sameer ya Kai ga magana Mahmud ya Riga shi.
"Meya faru ne a Asibitin naji wayarta a rufe ko jikin ne ta tashi da akayi Mata gwaje-gwajen?"
"A'a gaskiya normal muka dawo har muka biya nan Murtala Muhammad way sukayi sayayya Kasan
Rukayya bataso a zauna lafiya,idan tajita da kudi ba zaman lafiya. Dan Allah ka daina turo mata kudi har
madam tabar garin nan, kasan Ruky da yawo Kullum aka fita saita qirqiro zuwa wani gurin, wani Abun ne
ya faru yanzun ?"
"A'a ba komai, kada ka manta da maganar kayan da za'a sauke gobe a Nan kanon a turasu can Azaren
munyi magana da Habib dazu".
"Ok in Sha Allah".
Sukayi sallama, ji yayi baze iya fada masa komai ba. Wayar ya aje kusa dashi wani tunani yayi sai yaji dariya
ta kubce masa "zakiyi bayani da yaren garinku yarinya duk yanda akayi taji wata maganar yanzu a Asibitin
yasan Haseena farin sani yanda yaji ta damu da sanin relationship din dake tsakanin sa da zahra yasan
zatayi duk yanda zatayi ta shigo da wata maganar wadda zatayi touching dinta tunda shekarun da wayonsu
ba Daya bane.
Itama Zahra kasa cin komai tayi fridge ta bude ta saka ice cream din da chocolates tayi kwanciyar ta bayan
tayi Addu'a, amma barcin Kuma yace baisan zancen ba, tashi tayi zaune a tsakiyar gadon tana tariyo
rayuwarta ta baya "ko yaushe Zan Zama stable a rayuwata? sai hawaye suka zubo Mata "Ubangji ka hanani
ganin bakin cikin gidan Aure, lamarin Yana neman yafi karfina ka jibinci lamurana Dan isar fiyayyan halitta
Annabin Rahama Muhammad s a w.w.
Bansan ko waye ba wannan bawan naka, kafini saninsa ka amintar Dani a cikin lamarinsa daka barni na
tozarta, ka kareni daga dariyar makiyana Ubangiji kasan ko suwaye suke mini yankan Bata a cikin lamarina,
kayi min kariya ka bani juriyar abinda ka jarrabeni dashi kasa ya zamar min kaffara.
Tasa tafin hannunta a fuskarta taAUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
Page 40.
______ karfe takwas saura Zahra ta fito cikin shigarsu ta asali doguwar Riga baka Mai aikin zare maroon
sai kananan stones har kasa,tayi rolling da maroon din veil, cikin takunta na rausaya take gannaro steps
din, tana baza sansanyan kamshi, ba kowa a parlourn sai wani sanyi da kamshin freshners ke tashi, Dan Jim
tayi tana tunanin ta koma kota zauna sai Kuma ta jiyo alamun motsin kwanuka a kitchen gurin da taga suna
shiga ta nufa tunda ba sanin Kan gidan tayi ba, tunda ta shigo iyakarta Nan sai Kuma bedroom din da take,
tana dosar gurin wani kamshin girki yayi Mata sallama, babban kitchen ne na zamani Mai kunshe da
na'urori birjik kamar a wani babban Hotel ko irin modern restaurant din nan iya Rahane ta gani tana yanka
wani Abu yayin da zilai ke tsaye tana duba wani abu a tukunya.
Sallama tayi musu tana fadin "Ina kwanan ku".
A tare suka juyo suna amsawa tare da fadin "ya Kika kwana da jikin?".
Dan juya Kai tayi tana fadin. "Nifa Babu abinda ke damuna kawai dai Dan a dunga yawo ne da Bata lokaci,
wallahi har kunya nake ji" .
"A kul Kika Kara fadar haka tunda mijinki yace Kizo a duba aga menene matsalarki kada ki watsa Masa qasa
a Ido ki sage Masa gwiwa akan kokarinsa, kije idan Allah yasa Babu komai shike Nan idan Kuma anga
abinda ke kawo ciwon a magance shi".
"Wannan gaskiya ne".
Zilai ta fada tana sauke girkin.
"To in Sha Allah na daina iya".
"Yauwa kokefa fa ai idan Kika Fara da haka ko lalular da tafi haka baze Maida hankalinsa ba duk da ba fata
ake ba".
"Dan Allah Aunty zilai bani wayarki na Kira Ammah tawa tun jiya ta kashe kanta taki kunnuwa".
Ta fada tana istigifari a zuciyar ta Dan tasan karya ta shara.
" To Bari na dauko Miki tana can a daki"
Ta wanke hannunta ta nufi kafar fita Zahrar tana biye da ita, sai da suka fito zilan ta kalli Zahra "uwar
dakina Dan Allah Wai Kinga kuwa dakin da aka ajeni a ciki Dan Allah muje kiga wannan duniyar da aka
sakani kamar dakin gidanki,to acan dai bana Hawa gadon Amma wannan akai na kwana har naso in
makara Allah yasa ita Iya Rahane Bata makara ba".
Dariya Zahra tayi tana fadin "daina fada Aunty zilai sai a Raina mu wallahi, muje Naga dakin naki Daman
ban San inda kike ba Koda tsoro ze kamani sai nayo gudun hijira".
A parlour na biyu suka shiga wani corridor bazaka taba cewa da dakuna a gurin ba steps ne kamar goma
suka haura sama Nan ma wani parlourn ne da two three bedrooms biyu suna kallon juna sai Daya daga
gefe.
"Masha Allah" Zahra ke fada a zuciyar ta tana mamakin gidan Wai wane irin gida ne wannan gari guda
compartment guda kawai ya hada irin wadannan mahaukatan falukan da bedrooms din Nan to yaya
sauran parts din suke?.
Dakin dake hannun hagu ta nufa ta bude, daga inda Zahra take ta hango wani Royal bed milk Mai azabar
kyau, Bata Kara gaskata maganar zilan ba Saida ta shiga ciki, a gefen bed din Zahra ta zauna tana fadin
"Bari na Dana gadon Aunty zilai".
Dariya sukayi su suka "kin gani ko wallahi nifa a jiya da kyar nayi barci duk zulumi ya isheni ji nayi Ina
tsoron gidan yayi girma da yawa, na jinjinawa matar gidan".
"Wai Mai gidan Bai taba aure ba a gaba dai ze kawo matar".
Baki zilai ta Kama tana fadin "to shi wane irin kudi ke gareshi da ze Gina irin wannan gidan Yana
saurayinsa".
"Bani wayar Aunty zilai wannan hirar ba karewa zatayi ba kada lokaci ya kure yau daga Asibitin cikin gari
zamu gidan su oga Sameer na gaishe da mommy". Wayar ta Bata suka fito tare ta Kira Ammah suka gaisa
sun jima tana fada Mata abubuwan da akayi mata jiya da Kuma komawar da zasuyi yau, karfafa Mata
gwiwa itama Ammar tayi tana fada mata ta kwantar da hankalinta In Sha Allah ba komai.
Lokacin da suka fito har Iya Rahane ta shirya table din Rukayya ma ta fito.
Kallon su Rukayyar takeyi ganin daga bangaren da suka fito.
"Aunty Rukayya Ina kwana?"
Zahra ta fada.
",Lafiya kalau matar big bro, ya Naga kin fito daga bangaren mu".
"Au kema a can Kika zauna kika ki zama a dayan dakin kusa Dani".
Baki ta bade tana kallon Zahra. "Na shiga dakin Mai gidan na zauna tab ai wannan part din sai ku".
"Mu suwa daga zuwa bakunta sai mu zaqe Ina laifin can din wallahi transfer zanyi, Ina dalili Ni kadai kamar
mayya kufa Nan ku uku ko ihun neman taimako kayi an taimaka maka amman Ni kuwa ko kasheni za'ayi sai
dai a dauki gawar da safe".
"Tab wallahi ba inda Zaki zauna a Nan ba haka big bro yace ba,a can yace ki zauna Dan haka Babu Mai
canza wannan Umarnin".
Dan turo Baki tayi "Ni na taba ganin haka mutum ya ringa saka doka a gidan mutane inaga baisan girman
gidan ba shi yasa yake bada wannan Umarnin, gaskiya da sake".
Time Rukayya ta duba a waya kizo muyi break yanzu zakiga ya Sameer yazo tunda da wuri za'ayi Miki
sauran gwajin".
Suna cikin break din Sameer yazo Saida ya jira a mota suka Gama sannan suka tafi, a ANC department suka
samu doctor Haseenar sun awon ciki.
Ba yabo ba fallasa ta tarbesu ba kamar jiya ba ko yanda suka ringa Yi jiya da Rukayya yau ba haka bane
daga gaisawa Bata Kara cewa komai ba, itama Zahra saita Kama kanta Rukayyar ma haka. Gwajin jini ta
Kara tura Zahrar ta hadasu da wata ma'aikaciyar su ta rakasu main lab aka dauki jinin.
Lokacin da suka dawo sun Gama ante-natal din gwajin jira ta dauko da scanning din ta Kira Sameer tana
fadin mu hadu a office dina".
Ta kashe tana fadin Bismillah Ruky muje office dina tunda mun Gama da Ante-natal sai zuwa anjima zamu
Fara gyne".
A kofar office din suka samu Sameer din ya rigasu zuwa.
Sai da suka zauna sannan suka gaisa da Sameer din, bayani ta farayi Masa na gwaje-gwajen jinin jiya "a
cikin jininta ba wata cuta ko kadan kawai scanning ne ya nuna Mana akwai matsala a mahaifarta ta fibroid
amman be wani girma sosai ba za'ayi aiki a cire mata tun kafin ya girma Amma zamuyi admitting dinta
zuwa one week tana karbar magani kafin ayi surgery din, Dan haka sai ta Kira mijinta ta fada masa yazo da
mutane muna son jini leda biyu, zamu jira results din Nan ya fito total blood count za'ayi Mata".
Rukayya ce tayi farat ta tambayi doctor Haseenar "yanzu dole sai tiyata baza'a iya Shan magani ba a
warke?"
Kallon tsab Dr Haseenar tayi Mata kafin tace "hanya mafi saukin rabuwa dashi ta sai dai aikin gaskiya".
Tunda doctor Haseena ta Fara bayani gaban Zahra ya yanke ya Fadi idan da abinda taki jini a rayuwar
duniyar Nan to tiyata ce.
Nisawa Sameer yayi kafin ya samu karfin halin fadin.
"Thank you so much doctor kome kenan zakiji idan munyi communicating da mijinta saina kiraki later"
"Ok.ba damuwa Allah ya sauwaqe".
"Amin".
Rukayya ta fada Dan zahra ba bakin magana har suka shiga mota tana cikin tashin hankali, kuka takeyi irin
na zuci din Nan sai dai hawaye kamar an bude famfo.
Saida suka fita daga Asibitin har sun shiga court road sannan Sameer ya Dan juyo, Madam kiyi hakuri in
Sha Allah ba wata matsala idan Allah yasa yin surgery din ne yafi Alkhairi ayi kawai Kinga kema saiki huta
da zulumin ciwo duk wata".
Rukayya ce juyo tana fadin "gaskiya kada ki yarda a yanka ki haka kawai Ni banma yarda da maganar
Haseena ba, kawai ta jawo Miki wahala Ni Daman da anyi shawara Dani da Babu abinda zesa Haseena ta
duba matar big bro haka kawai taje ta jawo Mata matsala da gangan bakaga yau sai wani share mutane
takeyi ba, wani ya Hana big bro din ya aure ta".
Wata uwar harara Sameer ya zubawa Rukayya "Billahillazi Zan saukeki a Nan ke wace irin mutumce da
bakinki bashi da controlto me kikayi ke Nan? wannan ai shashanci ne keda Zaki kwantar Mata da
hankalinta shine Kika sokawa zancen wuqa".
Ita dai Zahra maganganun Rukayya sun daga Mata hankalin kenan da wata jikakkiya a tsakanin wannan
likitar da Mahmud.
Wallahi ko likitoci sun Kare wannan ba zata Kara dubata ba shi yasa Kennan jiya ta damu da sanin waye
mijinta da dangartakar ta da Mahmud.
Tunda Sameer ya yiwa Rukayya buyagi Bata kara magana ba har sukazo junction din gidan shatima. "Wai
yaushe mommy taje gidan Hajyr makwararin?".
"Dazu da safe na kaita Wai zasu karbi lefen mujahida".
"Ok Allah ya Sanya Alkhairi. Dan Allah ya Sameer Zan sayi alawar Madara idan ka tsallaka Zan kaiwa Hajiyar
makwarari".
"Kice dai Zaki saya bawai Zaki sayawa Hajiyar makwararin ba".
"Allah tana son shi sosai"
A kofar gidan Hajiyar yayi parking Babar mommy ce.
Da karadi Rukayya ta shigo gida yayin da Zahra da Sameerke biye da ita a baya, suna runfa ana hira da
kunnen Rukayya da 'ya'yan dangi da mommy masu karbar lefen basu Fara zuwa ba gaishe dasu yaran
sukayi suka fice, sukabar mommy kawai. Cikin nuna kulawar mommy ta kalli Rukayya dake gaba. "Ba dai
har kun gama da asibitin ba?"
" Mun Gama kin ganta Nan Wai doctor Haseena tace zata yankata tayi Mata tiyata Dan nace ban yarda da
ita ba shine ya Sameer yake ganin bekena".
Sallama Zahra tayi tana Dan tsugunnawa tana gaishe da mommy cikin muryarta Mai sanyi da nutsuwa da
Kuma alamun tasha kuka.
Mommy kallonta tayi tana fadin "Masha Allah tabarakalla sannu ya jikin naki?"
Da sauki sosai".
To Allah ya Kara lafiya naji Rukayyar na fadin tiyata za'ayi Miki".
"Eh haka suka fada"
Hajiyar makwararin ce ta fito tana fadin "wa nakeji kamar Rakiya a gidan nan waye ba lafiya naji ana
magana tiyata".
" Kin ganta Hajiya, matar Mahmud mutumin ki ce".
Mommy ta nuna zahra.
" Wai Amaryar ce? Sannu kinji menene ya sameki?"
Rukayya ce ta fada Mata.
Mommy ta kalla "Ni Zan hada Mata maganin wannan lalurar ba sai anyi Mata aiki ba, ki huta Rukayya ki
shiga Nan kurmi ki sawo min abin hada maganin a Nan na hada Mata insha Allah sai dai ya narke yabi jinin
al'ada.
"Amma gaskiya ba wanda ze yanka ta Kamar kabewa ku 'ya'yan zamani komai a yanka ta haka ne daji yake
shiga ai ta fama da rai idan yazo da karar kwana kiga an mutu, daina kuka, samiru kiwawo min mijin nata
na fada Masa da bakina Babu me yi Mata danyan aiki ko haihuwar fari Bata yi ba a jawo mata tsuguniya
mazan yanzu marasa hakuri".
Ta fada tana nufar uwar dakanta.
Ita dai mommy Shiru tayi Saida Hajiyar ta shige sannan ta dubi Rukayya "Wai Ke Sai yaushe hankali ze
Gama Miki jiki? Kinzo kin kwatsa zance gashi Nan kin tubzura Hajiya Mai hanata hada maganin Nan sai
Allah, itama Kuma Mai lalurar maimakon ki kwantar mata da hankalinta A'a tashin farko kin sokawa
zancen wuka, ai kin kyauta".
"Wallahi ba haka bane mommy Kinga dai muna good term da Haseena amma wallahi yau kamar ma Bata
taba gani na ba sai cin magani take yiwa mutane da dacin rai want ya Hana Ya Mahmud din ya aureta taga
yarinya ta gigice zatayi mata illa haka kawai".
Maficin dake kusa da ita Mommy ta jefawa Rukayya tana fadin fita ki bani guri tunda kin Zama babbar
kwabo kin tasa yarinya gaba kina fadar abinda be Dace ba".
Wata uwar harara Sameer ya saukewa Ruky ji yake kamar yayi Mata duka duk ta cakude lamarin tana
kokarin ta saka jinin yarinyar mutane ya hau, tun sassafe Mahmud ya Kira shi Yana fada Masa ya kira
Rukayya yace ta fadawa Zahra ta bude wayarta ya manta shaf sai fa yanzu ya tuna.
Wayarsa ce ta Fara ringing "shine ya kira" ya fadawa mommy.
"Ka dauka kayi Masa bayanin halin da ake ciki".
"Nasan Haseena ce ta fada Masa shine ya Kira yaji".
Wayar ya saka a speaker yanda zahrar ma zataji.
Bai jira komai ba ya Fara fadin "Sameer wace magana naji Haseena tana fada min? kada ka Bari su taba
min yarinyar nan Zan kaita inda ya Dace, naji tana fada min wasu nonsense wallahi idan na shigo saina
Bata Mata rai, ita harta isa ta fada min son ranta who is she? Yanzu ina ita zahran take? Tun jiya jikina ya
bani an samu problem wayar ta fa ta rufe ta Hana nayi magana da ita fa".
Tashi Sameer yayi tsam ya fita ya cire wayar daga speaker saboda kada yayi katobara.
"Gamu Nan a makwarari gidan Hajiya Zahrar sai kuka takeyi,ita Kuma Ruky sai tinzira ta take kada ta Bari a
yankata har Hajiyar makwarari taji tayi tsallen Albarka tace bata san wannan magana ba, ita zata hada
Mata maganin hausa Wanda ze narke ciwon, wallahi sun caza min kai har na rasa yanda zanyi da rigimar
Hajiyar, yanzu haka kasuwar kurmi zata aiki Rukayya ta sawo Mata mahadin maganin da zata hadawa
zahrar".
"Yanzu dai bazan Gane kome kake fada ba hadani da Zahrar muyi magana"
"Ok Bari na kira ta dakin mujahida Naga ba kowa a ciki ka kwantar Mata da hankali duk ta shiga damuwa
sosai sai kuka takeyi"
Rukayya dake zaune a tsakar gida ya yiwa nuni data Kira Zahra, lokacin da suka fito Yana tsaye suna ciga da
maganar.
Wayar ya Miko Mata ya nuna Mata dakin mujahida yayi nufi waje.
Tana shiga cikin dakin tana Jinsa Yana faman hello, hello tayi shiru karshe ma ta sakata wayar a flight mood
tayi kwanciyarta a katifar mujahadar tana goge hawaye.
"Me kake son fada min Kuma? naji komai me Za'ayi bazan zauna a garin Nan ba wallahi, gida Zan tafi
kuma idan ma ciwon ne ai Ina da inda za'ayi min maganin ba sai Nan ba, da gata na da komai na zauna sai
watangaririya nake yi Dani".AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
Page 41.
________Wani irin barci me nauyi yayi awon gaba da zahra, sai da Sameer ya shigo yace Rukayya ta duba
Masa Zahra oga ya Kira yace Masa da matsala.
Dakin Rukayya ta shiga ganin Zahrar tana barci ga wayar Ya Sameer a gefen ta, daukar wayar tayi tana
dubawa a airplane mode taga wayar 'yar dariya tayi tana fadin "good yarinya kinsan kanki kenan ai Ina
bayanki ki tsaya tsayin daka akan wannan mijin naki idanun Mata a kansa suke kinyi dai-dai wallahi".
Wayar ta cire daga flight mode din tayi waje da sauri tana fadin "gashi ya Sameer wallahi barci takeyi" .
Wayar ya Karba Yana dubawa gashi Nan a kunne take haka datar itama ba wani matsala.
Tsaki yayi kadan Yana fadin "duk nema suke su dagulamin lissafi wallahi har na rasa Yanda zanyi" .
Rukayya najinsa tayi Shiru haushinsa takeji tun buyagin da ya yi Mata dazu,waje ya juya ya fita Yana kokarin
Kiran waya.
Hajiyar makwarari ce ta fito daga daki da manyan tabarmin roba a hannu tana fadin "zo Nan Rakiya ki
shimfida su cikin baranda kafin mutane su Fara taruwa".
Zuburo Baki tayi "Allah ki daina fada min sunan nan ni sunana Rukayya haka a ringa batawa mutum suna".
Ta taso tana karbar tabarmin.
"Gidanku, nace Rakiya ba sunan ki bane, Kizo ki shiga kurmin ki karbo min masoro gurin Alhajin Baba nayi
na hadawa yarinyar Nan magani na Bata tun yau ta Fara amfani dashi ba'a bori da sanyin jiki".
Saida ta Gama shimfidar ta shiga gurin Hajiyar cikin falonta suna duba kayan da za'a bawa masu kawo
kefen robar da aka zuba chicken pepper ta bude tana fadin "bari na dauki Daya naji kamshin yayi min
Dadi".
"Ki rufe wannan gashi can a kitchen a waje ki diba harda snacks din duka, Amma ki Fara karbo Mata sakon
a kasuwar tukunna kuje da sadiya ta rakaki ku shiga a dai daita tunda ba nisa ga cunkoson cikin kasuwa
Kuma kinsan Sameer baze Baki motarsa ba, wadda mukazo da ita Kuma Aliyu yayi nasa gurin da ita".
Basu dauki minti talatin ba suka dawo da sakon har lokacin Zahra barci take sai da jama'a sun Fara taruwa
a gidan duk dangi need sai dai-daikun Yan uwan mahaifar mujahidar.
A blender hajiyar taba mommy ta nika Mata masoron ta juyo mata shi a cikin robar da Hajiyar ta bada a
zuba a ciki.
Lokacin da mommy ta kawo Mata Hajiyar da kanta ta nufi dakin mujahidar tana fadin "Ina matar
Mahmudun take?.
Barcinta take sadidan Dan tabata Hajiyar tayi tana fadin. "Tashi 'yar nan ga maganin lalurar ki da izinin
Allah".
Tashi zahrar tayi tana bin Hajiyar da kallo lokacin data aje robar kusa da ita.
"Bude ki gani sai nayi Miki bayanin yanda za'ayi dashi".
Batayi musu ba ta bude robar taga garin masoron.
"Kina jina? Abinda za'ayi dashi ki ringa diba Kashi Daya bisa hudu na karamin cokalin shayi kina zubawa a
ruwab zafi tafasashshe cikin kofin ok ki barshi yayi minti ashirin a ciki sai ki tace ki Shanye ruwan,haka Zaki
ringa yi har ya Kare in Sha Allah ze narke yabi jinin al'adarki ya fice, ki rabu da wannan shirmen komai ace
za'a yanka mutum kamar kabewa"
'yar dariya Zahra tayi tana fadin in Sha Allah zanyi na gode madallah Allah ya saka da Alkhairi".
"Allahumma Amin. Allah ya Baki lafiya,ayi ta hakuri irin mijinki Mata Ido rufe suke nemansu sai kin kauda
Kai zakiçi ribar zaman aurenki. Amma kada ki kuskura ki yarda a nuna Miki San iyawa akan mijinki, ki kula
da sukarki Bata da damuwa ko kalilan ki girmama Masa danginsa da kakarsa jiya ya wannan suna gidan
Nan sunzo ganin Mai sunan mijinki na wurin Sameeru, Ni cewa nake can wurinku zasu sauka ma sai naji
Sameeru na maganar su fito zasu koma a jiyan kinsan sha'anin tafiyar iska, ba wani nisa ke gareta ba".
Ita dai Zahra Jin Hajiyar take Dan ba komai ta fashimta ba.
Rukayya ce ta shigo da Abinci dasu snacks a babban tray tana fadin " Ai tunda naji shiru Hajiya Baki fito ba
nasan kin hanata barci kawai wallahi ke idan Kika so Abu ba sauki saina Allah idan kinyi hakuri zata tashi ki
bata".
"Ke tafi can waya fada Miki ana bori da sanyin jiki Baki San hadarin wannan abun bane baya barin haihuwa
fa ba dole a tari abun ba tunda wuri, wannan yarinya tubarakallah haka ai ba'aso a samu abinda ze kawo
Mata cikas a zaman aurenta ba, ni tunda na ganta ta kwanta min har maganin tsarin jiki Zan karbo mata a
Sanka, nan babban gida".
Baki Rukayya ta rike tana kakabin Abun "Ikon Allah to ke Hajiya fada Miki tayi tana son na tsarin jikin? Da
kike faman fadin Zaki karbo Mata".
Kafin Hajiyar ta Kara magana Zahra ta rigata.
"Haba Aunty Rukayya Ina laifin Hajiya kuwa tunda na sako Qafa gidan Nan Bata huta ba hidimata takeyi".
"Eh haka ne kam tunda har kasuwar kurmi ta aikeni, da girnana da komai nace bazanj ba tace nayi mata
kiwa dan rabon da naje cikin kurmi tun Ina secondary Dan ma ban manta shogon ba"
Ficewa Hajiyar tana fadin kyaji dashi idan Kaya ne".
Tashi zahrar tayi tana fadin Bari na dawo, ta fice daga dakin.
Toilet ta shiga ta Kara gyara Kanta, lokacin data fito dai dai lokacin masu kawo lefen suka karaso suma Nan
da nan gudan ya dauki jama'a Dan makota ma Wanda suka makara suka ringa shigowa.
Ganin gidan ya kacame da jama'a yasa Zahra tayi amfani da wannan damar ta nufi hanyar soron gidan, a
soron ta tsaya ta Ciro wani face mask da yake cikin jakar ta da eyeglasses dinta ta saka ta fice daga gidan.
Ba Bata lokaci tana fita Dan sahu Yana kawo Kai, ta dafe shi ta shige, tana fadin "Janbulo zaka Kaini".
"Hajiya sai dai drop gaskiya Dan hanyar ta baude ni rimi na nufa".
"Muje Zan baka kudin drop din".
Ta fada tana Dan leken gefenta kamar narar gaskiya, hankalinta be kwanta ba sai da taga sunyi nisa da
unguwar, ajiyar zuciya ta sauke tana "na barka da Dr Sai ku cinye kanku haka kawai za'a sabautani saboda
Kai,Wanda har yanzu bansan daga wace bahiyar ka bullo ba, ayi min sakiyar da Babu ruwa a cuceni a cuci
rayuwata shi yasa na taho da hirina idan tayi ruwa rijiya idan batayi ba ta Zama Masai"
Kafin su karasa layin su Ssjida tacewa Mai adaidaita din ya taya gurin me P. O.S zata ciri kudi.
Har kiofar gate din gidan ya kaita 10k ta bashi, cikin mamaki ya dubeta "Hajiya kudin sunyi over dari
bakwai ne kudin, Hala ke bakuwa ce?"
Gaga tayi Tana fadin na sani kaje kawai nagode Allah ya tsare".
"Na gode Allah ya rufa asiri ya kara Miki daukaka".
Tana tafiya tana fadin. "Allahumma Amin".
Ta shige gidan shi Kuma ya juya Kan mashin dinsa ya wuce Yana Fadin "Bari na koma na sallami gidan sai na
Kara fitowa".
***********
Bayan tafiyar masu kawo lefen an baje anata kallon kayan arzikin da suka kawo Masha Allah kayansu sunyi
kyau sosai Dan akwatuna set hudu suka kawo da manyan jakunkuna uku har da adudu biyu.
Saida komai ya lafa sannan hankalin Rukayya ya dawo jikinta ta shiga neman zahra, abin mamaki ba zahra
ba alamarta Abu kamar Wasa ya Zama gaske Nan da Nan tashin hankali ya wanzu a gidan Dan mantawa
akayi da murnar wani lefe Nan da Nan Rukayya ta Fara share hawaye.
Mommy ce ta Farayi Mata fada "Haba Rukayya menene haka Zahra Karamar yarinya ce ku shiga makota
Mana ko taron jama'a ne bataso ta shiga can ta zauna ba kince toilet tace Miki zata shiga ba? Kafin ta fito
Kuma bakin sun shigo?"
"Eh haka ne Amma Naga fitowarta harta tsaya a can daga Nan mutane sukayi yawa ban sake ganinta ba".
"Ke Zubaida maza ku shiga gidajen kusa ku duba ko can ta shiga ku kirawota".
"To mommy". Ta fada sukayi waje su uku.
Hajiyar makwarari kuwa cewa take "Ina yarinyar nan ta shiga ko masu kawo kayan tabi suka tafi".
Wani kallo Rukayya tayi Mata "kaji Hajiya da wani zance kamar wata 'yar baby ce zahrar da zatabi wasu
mutane".
"Ungo Nan".
Abu kamar Wasa karamar magana tana neman Zama babba, duk kukkuken babu it's Babu dalilinta komai
Kama da Zahra Babu.
Mommy da Kanta ta Kira Sameer tace duk inda yake yazo yanzu tana son ganinsa.
Daman ba nusa yayi ba Yana tare da abokansa na unguwar Dan a hannun Hajiyar ya girma harya Gama
secondary school dinsa.
A tsakar gida ya samu su mommy anyi cirko-cirko.
"Gani mommy lafiya na ganku haka?".
Hajiya ce ta Fara fadar "Ina fa lafiya ba'aga matar Mahmudu ba har makota anbi baku ko alamarta".
Mommy ya kalla. "Kamar ya ba'a ganta ba? To Ina ta shiga?"
"Allahu A'alam, da farko abin ban dauke shi haka ba sai yanzu da naga da gaske ne yasa nace Bari na Kira
ka".
"Ok, Bari naje Nan Ina zuwa"
Ya juya ya fice da sauri, cikin tashin hankali me ze fadawa Mijinta Ina ta tafi?.
Tambayar mutanen kusa masu sana'a a kofar gidan ya rinka yi, har ya juya sai wani Mai sayar da Mai yace
yaga fitowarta da face mask da glass a Ido ta hau a dai- daita sahu sunyi hanyar nan ya nuna hanyar gidan
shatema.
Dafe Kai yayi cikin tashin hankali, "wannan wace irin masifa ce haka kawai an tadawa yarinya hankali har ta
yanke Shawarar tayi tafiyar ta, to tana Ina? Ina ta tafi? Ba wani ta sani a garin Nan ba ga Babu waya a
hannunta, Saida ya fada masa ya fito Mata a mutum sak a wuce wannan wasan yaran ya kaita inda ya Dace
a duba Masa ita amma ya gano ya yiwa Haseena waya ta a duba Masa ita yasan karshen film din ba Mai
kyau bane"
Jiki ba kwari ya koma ciki..
Hankalin Zahra be kwanta ba so sai Saida ta ganta a cikin falon gidan su Sajida, Mai aikinsu ta bude Mata
parlourn tana fadin "A'a marhabin maraba da Amarya sannu da zuwa".
Ta fada tana murmushi, tare suka shigo ciki.
"Yauwa Mama Hauwa sannu da gida, ya naji gidan naku Shiru ko su Mamar basa nan ne?"
"Wallahi sunje Rimin sumaila duba kanin Baffa bashi da lafiya,a nan ya kwanta a Asibitin Murtala to shine
sukaje su Kara duba shi da jikin".
"Allah sarki ko kawu Musa?"
"Shine Ashe kin sanshi".
Eh nasan shi Mana, har a gidansa mun kwana lokacin da mukaje da sajida. Allah ya bashi lafiya yasa kaffara
ne"..
"Allahumma Amin, Bari na bude Miki dakin mutuniyar ki shiga na kawo Miki abinci can, inaga sai dare zasu
dawo tunda suka Kai har wannan lokacin".
Wanka ta shiga ta Dade a toilet din kafin ta fito tana tsane jikinta da towel, lotion ta shafa ta dauko Rigar
material marar nauyi ta saka a cikin kayan sajida.
Jallop din kuskus aka kawo Mata wadda Tasha kayan lambu da pepper soup na kayan ciki da kunun aya
Mai sanyi da ruwa.
Abincin taci ta koshi ta dora da kayan sanyi tayi hamdala ga Allah ta kishingida jinta take fresh idan Allah ya
kaimu safiya ta karawa motarta Mai, ganinta a araha yasa ake garata kamar kwallo.AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH
Page 42.
_______Abu kamar Wasa har kusan karfe taran dare ba zahra ba labarinta, iya Rahane mommy ta Kira
tana tambayarta kosu Rukayya sun dawo? Dan bazata fada ba direct tace ana neman zahrar hakan dabara
ce ta tambaya a fakaice.
Amsar data Bata ita ta Kara tadawa kowa hankali cewa tayi "Basu dawo ba tun fitar safe da sukayi ga zulai
ma duk ta shiga damuwa tace tun yamma Ammarta ke Kiran wayar zilan tace wayar zahara'un Bata shiga".
"Yanzu ya za'ayi kenan?"
Rukayya ta tambaya.
"Ni damuwa ta Daya kada ta fada mugun hannu Dan ma dai ba lallai ansan matar waye ba Amma yau abin
tsoro ce kiransa zanyi kawai na fada Masa halin da ake ciki ko yasan wasu 'yan uwansu a nan kanon, tunda
barin Kashi a ciki baya maganin yunwa gara ya fada kawai asan Yanda za'ayi tun guri be kure ba.
Number dinsa yayi ta try Amma amsar Daya ce a rufe take.
Da kyar ya mayar dasu mommy gida har Rukayya a gidansu ta sauka, to ta koma tacewa baiwar Allah da
sukazo tare zahrar ta Bata ko me?"
Duk wani lissafi ya gama suncewa Sameer, duk wannan Abu be tashi faruwa ba Saida sukazo gidan kakarsa,
ita kanta Hajiyar makwararin tashi Dan kukanta tana mitar yarinyar Nan Bata kyauta Mata ba ta rasa a inda
zatayi irin wannan shegantakar sai a gidanta.
Jiki ba kwari Sameer ya shiga gidansa, sau Daya Fateeha ta kalleshi ta dauke Kai ta cika fam da fushi tun
safe Daya fice Bata Kara sakashi a idanunta ba, ta kirawo shi ya Kai sau biyar sai dai yace Mata gashi Nan
Amma bezo ba sai yanzu wurin Sha dayan dare.
A kusa da ita ya zauna ta kauda Kai, hannu yasa ya dauki yaron a Kan cinyarta, yasa hannu Daya ya
tallabota ta hada da babyn ya rungumesu, Jin ajiyar zuciyar da yake saukewa a jajjere yasa Fateeha ta gane
da matsala.
"Wai menene?"
Ta fada cikin damuwa.
"Bari kawai wlh hankalina a tashe yake, tun bayan Azzahar Zahra ta fice daga gidan Hajiyar makwarari
bamu San inda ta nufa ba, duk inda muke tunanin zataje munje Bata nan".
Itama mantawa tayi da fushin da takeyi dashi ta Fara sallallami "Yanzu Ina ta tafi? Kadafa wani Abu ya
sameta kasan mutane yanzu gaskiyar su kadan ce".
Dafe kansa da yake Sara Masa yayi "Bana tunanin haka gaskiya da Kanta ta fita ta tafi kawai dai an Bata
Mata Rai ne ban Kuma yi tunanin abin yayi Mata zafi haka ba da bazan barta a gidan Hajiyar ba, amfani tayi
da masu kawo lefen mujahida ana can gurin karbar lefe ita Kuma ta fice daga gidan Dan akwai Wanda ya
fada min Yanda ta fito nasan da niyya ta fice abunta".
Zuru Fateeha tayi tana sauraren mijinta.
"Ka Kira ka fada masa?"
Kai ya girgiza Yana fadin na kasa samunsa nafi one hour Ina nemansa ban same shi ba".
Saida Umman sajida tayi wanka tayi sallah sannan ta fito har lokacin suna falon da yaran direct dining ta
nufa taci abinci sannan ta dawo falon.
Gaisheta zahra ta Karayi tana tambayar ya Mai jikin,
Dasu Baffa.
Sun dauki lokaci suna hira kafin Ummar tace "Wai daga Ina kikazo ne daga can Azaren ne ko Kuma kinzo
nan garin ne?"
Shiru zahrar tayi kafin tace "ganin likita nazo akan wannan ciwon marar da bakeyi duk wata".
"Ikon Allah kuma ke kadai Kika taho ganin likitan kamar marar gata".
"A'a bani kadai nazo ba tare da Aunty Zilai Mai aikin Ammah mukazo tana can a Nasarawa G.R.A".
"Ok, to mryasa baku taho tare ba Nan din".
Shiru tayi Bata ce komai ba, ganin da Yara yasa itama ummar tabar zancen.
Kafin kowa ya tashi Zahra ta tashi tana fadin "Umma Bari naje ba kwanta barci nakeji"
"To Allah ya tashemu lafiya.
Basu Dade ba Suma suka shige daki Daman duk sun gaji.
Lokacin da Ammah ta shiga dakin Abban samun Mama tayi kane -kane tana ta zuba zance da kudi a
hannunta masu Dan yawa da gani a gurin Abban ta Karba, cikin alamun rashin gaskiya mamar ta Fara fadin.
"Aina leka parlourn ki naji Shiru nayi zaton kina Nan wallahi Ashe Baki shigo ba"
Fuska ba annuri Ammah tace. "Eh ban shigo ba idan kin gama na dawo ta juya har Takai kofar ficewa
Abban yayi gyaran murya Yana fadin "dawo ki zauna Ina Kuma Zaki ita ta tashi ta tafi tunda ta gama abinda
ya kawo ta"
Jiki ba kwari Mama ta tashi tana fadin "ai Kam na Gama Allah ya tashemu lafiya nagode Allah ya Kara
arziki".
Ta nufi inda Ammah ke tsaye tana fadin "mu kwana lafiya ki tayani yiwa Abban yara godiyar abin arzikin
Daya bawa Najjahi na kudin registration".
"Masha Allah! An gode Allah ya bada sa'a".
Ta fada fuskar ta Babu walwala ko alama, da gaske ta kule Abun Yana so ya Zama rainin hankali tayi
noticing dinta duk ranar girkinta sai ta dunga Karakaina a part din Abban Amma idan tasan wata ai Bata
San wata ba.
Dawowa tayi ta zauna kusa dashi "meya Bata Miki Rai ne Kika juya Zaki bar dakin?"
"Ba komai".
Ta Bashi amsar in short.
Haka Nan yabar zancen badan ya gamsu da abinda ya fada ba.
"Neman izinika na shigo zanje Kano gobe in Sha Allah"..
Saida ya Kare Mata kallo tsab sannan yace. "me akeyi a kanon da zakije?"
Kai ta girgiza ba komai zanje barka ne na yaron nan Sameer ranar da yazo daukar su Zahra yake fadawa
magaji anyi Masa haihuwa an samu takwaran mijin Zahra".
"Kai Masha Allah, ai ban sani ba da nayi Masa barka ranar da yazo".
Tashi tayi zata fice Abban ya mayar da ita "Wai me yake faruwa ne Naga ranki a bace tun shigowar ki".
"Ba komai zanje na dawo ne yanzu in Sha Allah".
Ta Mike ta nufi kifar ficewa, haka Nan yayi Shiru badan ya yarda da ba yasan da abinda yake damunta taqi
fada Masa ne kawai".
Ammah na shiga part dinta ta Kirawo Abdul Hakeem, lokacin Yana kofar masallaci tare da Habib.
A parlour ya samu Ammar ta zuba tagumi.
Saida yayi sallama biyu sannan taji.
"Wa'alaika Salam".
Ta fada tana kallon Abdul Hakeem din, kusa da ita ya zauna Yana fadin "lafiya kuwa Ammah Ina sallama
bakya jina?"
Ajiyar zuciya ta sauke tana fadin "yanzu ba dadewa Umman Sajida ta kirani waiga zahra taje Mata zata
kwana a can Kuma ita kadai ba tare da zilai ba, na Kira zilan tace min tun fitar safe Basu dawo ba har
dazun, ka Kira Sameer kaji shin yasan da tafiyar ko Kuma wani Abu ya faru tayi musu yqji nasan halin
kayana zatayi abinda yafi haka ma in dai zahra ce, Dan haka ka kwana da Shirin Kano sakko zamuyi ko
Abban KU ban fada Masa wannan maganar ba ina tsoron ta fito duk da nasan ba lallai ta fito din ba amma
sha'anin mace da miji sai Allah"
"Allah ya rufa asiri".
Abdul Hakeem ya fada Yana Kiran Sameer duk da lokacin ya ja Sha Daya ta gota.
Ringing Daya saneer ya daga kafin Abdul Hakeem ya Fara magana Sameer ya rigashi Dan ko sallama Babu
ya Fara fadin "Abdul Hakeem zahrar tazo Nan ne?.
"Easy my man! Tana Nan Kanon a Janbulu gidansu Sajida, yanzu Umman su sajidar ta Kira Ammah ta fada
Mata saboda hankalin ta be kwanta da ganin zahrar ba duka yaushe akayi Abu da zata wani zo yawon
ziyara tasan da wata a kasa, shine ta Kira zilai ta fada Mata tun fitar safe baku dawo ba".
Ajiyar zuciya ya sauke, sai Yanzu ya samu nutsuwa dan Yanzu suka gama wayar da mommy akan ko akwai
wani cigaba? Yace Mata Babu Kuma tun lokacin da abun ya faru yake ta kokarin ya Sami Mahmud Abun ya
faskara.
"Na gode kwarai Abdul wallahi muna nan hankalin mu a tashe tun bayan Azzahar muke Abu Daya, Dan
Allah kayi min godiya gurin Ammah, kace Kuma tayi hakuri ba sai tazo ba Dan Allah ga mommy ta Isa tayi
komai ka fada Mata laifi akayi mata amma in Sha Allah hakan baze Kara faruwa ba wannan ma tsautsayi
ne".
Kai kawai Ammar ta gyadawa Abdul Hakeem ya gane me take nufi tunda handsfree ya saka wayar".
"To ba damuwa tace ayi maka godiya da kwaramniya"
"Ba komai yiwa Kaine ka turo min da address din gidan Yanzu na gode".
Sukayi sallama ta kashe Kiran Yana Maida hankalinsa a Kan Ammah.
"Ammah lokaci yayi daya kamata a zauna da Mahmud asan who's he? Aure ba Abun Wasa bane asan
asalinsa Kinga muna tare sosai wallahi be taba fada min asalinsa ba kawai dai nasan he's educated fiye da
tunanin mu badai ya nunwa ne kawai anyway kome Kenan dai kiyi abinda ya kamata kawai".
*** **** ***
Suna Gama waya Sameer ya lalubo Number Rukayya tana dauka yace ki fadawa mommy gani Nan zamuje
mu taho da Zahra tana janbulo gidansu friend dinta".
Bai jira tayi abinda zata fada ba ya katse Kiran ya saka jallabiya ya dauki key din motar yayi waje.
A kofar parlour ya tarar da Rukayya da Mommy.
Fitowa yayi yana fadawa mommy Yanda sukayi da Abdul Hakeem da Ammah.
"Dan Allah ki zauna mommy muje da ya Sameer kawai ana ganin mu dake za'a San ba lafiya ba Kinga ai
itama zato takeyi kawai muce Mata ya Mahmud ne ya dawo yace muzo mu taho da ita tinda da saura
lokaci".
"To shigo mu tafi tsari mistress".
Saida suka dauki titin rijiyar zakin sannan Sameer ya mikawa Rukayya wayar da address din da aka turo
Yana fadin " duba ki gani ko kinsan laying kune masu yawo lungu da sako na garin nan".
Dubawa tayi tana fadin " Nasan gurin layin gidan su saliha sani Musa ne tare mukayi Excel da ita".
Cikin ikon Allah suna tsayawa a kofar gate din motar ya Abba ta shigo shida Abie dinsu sun dawo daga
kwangwalam bodar NIGER inda sukaje gaisuwar mahaifar amininsa data rasu jiya, sun biya ta kazaure gurin
wani abokin aikinsa daya kwanta a Asibiti Shima a Nan sukayi dare.
Ganin mota a kofar gidan yasa Abie yace Abba ya tsaya yaje yaji ko lafiya Yana fita Mai gadi ma ya fito Yana
ganin Abba ya karasa gurin da sauri, fitowa Sameer yayi ya tarbesu Yana Mika musu hannu sukayi
musabaha Yana fadin "Ayi hakuri munzo cikin dare ba sanarwa,Daman munzo mu tafi da zahra ne tun
Rana tazo Bata Fadi zata kwana ba sai Yanzu mijinta ya dawo gashi ba waya a hannunta, ganin da sauran
daren yasa muka biyo samunta".
,"Ok. Ba damuwa muma Yanzu shigowar kenan munje unguwa tare muke da Abie".
"To mu karasa Mana na gaishe shi ya juya yabi bayansu suka nufi gurin Abie din, Rukayya gani tayi kamar
akwai rashin kyautawa ace tana kallo aje a gaishe da babban mutum tana zaune sai kawai ta fito ta rufa
musu baya.
Cikin girmamawa Sameer ya gaishe da Abie din sai Jin muryar Rukayya sukayi daga baya tana gaishe da
Abie din, hankalin Ya Abba biyu ya kasu ga wata murya data fizgeshi lokaci Daya ga Kuma bayanin da yake
yiwa Abie.
""Ba wani Abu Bari a Kirawo Umman tasu saita fada Mata ta fito wannan ai shashanci ne ya za'a bar
yarinya ta nemi gurin kwana da mijinta da komai".
Sameer ne ya Dan shafa Kai.
"Ayi hakuri Abie mijin ne baya Nan sai yanzu ba dadewa ya shigo kasar".
Mazaunin direba Abban ya koma suka nufi ciki tunda Daman Mai gadi ya bude gate Yana jiran su shigo.
A waya Abie ya Kira Umma har lokacin idanunta biyu da wuya tayi barci matukar tasan mijinta baya Nan da
sauri ta dauki wayar tana Masa sannu da zuwa.
"Yauwa ya amsa a takaice Yana fadin. "ki taso bakuwar da kikayi a gidan mijinta ya dawo gasu Nan a gate".
Ya kashe Yana nufar part dinsa.
Shiru tayi waye ya fada masa da bakuwar a gidan jiki ba kwari ta nufi dakin sajida, barci ta Samu tanayi
sadidan kamar Nan duniya Bata da damuwa Kota sisi dakin ta shigo tazo bakin gadon ta tsaya tana Kiran
sunan ta a hankali, tana fadin "tashi ki kimtsa ki fito ga Mai gidanki can zaku tafi gida". Idanun tadan zaro
tana fadin "wallahi bazani ba Umma kice musu bana nan
sai hawaye"..
MAMAN FATEEMAH.
Page 43.
_______ kuka zahra keyi ba kakkautawa a hankali Umman ta zauna kusa da ita, ki daina kukan Nan kiyi
hakuri ki tashi ku tafi, kiyi ta addu'a Allah ya kawo Miki saukin ko menene damuwar, kada ki Kara tunanin
yin irin haka idan Abu ya dameki ki tafi kibar gida ba shine maslaha ba kinji, tashi ki cire Rigar barcin ki
canza suna jiranki Kinga dare ya farayi inaga tun Rana suke bulayin nemanki sai Yanzu suka samu inda
kike".
Kai ta gyada tana goge hawayenta, Bata taba tunanin yau zata koma gidan Nan ba Dan ita a budget dinta
daga Nan gaba zatayi Dan kasar tayi niyyar tsallakewa tayi gaba abunta tunda passport dinta yana jaka, to
Wai ta Yaya suka gano tana gidan Nan Wama yasan gidan a cikinsu, to shi yaushe ya dawo?
Haka zuciyarta ta dunga sake-sake.
Fita Umma tayi ta Bata guri ta canza Kayan, jiki a mace ta fito ta iske Umma da Ya Abba a parlourn, gaishe
da Ya Abban tayi ya amsa Yana fadin "wallahi kin wahalar da mutane da wannan Daren Kika sakasu fitowa
har da mace Ina jinma mijinta ne"
.ita dai zahra Shiru tayi Masa ta nufi Hanyar fita daga parlourn tana fadin "ummah na tafi Saida safe".
Ta fada tana yin gaba "to Allah ya tashemu lafiya kiyi hakuri da safe idan Allah ya kaimu ki bude wayar
zamuyi magana".
"To Ummah in Sha Allah Zan bude". Suka fice daga Fallon. Ya Abban Yana biye da ita tun kafin ta karaso
Rukayya ta taho cikin sassarfa ta ringume Zahra tana fadin "wallahi kin dauki alhakina da Hajiyar
makwarari Kinga kukan da muka Sha yau? Tambayi Ya Sameer kiji duk kin tashi hankalin mu".
Wani sanyi ya ratsa Ya Abban Jin Rukayya ta ambaci Sameer da yayanta, daman Kuma yaga Kama ta zahiri
duk da dare ne Bai Hana shi ganin kamannin nasu ba.
Shiru zahrar tayi Mata ita sai Yanzu taji wata kunya duk ta rufeta, me kenan tayi? Shike Nan zasu dauka fa
tayi yaji ne dole ta magantu.
"Wai Dan Allah Aunty Rukayya ku kasa barina nayi kwana ko Daya ne a gurin Ummata nifa bada wata
manufa ba na taho kawai dai nasan idan nace zanzo ba Bari Oga sameer zeyi ba zece saina nemi izinin....."
Sai tayi Shiru.
"Izinin wa za'ace ki nema?".
Gaba tayi kawai ta nufi gurin da Sameer yake tsaye jikin kofar driver, da wannan damar Ya Abba yayi
amfani ya matso kusa da Rukayya yana fadin "Ashe Aunty tasha kuka zanso Naga kina matse hawaye".
Kallonsa tayi haka nan taji yayi Mata kwarjini.
'yar dariya tayi tana fadin "Ina yini?"
"Lafiya kalau beauty, ki saka min number ki Zan kira naji ya kukaje gida tunda sister Zahra har wayar tayiwa
tawaye".
Ya karasa Yana murmushi itama murmusawar tayi tana karbar wayar, number ta saka Masa ta Mika Masa
wayar tana fadin "bari na wuce ya Sameer Yana jirana"
Tayi gaba.
"Ok saina kira shima gurin Sameer din ya nufa sukayi sallama, ya leka ta window Yana yiwa Zahra magana.
Tunda suka dauki hanya ba Wanda ya Kara magana sai ajiyar zuciyar Zahra ke sauka kadan- kadan.
A hankali zahra ta bude Baki tace "Dan Allah oga sameer kayi hakuri na Bata maka Rai bada niyya nayi ba
kawai dai Ina son Naga Ummah ne Naga kuma kamar bazaka yarda naje na kwana ba".
"Ba komai kawai, Daman Yanda su mommy suka tada hankalin su ne ya daga min hankali nasan ba Bata
zakiyi ba tunda da kafarki Kika fice".
Shiru tayi tasan magana ce ya fada Mata a kaikaice, tasan a kule yake da ita kawai dai Batasan dalilin Daya
hana yayi Mata buyaji ba, Dan taga alama ya iya tijara Yanda ya karewa Rukayya dazu ko shi yasa taja
bakinta tayi shiru Yanzu.
Sha biyu da minti goma yayiwa Mai gadin gidan horn Saida ya leko shima Sameer din ya fito Yana ko waye
sannan ya bude.
Yana shiga da motar Maimakon yaje kofar main parlourn sai taga yabi ta baya ya nufi wani gani Mai azabar
kyau ko Ina tar kamar dauko ginin akayi aka aje ga wata 'yar baranda data hade ginin biyu an saka glass
anyi kamar katanga da wasu irin flowers masu kyau a jere ana ganinsu gurin yayi matukar kyau da burgewa
a kusa da steps din da ze sadaka da
Main parlour, Zahra ba tayi kokarin bude side din da take zaune ba, dan juyowa Sameer yayi "Dan Allah
kada maganar nan ta fita kawai da safe ki fada musu mun Dade a Asibitin ne yasa Kika bamu dawo da wuri
ba sun kulle, kiyi using da Nan kawai ki barsu su a can, Rukayya zata kawo Miki kayanki da safe kiyi idan
Allah ya kaimu".
"To nagode".
Abinda ta iya fada kenan, ta bude ta fita Rukayya man ta fito tana fadin " Bismillah kizo muje na rakaki".
Tare suka jera suka hau zuwa kofar, ita Kanta kofar abin kallo ce ita Yanzu zahra abin har ya daina Bata
mamaki so take taga iya gudun ruwan bayin Allah nan Kullum lamarin su ba baya yake ba gaba yakeyi daga
Nan sai can suna shiga ta Kara jinjina girman lamarin Wai shi wannan abokin nasu wane irin kusancin ne a
tsakanin su da za'a dunga sauke ta a duk inda akayi ra'ayi. Wannan part din yafi wancan komai parlour sun
Kai hudu, a cikin parlour na uku ne suka taka steps ya Kai shida sannan suka shige want korido ko Ina tadal
sai wani special kamshi ke tashi bedrooms ne guda biyu a jere, Rukayyar ce ta Dan juyo tana murmushi "to
madam gasu Nan saiki shiga Wanda kike so ki kwanta, tunda kin samu muna yawon dare kamar marasa
gaskiya, Zan Baki shawara sai kin Zama jaruma fa a gidanki Dan Ya Mahmud wallahi Mata rubibinsa suke,
idan kikace Abu kadan Zaki fece kece ki tafi kece a kwana Dan idan yayi wata tafiyar sai ki kwana hamsin
Baki saka shi a idonki ba, pls you have to be very strong gaskiya kada ki yarda a gano Ina kike da lapse
akwai damuwa kwarai ki rike mijinki da kyau ki mutunta shi ki girmama iyayensa zakiji dadin Zama dashi in
Sha Allah, zabi na rakaki dakin na wuce barci Kuma nakeji tunda Allah yayi Mana gyadar dogo ya rabamu
da kwanan zaune to matar big bro ta Bata Ina Ni Ina barci ai sai kwana sallah".
Ta fada tana 'yar dariya.
"Ki sakani kowanne Wanda za'a sanwa ya taba cewa way gutsiri nan? Duka zaman na yau zuwa gobe ne
Dan gida zamu koma bana son wani surgery a Nan idan ma yimin din za'ayi ba wannan Mai fuska kamar
Jan karas din zatayi min ba muma muna da qualified a can Dan dai kada nayi musu dashi ne kawai".
"Kinga mu Shiga na koma dare Karayi yakeyi gara naje na kishingida".
Dakin da yake facing dinsu ta bude MashaAllah" ta fada Tana karewa dakin kallo sannan ta juyo tana fadin
mu kwana lafiya"
Kallonta Zahra keyi tana son tayi Mata tambaya Amma ta rasa ta Ina zata Fara, Dan Yanda tasan gudan Nan
da Yanda take fadar wasu abubuwan akan Mahmud ga Kuma abinda Hajiya kakarsu ta fada Mata dazu
maganganun suna kamanceceniya da juna amma Bari ta Adana tambayoyinta da sauran lokaci.
"Nagode Aunty sai da safe, Amma fa Ina Jin tsoron gurin nan fiye da can din wallahi, Kinga Nan ba kowa.
Allah mu kwana tare ko kin tafi bazan iya barci ba".
Dan Jim tayi tana tunani ita Kanta Bata San dalilin Ya sameer na kawota Nan ba, amma tasan dole da
dalilinsa nayin hakan.
"Ok ba damuwa Bari naje na dauko sleeping dress Dina da naki saina dawo"
"Ok, yauwa Aunty ki taho min da phone Dina tana cikin bedside".
Ta nufi Hanyar fita, wayarta ce ta dauki ringing number ce tasan Wanda ya Karba ne dazu a ta daga da
sallama suka Kara gaisawa ya tambaye ta ya suka zo gida ta fada masa lafiya kalau sukayi sallama ta fice.
Kofar ta rufe ta farko tayi gaba tana fadin "kamar wata Rukayyar mahaukata na shigo wannan part din na
kwanta a can ma naki kwana ballentana a Nan yarinya Allah ya kawo mijinki ki tarairayi kayanki kuna gefe
Naga alama sai nayi Mata budedden karatu sannan zata gane mace har Mace ta fita kunya Amma ki tsaya
kina Wasa da damarki".
Ta wannan barandar Mai glass ta Shiga Daya part din da yake tasan wanancin lambobin kofofin tunda duk
sati suke zuwa da sauran yaran gidansu suna gyara bedrooms din kawai sauran Kuma da masu aikin da
sukeyi dakunan kwanan ne dai Batasan dalili ba masu aiki basa shiga.
Ko Ina tsit a gidan baka Jin komai sai kukan kananun kwari da dai daikun tsuntsaye ta gefen inda zahrar ta
kwana ta wuce da gaske ko ita data Saba da Shiga gidan wani lokacin tsoron Yana kamata bare a irin Nan
da sauri ta shige parlourn na uku ta wuce corridor da za sadata da dakunan.
Tana bude dakin zilai ta bude ta fito tana fadin "sannunku da dawowa, Dan Allah lafiya kuwa tun rana sai
Yanzu sha biyu ta wuce?'.
"Lah ba wani damuwa munje unguwa ne motar ta samu matsala sai dazu muka shigo garin muka biya
gidan mommy a can muka Shantake Sai Yanzu ya Sameer ya kawo mu".
Wani sanyi zilai taji a ranta, "to ai shikenan Allah huta gajiya da ko barci na kasayi ina ta tunani barkatai".
"Kai haba ba komai Allah ya tashe mu lafiya ta bude kofar ta shige itama Zilan ta Koma ciki.
Tun bayan fitar Rukayya zahra ta dosana gefen ta zauna ta zabga uban tagumi, da sauri tashi ta fito ta
dauko handbag dinta ta biyo Hanyar da suka shigo kofar fitar ta murda tajita bam ko motsi batayi, tayi tayi
taji kamar tana taba dutse, hakuri tayi ta juya sai lokacin tsoron ya rufeta da gudu ta shige dakin tana turo
kofar, dube-duben makulli kofar ta Farayi ita dai bataga gurin wani key ba har zata hakura taga wasu
numbers a jikin wani Abu kamar switch din kunna wuta numbers din ta Danna Yanda suke a jere taba taba
ta karshe taji want Dan sound daga jikin kofar handle din ta Kama zata bude taji ta rufe gam, sai lokacin ta
Dan samu peace of mind, ta nufi gadon ta aje jakar a gefe ta nufi toilet dole saita sake gyara jikinta. Tana
Shiga ta cire rogar material din sajida data sako ta taho da ita ruwan zafi ta hada tayi wanka ta fito da towel
a jikinta sanin ba wasu kayan sakawa a Nan yasa ta Haye gadon daga ita sai towel ta rage hasken dakin ta
janyo lallausan bargo ta rufe jikinta sai fuskar kawai ta Bari a hankali ta Fara Addu'oin kwanciya barci, kafin
ta Gama barcin yayi awon gaba da ita.
Karfe Daya da rabi daidai jirgin Max air ya sauka da duban jama'a daga kasahe daban daban na duniya,
cikinsu harda Muhmud Muhammad Dange, a hankali yake tako stairs din jirgin sanye yake da kananun
Kaya Ash T- shirt da black jeans a jikinsa sai jakar laptop dinsa a kafadarsa.
Yana karasa saukowa wani matashi fari marar jiki ya nufe shi Yana fadin "barka da sauka yallabai, ga key din
motar Nan a hannunta oga yace na kaika gida, sai Balarabe ya bimu da wata motar sai mu dawo tare
dashi".
Hannu ya mikawa Mai bayanin Yana fadin "bani key din kawai kace masa na gode kwarai da kulawasa,
zanyi driving da kaina".
Mika masa Yana fadin "Allah ya tashemu lafiya kayi min godiya sosai ya Ciro kudin America ya mika Masa
sannan ya bar gurin.
Lokacin Daya fito daga airport din Daya da minti ashirin da bakwai, tuki yake cikin nutsuwa sau biyu kawai
ma'aikata suka tsayar dashi, har yazo gate din gidan ba Wanda ya Kara tsayar dashi, sau Daya yayi Horn
Mai gadin ya falfalo da gudu yana leken waye a Nan baisan motar ba Dan haka ya koma ya dauko abinda ze
Bashi kariya.
Kafin ya bude ya fito, Mahmud ya fito ya harde hannusa a kirjinsa ai Mai gadin Yana ganinsa yayi sauri ya
koma da gudu Yana Fadin "barka da sauka fari Mai farar Aniya Allah ya Kare gabanka da bayanka baya Mai
goya marayu"
Dan murmusawar Mahmud yayi Yana fadin "wani Abu sai Malam Musa shi Babu ruwansa da dare". Ya fada
Yana kunna Kai harabar gidan wadda take kamar rana, mutane hudu ne suka bullo daga mabambantan
gurare. Parking lot suka nufa sun San Mai gidan ne tunda suka jiyo hargagin Malam Musa. Shima da gudu
ya karaso gurinsa Yana cigaba da Yi Masa kirari.
Sun gaisa sosai dasu har kusan minti biyar sannan yayi musu sallama Saida safe ya nufi babban part din,
Murtala ne yayi sauri ya sameshi "yallabai Ina ganin madam din kamar tana can sabon gurin can Dan Nan
Naga Sameer ya ajesu dazu ita da Rukayya kanwarsa, can ya nufa Yana mamakin me yasa Sameer ya kaita
can alhalin yace a barta a tsohon part din.
MAMAN FATEEMAH.
Page 44
_________ kamshinta ya Faraji Yana shigowa parlourn, wani limshe idanu yayi Yana ayyana abubuwa da
yawa a ransa, direct ya wuce bangaren bedrooms din Yana jinsa cikin nishadi, wato Sameer Yana expecting
dinsa ne a kasar shi yasa ya bude Mata nan kenan, a hankali ya taba handle din kofar farko ya jita a bude
Shiga yayi komai tsab, iska ya huro daga Bakinsa ya aje jakar laptop dinsa a Kan sofa da take dakin, ya
zauna a gefe Yana cire takalman kafarsa, wanka yake son ya Fara kafin ya Shiga gurin waccen danger girl
din "yar yarinya ta Hana shi sakat duk ta birkita Masa Lissafi" ya fada a fili Yana rage kayan jikinsa.
Wanka ya shiga bai wani dauki dogon lokaci ba ya fito saboda dare ya Fara nisa ga gajiyar zaman guri daya,
pyjamas ya saka masu kalar sky-blue ya fesa turarensa ya dauki wayoyinsa ya fice daga dakin ya nufi dakin
da zahrar take, wani Abu ya taba mai Kama da socket din electric na kunna wuta sai kofar ta bude,a hankali
ya shige Yana Jin kamshinta yanda ya cika dakin, shi dai yawanci duk matan da suka zamar Masa dolensa
suna bala'in son kamshi, yana ida shigowa kofar ta rufe Kanta Wai Abu ya taba ba Wanda zahra ta taba ba,
yayi gaba Yana nufar gadon inda ya hangeta ta kudundune cikin bargo, da gani a tsorace tayi barcin,
wayoyinsa ya aje a Kan bed side ya zauna a gefen gadon Yana Kare Mata kallo, shifa duk hankalinsa ba a
kwance yake ba tunda aka fada masa matsalar dake damunta yaji ba shida sauran nutsuwa idan ba zuwa
yayi ya ganta ba, Kuma Dole ma yasan abinyi akan ciwon Nan ko ana Wasa da wasu lamuran Banda lafiya
baik'i tasan kowaye shiha a wannan lokacin dole ya dauketa ya kaita inda za'a dubata Masa ita duba na
gaske.
Remote din AC ya dauka ya rage gudunta dakin yayi sanyi da yawa duk da Yana son sanyi amma wannan
yayi yawa, a hankali ya saka hannu ya janye bargon daga fuskar ta barcinta takeyi shower cap din dake
Kanta ta cire sai gashi Baki sidik Yana ta walqiya a cikin Dan hasken data Bari a dakin, Kara zame rufar yayi
har zuwa kirjinta jikin sai wani glowing yakeyi Jin sanyi Yana shigarta yasa ya juyo da fuskar ta inda yake
zaune "ya Salam". Ya fad'a a hankali, gani yayi ta Kara yi Masa wani kyau na musamman, Kare mata kallo
yayi yaga daga ita sai towel a jikinta, murmushi yayi da gani Batasan da Kaya a dakin ba.
Kayan jikinsa ya cire ya Zama daga shi sai boxer short ya shige jikinta ya janyo lallausan bargon ya rufesu
Yana sauke ajiyar zuciya, a cikin barci taji an rungumeta gaba dayanta jikinta ne ya dauki rawa shikenan
tasan tata ta Kare shi yasa suka nemota da tsohon dare suka kawota Nan Yan ko wane irin ihu zatayi ba
Mai jinta, cikin murya Mai rauni tana cracking ta Fara farin "innalilllahi na Shiga uku wayyo Allah na....
Bata katasa fadin abinda tayi niyyar fada ba taji yace "shittt...Ni ne fa cool down precious ba abinda ze
sameki a cikin gidan Nan sai ikon Allah, akwai kyakykyawan tsaro".
sansanyan kamshin turarensa ne ya shiga hancinta, kokarin kwace jikinta takeyi Dan yayi Mata kane-kane
so take taga zahirinsa Amma ya Hana hakan, ita mamakinta Daya yaushe yazo garin kuma ta Ina ya shigo
Dan ita dai tasan ta rufe kofar nan. Dai dai kunnenta ya saka Bakinsa "ki kwanta muyi barci na gaji da yawa
kin hana duniyata kwanciyar hankali kina min kisan mummuqe ko wayar ma kin haramta Mana yinta,
tunda Naga alama Nima Mai laifi ne". Ya fada yana shafa gashin kanta zuwa bayanta, hannu Daya yasa
Yana zare towel din data daura a jikinta da sauri ta rike tana girgiza Masa Kai.
"Dan Allah ka Bari bafa kyau muyi barcin to".
Wani guri ya taba a jikin gadon wasu irin fitilu suka Kama kamar star masu haske sosai, Bata ankara ba ya
fizge towel din gaba Daya daga jikinta Yana Mata wani mayen kallo hannu tasa ta kare kirjinta cikin
matsananciyar kunya tace Masa "Dan Allah ka kashe hasken Nan wallahi kunyarka nakeji".
"Ni kike Jin kunya?"
Kai ta gyada Masa, 'Well done Yanzu kuwa Zan cire kunyar nan daga idonki".
Wani bed sheet data gani a gefen gadon ta janyo da sauri ta lullube jikinta dashi tana Kara sadda Kai kasa
Dan da gaske ya saka taji kunya sosai.
Wutar ya kashe ya matso sai Jin mutum tayi ya shigo cikin Bedsheet din data rufa dashi ya hanye shi ya
maye gurbinsa da lallausan bargon.
"Ki hanani Zama a gurin neman abincina sannan na dawo ki Kama guduna, ai impossible wallahi muyi
barcin da safe mayi bayanin".
Ya Kara mannata a jikinsa suka samu body contact da kusancin zahiri.
Sun jima yana sarrafata.Tayi laushi iya laushi dan da gaske da kishirwarta ya shigo garin tamkar
mayunwacin Zaki badan tana cikin rashin tsarki ba da Babu abinda ze Hana labarin sauya salo, dan tuni ya
wani manta da Alkawarin da ya daukarwa Kansa, Saida tafiya tayi nisa ya ji abinda yayi Masa cikas Dole ya
saurara Mata, sun kai kusan karfe uku da rabi a haka shi Mai fad'ar barci ya keji sai gashi ya bige da Hana
Mai barcin yin Bata barcin.
Sai sauke ajiyar zuciya suke su duka har lokacin hannunsa Bai daina shafe shafe ba, wani irin yanayi jikinta
keyi har mararta ciwo ta Dan Fara Mata cikin dashashshiyar murya mai dauke da salon shagwabar da
Batasan iya ba,ta kankame Shi jikinta na wata irin tsuma muryarta ta dishe tamkar me yin mura ta Fara
magana.
"Dan Allah ka bari wallahi marata ciwo takeyi...".
Baiyi magana ba sai kakkameta da yayi kamar ze shige jikinta shima ya hade bakinsu Yanda ba Yanda za'ayi
ta iya furta wata maganar ba, hannunsa ya tura Yana shafar marar ji yayi tadan tasa kamar ta Dan
kumboro, hannun ta rike tana girgiza Masa Kai.
Zare hannun yayi ya dawo dashi sama yaci gaba da sabgarsa ya Kuma ki sakin bakin da zatayi korafin, suna
haka har wayarsa ta Fara rera kiran sallah.
A hankali cikin muguwar kasala ya saki bakinta yana Maida numfashi da sauri da sauri gefe ya margina
Yana dafe da tasa marar idanunsa a rufe, Zahra naji ya raba jikinsu ta Kara takurewa a cikin bargon wani
irin tsoro ne ya lullube ta da gaske yazo Mata da wani lamari Mai girma, ita ai ko idanu bazata yarda su
hada ba ai da kunya wallahi duk yabi ya tsorata tas ya lalube ko Ina na jikinta, Ashe can baya Wasa ne
kawai yayi Mata yanzu ne ya nuna Mata true colour dinsa tana ganinsa salihi Dan bawan Allah Ashe shima
guda ne ba gyale ba, kirjinta sai zogi da ciwo sukeyi mata yayi son ransa da jikinta.
Tana jinsa ya tashi ya shige toilet ya jima tana jiyo motsinsa, sannan taji ya fito alamun tsayuwarsa taji a
Kanta,a hankali ya saka hannu ya janye bargon kankame jikinta tayi Dan daga ita sai pant Kare Mata kallo
yakeyi take yaji alwalarsa na neman warwarewa, laimar hannunsa ya Dan yarfa Mata a jikinta "wash...Allah
na!".
Mayar Mata bargon yayi ya shige clothset din dakin jallabiya ya sako Fara tas da hula mahadinta
raka'atanul fajri yayi, jikin gadon ya matso ya Dan zauna "zanje masallaci".
A dawo lafiya tayi Masa tana kudundune Yanda take, tanaji ya fice daga dakin.
Sai ta tabbata ya Kai masallacin sannan ta yunkura ta tashi ta nufi toilet, tsabtace jikinta tayi sannan tayi
wanka ta fito,lotion din data gani ta shafa sai body mist na itacen sandal wood Dana oud ta hada ta fesa
kayan da zata saka ne ya zama cikas Dan bazata iya mayar da Wanda ta cire ba Kuma bazata Kuma Zama da
towel ba tunda taga abinda hakan ya janyo Mata, Shawarar duba clothset din tayi idan taga Kaya sabo
Kona waye zata saka, tana mamakin ace Mai gidan Nan bashi da Mata Kuma ya sakarwa abokai irin haka
baya gudun a ring aikata fasadi a cikinsa, were Dan wannan sai ka shekara a ciki ba'asan kana nan ba.
Ba karamin mamaki tayi ba ganin kayan Mata masu yawa har Sunfi na wancen apartment din ba wani d'ar
undies ta saka ta saka doguwar Rigar material Bata daura Dan kwalinba wasu hulina na Mata ta gani da
yawa ta duba kalar ash irin flowers din jikin material din ta saka a Kanta, barci takeji sosai Dan tunda Allah
yasa ya tasheta da aalonsa Bata Kara rintsawa ba shiko gogan Allah besa an raba barcin jiya dashi ba.
Harta juyo zata bar gurin taji tana son ta bude dayan side din, kayan make up ne dasu turarika shoe and
bags turaren ta dauka tana dubawa duk yawanci irin nata ne sai wasu irin nasa ga Kuma kayan maza nan
Lodi Lodi dasu underwears tana tsayen tana dubawa taji kawai an rungumota ta baya, ajiyar zuciya ta
sauke tana lumshe ido Sam bataji alamun bude kofa ba ko takun tafiyarsa, Kansa ya Dora a kafadarta Yana
Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunne "Good morning my previous".
"Morning Yayana".
Ta fada da wani salo, juyo da ita yayi suna facing din juna.
"Bude idonki ki kalleni ki fada min waye yayan naki? Wato har yanzu da sauran Rina a kaba kenan ko? Nifa
bazaki tauyeni ba Ni ba wani Yayanki bane a bani special name Dina, kodan kinga mu 'yan gargajiya ne
"ya'yan Alarammomi Malam soro, bamu da wayewa irin taku ko?"
Batasan lokacin data sauke ifanunta a Kan nasa ba, tana jinjina maganarsa.
"Wayewar saita kasheku".
Tayi subul da baka ta fada harga Allah a zuciyar ta tayi niyyar fada bakinta ya subuce ya fada.
"Kai! Nine wayewar saita kashemu to nida waye zata kashe din?"
Kauda Kai tayi tana Jin kunyar maganar.
*Ni ba haka nake son fada ba Bakina ne ya furta hakan".
*Ok, zomu kwanta barci nakeji tunda kin hanani barci da fitinarki".
Rigar ya zuge zif din ya cire mata ita ya barta daga ita sai undies kawai ya dauketa can ya nufi bed din da ita
tana mutsulmutsultun ya sauketa ya kiya Saida ya dangana ta da saman bed din, shima jallabiyar ya zare ya
janyota ya lullubesu da gaske barcin za'ayi Dan tunda ya sakata a jikinsa Bai Kara yi Mata komai ba.
Tunda Ammi tayi sallah Bata Koma barci lazimi ta zauna tana yi amma zuciyar ta Babu dadi kwanan nan
kusan Kullum sai tayi mafarkin Mahmud da wata yarinya budurwa Yana rike da ita da hannu Daya dayan
Kuma Yana ta faman fada da wasu irin halittu mara kyawun gani, to yau ma shita Karayi Saida taga wasu
mutane dattijai guda biyu sunzo sun Taya Shi kashe wadannan halittun sun tasa su shida yarinyar har wani
gida sai da suka shige sannan suka juyo suka tafi.
A haka Mai gidan ya sameta Saida ya zauna ya Kare Mata kallo yasan da akwai damuwa a tare da ita sai dai
tana kokarin biyewa.
"Ammin Yara me yake damunki duk kwanakin Nan Baki da walwala Sam ko kula dani ma tayi baya ko Baki
huce bane har yanzu?".
Kai ta girgiza "A'a kawai dai lamari Hussain ne yake damuna kofa da Rana Daya Bai taba kirana ba ko sako
ta email Bai taba Yi min ba, gashi a kwanakin nan sai wasu irin mafarkai nakeyi dashi marasa dadi abinda
yafi tsaya min a Rai Kullum da wata yarinya budurwa kamar 'yar India nake ganinsa da ita Ina tsoron wani
Abu wallahi na rasa yanda zanyi Dan Allah kayi wani Abu akai".
Sai hawaye sharrrr.
"Subahaballahi! Haba zainab ya Zaki ringa yi Masa kuka kinsan masifar zubarwa da d'a hawaye kuwa ko
wani abun yake aikatawa ai saiya karu idan kina Masa kuka, addu'a zamuci gaba da Yi Masa nifa jikina Yana
bani Yana Dubai Dan last week na samu leakage akan Yana can din Dan yayi wasu ziyarorin bazata a can
harya dakatar da wasu ma'aikatansa sai dai duk kokarin a gano min masaukinsa sabo hakan yaci tura Dan
ba'a inda yake sauka ya sauka ba tunda gudun hijira yayi".
Hawayen ta goge ta tashi tana ninke sallayar ta zauna kusa dashi. "Shikenan Allah ya shiga cikin lamarin ya
kureshi daga sharrin zinace zinacen zamani wallahi badan komai nufin Allah bane Wanda yaso yake bawa
kyautarsa danace dama bashi ya samu wannan budin ba da kananun shekaru to yanda yaso haka yake
tsara kayansa, Amma ga yayunsa Nan ba Wanda ya takura musu Suma ai suna da wadatar,tunda Allah yayi
muku karfin arziki waye talaka a cikin family din nan?".
Dan murmushi general yayi Yana kallon yanda take fadin magana abinda ba halinta ba inda akan twins ne
sai dai wani yayi magana Amma ta zage tana fadin son ranta.
"To ya zamuyi da hukuncin Allah shi yaso ya daukaka a cikin zuri'ar da Wanda ya Isa yace a'a Ina cewa
Alhaji Ishaq ne ya bashi jarin Daya Fara sana'a dasu tun Yana hannun Hajja, Amma yanzu zaki hada
arzikinsu ko kusa ko alama Babu Hadi,.koni Dana haifeshi ya mallaki abinda bani da kwatqnkwacinsa, Keda
Kika haifeshi kin mallaki abinda yake dashi? To kiyi istigifari ga Allah tunda shine yace Yana azurta Wanda
yaso ba tare da hisabi ba,ai kin gane?".
"Na gane Allah ya Zama gatansa a duk inda yake,Amma fa yarinyar Nan ta tsaya min a rai idan Yana kusa da
wannan ai zai manta da kowa ne tunda cikin bacin rai yabar gida ga Kuma kudi a tare dashi kaga sai Allah
kadai ze kare shi".
Dariya ta bashi sai da yayi sosai kafin yace.
*In Sha Allah in dai Zina gado ce to Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w zuri'ar mu bazasuyi ba Ni ba mazunaci
bane haka kema ba ita bace in Sha Allah.Allah baze jarabcemu da ita ba, Kika sani ko bushara ake Miki ke
uwa kin samu sirika".
"Haba dai har abun ya Kai haka yayi aure ba sanin iyayensa ai kuwa da lamarin ya lalace".
'yar dariya yayi.
"Kedai kije ki shirya min breakfast daurin Aure zamuje kabba na Dan gidan sanata Abdul Aziz"
Tun idar da sallar Rukayya ta taso ta nufo part din da zahra ta kwana,abin mamaki an canza pin kofar dan
ta kwada yafi sau goma Amma taki budewa. Nan da Nan taji hankalin ta ya tashi me Kenan badai wani
bane ya shigewa 'yar mutane ba gashi jiya Taki Kai Mata wayarta da ba saita kirata ba, gudun kada tace sai
sun kwana ya hata ta Kai mata.
Number ya Sameer ta lalubo lokacin Yana barci,
Yana dauka ko gaishe shi bata tsaya yi ba ta Fara fadin "Ya Sameer ka taimakeni wallahi tun sassafe bake
kokarin shiga part din da zahra take Amma kofar kofar kamar an canza pin din na saka yafi sau goma Amma
yaki budewa".
Tsaki yayi "Waike Dan Allah Ruky yaushe Zaki girma ne? to oga ne ya shigo cikin dare Nima da asuba naga
text message dinsa Dan haka ki Zama ready idan na shigo saimu wuce tare Amma yanzu kada kuyi komai
za'a kawo abinci".
"To ai su Iya Rahane har sun kusa gamawa baka fada min ba tun dazu".
Ok, ba komai sai a hada tunda gidan da jama'a, yauwa zuwa an Jima ki bude musu part din Nan na kusa da
parking lot sai su zauna a nan tunda shima ogan Bai san ze shigo kanon ba harsu Gama su koma to
matsalar madam din ce inaga ta caza Masa Kai Wai cewa fa yayi daina amsa Masa waya tayi".
"Kamar ya Bata amsa masa waya? Batasan kowaye bane da zata ringa yi masa haka?"
"Eh kusan hakan ne gaskiya"
"Allah ya rufa asiri" ta fada.
Sukayi sallama ta kashe Kiran tana dariya "su oga anzo hannu ana walagigi da rayuwar 'yan Mata gashi
kaima kazo hannun yarinya tana juyaka son ranta, nasan bana raba Daya biyu saboda shi ta rufe wayarta
jiya, taki magana dashi a wayar Ya Sameer karshe ma ta sakata jirgi, yes! Haka nake son irin matansu su
kasance, idan suka samu wadda ta mace a kansu ta Zama sorry Amma wannan ta shuka mulkinta yanda
takeso tunda Batasan waye shi ba".
Ya juya ta koma kitchen inda tabar su zilai suna aiki, tana shiga zilan tace Wai ni lafiya yarinyar Nan? naji
shirun yayi yawa ko dai rakani zakiyi na gano lafiyarta kada na Zama babbar kwabo an hadoni da yarinya
nayi wasarere da lamarinta".
'yar dariya. Rukayya tayi "gaskiya kinaji da matar big bro irin wannan shiga damuwa jiya fa ko barcin kirki
bakiyi ba kina zaman jiranmu yau ma tun Asuba kike ta nemanta, ki kwantar da hankalin ki Aunty sirikinki
ne ya taho ba Shirin wannan 'yar taki tsaye ce taki saurarensa ko a waya dole ya tsallake hidimominsa ya
nufo Nigeria".
Iya Rahane ce ta aje Wukar hannunta tana duban Rukayya "kikace uban gidan mu ya shigo garin?"
"Kwarai kuwa iya jiya cikin dare ya shigo Kinga kuwa sai ki fadawa Aunty ta kauda Kai kawai gurin son ganin
'yarta ba yanzu ba gaskiya, Dan haka da an gama aikin Nan zamu bar Nan Bangaren mu koma wancan".
"Wannan gaskiya ne inba tayi dalili ba yaushe zamu shigo wannan guri harda kwana a cikinsa, Amma
dalilin uwar dakinmu mun dangwali arziki ai wannan ba komai bane akan gidan da aka sauke mu a sokoto,
Kai Naga inda arziki ya amsa sunansa wannan yaro uwarsa tayi farar haihuwa wallahi Nan kusa Banga
mutane masu karamcin su ba, uwarsa yarinya karama sai halin girma".
Ita dai zilai sai ta rasa Wai wannan maganar dawa ake ne waye suke zance a kansa ne ita fa maganar Zahra
take musu su Kuma sun kamo wata tashar Ina hadin zahra ba Wanda suke magana a kansa ko dai Mai
gidan ne ya dawo Basu gane me take nufi ba, ita Zahra matar Almajirin Malam Bukar Wanda gidan zaman
ma na Baba Malam ne mutanen da yaje yiwa aiki turawa suka gyara Masa shi, to Ina shi Ina wannan
Aljqnnar duniyar suda aka kawosu zaman 'yan kwanaki na ganin likita.
Cikin nuna mamaki zilan tace "ikon Allah ai ban sani ba kice da anyi uwar banza gara da Kika fada min kada
naje nakai kaina girma ta Fadi".
"Ai Koda kin shiga basa Nan ba a nan suka kwana ba".
Wayar Rukayya ce tayi qara ta dauka ta fice daga kitchen din shine abinda ya Hana zilai fadar abinda tayi
niyyar tambayarki Rukayyar.
Hira iya rahane taci gaba da yiwa zilai a Kan Mahmud amma ko Daya zilan Bata gano ainishin waye take
magana a kansa ba.
✨✨
✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page 45.
________Sai kusa karfe Sha Daya da rabi Mahmud ya farka shima yunwa ce ta tashe shi, ido ya tsura
Mata barcinta take hankali kwance tayi pillow da gefen kafadarsa, hannu yasa ya shafi gefen fuskarta da
gashi ya kwanta lambam, hancinta ya dan ja kadan, dan yamutsa fuska tayi tana bude idanunta a hankali,
Ido cikin ido sukayi dashi da sauri ta Maida nata ta rufe.
"Ki tashi muyi wanka ki bani abinci Naga alama ke barci baya isarki".
Zare jikinta tayi still dai idanun a rufe, tana Jan bargon zuwa kirjinta.
"Kaje ka Fara Yi sai nayi nima".
Ta fada tana juya Masa baya, Dan murmushi yayi ya Dan rankwafa dai dai fuskarta.
"Ok, ba damuwa jeki hada min ruwan saina Farayi kafin na fito, saiki hada min abinda zanci".
Yunkurawa tayi ta tashi zaune, tana mutsumutsun yanda zata tashi haka a gabansa.
"Ka Miko min Riga na saka saina shiga na hada maka".
Ba musu ya dauko Mata Rigar ta Karba ta saka ta Mike ta nufi toilet din.
Saida ya tabbatar da ta shagala gurin abinda takeyi ya tashi ya nufi toilet din, tana zuba turaren wanka
cikin ruwan data hada ya shigo ciki ba zato ba tsammani sai ganin mutum tayi ya shigo daga shi sai boxer a
jikinsa, gurin da take tsaye ya nufo, da sauri ta matsa gefe kanta a kasa Bata yarda sun sake hada Ido ba
tace Masa.
"An Gama hadawa".
Tana aje robar dake hannunta ta juya da zummar barin gurin. Taku biyu tayi taji anyi sama da ita cak sai
cikin ruwan daga ita har kayan jikinta, wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadin "Dan Allah ka Bari wallahi
nayi wanka fa".
"I know, tayani zakiyi Dan rashin kirki ai ni bakonki ne ya kamata ki tarairayeni har wankan ma kiyi min
tunda kin hanani sukuni Saida Kika gargadoni na dawo gurinki Kinga kuwa ai duk lokacinki yanzu nawa
ne".
Har ta bude Baki zatayi magana ya Dora Dan yatsansa a Kan lips dinta "kin manta ba'a magana a cikinki
toilet? Muyi wankan later munyi maganar".
Janyota yayi jikinsa ya Fara cire Mata jikakkun kayan jikinta, a tsorace da Kuma wata azababbiyar kunyarsa
da takeji ta Kara ninkuwa, dan wani Abu ne da be taba faruwa da ita ba a tarihin rayuwarta irin wannan
kebewar da namiji baligi da uwar tana irin wannan Bata taba yiba shi yasa Daya hade jikinsu ta shiga tsuma
kamar wadda Zazzabi ya rufe, wankan sukayi tare duk da shi dai kadai yake sha'aninsa Dan ita dai kam sai
hankali.
Saida ya Gama son ransa sannan ya karasa wankan ya fito ya barta a ciki,Saida ta kimtsa kanta sannan ta
fito, lokacin har ya shirya cikin wasu kananan Kaya Yana daura agogo, tsaye tayi a kofar toilet din ita Bata
koma ba ita Bata karaso inda yake ba, kallon kasa kasa take masa gani tayi gaba Daya ya canza Mata kamar
anyi musanyarsa da wani ya Kara zaman wani handsome dashi jikinsa ya Kara Zama fresh dashi.
Inda take tsayen ya nufa "pls ki shirya Ina son fita ne wurin after zuhur".
Kofa ya nufa ita Kuma ta nufi gurin mirror tana goge jikinta, hand dryer data gani a gefen mirror ta dauka
ta jona ta busar da kanta, cikin kankanin lokaci ta shirya gurin kayan ta nufa tsaye tayi tana kallonsu. To
Wai ita Nan din Ina ne gidan waye taga ya shigo ya barrarraje Yana tsula sha'aninsa ga kayan Mata birjik
Kuma ance mamallakinsa ko aure beyi ba to Ina ba"asin kayan nan na can part din Aunty Rukayya tace
nata ne to wannan fa na waye su kuma? Qundunbala tayi ta dauko wasu English wears, ta saka masu kalar
brown dark sai veil milk colour tayi rolling ta fesa turarenta dake cikin handbag dinta sai lokacin taga
maganin da Hajiyar makwarari ta bata, Dan murmushi tayi a zuciyarta ta ayyana "zanzo na Baki hakuri
Hajiya nasan ban kyauta Miki ba dole ce tasa na aikata hakan".
Dakin ta Fara gyarawa ta cire bedsheet din ta duba gurin da take tunanin zata iya ganinsu ta duba.
Very luckily ta gansu ta Ciro Daya ta baza zata Fara shimfidawa ke Nan ya shigo dakin Yana waya, da hannu
ya nuna Mata ta taso, ba musu ta taso ya nufo inda yake hannunta ya kama ya nufi kofa wani Abu kawai ya
taba daga can kasa kofar ta bude, da kallo ta bishi tana mamakinsa gaba Daya ya canza Mata Kuma yanda
yake mu'amala da gidan Yana Bata mamaki, har suka fito parlour na biyu Yana ta wayarsa wadda ta
fuskanci kamar suna maganar kasuwanci ne sabo da aka Riga aka fara, direct dining ya nufa da ita Saida ya
zaunar da ita sannan ya zauna.
Wani Dan guri ya danna jikin table din, ba'a Jima ba saiga wani saurayi ya shigo ta wata kofa.
Baiyi magana ba tun bayan sallamar da yayi Zahra ta amsa masa, wayar ya kashe ya juyo Yana duban
Wanda ya shigo din.
" Safwan Kada naji labarin Ina garin nan a bakin kowa, kaje inda na turaka jiya?"
"Naje oga komai ya Zama normal, harma sun Fara aiki saidai Zayyan yace wannan Matar tana yawan zuwa
kusa da gidan amma dai Bata karasowa take komawa".
"Ok ba damuwa kaje kawai idan ka dawo ka taho da fresh milk da fruits a saka a kitchen din nan".
"Ok sir, na gode ya juya ya nufi inda ya fito har ya danyi nisa yaji maganar Mahmud.
"Safwan banji ka gaishe da madam ba, bahaushiya ce ba wani yaren zatayi makaba, Naga alama saina
miqaka makarantar koyon turanci tunda Naga shi kadai ne kake da matsalarsa".
Dan Sosa Kai yayi yana dawowa baya.
"Afuwan Auntyn mu wallahi na dauka bakijin yaren mu, Ina kwana?"
"Lafiya kalau ya aiki?".
"Alhamdulillahi Auntyn mu, Allah ya Kara sutura ya bar Mana ke a gidan oga Dan isar Annabin Rahama".
"Amin ya Hayyu Ya Qayyum".
Muhmud ya fada.
Hanya ya nuna Masa alamar ya wuce bai Kara tofa wata maganar ba ya juya yabar gurin.
Ita Zahra kallon ikon Allah takeyi wallahi wannan ba Wanda suka zauna a Azare bane da banbanci nesa ba
kusa ba.
Iskar Bakinsa ya hura Mata a fuska saitin idanunta, "kallon na menene Kona canza Miki ne? Kika tsareni da
wadannan eyes din naki masu hanani sakat idan Ina kallonsu Dan Allah ki barni naci abinci kome kike
bukata saina Baki badai kin hanani zaman can ba, to aini gaba ta Kaini gobarar Titi a jos, haka ake fada ko?"
Ya tambaya Yana bude abincin.
Dan kwabe fuska tayi tana Dan turza kafa a kasa.
"Ni wallahi bani nace ka dawo ba kawai Kaine kayi niyya da kanka ka dawo Ni ba ruwana to na kiraki nayi
maka me?".
"Au haka Zaki ce shike Nan yanzu dai bani abinci daga baya sai kiyi min bayanin yanda aka haihu a ragaya".
Bata gane hausar tasa ba tayi Shiru dai kawai.
Abinci ne kusan kala biyar Banda pepper soup na turkey.
Kasa hakuri zahra yayi Wai daga Ina wannan abincin irin haka?"
"Daga jama'ar Annabi, kinsan mu 'ya'yan malamai ko Ina muka sauka gida ne".
Shiru tayi ta zuba Masa abincin zata Zuba nata ya dauke plate din.
"Kin manta ai ba raba Abinci a tsakaninmu muci kawai".
Tare sukaci abincin suka Gama, tana Dan kallonsa lokaci-lokaci, da gaske yazo Mata da abubuwan mamaki
da yawa Amma azarbabi ba nata bane. Dole tabi kamai a hankali saida ya tabbatar ta koshi sannan ya
saurara mata, Nan cikin parlourn suka dawo suka zauna ya dorata a cinyarsa yasa hannunsa ya zagayo
cikinta yana ta faman
amsa wayayoyi, sai ya amsa way kamar uku, sannan ya aje ya fuskance ta. Wasu irin wayoyine guda uku
Wanda ita dai sai a T.V take ganinsu amma sai gasu a hannunsa kuma ya wani ci magani Dan kada ta Tama
Fara masa wasu tambayoyi.
'
"Bani labari ya akayi ciwo Bai tashi kamaki ba Saida nayi Nissan Zango, naji doctor tace Wai rashin samun
biyan bukata ne yake kawo miki yawan ciwon marar saboda sha'awarki tana motsawa Baki samun biyan
bukata".
Waro Idanu tayi Baki bude tana Masa wani kallo.."Ni kuma? Wane irin magana ce wannan bayan fibroid
din Kuma harda bita da kullin sharri? ta Nan Kuma ta bullo? To ai sai tazo ta ta cire min sha'awar tunda ita
ta ganta, kawai ta Fadi gaskiya tanaso tayi amfani da aikinta ta cuceni,tunda da hadin bakinka Ashe ni aka
mayar sakarya aka tasoni tunda daga kauyen mu aka kawoni gurin budurwaka ta dubani,ta ganeni ciki da
bai kaga ko idan ta aureka bani da wata fuffuka da zanyi Mata, wata Kila da Allah baisa ta fito da maitarta
fili ba da Allah kadai yasan illar da zatayi min.Da Jin saita cire min mahaifa gaba daya, ka fada Mata wallahi
da gatana Ina da gatan da wallahi ta cutar da lafiyata Saida ta kare rayuwarta a life in prison, kuma indai
Kaine nabar Mata taje ta hadiyeka kada wata ta Kara ganinka tace tana so, an fada Mata Ni Ina da damuwa
ne da zata ringa wulakantani in dai saina Kara zuwa ta dubani ciwon yayi min abinda Zeyi min Kuma yau in
Sha Allah gida Zan koma bazan iya Zama a Nan ba Ni duk kanon ma ta fice min daga Rai, ka mayar Dani
inda nafi wayo".
Ta karasa fada tana juyar da fuskar ta gefe.
Kwanto da kansa yayi gefen wuyanta. "Cewa fa nayi ki bani labari ba cewa nayi meye damuwar ki ba, Ni
meye laifina daga na turoki a duba min lafiyarki".
Ai fadar hakan saiya tunzurata nan da nan sai hawaye.
"Oh! My God!, Mena fada Kuma? pls tell me".
"Kwace Kanta ta shiga yi tana fadin.
Daman nasan ba Sona kakeyi ba tunda Ni matar shige ce Bata da daraja kuma wallahi duk Wanda ya Zama
sanadin da wannan gararin rayuwar ya sameni ban yafe Masa ba, da qimata da mutuncina an mayar Dani
wata shakatafi kowa saiya takani yanda yaso bani da wata qima".
Ta sunkuyar da kanta tana wani kuka Mai cin zuciya.
Iya dagula lissafi tayi Masa Dan kasa cewa komai yayi sai sakata da yayi a jikinsa ya kwantar da ita shi kadai
yasan abinda yakeji, suna haka yaji wayar Daya Bari a kunne wadda yake amfanin yau da gobe ta dauki kida
Mai Dadi.
A hankali ya Kai duba gurin wayar, Sameer ne.
Dauka yayi baice komai ba "Ina kofar part din Nan kana da bakuwa".
"Dude ka shigo sai muyi maganar".
Ya kashe ya aje wayar, Jin ya ambaci Sameer ya shigo yasa zahra yayi kokarin zare jikinta amma Dan bawan
Allah nan kememe yaki sakinta saiya gyara Mata Zama kawai.
Dago Kai tayi da niyyar yi Masa magiyar ta saketa ta tashi dai dai lokacin Sameer ya karaso gurin, be taba
tunanin tana jikinsa ba tunda shi kadai ake hangowa Saida ya kure musu yanda ba yanda za'ayi ya koma,
tsaye yayi shi Bai Kona ba shi Kuma be karasa gurinsu ba ita kuma Zahra kunya kamar ta nutse wallahi Bata
taba tunanin rashin ta idonsa ta Kai har haka ba.
"Have a seat, kazo ka tsaya Wai kuka take min na kawota an Mata wulakanci na Maida ta gida ita ko sunan
Kano Bata sonji".
Sameer 'yar dariya yayi "Ni ba ruwana a ciki Dan aikene ni kasan Mata Dan Abu kadan saiya tada musu
hankali, Daman bakuwar tata ce Hajiyar makwarari ce ta kirani bayan nabar Nan Ina gidan mommy na
mayar da Rukayya saiga kiranta Wai lallai saina daukota tazo taga madam shine mommy tace na kawo ta
indan ba haka ba zata iya rikita lissafin kasan halinta dai".
"Ok ba damuwa ku shigo tare ai Hajiyarmu ce ba inda bazata shiga ba".
"Ok sir".
Ya juya ya fice daga parlourn da sauri,mamakin Mahmud ne ya kamashi sosai ya rasa wane irin so yake
yiwa yarinyar Nan ne haka? Yana tare da wannan mezeyci da wata Haseena ai saidai tayi hakuri da can
Bata you tasiri ba gurinsa ba bare yanzu daya Sami abinda ya kwallafa rain a kansa.
Zahra Jin Sameer ya fice yasa ta dago da kanta daga kijinsa tana ajiyar zuciya, Dan just tayi kukan ta Kama
nasa guri sai mamakin furucin oga Sameer daya cika Mata zuciya wai sir to me hakan ke nufi itafa kada su
manna Mata Dan karamin hauka gaskiya.
Dan Allah ka barni na tashi kaji fa Hajiya ce yace fa
Zata shigo, Kuma Dan Allah bakaji kunya ba ka wani sakani a jikinta salon yace bani da tarbiyya".
Wani kallo ya watsa Mata "ai yau ko waye ze shigo gurin Nan a haka ze samemu gara asan Ina sonki tunda
kina ganin ba sonki nake ba har kina kallona kina fadin Wai matar shige ce ke idan aka sameni rungume da
kayana Ina lallashi kuwa koya saiya sheda ina son abuna, nine dai ba Sona ake ba anfi son wannan Mai jan
kamar karas tunda saboda shi aka yarfeni da bakaken maganganu".
Har ta bude Baki zata bashi amasa taji rangada sallamar Hajiyar makwarari, ai ita kanta Bata San yanda
akayi ba ta tsinci kanta a tsaye ballentana shi da ake zaune a jikinsa, shi dai Sameer Bai San lokacin da
dariya ta kubce Masa ba ganin yanda Zahra tayi wani wuk'i-wuk'i da ita shima gogan dariyar yake Amma a
ciki.
"Wai ni Hajiya waye Mai gidan nan ne? na Ya Sameer ne? ko kuma na wani abokin nasu ne? Naga ya sakar
musu ragamar ko Ina na gidan Baya tsoron abinda zeje yazo,nifa tsoro ma yake bani kamar baza'a mutu ba
gaskiya ya mayar Dani gida inda nafi wayo, anan mutum saiya shagala da duniya wallahi".
Baki Hajiyar ta rike tana yiwa zahra wani kallo.
"Amma yarinyar nan lamarin ki da sauran gyara, gidanwa ze daukoki ya kawo idan ba gidansa ba, yo
wannan ai Bai kama kafar gidajensa na sokoto da Abuja ba, ni duk naje Kinga na Abujan,? ganin likita naje
lokacin Ina ciwon kafa, na sokoton Kuma bikin kanwarsa wadda take a can Germany mukaje, wannan
mutane da karamci suke, gashi kinyi sa'ar suruka Hajiya zainab Bata da damuwa ko kankani" .
Tsai Zahra tayi da ranta Kenan da gaske shi Dan Sokoto ne kamar yanda ya fada Mata sannan da gaske
sunan Babar tasa zainab din Kennan lokacin da take fadar iya Abu yace ta daina fada gatsal sunan
surukarta ne ta dauka Wasa yake Mata wallahi kenan duk abinda ya fada ba joking a ciki.
"To ai shike nan nayi zaton ko gidan na wani ne muka Mike kafa a cikinsa"..
'Ko alama ranar dasu Hajiya Inna sukazo ai nayi zaton fa a Nan zasu kwana gurinki sai Kuma suka juya
surukar Taki ce Bata samu zuwa ba sai ita kakarsa da matar kanin mahaifinsa, ki yiwa Allah ki taushi
zuciyarsa yayi hakuri ya koma gida tunda Naga alamar kece Zaki iya wannan jahadin, wani irin fushi yayi da
kowa har Amminsa abin ya shafa ranar da nace Miki su Hajiya innar sunzo Saida Tasha kukanta a dakina,
wallahi Banda idan na Fadi ga inda yake abin ze iya shafar tarensu da Sameer da saina fada musu kodan
samun kwanciyar hankalin Ammin tasa tafi kwanan watanni Bata gidan ubansa saboda rikicin da akayi a
gidan yanda mijinki ya fice yabar gidan itama ta fice ta bar musu gidan, abunfa Babu dadi kiyi wannan aikin
ladan Dan Allah ko an samu kwanciyar hankali a zuri'ar su.
Ita dai zahra Banda gyada Kai babu abinda takeyi, Dan ji tayi abin yafi karfin dan karamin tunaninta.
✨✨✨
Page 46.
_______Sun Jima a gurin suna hira da Hajiyar tana Kara Bata labarin taren Sameer da Mahmud, anan
tasan mamansa 'yar Niger ce Kuma cewa shi din da gaske twins ne su kamar na Ammah mace da namiji.
Suna nan suna hira har aka Kira sallah, da sauri Zahra ta tashi tana fadar "Hajiya Kinga guri Yana neman
kurewa ban Dora miki abinci ba ko".
"Kinga dawo ki kaini inda zanyi alwala nayi sallah Banda kinibibi ki wani ce Zaki dafa min abinci, to Wanda
Rahane da wannan yarinyar Dana gani akace tare kuka taho da ita Wanda suke faman aikinsa kuma ayi iri
dashi? Ina fada Miki ki nutsu mijinki yawa ke garesu Kuma duk cikinsu mijinki daban ne sai kin koyi
kamewa da gaske sannan Zaki fuskanci yanayin kowa Ina ke Ina wani dorawa Baki abinci banqiba dai in
mijinki Zaki ringa yiwa wannan ba laifi,amma ba kowanne karabiti ba kice Zaki wani kama rawar jikin yi
Masa, mujeni ki nuna min nayi dahara kafin a shiga sallah".
'yar Jakarta ta hannu ta daukar Mata suka nufi bedroom din da suka kwana.
Saida ta rakata har cikin toilet din ta nuna Mata duk abinda ya kamata sannan ta fito, sallaya ta shimfida
Mata sannan ta karasa gyaran gadon da Bata Ida ba dazu ta saka freshner ta Daki ta rage karfin A/C din
dakin. Hajiyar ce ta fito tana fadin "Ina dalili komai ya Zama na tab'e tab'e sai mutum yasha wahala kafin
ya tantance yanda za'ayi"
Dan murmushi Zahra tayi "Haba Hajiya me yake da wahala saboda Allah?"
"Babu Miko min gyalena nayi sallah naji kamar an tada sallar"
Hijabin ta Mika Mata tana fadin "Bari naje na dawo ta nufi kofa ta fice.
Gaba Daya ta fice daga part din, ta cikin barandar Nan tabi ta shiga babban part din, ko Ina tadal sai sanyi
da sansanyan kamshi ke tashi Nan ma wani bangaren ne daban da gyar ta gano inda ta kwana saboda duk
gurin shine parlourn da yafi kankanta Amma yafi sauran tsaruwa, a hankali ta bude dakin ta shiga yana nan
yanda tabar Shi direct bedside din ta janyo wayar na Nan yanda ta ajeta Saida kudin America dollars data
gani a ciki shiya Bata mamaki Daman dasu a ciki ta saka ko Kuma daga baya aka aje Dan tab'e Baki tayi
tunda ba matsalarta bace, gurin mirror taje ta dauko kayan da Aunty Rukayya ta saya Mata ta dauko
luggage dinta ta zuba kayan ta duka ta fito daga ciki, a nan parlourn ta aje luggage din ta wuce ta ratsa duk
parlours din Shiru ba motsin kowa, ta nufi inda su Aunty zilai suke Nan ma shiru, ta dawo kitchen Nan ma
shiru abin ya Bata mamaki to suna Ina ne? Hanyar fita ta nufa sai Kara jinjina maganganun da sukayi da
Hajiya takeyi abin yayi matukar daure Mata Kai shin abinda Hajiyar makwarari ta fada haka yake ko Kuma
rudun tsufa ne kawai.
Cikin sa'a tana fitowa ta hango iya Rahane ta bullo ta bayan wani gini da wani babban basket a hannunta,
ganin zahra yasa ya tsaya tana fadin "ai Daga can nake nayi zaton ko tare kuka fita Maida Hajiyar
makwarari da shiga naji Shiru a gurin naku".
"A'a Iya Ina nan Hajiyar ma tana nan sallah takeyi Ina wuni? Wallahi tun dazu naso fitowa to saiga Hajiya
ita ta zaunar dani sai data shiga sallah na fito".
'yar dariya Iya Rahanen tayi "Lafiya kalau ya jikin naki? Sai Kuma ga Uban gidan mu yayi Mana zuwan
bazata ko? Masha Allah, ai Hajiyar sai ku kai almuru Bata gaji ba kin Sha labari dai Kam".
"Lallai kam nasha hira, Wai Kuna Ina ne? Na duba banganku ba a can".
Rike Baki tayi kamar yarinya " ke! 'yar Nan ki rufa Mana asiri, Banda dalilin wadalilatan Ina mu Ina kwana a
bangaren yallabai, tun sassafe muka dawo nan kafin Rukayya ta tafi, Bari na yiwa zilan magana ko?".
"A'a mu shiga kawai".
Tare suka karasa shiga cikin bangaren. Masha Allah guri ne Mai kyau tamkar gidansu na Azare abinda ya
banbanta su kalilan ne tunda wancan Renovation ne,wannan Kuma haka aka tsara shi sai banbancin
furnitures kawai, nan ma question mark tayiwa abun.
Jin sallamar zahra yasa zilai fitowa daga kitchen din tana fadin "Masha Allah, wallahi jiya ban samu
kwanciyar hankali ba Saida Rukayya ta shigo tace min kin wuce Daki kin kwanta har Ammah na Kira na fada
Mata Baku dawo ba, tace min na kwantar da hankalina ba komai tunda bake kadai Kika fita ba, Kuma sai
muka wayi gari da zuwan yallabai? Ai ya shigo shida oga Sameer mun gaisa".
"Eh wallahi muna cikin gari gidan Hajiyar makwarari kakar oga har dare, kunyi waya da Ammah kuwa yau?"
Saita share zancen Mahmud din.
"Eh mun gaisa tun wurin karfe shida na safe har take tambayar ya jikin naki tunda wayarki Bata shiga, nace
mata da sauki amma dai kun wuni a Asibiti Dan sai wurin Sha biyun dare kuka dawo".
"Ok.ba damuwa Bari na bude wayar na kirata sai yanzu na dauko wayar, Bari na koma na baro Hajiya tana
sallah inaga yanzu ta Gama kada ta jini Shiru amma dai Zaki zo can din ko?".
Sallama ta yiwa Iya Rahane suka fito tare da Zilan, Saida sukayi nisa sannan zahra ta tsaya itama Zilan
tsayawa tayi.
"Aunty zilai me Kika fashimta daga lokacin da mukazo zuwa yanzu?"
Zahra ta jefa Mata tambaya.
"To abin ne da yawa gaskiya, Dan ni lissafina ya kwance gaba daya wallahi na rasa tudun dafawa Amma dai
komai rintsin mijinki shine ke Jan ragamar gidan nan Dan dazu lokacin da oga Sameer ya kawo Hajiya naji
suna magana da wasu ma'aikatan gidan Nan akan oga yayi zuwan bazata, sai Kuma lokacin Daya fito a can
gurin Naga ya Tara su yana magana dasu oga Sameer Yana gefe harya gama oga Sameer ya rarraba musu
kudi muma har ya aiki wani Wanda Naga ya shigo da waccen babbar motar ya kawo Mana dubu ashirin
ashirin nida iya Rahane".
Ajiyar zuciya zahra tayi tana duban bangaren motocin hango motarta tayi a cikin parking lot din, kenan a
Nan ya ajeta ko kuma jiyan yazo da ita Nan Dan kamar Bata ganta ba jiya, rausayar da Kai tayi tana wani
tunani kafin tace.
"Muje kawai Aunty zilai mu zuba idanu a hankali gaskiya zatayi halinta, nifa duk hankalina ya koma gida
Amma naji yana fadin zasuje Azare jibi za'a dawo min da Aunty Rukayya, Kinga ba zancen komawar mu
kenan, ni Kuma abinda bazan yarda ba kenan ya ajeni a wannan gjdan da bansan asalinsa ba gashi Nan
Kashi-kashi kamar gidan marasa gaskiya".
"A'a kada kiyi haka ki Bari kiga iya gudun ruwansa Mana nasan dai baze cutar dake ba, to kiyi Masa biyayya
a duk abina ze umarceki matukar Bai sabawa shari'a ba,kiyi hakuri wata rana ma garinsu ze koma sai kice
bazaki bishi ba? ai shi aure ba inda baya Kai mace, ki duba Maman Akwanga kin taba cewa tayi rayuwar
Azare".
Haka zilai ta dunga tausar zahra har suka shiga part din da suka zauna Zahra ta dauki luggage dinta Zilan ta
karba suka shiga ta ciki suka fito barandar nan zilai sai mamakin abin take Bata taba tunanin da wani ginin
a bayan wannan ba, Bata Gama sarewa da lamarin ba Saida suka shiga ciki, a parlourn farko suka tarar da
Hajiya ta rabsa uban tagumi ta zubawa kofa idon suna shigowa ta sauke ajiyar zuciya tana fadin "Haba 'yar
Nan daga Bari na dawo Kika nemi gurin Zama Kika manta Dani saboda Allah kin kyauta min kenan? duk
sanyi ya game min jiki har attishawa na Fara nasan mura Kuma sai abinda hali yayi kawai".
Da sauri zahra ta karasa kusa da Hajiyar tana fadin "Ayya wallahi nayi tunanin ko zakiyi nafilfili ne fa shi
yasa na fita dauko wayata da kayana Dana Bari a wancen dakin, taso muje kici abinci kinji Hajiyarmu insha
Allah bazakiyi mura ba, Aunty zilai Naga da kaji a can bangaren inda muka fito kiyi Mata irin pepper soup
din da Naga kin yiwa Inna maimuna lokacin tana mura, ko a soya Mata ta tafi gida dashi".
"To in Sha Allah Bari naje ai kayan dazu wani mutum ya debesu ya mayar kitchen din part din da muka
koma harma an karo wasu kayan masu yawa mun shafa'a mu nuna Miki su".
Ta fada tana mik'ewa ta nufi kofa ita Kuma zahra ta nufi dining ta daukowa Hajiyar abinci.
*** *** ***
Tunda garin Allah ya waye Mama ke faman Kai kawo a cikin Daki ta Kai gwaro ta Kai mari, tun bayan wayar
da sukayi da Aunty larai hankalinta Bai kwanta ba sai yarfe gumi takeyi baji ba gani, ta Kira wayar Asabe
yafi Shurin masaki amsar Daya ce switch off.
Wannan wane irin Abu ne Kullum tana tubkar gaba baya na warwarewa, Wai ita wannan Matar meta taka
ne, duk abinda takeyi ya tashi a banza Kenan?
Tun bayan kaiwa Mai gadi sakon Nan Basu Kara samun damar shiga gidan Nan ba ko kofar ma tafi karfin
zuwansu gashi yanzu Kuma aunty larai tazo Mata da wani Abun d'aga hankalin ga sako Amma isar dashi
shine aiki ga wayar Asabe Bata shiga da sai ta Kai ko ta bayan gidan ne ta jefa abin bukatar dai ya shiga
gidan ga sakon ya taho daga Jos din Kuma ance ba'a son ya kwana ba'a aiwatar dashi ba, akwai matsala
Dan ze iya warware duk ayyukan baya, kuma wani aikin ze iya yin kome a Kanta ko 'ya'yan ta shine ta tada
hankalin ta, tunda tasan idan tayi sake kwabarta ce zatayi ruwa, tayi tunanin ko sahura zata aika Tasha ta
karbo sakon idan yaso sai tayi Mata bayanin yanda zatayi da sakon idan ta Kai can gidan zahrar, tayi
tunanin ko zilai zata Kira tace Mata ta fadawa Zahra sahura zata je tayi musu share-share kafin su dawo,
Nan ma taga abun ba lallai ya yuwu ba. Kara Kiran Asaben ta gwada still dai a rufe, dangwarar da wayar
tayi duk abin duniya ya taru yayi Mata yawa.
Duk iya tunanin ta ya Kare ta rasa Ina ne mafita dole ta tashi ta fice daga dakin tana tunanin dole ta tura
sahura taje ta Kirawo Mata Asaben in ba haka ba tasan watan Jin kunya ne yake neman Kama Mata.
Wannan kenan.
Tunda Ammah ta fita daga bangaren Abban take kokarin neman zahra Amma Shiru har bayan Azzahar inda
taji Dadi da zilai tace Mata zahrar a gidan ta kwana Kuma Mai gidan ma yazo, tasan kome ne ne zezo da
sauki. Banda kada yaron Nan Sameer yaga Kamar ta raina abinda yakeyi da yanzu ta tsufa a Kano, sakon
text ta turawa zahrar ta tashi ya nufi bedroom dinta.
Tun bayan fitar zilai zahra ta wuce bedroom tabar Hajiya nacin abincin ta, a gurguje ta sake wanka ta gyara
jikinta Bata wani Bata lokaci ba ta shirya cikin wata doguwar Rigar lace cotton Mai kalar blue black, anyi
touching dinsa da silver ash yayi Mata kyau sosai.Bata daura dankwalin ba rolling tayi da ash din gyalen ta
feshe jikinta da turenta ita abin har mamaki yake bata, ta rasa yanda akayi duk inda take sai taga turaren
da take amfani dashi a gurin. Dan watsa hannu tayi irin baka gane Abu ba din nan.
Parlourn ta koma gurin Hajiya dai dai lokacin da su Sameer da Mahmud suka shigo.
"Bakin Hajiya ne yaki rufuwa data hango zahra ta nufo ta Fadi take "Masha Allah! Haka ake so wwnnan 'ya
naga alama bazakiyi saken da za'a karbe miki miji ba, ki Kama abinki ki rike wallahi sonsa akeyi kamar
goron hannun sarki ki matse kayanki tunda Allah kadai yasan gwagwarmayar da yasha kafin ki shigo
hannunsa..."
Sameer ne ta katse Mata hanzarin zancen data dauko ya Fara fadin "ki tashi na mayar dake gida garin Zan
Bari yanzu Banda kina Nan da nayi nisa a Hanya".
Shi kuwa Mahmud Banda kallon zahra ba abinda yakeyi gani yayi ta Kare Masa wani sanyin kyau a
idanunsa, Kuma fir Taki yarda su hada Ido dasu duk kowa da kalar kunyar da takeji tasa.
✨✨✨
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page. 47
________Duk yanda Mahmud yaso zahra ta bashi amsa abun yaci tura da gaske take kunyarsa Bata taba
zaton Yana Jin yaren ba, shima kyaleta yayi dan bashi da amsar tambayarta a yanzu dai sai hakan yayi Masa
dadi, wata hirar ya dauko Mata ta tafiyar da yayi da ire-iren cigaban da yake ganin makarantun mu zasu
samu, har aka Kira sallar la'asar suna gurin tashi yayi suka shiga ciki yayi Shirin masallaci.
Misalin karfe takwas da kwata suka fito zuwa unguwar da zata raka shi, sunyi wata irin dacewa dole idan
ka kallesu ka Kara, Dan kallonsa tayi "Zan leka na yiwa su Aunty zilai sallama".
Daka ya amsa Mata saboda Yana amsa waya.
A parlour ta iskesu suna Hira, a gurguje suka gaisa ta fada musu zasu fita, a dawo lafiya sukayi Mata ta
juya ta nufi kofa har ta kusa fita ta ji maganar Aunty zilai bayanta.
"Uwar dakina Ammah tace a fada Miki ki bude wayarki tana son magana dake, yanzu ba dadewa ta
kirani tace na Kai Miki tawa, na fada Mata Mai gidan Yana Nan shine tace to idan kin fito na fada Miki lallai
ki bude zakuyi magana".
Dan rausayar da Kai zahra tayi da alamun damuwa a fuskarta.
"Ni wallahi na kasa bude wayar ne laifi nayi Mata fa".
"Laifi Kuma kina Nan tana can akayi laifin?"
Kai ta gyada Mata alamar Eh.
"Dan Allah ki bude wayar kuyi magana ko hankalinta ya kwanta,Allah a cikin damuwa take".
"To shikenan sai mun dawo din".
Ta fice tana amsa a dawo lafiyar Aunty zilan.
Motarta daya kawo ta gani, Wanda ya Kira da safwan dazu ya fito daga ciki da alamar shiya kawota nan
seat din kusa da driver Mahmud ya budewa Zahra Yana fadin "Bismillah"
Saida ta zauna sannan ya nufo gurin safwan din yayi Masa magana sannan ya shigo ya tayar da motar
suka nufi gate din fita, a dawo lafiya masu gadin sakayi musu Dan ba mutum Daya zahra ta gani ba.
Sunyi tafiya Mai Dan nisa kafin ya riko hannunta Bai kalleta ba gabansa yake kallo yace.
"Kina tambaya ta wannan gidan na wanene ko?"
Ya Dan juyo Yana kallonta.
"Eh" ta fada a takaice.
"Gidan a hannuna yake, kusan Kuma ni aka wakilta a Kan ma'aikatan cikinsa to Yana yin rayuwa ne yasa
nayi nesa dashi Amma yanzu bani da sabgogi da yawa Ina ga ma anan zamu Dan Zauna na wani lokacin
kafin muga yanda za'ayi akan matsalarki ta fibroid din nan dan tunda aka fada min hankalina kasa
kwanciya yayi Saida na Kira likitan dana fada Miki, shine yace ya kamata muje suyi nasu binciken su tabbar
da abinda Nan din suka fada".
Dan marairaice Masa tayi.
"Nifa wallahi na warke na fada maka ba wani ciwo fa yanzu Dan Allah ka hakura, kaga su Ammah Basu San
zamu Dade ba, kaga harda Mai aikinta ta bani aro fa Kuma kusan itace ma'aminciyarta a fannin abincin
bangaren ta".
"Kin warke kamar Yaya? Ai abinda ze Hana a duba min lafiyarki sai ikon Allah kinaji fa Yana Hana Mata
haihuwa Ni Kuma da nake son duk shekara ki aje Mana baby koma babies, idan Allah yasa nafi ki karfin jini
ki dinga bamu twins, kawai lokaci kadan ki ciki gidan da 'ya'yan mu".
Ya fada Yana Kai hannunsa akan cikinta Yana kashe Mata Ido daya.
"Oya talk Mana kinyi shiru".
"To me kakeso nace ai ka Gama Yanke hukunci".
Saita share maganarsa ta biyu.
Gidan Sameer suka Fara nufa Sam Sameer din besan da zuwansu ba Saida ya kusa da shiga kuntau din
sannan ya kirashi ya fada Masa gasu Nan zuwa.
"Masha Allah gida ne shima Babba Mai kyau sosai Amma baiko Kama kafar inda sukayi masauki ba, da
fara'a sosai Fateeha ta tarbi zahra wannan shine haduwarsu ta farko face to face ba karamin mamaki
Fateeha tayi ba, duk da Sameer ya nuna Mata wani hoton zahra amma sai taga hoton Wasa ne akan zahirin
gaskiya ba karya oga Mahmud yayi mace dai dai da level dinsa Dole 'yan bani na iya su dauki na wuta Dana
gashi da ita, me wannan mezeci da irinsu Haseena.
Da sauri ta garasa gurin zahrar tana fadin "maraba da babbar bakuwa irin wannan zuwan bazata?
Ta mika Mata yaron da yake hannunta tana murmushi, itama zahrar murmushin ta mayar Mata.
Cikin parlourn suka shiga gaba daya, gaishe da Muhmud din Fateeha tayi, yayi Mata barka, sannan zahrar
ma suka Kara gaisawa da oga Sameer, taje ta Mikawa Mahmud Babyn.
"Ki rikeshi a haka na ganshi, wallahi bana iya daukar Yara a haka tausayi suke bani, Sai naga kamar Zan
karya su ne idan na dauke su".Ya fada Yana jifanta da wani kallo.
Itama kallon nasa Zahra tayi da yi Masa alamar zakayi bayani da hausar garinku, tana Dan kada Masa sexy
eyes dinta. A haka yayi masa addu'a ya shafa kansa, cheque ya Dora Masa a jikinsa abinda ta gani jikin
cheque din ba Karamin mamaki ya Bata ba, shi Kuma Dan gogan Saiya fuske yayi kamar baiga kallon
tuhumar data bishi dashi ba.
Godiya sosai Fateeha tayiwa Mahmud ta dauki cheque din ta kaiwa Sameer, ba karamin mamaki yayi ba
yana Kara duba cheque din Yana kallon Mahmud. Kai ya girgiza Masa "don't say anything pls shi yasa ban
baka ba na madam ne wadda tayi nakudar haifar min takwara"
Shiru yayi kawai Dan wata kyautar tafi gaban godiyar fatar Baki, a haka Fateeha ta wuce ta barsu tana
kakabin abun a zuciyarta Wai shi wane irin kudi wannan bawan Allah ya mallaka Wanda baya Jin ciwon
kashe da kyautar su irin haka?.
Abubuwa motsa Baki Fateehar ta kawowa Mahmud, sannan taja zahra suka shige bedroom dinta.
Kan sofa zahra tayi masauki tana rike da Ayyan sunan da ake fadawa yaron kenan, Fateeha na fadin "
Masha Allah, Amarya kin Sha kamshi sai yau Allah yayi haduwarmu?".
"Wallahi kuwa Aunty, barka Allah ya Raya Mana".
"Amin ya Rabbi, nifa na dauka da Rana zakizo mu yini muna hira Amma sai naji sweetheart Yana fadar Wai
gaku Nan a harya".
Da gyarawa Ayyan riko tayi tana zame rolling din kanta. "nima bansan da fitar ba sai dazu da yamma yace
zamuzo nifa naso ya barni nazo suna lokacin Amma yace a'a saiya dawo zamuzo".
Har Fateeha ta bude Baki zatayi magana ta tuna gargadin Sameer akan sakin bakin magana yace ta iya
bakinta akan abida Zata fadawa zahrar.
"Kinsan komai nufin Allah ne sai yau ne ya kaddari mu hadu,munga sako Allah ya saka da Alkhairi yabar
zumunci, Kaya irin haka kamar za'a bude Masa Boutique dasu, wasu ai har ya shekara biyar sannan yayi
amfani dasu, Kinga wannan material din da Kika sako min me kalar peach wata sister dina da za'a yiwa biki
ta kwallafa rai a kansa tana son tasa ranar dinner da taje kasuwa kasa sayensa tayi 350k 4yrd, saita gano na
sayar Mata da nawa tunda suna gidan safwan ya kawo kayan".
Ita dai Zahra Shiru tayi Dan ji tayi wani bambarakwai tunda ita dai bataga wasu Kaya ba, amma saita
wayance da fadar "lah ba komai ai dan "komai nayiwa d'ana ban fad'i ba, Allah dai ya Raya Mana yayi
musu Albarka".
"Allahumma Amin".
Knocking akayi daga waje, umarni Fateeha ta bayar wata yarinya 'yar matashiya ta shigo da babban tray da
kayayyakin motsa Baki a Kai ta aje ta gaishe da zahra ta juya ta fice.
Suna cikin hira Sameer ya Kira yace zahra ta fito zasu wuce.
Har gurin mota suka rakosu suna ta godiya, jikin window din da zahra take ta Dan leka tana "Fadin zamu
mu shigo in Sha Allah mu yini a gurinki tunda ni bakizo Mana da rana ba".
"To ai ba laifina bane Kinga niba sanin garin naku nayi sosai ba sai a yanda akayi Dani".
Dariya Fateeha tayi "to ai kin Zama 'yar kanon kema tunda gaki a cikinta Baki San ranar barinta ba".
Sameer ne ya yiwa Fateeha magana ta yiwa zahra sallama, ta bude back seat ta saka ledar dake hannunta.
Direct gandun Albasa suka nufa gidan mommy, zahra Bata tashi Jin abinda tayi da Bata kyauta ba Saida
suka shigo harabar gidan mommy din.
Dan marairaice Masa tayi da fuska a Karon farko ta riko hannunsa.
"Please me amor ka shiga Kai kadai wallahi kunyar mommy nakeji bazan iya shiga ba".
Ta fada a shagwabe kamar zatayi Masa kuka.
Saida ya gyara parking sannan ya maido hankalinsa gaba Daya gurinta.
Meya hadaki da mommy Kuma da kike Jin kunyar haduwa da ita?".
"Jiya fa harda ita a gidan Hajiyar oga Sameer".
Mai gadi ne ya karaso Yana gaishe da Mahmud tare da jera masa godiya wadda zahra Bata Dan isalinta ba,
fitowa Mahmud yayi suka gaisa da Mai gadin,abinda ya tilastawa Zahra fitowa, gaishe da Mai gadin tayi ta
Dan Fara tafiya duk da Batasan inda kofar shigar take ba.
Gurin wasu kujeru data gani ta nufa ta zauna da alamar Kamar Baki ne suka tashi daga gurin.
A Nan ya sameta ya Mika Mata hannunsa ta kama ya mikar da ita tsaye, "zo muje ciki dare Yana karayi kin
zaunar damu a gurin Fateeha kome kuje fada ma oho Allah yasa dai ba gulma kujeyi ba".
Kafin tayi yunkurin bashi amsa daga bayansu sukaji maganar Rukayya "lah wa nake gani kamar Ya Mahmud
da Auntyn mu?"
Da sauri zahra ta zame hannunta ta juya baya tana Fadin "wallahi Aunty Rukayya nayi fushi saboda Allah
saiki taho bako sallama".
"Ayya sorry wallahi Nima karfina akafi dole tasa na taho kinsan Ya Sameer ba sauki shine ya tattaroni ko
wanka fa sai a gidan Nan nayi".
Ta juya ya Mahmud Ina yini an dawo lafiya?".
"Lafiya kalau Ruky ya kikaji da 'yar rigima Ashe Kuma yaji tayi muku ta gudu".
"Wallahi kuwa ya Mahmud ai jiya nayi kuka kamar ba gobe tashin hankalina Daya idan ta B'ata me za'a
fada maka idan ka dawo Ashe kana hanya".
Baki zahra ta zubura tana kiftawa Rukayya Ido.
Kafin yayi magana sukaji magana daga bayansu.
"Waye nake gani kamar DANGEN SHUNI!?"
Da sauri Mahmud ya juya itama zahra juyawar tayi Jin kamar muryar data sani ce take Fadin hakan.
"Lah! Lah! Lah! Wa nake gani haka? Zakariyya Daman ana ganinku, rabon da mu hadu tun zuwana na
karshen kontagora".
Zahra ce ta Matso tana Fadin Lah Ya Abba, Kaine ina yini?"
"Lafiya kalau ya kukaje gida? ai da safe na Kira Rukayya take fada min bakwa tare ta dawo gida".
"Eh wallahi, yasu Umma?"
"Suna lafiya daga Ina haka?"
Dan kallon Mahmud tayi kafin tace Masa "daga gida muke Mommy mukazo gaishewa".
Kusa da Mahmud ya matso Yana Fadin "DANGEN SHUNI! Allah ya taimaki manyan kasa. Daman ana
ganinku haka available? Gaskiya na zama lucky. Daman wallahi neman number ka nakeyi nayi interview da
kamfanin ku na Nan Kano last two weeks Amma har yau ban samu number ba, kasan lamarin kasar Saida
wakasani,to ya akaji da jama'a?"
.
"Lafiya kalau Alhamdulillahi, Rukayya ki bashi number ta zamuyi maganar later, ko kana Shirin Zama
sirikina ne?".
'yar dariya yayi "Hakan nake fata ai zuwan zahra jiya Ni Alkhairi ya zamar min".
Dan Jim Mahmud yayi, me kenan zakariyya kenan brother din sajida ne?
"Anyway we'll talk later in Sha Allah, madam let's go".
Sukayi sallama da Ya Abba suka nufi ciki zuciyar zahra fal murna wato duk abinda Allah yayi akwai hikima a
cikinsa, wannan dalilin ne yasa ta tattara ta nufi Janbulo Ashe ita zata Zama dalilin haduwarsu.
Saida suka gulewa ganinsu sannan Ya Abba ya kalli Rukayya, "Daman Kuna da relation da DANGE?".
"Eh aminin Ya Sameer ne tun suna secondary School, yanzu haka shine P.A dinsa ai jiya zahra da muka
dauko daga can wife dinsa ce an samu wani incidence ne tayi tafiyar ta can Janbulo din".
Baki sake yake kallon Rukayya abin jinsa yake kamar Almara badan ya gansu tare ba baze taba gaskata
zance Rukayya ba, gaskiya he's surprised to ai shi ba haka maganar tazo Masa ba daga bakin sajida.
"Nima naji kadan daga labarinta gurin ya Sameer to ga dai mijinta Nan sauran bayanin Kuma ban San
yanda akayi ya faru ba, tunda ya Sameer ba fada mana zeyi ba".
A parlour suka Sami mommy da kannan Rukayya Mata Bilkisu da Husna sai karamar yarinya 'yar Auntyn su
Sameer Afra.
Tunda suka shigo zahra ke sadda Kai kasa da gaske nauyin mommy take ji, gaisuwar yaran suka ringa
amsawa da gudu Afta ta nufo zahra tana Fadin "welcome Aunty" ta shige jikinta tana tattabata.
Hannunta zahra ta riqe suka karasa gurin da mommy ke zaune yayin da su Husna suka koma dayan
parlourn.
A kasa Kan carpet suka zauna, a tare suka gaishe da mommy din, ta yiwa Mahmud sannu da dawowa
sannan ta Dora da godiya, hidima da akeyi da Sameer. Zahra ta kalla ganin sai sadda Kai tajeyi yasa tace.
" 'ya ta ko jikin ne Naga bakya walwala sosai?".
Yana ji yayi fuska Bai tankaba ba dai iya shegen da tayi ba kenan jiyan saita magantu da bakinta.
Bata yarda sun hada Ido ba tace.
"A'a ba komai mommy lafiya ta kalau".
"To Masha Allah haka nake son ji, kina jina ki saki jikinki Dani ki daina Jin nauyi na kinji, ni uwace idan kina
da damuwa duk da bama fatan hakan ki sameni ki fada min ki daina yanke hukunci da kanki".
"To in Sha Allah bazan qara ba na gode". Ta fada tana Wasa kitson Afra kanana Yar dasu.
Tashi mommy tayi tana fadin "Bari na fadawa Alhaji kunzo sai ku shuga ki gaisa yaga 'yar tasa wadda bai
sani ba".
Ta nufi nufi wani corridor dake hannun dama.
Bata dade ba ta dawo tana fad'in "Mahmud kuje Yana parlourn kasa". Saida aka yiwa Afra wayo da
chocolates sannan ta yards tabi mommy dakinta ita Kuma zahra suka nufi bangaren Abban su Sameer din.
A Nan suka same shi a parlourn Wanda yaji kayan more rayuwa dai-dai da shekarunsa, babban mutum mai
cikar Kamala, fari sosai kamar irin buzayen nan, a Nan zahra ta gano inda Aunty Rukayya ta samo farin ta
dan mommy dai irin wankan tarwada din nan ce shi yasa tayi mamakin Jin Rukayya kanwarsa ce uwa Daya
uba Daya.
Da madaukakiyar fara'a ta taresu Yana fadin "Masha Allah sannunku da zuwa, ka kyauta Mahmud daka
kawo min yarinyar nan kaga na Riga Alhaji Muhammad ganinta ko? masha Allah ku zauna".
Ya fada Yana nuna musu seat din Zama, basu zauna ba a kasa suka zauna suna gaishe shi, ya amsa cikin
sakin fuska, da gani shi mutun ne Mai yawan fara'a.
"Allah yayi muku Albarka ya kade fitina a tsakaninku naji Dadi kwarai daka kawo min ita, yarinya ayi hakuri
da juna kinji, mijinki na jama'a ne Saida hakuri kiyi Masa biyayya gwargwadon iyawarki, Kai Kuma ka kula
da lamarin ta kada ka yarda wani ya wulakanta maka ita amana ce suka baka, a yanda kaje musu ba kowa
ne ze dauki yarinya kamar wannan ya baka ba, to ka kula da ita sosai ka Bata dukkan farin ciki tayi rawar
gani, daga karshe Ina rokonka abinda ban taba saka Baki a cikin duk kwaramniyar da akayi a baya ba sai
yau, kayi hakuri ka koma gida ba girmanka da mutuncinka bane haka ai ba'a fushi da iyaye duk rintsi
albarkarsu ake nema kome ka Zama indai kana da iyaye yaro ne Kai, nasan an bata maka Amma idan ka
duba ko tukwicin wannan yarinyar da Allah yayi Maka ai sai ka huce ka nuna godiyarka ga Allah Daya baka
ita, Kai ba karamin mutum bane a kasar Nan Koda kuwa a shekaru kake da karancin girma, kaje gida ka
hada hankalin ka guri daya, Allah yayi Albarka ya Kara daukaka numa ganin sakonni mun gode kwarai da
gaske, idan Kuma naji Shiru baka koma ba da kaina zanyi abinda baka so ayi din, Dan ko shekaranjiya Saida
Hajiya Inna Tasha kukanta a dakin Nan Ina amfanin irin haka ai musulmin kwarai da yafiya aka San Shi kaji
Mahmud ayi hakuri ayi afuwa Allah yasa son masu yafiya".
Tunda Alhajin ya Fara magana jikin Mahmud yayi sanyi da gaske duk badak'alar da akayi ko uffan Bai tofa
ba sai yanzu Kuma yasan baya raba Daya biyu damuwar da yaga hajiya Inna a ciki ta Dame shi.
Cikin ladabi Mahmud ya Fara magana. "Nagode Abba in Sha Allah Zan koma, Nima nayi wannan tunanin
ba fushi nayi dasu ba sune dai sukayi fushi dani, Ina son su huce ne tukunna kada na koma a maido
hannun agogo baya".
"Kai haba wannan maganar ai babu ita to ai itama zahara'u ta zamar maka garkuwa, ki tashi ku tafi dare ya
Farayi ga yanayin sanyi Allah yayi Albarka ayi kokari ayi yanda nace".
"In Sha Allah Abba".
'yar karamar Leda Fara Alhajin ya mikowa Mahmud Yana fadin "ungo rikewa 'yata".
Godiya sukayi Masa Sosai suka nufi kofa Yana saka musu Albarka.
Lokacin da suka fito Rukayya ta shigo suna tare da mommy.
"Aunty Rukayya har Ya Abban ya tafi?". Zahrar ta fada tana nufar inda Rukayyar take.
"Eh ya wuce tun dazu".
"Ok shikenan da sako Zan bashi gurin Ummah Amma na Kirata a waya".
Sallama sukayiwa Mommy Rukayya ta rakosu har gurin mota da ledar da mommy ta bawa zahra kyautar
dangin turaren wuta dasu humra.
Da sukazo fita kudi masu yawa taga ya bawa Mai gadin gidan sannan suka wuce, tunda suka fito daga
parlourn Alhaji Abban su Sameer Mahmud yayi dif da alamar anyi Masa famin wani Miki a zuciyarsa.
Ganin haka yasa zahra ta Kama kanta itama.
Titin gidan Bashir tofa suka fito gasu can sun fita gidan Buhari, sahad store taga ya shigo ya nemi guri yayi
parking sannan ya bude Yana Fadi ki jirani ina zuwa ya wuce ciki.
Bai Dade da shiga ba wata mota tayi parking kusa da tasu, gurin akwai wadatar hasken da yasa kana iya
ganin Wanda yake cikin mota.
Ba zato ba tsammani kawai idanun Zahra suka sarke Dana Musbahu Wanda ya fito daga gurin driver suna
tare da wani Guy da alamar dayan irin ya'yan hutun Nan ne, da gani Suma sayyayar sukazo, da sauri ya
nufo gurinta jikinsa har rawa yakeyi Yana fadin "Zahra!" dai-dai lokacin Kuma Mahmud ya fito tare da
ma'aikatan gurin sun dauko Masa Kaya sun nufo motar, shi Kuma wannan gayen Yana ganin Mahmud yayi
wata irin zabura ya nufeshi ya rungume shi jikinsa na wata irin tsuma Yana fadin "Ya Mahmud Ina ka shiga
ka barmu".
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page 48.
___ Rungume juna sukayi sosai, kuka ya saka Masa kamar karamin yaro da gani ba karamin missing
dinsa yayi ba , Shima Mahmud Jin wani Abu yake yi a zuciyarsa badan namijin duniya bane da Babu
abinda ze hana shi zubda hawayen shima, yayi kewar Faruq sosai saboda sunyi wata irin shaquwa dashi ta
ban mamaki,duk da ba uwa daya ta haifesu ba Kuma kusan sa'anni ne Dan baifi wata hudu Mahmud ya
bashi ba, Amma Yana bashi girma sosai,duk abinda yakeyi hankalinsa dari bisa dari Yana Kan musbahu
Wanda yayi mutuwar tsaye shi Bai karasa gurin zahrar ba, shi kima bai dawo baya ba, me yake Shirin
faruwa ne? wannan din meye dinta yasan dai tayi aure ance wani k'olo aka aura mata, to Ina auren kada
dai gudowa tayi ta shigo yawon duniya?.
Ita ma zahrar ji tayi komai ya tsaya mata, har wata zufa taji tana tsatstsafo Mata a jikinta abun kamar a
mafarki, gurin da su Mahmud suke ta kara kallo still suna yanda suke Saidai gaba Daya hankalinsa Yana
gurinsu fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin kamar dade duniya be taba dariya ba, sadda Kai zahra tayi
dan ji tayi wani irin tsoronsa na shigarta tuna karonsu tayi wanda ya kusan cinye mata lebe, kasa tayi da
kanta jiran taji ya zata kaya.
Bayansa ya Mahmud ya ringa Dan bubbugawa da tafin hannunsa Yana fadin.
"Haba Faruq meye na kuka da girmanka da komai Kai ba mace ba, ka nutsu ka share wannan hawayen,
akwai mace fa a kusa damu tana kallonka, wallahi wata Rana sai tayi maka gorin ragon maza"
Ya fada Yana sakinsa da sauri yama duban masu rike da kayan daya saya a hannu "sorry na barku da Kaya
kuyi hakuri Dan Allah mu karasa ku saka a mota"
Yayi gaba yana yiwa Mushahu wani shegen kallo, Faruq na rike dashi ram Kamar Yana gudun ya bace Masa.
Back seat Faruq ya bude suka zuba kayan,Faruq din ne ya curo kudin da baisan yawansu ba ya Mika musu
sukayi godiya suka wuce bakin aikinsu.
Jikin motar Mahmud ya tsaya Yana facing din musbahu da fuskar shanu.
"Dan Allah Ya Mahmud kana Ina ne duk tsawon wannan lokacin? Kuma wacece wannan da kuke tare?"
Fuska Babu annuri Kona sisin kwabo ya Maida dubansa Kan Faruq din "Idan ka Gama abinda kazoyi ka
sameni a Bawo road komai dare Ina jiranka". Ganin yanda mahmud ya daure fuska yasa yaja bakinsa yayi
shiru be kara tambayarsa komai ba.
"Ok. Zan shigo yanzu ma in Sha Allah, Nima yau na shigo around four thirty, yanzu ma uncle mushahu na
rako, dan yayar Mamee ne gashi nan,bari nayi masa magana ku gaisa be ganeka bane".
Da hanzari Mahmud ya daga masa hannu "pls Faruq no need". Ya fada yana dhugewa motar, abinda ya
daurewa Faruq kai kenan, wai Ya Mahmud ne yake driving da kansa, sai yake ganin kamar an canza masa
Ya Mahmud dinsa da wani.
Saida ya fice daga harabar gurin sannan Faruq ya karaso gurin Uncle dinsa yana fadar "Yanzu fa a hanya
muke maganar Ya mahmud da kai ashe yana kusa damu wallahi ba wanda ya zaci yana kasar nan, abinda
ya bani mamaki wannan Babyn da suke tare a sanina da Ya Mahmud baya harkar mata gaskiya, sai dai ban
sani ba ko bacin rai ya saka shi yin hulda irin wannan dasu".
Faruq be ankare da shi kadai yake zubarsa ba sai da ya kai aya yaji Musbahu be tofa masa ko A ba sannan
ya dan taba shi.
Firgigit yayi alamun yayi zurfi a cikin dogon tunani.
Dogon numfashi yaja yana yiwa Faruq duban tsanaki, kafin yace.
"Faruq waye wannan nake gani kamar Mahmud?".
Tunda Mahmud ya fice daga harabar sahad store ya saki motar yana wani irin tuki, ko iskar data aje zahra
be duba ba itama takurewa tayi jikin kofa da gaske shakkarsa takeji dan ya hade gabas da yamma kudu da
Arewa, ya doki sitiyari yafi sau shurin masaki.
Ita dai zahra sai addu'a take Allah ya sauke su lafiya, gaban wani gida taga ya tsaya Mai shegen kyau haske
ya cika ko Ina da karfi ya danna Horn din kamar ance masa Mai gadin sabon kurma ne, da sauri ya fito ya
nufo motar banban mutum ne ba yaro ba, ganin baisan motar ba yasa ya karaso da sauri ganin Wanda
yake wannan mahaukacin horn din.
Bazato yayi arba da Mahmud, da sauri ya zube Yana kwasar gaisuwa, hannu kawai ya iya d'aga Masa da
sauri ya koma har Yana hadawa da gudu yaje ya bude gate din, da gudun dai ya shige har kofar ya nufi ba
parking space ba, kofar da zata sadaka da main parlourn ya tsaya ko motar be tsaya kashewa ba ya zagayo
ya bude side din zahrar take zaune yasa hannu ya fisgota waje, be saurari komai ba ya nufi steps din shiga
ciki da ita, ganinsa kamar mahaukacin Zaki ya saka zahra cikin tashin hankali, da hannu Daya ya zura katin
ya bude kofar, be tsaya a parlourn ba direct upstairs ya nufa da ita tana turjewa tare da fasa masa kuka
Dan wani irin riko ya yiwa hannun Kamar ze tsinke Mata tsintsiyar hannu, be saurareta ba Saida ya
dangana da inda yayi niyya bedroom din da suke sama guda uku, ya nufi na kusa dashi da karfi ya tura
kofar da suka shiga yasa kafa ya Maida kofar,Kan wani lafiyayyan Turkish bed yayi musu masauki, yana
zuwa Bai bi takan kukan da takeyi ba ya saka hannu ya fisge Rolling din da tayi yana huci.Dan magana ma
ya kasayi saboda wani Abu da yake taso Masa, baya tayi da sauri ganin Yana neman cakumo rigarta, Kan
gadon ya hauro Shima ko takalmin kafarsa be cire ba, Rigar jikinsa ya cire yayi jifa da ita, ya kamota tata
Rigar ms yasa hannunsa ya karketa tun daga sama har kasa, take jikinta ya bayyana, ya kasance daga ita sai
farar bra tas da farin pant a jikinta,jikin Nan sai wani glowing yake kamar kifi tarwad'a, cikin tashin hankali
da matsananciyar kunya ga kuka take fadar "Dan Allah kayi hakuri me nayi maka wallahi bani na kirasa ba,
shine ya ganoni ya taho ko magana banyi Masa ba,ai kana kallon mu, wallahi bansa zasuzo ba ba Kaine ka
kaini gurin ba?".
Ta fada tana kankame jikinta.
Duk abinda ke jikinsa ya cire ya jefar, Shima Dan ganinta a haka ba karamin bijiro Masa da tsohon tsimi yayi
ba Rabon da yaji haka tun karonsu a Azare lokacin data farfada Masa maganganu Hannu yasa ya fisgota
jikinsa ya fisge brezier da karfi ya jefar, Yana fadin.
"Daman kun shirya had'uwa dashi shine yasa Kika gudu d'aga gidan Hajiyar ko? saboda ki samu damar
sheke ayarki tare dashi tunda be aureki ba ai sai kije yayi abinda yaga dama dake ko? Niga sakarai Wanda
besan inda yake masa ciwo ba, yau basai gobe ba zamu raba wannan rainin ni dake, ganin na daga Miki
kafa Ina tausayinki yasa raini ya Fara shiga tsakaninmu ko? abun har ya Kai a gabana ake neman
rungumarki wlh da yayi wannan gangancin Daya gane maza suna suka tara, idan kina cikin matsuwa saiki
fada min ba kije kina kyarkyara ba a waje na isa nayi satisfied din duk fitinarki yarinya, sarauki ne ni Zan iya
da duk bukatarki, ya Kamo hannunta ba zato taji ya Dora shi a......."
Cikin wata irin zabura tayi wani juyi kafin ta Kai ga sauka ya cakumota gaba dayanta ya dawo da ita jikinsa,
jikinta sai tsuma takeyi kamar ana kada Mata gangi.
Dai dai kunnan ta ya saka Bakinsa.
"Ina Zaki ai yau no way out, badai abinda kike muradi ba kenan?Baki da matsalarsa na fiki finita Dan haka
kizo mu kwada daga Nan zuwa wayewar gari". Yana gama fada ya hade bakinsu guri daya Dan kukan ta
nema yake ya karya Masa zuciya.
Da zafi- zafi yake tafiyar da ita Dan da gaske duk wani Alkawari ya jingine shi a gefe yau jinsa yake kamar
mayunwacin zakin da ya kwana uku baici nama ba ko yaron Daya wuni baisha Mama ba Saida tafiya tayi
nisa yaji labarin ya canza salo dan shi harga Allah ya wani manta tani wani period.
Kankameta yayi Yana wani irin numfashi har Saida tsoron da tajeji ya ninku ta dauka ko somewa zeyi cikin
wata dasheshshiyar murya yace Mata "marata ciwo take min duba dakin tsakiya ki dauko min wani
magani a cikin kwalba a bed side din jikin gwdin " ya Kamo hannunta ya Dora akai taji wani dumi a marar
tasa, matse hannun nata yayi Yana sakin wani Nishi cikin galabaita, take ta Kara rudewa da sauri ta tashi ta
daura gyalen ta tunda Riga ta tashi daga aiki da sauri ta fita tana waiwayensa ya rintse idonsa hannunsa
Yana Kan mararsa.
A bude dakin yake Bata tsaya kallon dakin ba, bedside din ta nufa direct cikin ikon Allah wadda ta Fara
dubawa a Nan taga kwalbar da kananun tables a ciki, har zata fito taga irin karamin fridge a dakin, budewa
tayi da sauri cikin sa'a ta samu ruwa a ciki ta dauki Daya ta fice da sauri tana shiga ta nufe shi da sauri tana
Fadi tashi kasha ga maganin, taji Shiru Kara matsawa tayi tana Masa magana Nan ma shiru taji da sauri ta
hau gadon tana girgiza shi cikin tashin hankali.
✨✨
MAMAN FATEEMAH.
P. 49
______ Duk budirin da take Yana jinta tana ta faman jijjiga shi Sai da yaga da gaske hankalinta ya tashi
sannan ya dago kansa Yana kallonta da hargitsatstsun idanunsa, wata ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta
kauda idanunta da gasken gaske wani irin nauyinsa takeji, matsowa jikijnta yayi a hankali ya sakata a jikinsa
Yana fitar da numfashi a jikin wuyanta, wata irin kasala ta kara saukar mata gashi ba halin kwacewa ya
kanainayeta ta ko ina.
Cikin kunnenta yayi maganar da wani yanayi Mai wuyar fassarawa. "bani maganin na Sha".
Da sauri ta Mika masa 'yar kwalbar, jikinta ta janye da sauri ta dauko robar ruwan data Dan gangara wurin
karshen gadon.
Kwara biyu ya Ciro maganin ya karbi ruwan ya watsa maganin a bakinsa yabi da ruwan, Saida ya shanye shi
tas sannan ta karbi robar.
Zanewa yayi ya kwanta rigingine, hannunsa Yana dafe da goshinsa Dan ji yayi kansa Yana wani irin Sara
masa, ganin haka yasa zahra janyo blanket din ta rufe jikinta dan itama har lokacin jikinta Dan karkarwa
yake mata daga ciki.
Sun jima a haka kowa da abinda yake sakawa a tasa Zuciyar, Amma ita zahra Hamdala take ga Allah Daya
tarfawa garinta nono, tab da yanzu ba wannan batun akeyi ba, tsikar jikinta ce ta tashi sharrrrrr.. jikinta ta
kankame guri Daya tana ayyana wani Abu a cikin ranta, Jin motsin tashinsa tayi, dan waiwaya inda yake
kwance tayi taga ya tashi ya nufi toilet Yana hada hanya.
Har ranta taji tausayinsa sai dai tafi tausayin kanta a kan halin da yake ciki.
Ya jima tsakiyar ruwan sanyi Yana dukan jikinsa,sai ajiyar Zuciya yake saki ba kakkautawa tamkar yaron
Daya wuni kuka baiga uwarsa ba, Saida ya samu nutsuwa sosai sannan yayi wanka ya fito har lokacin tana
kudundune a cikin blanket din.
*
Har gate din gidan Mai adaidaita sahun ya kawo Faruq yana fadin "Yallabai kayi muhalli Mai kyau Allah ya
kawo abokiyar Zama ta gari Masha Allah".
Shi dai Faruq hankalinsa in yayi dubu to Yana Kan ya shiga yayi arba da Ya Mahmud dinsa badan yaso ba ya
taho ya barosa, yaso kafarsa kafarsa su taho dan gani yake kamar guduwa zeyi ya rasa inda ya shiga, kudin
da baisan adadinsu ba ya Ciro ya mikawa Mai Dan sahun yayi gaba. Yana Jin Mai Dan sahun na fadin "
Yallabai kudin fa sunyi yawa ka duba kuwa?"
Bai waiwayo ba ya dago masa hannu Yana fadin "kaje ka Kara petrol da sauran". Yayi gaba abinsa, yana jiyo
yanda yake kwararo Masa addu'a kamar ba gobe, da yake irin mutanen Nan ne masu kaifin harshe kamar
jikan maroki.
Sau biyu Faruq yayi knocking din gate din,malam Musa ya leko ta kofofin dake jikin gate din, ganin shine
yasa da sauri ya bude Faruq din ya shigo, sun yiwa juna farin sani tunda sun Sha zuwa da Mahmud suna
kwana idan wani Abu ya kawo su kanon, sauda yawa anan gurin malam musan yake zama idan baya son
fita ko Ina.
Cikin mutunta juna suka gaisa malam Musan yake fadar "Ashe tare kuke da yallaban Amma kunyi shigowar
dare gaskiya, kaga motar can ma a kunne ya barta Naga kamar Matar tasa Bata Jin Dadi, dan da sauri suka
wuce ciki ko motar Bai samu damar rufewa ba, nayi mamaki da naga yau yallabai da kansa ma yake tukin
motar".
'yar dariya Faruq yayi, Bai tofa ko kalma Daya ba akan maganar tasa da yayi akan Ya Mahmud din, gurin da
motar take Ya nufa Yana fadin.
"Ina zuwa Baba Musa Bari na gyara parking din".
Zuciyarsa fari tasss, Daya samu Mahmud a gidan ba kafa ya bashi ya gujewa haduwarsu ba kamar yanda ya
yanke hulda da kowa, bai San Yana da irin wanna Zuciyar ba Saida aka samu matsalar, Amma Abu mafi
daure Kai yanda Baba Musa yasan matarsa ce har yake fada Masa, ko a Ina ya samu labarin dasu Family
dinsa Basu sani ba?.
Saida ya Kai motar parking lot sannan ya dawo gurin Baba Musa ya zauna suka Fara Hira, tunda mutuminsa
ne sosai, sai da sukayi nisa a hirar sannan Faruq ya tambayi Baba Musan ko da sabuwar lambar Ya
Mahmud a gurinsa shi ya baro wayarsa Mai sabuwar lambar a gida, tunda ya fada Masa ba tafiyar su Daya
ba, shi biki yazo garin, shine ya shigo tunda ya fada masa Yana garin.
Ba musu ya Miko masa wayar yana fad'in.
"Duba ka gani Nima jiya jiya nan ya kirani da ita yake fada min za'a kawo kayan gyaran wancen sabon ginin
da aka Gama".
Ya fada Yana nuna Masa inda su Mahmud din suka shiga.
Number ya saka a wayarsa ya maida Masa wayar Yana fadin "dauko min keys din wancan part din na shiga
na kwanta na gaji sosai".
Dakinsa ya shiga ya fito Yana fadin gasu ka duba niba banbancewa nakeyi ba. Amsa yayi yayi masa sallama
ya nufi part din Zuciyar sa fal da tambayoyin Daya Kamata ace ya yiwa Baba Musan Amma gudun bada
wata kofa da za'a Sami wata kofar sanin wani abun yasa yaja bakinsa yayi shiru.
Har Mahmud ya shirya cikin pyjamas dinsa sky blue tana kudundune a cikin blanket din, duk Kai kawon da
yake tana jinsa amma ko motsin kirki batayi ba, sai ya Gama komai ya nufi kofar ficewa daga dakin ya juyo
kadan Yana Kare Mata kallo da gaske ita ce rauninsa yaga alama, a hankali ya koma cikin dakin yaje har
inda tayi wurgi da hand bag dinta ya tsuguna ya dauka ya koma gefen gadon ya zauna ya bude jakar,
wayarta ce da sauran tarkace irin na Mata sai ATM cards dinta da 'yar robar maganinta a ciki na wajen
Hajiyar makwarari, ATM'S din ya dauke da wayar da sauran kudin data Ciro jiya a Hanyar Janbulo, harya
mayar da jakar ya ajiye sai kuma yayi saurin Kara daukota kamar Wanda aka tsikara ya Kara budeta cikin
wani zip na gefe ya bude takardu ya gani ya cirosu duka passport dinta ya gani da wasu magungunan da
aka Bata na Asibiti sai takardun tests da akayi Mata na Azare Dana Nan kanon.
Passport din ya dauke ya hade da abubuwan daya dauka ya Mike ya fice daga dakin yana saka Mata alamar
tambayoyi masu yawa.
Saida taji ya fice daga dakin da kusan minti goma sannan ta samu zarafin tashi zaune tana Dan turo Baki
tana 'yan matanganunta a ciki Wanda ita kadai tasan me take fada.
Sai lokacin ta shiga bin jikinta da kallo ita fa duk ya dagula Mata Lissafi. Banda taimakon Allah da yanzu ba
wannan batun akeyi ba, tsikar jikinta ce ta kara tashi yarrrr kankame jikinta tayi tana sauki wani malalacin
numfashi, tare da furta "Narrow escape".
Ta Kai dubanta inda yayi Mata wurgi da kayan jikinta, ita har zuwa lokacin ta rasa meya tunzura shi haka
daga ganin Musbahu ita ba ita takai kanta ba, ba ita tace ajeba ballentana yayi tunanin setup ne.
Itama wankan ta shiga yi tana zuwa ta duba jikinta cikin ikon Allah period din ya dauke Daman tun safe
taga alamun hakan duk pad din data saka a yinin haka nan take cirewa, ta yanzu ma hakan ce ta kasance,
tayi hamdala ga Allah tafi a qirga wato ba karamar kariya wannan pad din ta Bata ba.
Wankan tsarki tayi tare da wankan sabulu ta fito daure da towel, yanzu ta Zama 'yar gari gurin suturar
sakawa, gurin kawai ta nufa ta Ciro Riga da wando sleeping dress masu rawa ta saka ta dauko hijabi ta
shimfida sallaya ta tayar da sallar magariba da insha'i.
Mahmud Yana fitowa dakin Daya tura zahra dauko Masa magani ya shiga, direct wurin wasu lokoki ya nufa
a ta tsakiya ya bude ya zuba duk kayan daya dauko a Jakarta, wayar kadai ya rike a hannunsa.
Kira ne ya shigo wayarsa yana dubawa ya gane number Faruq ce.
"Ya Salam". Ya furta a hankali wallahi ya manta da batun Faruq kwata kwata Saida yaga kiransa ya tuna
Daya hadu dashi ma, to Ina ya samu wannan number din shidai yasan be Kira wasu mutane da yawa ba da
layin Dan sabo ne jiya ya Fara amfani dashi, sai Kuma ya tuna ya Kira malam Musa dashi jiya yasan a
gurinsa ya karba, tasowa yayi ya nufo parlourn farko Yana dealing number din Faruq din.
Yana dagawa yace Masa "ka shigo sabon part din nan ka sameni a parlour". Ya yanke Kiran..
Cikin kujera two seaters ya zauna a kasalance badan Shima Yana Jin kishirwar haduwa da Faruq din ba da
Babu abinda ze fito dashi ba.
Fitowa yayi da zummar dauke motar Daya Bari a gurin, ga mamakinsa Bata gurin a parking space ya hango
ta, Dan murmushi yayi yasan aikin Faruq ne.
A Nan ya tsaya ya Zuba hannunsa a cikin aljihun rigar Yana shaqar iskar dare da take kadawa a hankali Mai
dadi, malam Musa ne ya hango shi a tsaye a gurin da sauri ya nufo gurin Yana fadin "barka da dare yallabai
anzo lafiya?".
Hannu ya Mika masa duk da nokewar da malam Musan yakeyi sai da sukayi musibaha. Mahmud din na
fadin "lafiya kalau Alhamdulillahi, nagode kwarai, ya iyalin naka da jikin".
"Wallahi Alhamdulillahi kamar ma batayi lalurar ba, Allah yaja da Rai ya Kara daukaka yaja da ran mahaifa
ya baka zuri'a d'ayyiba".
"Allahumma Amin".
Faruq ya amsa addu'ar lokacin da yake karasowa.
Komawa bakin aikinsa Malam Musa yayi su Kuma su Mahmud Maimakon su koma Daki sai suka gangaro
kasa gurin irin hut (bukka) din Nan ta zamani an wadatata da isashshen haske Mai wani daukar hankali
Wanda ya Kara kawata gurin.
Zama sukayi a tare kusa da kusa tamkar Muhmud din ze gudu cikin murye me rauni Dan har idanunsa sun
cicciko da hawaye Faruq ya Fara fadin "why me yasa kayi haka Ya Mahmud? Kasan yanda kabar baya da
kusa kuwa? Rayuka da yawa sun baci Kasan Ammi ma zazzagewa tayi tayi tafiyarta Niger, sai fa a wancan
satin ta dawo sokoto. Lamarin babu Dadi ko kadan ga Hajiya Inna ma ta tashi hankalinta Wai itace tayi silar
barinka gida tunda ita ta kara tunzuraka da maganganunta, ga Abie ya Kori Aunty Samira da Safna har da
masu aikin part dinta Dan sai daga baya maganganu suka dunga fitowa har da asiri fa sukayi maka akan
kabar Sokoto har abada ko sunanta kada kara tunawa, Kuma Duk abinda kake dashi ya lalace,kasan wani
abun mamakin Wai a cikin masu tayata wannan shirkar harda uncle Saminu".
Sai lokacin Mahmud ya dago da Kansa ya kalli Faruq dan tunda ya Fara maganar yaji kamar a lokacin abin
yake faruwa.
Cikin cikakkiyar kamalarsa yayi wani murmushi kafin ya bude bakinsa cikin Jin Kai Dan maganar ma kamar
baya son yinta Dan har lokacin jikinsa ba daidai yake jinsa ba yace "Na sani mana sosai ma kuwa, ai kome
akace yayi ba zanyi mamakinsa ba, kasan ya tareni gaba da gaba yace min ba dai Ina takama da nafi 'ya'yan
su rufin asiri ba shi yasa nace bazan auri 'yarsa Asma'u ba, shima ai ba matsiyaci bane to sai yayi min
sanadin da sai zaman sokoto dama kasar Baki Daya yayi min wahala, Sam ban kawo komai ba akan
furucinsa Dan nasan ba abinda ya Isa yayi min Saida Izinin Allah, Kasan Abu mafi yi min ciwo a duk cikin
jumurdar da akayi tayi?" Kai Faruq ya girgiza Masa.
"sharrin zina da akayi min Wai harda Cikin shege, ko Ina Zina me zaci da Safna kazama kawai yarinyar data
Zama karya ko wane kare binta yakeyi har ayi kokarin hadani aure da ita, wallahi Dana auri yarinyar nan
gara na mutu a gwauro babu aure, sannan Abu mafi ciwo babu Wanda ya ji view dina an dauki abin da zafi
kowa bakinsa yana kaina har Ammi Taki yarda Dani, tana ganin D'an yanzu babu abinda baze iya aikatawa
ba, shi yasa na nufi gurin Hajiya Inna Nan ma gurinta babu sauki shi yasa naji gara nayi nesa da gida tunda
kowa ganin mutumin banza yake mini. kasan kuwa duk abinda yake faruwa Ina da masaniyarsa? har barin
Ammi sakoto, kawai dai na Kai zuciyata nesa ne sau uku Ina zuwa Yamai amma sai naji bazan iya tunkararta
ba saboda tana ganina wannan badakalar zata sake dawo mata a zuciya duk da gaskiya tayi halinta, so nake
kowa ya ji yanda naji lokacin da akeyi min nak'i aka juya min baya! Kamar bani da gata, wallahi nayi Dana
sanin Fara business dina da kananun shekaru Dana San idan na Fara haka Zan Zama yanda na Zama da ban
yarda uncle Ishaq ya dorani akan kasuwanci ba, Allah swa yayi gaskiya Daya ce dukiya da 'ya'ya fitina ne, da
Ina level irin na kowa a family din ba Wanda ze dameni tunda duk familyn wanda baya da rufin asiri da
nasa wadatar? To ni abin ne yayi min waya wallahi ga kananun shekaru, kasan uncle Saminun dai ya taba
fada min ko kungiyoyin matsafa dai na shiga, shi yasa na Zama abunda ba Zama cikin kankanin lokaci, a
gaban Hajiya Inna da uncle Mustapha akayi har Saida suka samu mugun sabani da uncle Mustaphan Dan
ma Hajiya Inna ta tsawatar kasan Bata da Wasa a gurin 'ya'yanta, sosai ta ciwa Uncle Saminun mutunci
tace ze Bata Mata zuri'ar ta, na rasa mena tsare masa haka da zafi Sam baya kaunata ko alama, haka Sam
baya ko shiga part din Ammina sai dai idan guri ya kure su gaisa Dan dole".
Ya fada cikin bacin Rai sosai Dan idanunsa sun kada sunyi jajir, kwantar da Kansa yayi jikin kujerar yana
sauke ajiyar Zuciya, da ganinsa kasan yayi famun ciwon da yake Zuciyarsa.
Dan muskutawa Faruq din yayi shima abin saiya dawo Masa sabo.
"Kayi hakuri Dan Allah Ya Mahmud kasan idan Allah yayi maka daukaka zaka gamu da kalubale kala-kala ba
cikin family ba ba cikin jama'ar gari ba ba cikin abokai ba dole hakan ta faru yanzu dai ka koma gida, ayi
duk wacce za'ayi duk da gaskiya tayi halinta an banbance tsakanin aya da tsakuwa, wallahi rayuwa lami ta
zamar min da baka Nan, kofa a email na turo maka sako baka bani amsa nayi magiyar har naba uku lada,
amma baka kulani Nima fushin ya shafeni ko? Wallahi yanzu ma nasan addu'ar da nakeyi ce ba dare ba
Rana Allah ya amsa min ya kawo dalilin zuwana kanon Nan dafa harna cewa mamee ba, Kuma wallahi
Allah kenan harna kwanta naji uncle musbahu ze fito sayan wasu abubuwan na amfani da mamee ta bashi
ya list ya sawo Mata shine fa nace Bari na rakashi na Jima ban shigo garin ba na Dan Zagaya tunda ba
dadewa zanyi ba, Ashe farin gani zanyi Dan Allah Ina ka shiga a kasar nan? Wallahi babu Wanda ya taba
kawo kana kasar Nan ko alama Dan anfi maida hankalin nemanka a European countries da Asia wallahi ba
Wanda ya kawo zaka zauna a 9ja".
Girarsa Daya ta gefen dama ya Dan dage Yana yiwa Faruq wani kallo.
"Au kunyi zaton Ina waje kenan ko? To Ina gida Bauchi state, cikin garin Azare katagum local government,
nasan ba sai nayi maka bayanin komai akan Zahra ba, an fada maka wacece ita tunda Wanda na ganku
yasan komai a Kanta watakila Abu Daya ze bashi mamaki ganin mu tare a Nan tunda ya sanni ko ba sosai
ba a can tunda time to time Yana shiga gurin malamina suna gaisawa idan ya shiga garin, sai albishir Daya
Zan maka itace yarinyar da nake fada maka mun taba haduwa da ita a cikin jirgi ita da Babanta wadda na
tura Sameer ya bisu Zuwa Jordan,ai ka gane bayanin ko?"
Kai Faruq din ya jinjina Yana fadin "Yes". Ya fada yana mamakin abun sosai wato shi Mahmud komai ya
sake a gaba saiya cimma burinsa. "Sai yanzu ya gane ka har hotunan daurin auren ya nuna min a phone
dinsa, Shima ya Dade Yana tunanin a Ina yasan fuskar ka tunda ba farin sani yayi maka ba sai dai a hoto, shi
yasa Sam be ganeka ba tunda ta Ina za'ayi tunanin zakayi irin wannan rayuwar, Dan Allah fada min ta Yaya
hakan ya faru harda Auren irin wannan yarinyar haka wato ribar kafa kenan ko?"
"To abubuwan da yawa Dan Ni dai nasan na baro gidan Hajiya Inna cikin fushi kofa takalmana ban iya
tsayawa na saka ba kawai dai nasan duk phones dina suna jikina na kamo hanya a kafata Amma Abu Daya
nayi noticing kamar jama'ar da nake wucewa basa ganina sam, nayi tafiyar da bansan iyakarta ba daga Nan
Kuma ban Kara sanin abubuwan da suka faru ba na dai tsinceni ne a gadon Asbiti bana magana ko kadan
amma Ina Jin abinda ake fada mayarwar ce Bana iyawa, Wanda suka shinceni wani babban malami ne da
marikin zahra da d'an Kanwar Malam din, shifa Malam din ya dage min da Addu'oi a kaina Dan har Taraba
Saida yaje akan matsalata gurin wani tsoho malaminsa, a haka har Allah ya bani lafiya, sai Kuma nayi arba
da Zahra a garin duk da Daman a bincken Sameer ya gano mazauna Bauchi state ne, sai naji Naga gurin
Zama na dage da Addu'a da sadaka amma fa ban fadawa kowa ba ko Sameer saboda a lokacin maganar
aurenta akeyi na shiga wani Hali a lokacin sai dai nayi Alkawari sai halarci daurin aurenta Kuma sai nayi
Mata kyauta ta ban mamaki kafin nabar garin, sai kuma ubangijin da yake amsa addu'ar bayinsa ya juya
lamarin cikin kankanin lokaci, aka bani aurenta lokacin Dana yanke kauna da samunta a matsayin matar
aure uwar 'ya'yana".
Ba karamin mamaki Faruq yayi ba ya Kuma Kara jinjinawa girman Allah swa, wato duk gwagwarmayar da
aka Sha Rabon wannan yarinyar ne ya rantse Kuma ya kaddaro shine ze taka da kafarsa ya karbi aurensa ba
tare da wakilcin iyayensa ba sai iyayen Amana.
"Wato Ni duk lamarin ya juye min wallahi".
Dan murmushi Mahmud yayi Yana fadin.
"Kaima kenan da ba a kanka hakan ya faru ba, sometimes idan na zauna sai naga kamar Almara wasu
abubuwan da suka faru, kasan abinda zakayi min".
Kai Faruq ya girgiza alamar "A'a.
Fuska ya hade Sosai Yana kallonsa Ido cikin ido.
"Kada naji labarin ka hadu Dani a Sokoto Koda wasa, Nina fita da kafata Kuma ida kafata Zan koma Amma
ba yanzu ba, Kuma kada naji labarin nayi aure a gurin kowa koda nazo da Zahra kada ka nuna kasanta ko a
fuska, Nina taro match din ni zanji da kayana".
Kai kuwai Faruq ke gyadawa tunda ya Fara maganar yasan ba Wasa a cikinta.
"In sha Allah hakan bazata faru ba".
Sun Kai kusan karfe uku suna tattaunawa akan abubuwan da suka ringa faruwa bayan bayanan, kafin kowa
ya nufi NASA gurin kafin lokacin sallar asuba. Ba karamin mamaki Faruq yakeyi ba idan yaji Mahmud Yana
fada masa wani abun Dan shi sai gurinsa yaji wasu abubuwan duk da Yana cikin gidan.
Itama zahra Bata kwanta ba sai kusan biyu da rabi bayan ta gama karatun Alqur'ani ta Fara nafifili sannan
ta kwanta, harta gama addu'ar kwanciyar barci sai Kuma ta canza Shawara ta tashi ta dauko Jakarta tana
fadin "Bari na kunna wayar nan ba turawa Ammah text na ban hakuri tayi breakfast dashi sai Kuma da Dan
hantsi na kirata nasan zata huce ta saurareni lokacin, sannan na Kira bestie musha hurar yau she gamo".
Jakar ta dauko ta koma saman gadon Tana gyara Zama, duk iya binciken ta tayi Babu duk wani Abu Mai
mahimmanci data saka a ciki, zazzage jakar tayi wayam kamar ba'a taba ajewa a cikinta ba.
Tagumi ta buga tana tunanin, to a Ina suka zube wadannan kayan? Kuma me yasa sauran Basu zube ba? ko
jiya lokacin da suka fito daga gidan mommy komai Yana ciki Kuma ai ko daga motar Bata fito ba lokacin da
sukaje sahad din.
Jiki ba kwari ta matsa tsakiyar gadon ta kwanta ita duk lamarin ya tsinke Mata wa zata tambaya Ina
kayanta na jaka suke da wannan tunanin barci yayi gaba da ita.
Hudu da rabi Mahmud ya tashi as usual, duk da Daren da suka raba da Faruq besa shi ya makara ba, nafila
yayi sannan yayi raka'atanul fajri ya fito Jin an Fara Kiran sallar na biyu, harya nufi Hanyar fita daga
corridorn sai ya dawo baya ya tura kofar dakin da take, a kwace ya ganta tsakiyar gadon hular data saka ta
cire gefe guda Ribom din shima yayi nasa gurin blanket din ya sauka har saman cikinta ga rigar ita da Babu
duk Daya, a hankali yake shigowa cikin dakin kamar Mai tsoron kada ya tasheta, Yana Kare Mata kallo
yanda tayi wani mahaukacin kyau a cikin dinligh din dakin, har ze tasheta saiya tuna condition din da take
ciki ya juya ta fice daga dakin, yaso ya gyara Mata gashin Amma yasan matukar ya tabata sai ya sake
alwalasa, a waya ya Kira Faruq ya fito su wuce masallaci.
A cikin barci taji kamar an bude kofa dakin, fargigit ta tashi tana addu'ar tashi daga barci, kamshin
turarensa da taji ya hade dakin shiya tabbatar Mata daya shigo cikin dakin. A gurguje ta nufi toilet jin har
an Fara sallah a masallatai, fatan ta Allah yasa har ta Idar Bai dawo daga masallacin ba Dan ita fa wallahi
tsoronsa takeji Bata shuryawa abinda yake muradi ba...
MAMAN FATEEMAH.
Page 50.
_______Tun idar da sallar Zahra ta shiga kakkabe gadon Tana dubawa ko Allah zesa tayi arba da tarkacen
ta na cikin jaka amma ko alamarsu Babu dole ta hakura ta linke sallayar da hijabin Adana saboda tsaro.
Bata koma barci ba gyara dakin tayi duk da ba wani datti Dan da gani sabon guri ne da alama ma kamar
a jiyan aka Fara amfani dashi Dan ko toilet din shima haka ne, Bata dauki dogon lokaci ba ta gama komai ta
bazawa dakin kamshi Dan ga Room freshners Nan kamar anyi gorinsu, wanka ta shige, ta Jima tana gasa
jikinta da ruwan dumi sannan tayi wanka ta fito haka nan taji tana son tayi kwalliya Sosai.
Zama tayi ta tsara light makeup tabi jikinta ta Sanya turaren gabobi Dana bayan kunne duk ta saka tunda
gasu nan kamar ba da kudi ake sayensu ba, ita dai ta zubawa sarautar Allah Ido taga inda wasan ze Kare,
clothset din ta nufa ta bude dayan bangaren, English wears ta saka riga da siket blue black masu ratsin fari
a jikin coat din,rolling tayi da farin veil ta fito Shar da ita gefe gadon ta zauna tana karanta addu'ar Azkar
din safe.
Su Mahmud Basu shigo gidan ba sai wurin bakwai tun bayan idar da sallar sukayi zaman karatun
alqur'ani da Azkar din Suma a masallacin. Faruq yaso ya wuce gida amma Mahmud ya Hana shi yace yayi
zamansa a Nan ze fiye Masa shi yau ze koma Nasarawa Daman akwai abinda yazo yi Nan din zuwa anjima
Idan ya gama zasu wuce Kuma ma Basu gaisa da madam ba, part din Daya kwana ya wuce shi kumq
Mahmud ya nufi sabon part din har ya Fara hawan steps din ya dawo Yana Kiran Faruq.
Shima gangarowa yayi Yana nufo Mahmud din Saida ya Karaso yace masa.
"Ina key din waccen car din akwai Kaya a baya za'a fito dasu".
"Oh! Sorry, wallahi na manta Yana ciki trouser din Dana sake jiya, harna na fito dashi na manta ban
baka ba, daman ni ka barwa ita Naga tayi maka kadan motar five millions ai sai mu Kuma ma motar
Mata ce"
"Nima ba tawa bace ta madam ce idan kana so ka tafi da ita kawai".
Baki ya rike alamar mamaki Yana 'yar dariya.
"Haba dai yaushe za'ayi haka da Wasa nake gani nayi dai tayi kankanta a gurinka harma ita din gaskiya".
"To Yaya kake son ayi kenan?kaga dai bani na Bata ita ba Babanta ya saya Mata Kuma saina ce batayi ba,
Ina laifi da ake bani aro da ita fa nazo airport lokacin da zanyi tafiya,Kuma anan na aje ta harna dawo
sannan na dauko Mata abarta, Kuma kawai saina ce Mata tayi kadan to ina wadda tafitan da Zan bata?".
Ya fada Yana kallonsa, shima kallon nasa yake yi, shi wani zance yake masa me Kama da zaurance me
yake nufi da hakan Yana nufin a baibai ya ninketa kenan kome?.
"Pls jeka dauko min we will discuss later". Da sauri ya nufi ciki ya dauko key din suka nufi gurin da motar
take.
Kayan ciki suka dauko, da gudu malam ya taho ya karbe kayan hannun Mahmud Yana fadin "Haba
yallabai meye amfanin na a gidan da har zaka dauki kaya". Ya karba yayi gaba da sauri Faruq ba biye dashi
suka nufi parlourn kowa da dauke da ledojin a hannau.
Har gurin dining table ya Kai kayan ya Dora kayan Faruq ma a Nan ya dora na hannunsa, Malam musa ne
ya koma ya dauko sauran da suka rage a cikin motar.
Maimakon Mahmud ya shigo saiya Koma dayan part din bai jima ba ya fito rike da laptop da wayoyi tablet
guda biyu.
A parlourn ya iske Faruq Yana tsaye kusa da wani freme Mai hoton wani tsibiri a tsakiyar teku gurin yayi
matukar kyau sosai.
Jin shigowar Mahmud yasa ya baro gurin Yana fadin "gaskiya tsarin gurin Nan yayi kyau sosai banyi zaton
ze kai haka ba kafin a gama".
Wani kallo Mahmud din yayi masa Yana aje abubuwan dake hannuwansa.
"Amma Faruq ka fiye gulma, Ina cewa Kaine ka zana ginin Nan da hannunka zakazo kana wani zance daban
a Kai Kuma, ni zonan ka shigar min da wasu sakonni cikin laptop din nan jiya naso yin aikin ka hanani".
Ya fada Yana kokarin kunna wayoyin dake hannuwansa.
Saida ya nuna masa komai sannan ya nufi upstairs.
Tunda ya doso saman yaji wani kanshin Dadi Wanda ya kasa tantance Kona menene, direct dakin Daya
kwana ya shige Yana son ya sake wanka yana son ya fita wasu sabgogin nasa wanda yaken son yayi da
Kansa.
Ya shiga ciki ba dadewa Zahra ta fito ta nufi kasa tana ayyana bari ta duba Koda kayan amfanin kitchen
Dana abinci tasan abinda ya kamata tayi kada ta Zama sakarya wadda ta rako Mata. Plat shoes ta saka fari
tas dashi ta nufo down stairs din cikin takunta mai daukar hankali, Bata ankara da mutum a zaune ba Saida
ta ahigo tsakiyar falon taja ta tsaya tana rarraba idanu tana son tantance ya fasalin ginin yake da inda ya
Kamata ta dosa,.
Carab suka hada Ido dashi ya aje abinda yakeyi ya Zuba Mata idanu irin kallon Nan na wuce shari'a Yana
tsarkake ubangijin da ya yi wannan halittar da take gabansa.
Dan zabura zahrar tayi ganin mutum ba zato ba tsammani.
Aje abinda yakeyi yayi ya taso har lokacin Yana kallonta Dan ja baya tayi ganin ya nufo ta.
"Ina Zaki Kuma nida na taso na gaishe da Aunty na".
Ya fada Yana murmushi, saida ya matso ta Dan gane shi, shine jiya ya rungume Mahmud a kofar store din
da yayi sayayya.
Sai lokacin ta Dan nutsu amma da tana tunanin ta Ina zata fece ta Koma saman tasan ko banza tana da
mafaka a can.
Dan murmushi tayi itama tana fadin "Yaya sunan bakon da babu sallama? Kawai na wayi gari da ganin
mutun ai dole na rasana".
Dariya yayi Yana fadin "Good morning Aunty".
"Morning".
Ta amsa masa a dan darare din nan ba wani sakewa, tana kallonsa.
"I am Faruq Dange".
Ya fada Yana juyawa zuwa inda yake aikinsa.
A hankali ta bude bakinta tace Masa.
"Sunana Fatima Zahra Muhammad Sani, Ina maka.barka da zuwa".
Tana Gama fada ta wuce can inda ta hango Kaya akan dining table.
Sakato yayi Yana kallonta Bai taba tunanin tana Jin yaren ba, Kai kawai ya girgiza Yana dan murmushi Yana
fadin "wato Ya Mahmud sai a barshi kawai sannin inda ya dosa sai Allah, shi yasa kenan duk yayi d'iban
Karan mahaukaciya da matan daketa rashin hankali a Kansa yayi tafiyarsa ya kyale kowa da nata salon
rashin hankalin".
Ledojin ta shiga dubawa taga Dame Dame Nene a ciki, Wanda su Fateeha da mommy ta Bata ta cire ta aje
a gefe sai Kuma Wanda ya sawo jiya ta cire na kitchen, kofar data gani a tufe taje tadan tura ga mamakinta
a bude ta ganta shiga tayi kitchen ne modern sosai babu abinda babu a cikinsa tsayawa tayi tana nazarinsa
kafin ta juya ta koma dauko Kayan.
Saida ta aje komai a muhallinsa sannan ta bude freezer data gani ta kwance, nama ne dasu kifa da kayan
miya a Nike cikin manyan bikitin roba, kaji biyu ta Ciro da Zuba a roba ta tarasu a famfo saboda kankarar ta
saki.
Filawa ta diba ta kwaba da yeast da barking powder ta rufe ta koma ta gyara Naman ta Dora a wuta.
Wani ruwan ta Dora daban ta dauko Madara ta bude ta diba Mai yawa ta dama Zuba akan ruwa data Dora
ta Dan zame murfin sannan ta ciro hollandia custard ta fasa ta dibi yanda take ganin zata ishesu ta dama ta
aje a gefe. Plates da cups da duk abinda tasan za'a bukata ta dauko ta wanke ta aje a muhallin Daya dace.
Filawar data kwaba ta dauko taga ya tashi ta ringa murzawa round sai ta Gama ta shafa Mai a frying pan ta
rage wuta ta shiga gasawa tanayi tana juyawa.
Biyu ta raba Naman ta dattaka rabi tayi source Rabin Kuma tayi pepper soup dashi ta dama custard din ta
dafa coffee Kuma.
Tun daga sama Mahmud ke jiyo wani irin kanshi girki yayi tunanin ko da wani sabon restaurant a Nan kusa
dasu, Saida ya fito yana saukowa yaji kamshin ya cika gidan.
Shigar kananun Kaya yayi yayi masifar kyau, yau shigar da yayi ta fito da ainihin ko waye shi Dan ba karya
kana kallonsa kasan matashi ne Mai cike da Jin Dadi da wadatar arziki Dan agogon dake hannunsa kadai na
millions of naira ne, shigar da ya Jima da daina yinta Nan gida Nigeria rabon da ya fito haka tun kafin ya
shiga rubibi.
Hannu Faruq ya shiga tafawa Yana fadin "perfect match, wallahi kun Dace Ashe haka Auntyn tawa take?
Haba shi yasa baka sauraren masu yi maka rawar Kai, ya Mahmud Ashe da abinda ka taka shiyasa kayi
shuru ka kyale kowa, Mai irin wannan matar mezeci da tarkace irinsu Safna, wallahi na Dade Banga
ma'auratan da suka tafi da imanina kamar kai da Aunty na ba, Dan Allah ka tsaya min na auri kanwarta pls
🙏".
Ikon Allah Mahmud ya tsaya yana kallo lokaci Daya faruq ya gigice masa wato yaga zahrar kenan tunda ya
sauko yaji gidan ya hade da kamshin girki yasa itace a kitchen, ko ba komai yasan Allah yayi Mata baiwar
iya abinci a Dan zaman da sukayi ya fashimci hakan.
Shi rasa abin cewa ma yayi a Kan kalaman Faruq, Dan uwansa ne na jini, amma ya gigice da ganin matarsa,
tab lallai da matsala Babba.
Bai nuna Masa komai ba sai Dan murmushi da yayi Yana fadin. "Ai mata ta ita kadai ce Bata da Kani ko
kanwa, nine wanta nine komai nata Sai dai ka duba ko a Ina ne Zan shige maka gaba in Sha Allah".
"Dan Allah nidai ka taimaka ko cikin family dinta ne ayi min wanna alfarmar ka shige min gaba".
Kyale shi yayi ya nufi kitchen din lokacin ta Gama hada komai ta juyawa kofar baya tana cire jan bayan
kwakwa zatayi amfani da ita in anjima.
Kamshinsa ya Fara fada Mata ya shigo gurin a hankali ta juyo, Yana tsaye ya harde hannuwansa a kirjinsa
ya zubawa bayanta Ido,yanda ta juyo din nan shi Kansa da take halalinasa Saida yaji wani yarrr a jikinsa
Dan gani yayi gaba Daya ta canza Masa ga wani irin cikowa da kirjinta yayi sosai.
Lumshe Ido yayi Yana tunanin lallai dole addinin musuluci da yayi Hani ga mutum baligi ya shiga gurin
macen daba muharramarsa gaskiya. Yana can Yana tunani ya tsinkayi muryarta tana fadin "Ina kwana"
batare data Kara kallon inda yake ba.
Bai amsa ba ya danyi gyaran murya.
"Meye Kuma Ina kwana? Na fada Miki ki iya tarairaya ta wallahi, kada garin kallon ruwa kwado yayi Miki
Qafa, kina da kishiya fa kinsan idan ta fiki iya lafazi da tarairayata can Zan tare a gurinta".
Warrr tayi masa da sexy eyes dinta tana Masa wani kallo.
"Yes ko Baki yarda ba? yanzu na Kira Miki ita ku gaisa".
Kai ta girgiza Masa alamar A'a.
"Come on, zo Nan ki fada min bakya son kishiyar?"
Ya bude Mata hannuwansa alamar ta shigo, kafada ta make ta aje kwakwar ta nufi famfon cikin sink ta Fara
wanke hannunta.
Cikin takunsa na nazantaka ya shigo ciki directly gurinta ya nufa Yana fadin "Ni gani na shigo sai nazo ki
bani hot one tunda ni ba'a son nawa".
Bai jira tace komai ba ya saka hannunsa ya rungumeta ta baya Yana shafa cikinta.
Shiru tayi Masa kamar ruwa ya cinyeta, Jin hannun nasa ya nufi wata jihar yasa tayi saurin rike Masa hannu
tasan idan ya karasa akwai damuwa sosai.
"Pls Dan Allah ka Bari kaga da bako a gidan kada ya jiyo mu fa".
Ta fada tana kokarin kwace kanta.
"Ok saboda shi Zaki hanani na sake kenan? To Bari na sender shi inda yafi wayo".
Dayan hannun ya saka ya ciro wayarsa yayi dialing din number Faruq, Sam batayi zaton kiransa zeyi ba,
Saida taji Yana fadar "Faruq kaje wancen part din ka qarasa aikin gani Nan zuwa".
Bai jira yaji abinda yake kokarin fada ba ya kashe wayar ya Dora a gefen cabinet din kitchen yana fadin "to
saiki sake ki bani hakkina tunda sirikinki yabar gurin".
Juyota yayi ya hade bakinsu ya cire rolling din, yana shafar gashin da yaji gyara ga qamshin hair spray sai
tashi yakeyi ya jima Yana yamutsata kafin ya janye Dan Kansa yana Maida numfashi.
Tsugunnawa yayi ya dauko Mata veil din ya rufa Mata a Kanta Yana fadin "dauko wasu flask din ki zubawa
Faruq nasa ki saka a basket na Kai Masa can idan ya gama ya tattara ya tafi gurin bikin da yazo".
"Me yasa? ba yace min shi qaninka bane".
"Ok. Dan Yana qanena saina zauna dashi gida Daya Yana kalle min Mata ko? Ai ya tafi shine mafita Dan
akanki zamu iya batawa da kowa to maganin Kar ayi kada a fara, Dan Allah ki ringa saka hijab idan munyi
Bak'i ba kowa ne ze iya kawar da Kai a kanki ba Kinga kuwa yanda Faruq ya gigice min na Nemo masa sister
dinki, na fada masa babu Amma ya kasa fahimta sai rokona yake na samo Masa mace ko cikin family dinku
ne"
Ya fada a Dan zafafe.
Shiru tayi ta nufi abinda ya sakatayi Saida ta Zuba Masa komai ta saka basket din ta aje a gefe ta dauko
Wanda ta zubawa Mai gadi ta aje a kusa Dana Faruq din.
Malam Musa ya Kira yace yazo kofar parlourn su hadu, dauka yayi ya fice daga kitchen din yabar zahra da
dogon tunanin akan abinda yace Faruq din yayi.
___
Tunda garin Allah ya waye Ammah ke faman neman number zahra abin yaci tura, a yau dai hakurinta ya
Gaza Dan tun Daren jiya da zilai ta Kira Ammah tana fada Mata yanda fasalin gidan da suke yake da kuma
kudin da tace an Basu dubu ashirin da safe da yamma ma an kawo musu wasu kudin dubu dari-dari ita da
iya Rahane ga turamen atamfofi guda hudu hudu da lace bibiyu, Kuma ta fada Mata tunda su zahrar suka
fice Bata Kara ganin giccinsu ba ga wayar ta ma a rufe.
Akalar Kiran Ammah ta canza ta shiga lalubo Number Abdul Hakeem.
Ringing din farko ya dauka yana Fadi "barka da Asuba Ammah, an tashi lfy?.
"Alhamdulillahi, idan ka tashi ka shigo Ina son ganinka" ta fada cikin damuwa.
"To in Sha Allah, gani nan shigowa"..
Ta kashe wayar, ta ajiye a gefe tana fadin "kazo ka nemomin wannan yaron ya fada min waye shi Ina Kuma
ya Kai min 'yata ko waya ya Hana muyi da ita inji meye dalilni Daya hana ta amfani da wayar, tunda Naga
Abban ba wani Abu zeyi ba, ga wannan kinibabbiyar matar tasa da koma sai taji Masa kwakwaf".
Tsaki tayi tana Jin duk Zuciyar ta ba dadi ko kadan, tana Nan zaune Abdul Hakeem din ya shigo sanye da
jallabiya coffee colour a jikinsa ya gaishe da Ammah ya nemi guri ya zauna Yana fadin "lafiya kuwa
Ammah?".
"Da sauki, Nemo min mijin Zahra a wayarka naji dalilinsa na yanke ma'amalarta Dani tunda suka bar garin
Nan ban Kara Jin duriyarta ba".
Shiru Abdul Hakeem din yayi kafin yace "ba haka za'ayi ba, Zan kirasa na saka handsfree sai kiji yanda
zamuyi dashi idan munji da alamun rashin gaskiya sai a San abunda ya Kamata tunda ba'asan dalilinsa. Ba
na hanata amfani da wayar, ke uwace kiyi hakuri babu abinda ze Samar Miki 'ya da izinin Allah, in Sha Allah
sai kinyi alfahari da Auren Nan Muhmud mutumin kirki ne bashi da wata alama ta rashin gaskiya, kinsan ya
fada min shi Dan Sokoto ne,.har unguwar su da iyayensa duk ya fada min lokacin da zeyi tafiyar nan, yace
saboda halin Rai Koda be dawo ba na nemi Sameer ko sabon mai gadin Daya kawo a can gidansu na hayin
banki, ko Binya na gidan Baba malam duk mutanensa ne. Bari na kirasa Dan hankalinki ya kwanta".
Ya Fara dialing din number sa.
Sun Gama break fast din kenan wayarsa ta dauki slow music daga kitchen inda ya barota tsam ya tashi ya
nufi kitchen din kafin yaje Kiran ya yanke, sunan Abdul Hakeem ya gani, kafin ya Kira wani Kiran ya shigo.
Saida ya zauna daf da ita ya daga kiran.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu babban yayan mu, barka da Asuba".
Ya fada Yana murmushi.
"Wa'alaika Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu barkamu kadai, ya iyalin?" Dariya abin ya bashi
"Gasu Nan muna ta basu hakuri kasan Mata sai a hankali".
Ya fada Yana Dan Jan tsunin hancinta, Batasan dawa yake wayar ba.
"Wai meya samu wayarta ne Bata shiga kwata-kwata duk hankakii Ammah fa ya tashi, Jin kwana biyu shiru
ba suyi magana ba idan tana kusa ka Bata suyi magana Dan hankalinta ya kwanta".
"Ya salam Dan Allah ka bawa Amman mu hakuri laifi tayi min na karbe wayar, amma Zan Bata ita yau in Sha
Allah, ai Zan shigo garin gobe ko jibi".
Tunda ta fashinci da Ya Abdul Hakeem yake wayar taji hankalinta gaba Daya yayi gida Jin cewa zeje Azaren
bada ita ba sai taji duk ta shiga tashin hankali da gaske gida take son komawa, ta dauka da Wasa yake Mata
lokacin da yace ze dauko Mata Rukayya idan zasuje Azare.
Wayar ya Mika Mata ya Mike ya fice daga parlourn gaba Daya.
Sallama tayiwa ya Abdul Hakeem din sannan ta gaishe shi.
Sannan ya dora da fadin "ga Ammah nason magana dake".
"Dan Allah Ya Abdul Hakeem ka Bata hakuri wallahi saboda bansan abinda Zan fada Mata ba na kashe
wayar Allah ba yaji nayi ba, kaina ne yayi zafi gurin fa buduwarsa ta turoni Asibiti ita Kuma ta shiga
wulakantani, Dan Allah ka rokarmin shi ya maidoni gida wallahi na gaji Ni tsoro nakeji bakaga irin gidajen
da yake kawoni ba kamar baza'a mutu ba fa". Ta ida fada tana kuka.
Duk abunda ke wakana Ammah na zaune tayi tagumi tana Jin wani sanyi da tausayinta a Zuciyar ta, amman
koba komai ta samu nutsuwa taji lafiyar ta sauran Kuma tasan shegantake ce kawai.
Wayar Abdul Hakeem ya mikawa Ammah ya tashi ya fice shima gara ya Basu guri su tattauna.
"Wai kukan Kuma na menene haka? ai kowa ya gyara ya sani kowa ya Bata ya sani, kiji tsoron Allah ki rike
sirrin mijinki kinsan baqi kinsan fari keba karamar yarinya bace,saboda me Zaki tafi wani guri har ki nemi
kwana bada izinin mijinki ba, haka kawai kin tashi hankakin jama'ar da suka daukeki da mutumci kin kyauta
kenan? To wallahi kada na sake Jin wani Abu makamancin haka daga gareki ki nutsu ki rike aurenki kada na
Kara Jin kin ambaci ya dawo dake nan, kinsan dai ba'a nan zaku dawwama ba ina cewa ya fada Miki garinsu
wata Rana dole ze koma gida sai kice bazaki bishi ba? Akul na karajin magana makamanciyar wannan daga
bakinki".
Tunda Ammah ta Fara magana Zahra ke shashsheka a hankali.
"Kiyi hakuri wallahi na daina bazan Kara ba, wallahi bansan laifin da nayi Masa ba ya dauke min wayar da
passport dina har da kudi da ATM duka".
Salati Ammah ta dauka tana fadin "Ni Asma'u yanzu harda passport dinki Kika dauka dole ya kwashe wato
guduwa kuka shirya zakiyi kibar kasar ko?"
Cikin gigita Zahra ta fashe Mata da kuka sosai tana Fadi "wallahi ba guduwa zanyi ba Daman suna cikin
jakar fa".
Ji tayi an zare wayar daga hannunta Batasan lokacin daya taso ta shige jikinsa ba tana fadin "Dan Allah ka
fadawa Ammah abinda take zargina dashi ba haka bane".
Ai Jin wannan furucin na Zahra yasa Ammah yanke Kiran cikin gaggawa.
Jin alamun yanke Kiran yasa shi Kara sakata a jikinsa baya son kukanta ko misqalazarratin.
Page 51
___Dan murmushi Ammah tayi,koba ba komai ta Sami peace of mind, yanzu Bata da wata fargaba,zata
Kira zilai ta fada Mata ta kwantar da hankalinta babu wata damuwa Zahra na Nan lafiya kalau ita dai tayi
zamanta sai lokacin Daya bukaci su dawo sai su taho din kawai.
Tashi tayi da wayar a hannunta ta wuce Ciki tana Jin wata sabuwar nutsuwa tana shigar ta. Addu'ar da
takewa yarinyar Allah ya Zama gatanta a dukkan al'amura.
***
Sun Jima a yanda suke ita Bata janye ba shi Kuma be saketa ba, ajiyar zuciya kawai take saki a hankali.
"Wai me kika yiwa Ammah ne haka da zafi har kike neman bayi Miki shaidar zur".
Tsuntse idanu tayi sai wasu hawayen. "Ya salam! Pls bana son kuka sam, ki adana abinki Mana Yana da
lokaci, ai kin gane?".
Shiru tayi masa, me zata fad'a Masa tace Ammah tace Mata niyyar guduwa take yi.
"Pls ki fada min Mana ko saina Kira na tambayeta laifin da kikayi Mata sannan zanji Kan maganar?"
Da sauri ta shiga fadar "wai fa Dan naje gidan su bestie shine take min fadan me yasa nayi yaji, shine na
fada Mata ba haka bane".
Dago fuskarta yayi yaga yanda idanunta suka sauya kala daga farare zuwa ja.
"Shi kenan ai komai ya wuce tunda Nina janyo akayi yajin tunda na turaki gurin Haseena, nayi zaton zuwa
yanzu ta aje maganar soyayya a tsakanin mu sai zumunci kawai, kiyi Hakuri nayi Mata last warning akan
shirmen da tayi".
"Ni dai dan Allah ka maidani gida na gaji da garin kwata kwata".
Ta fada tana turo baki.
Baice Mata komai ba ya nufi one seater ya zauna ya dorata a cinyarsa suna facing din juna.
"Ki cire ranki da komawa Azare Saida ganin gida daga Nan sai Sokoto birnin shehu, kina tunanin Zaki koma
can ne? Ai shi yasa nace a hadoki da house maid wadda take da Amana tunda a yanda Naga takunta zatayi
amanar, shine dalilin da ze kaini can na fadawa Abban mu da malam Zan koma gida tunda the game is
over, na samu a binda nake nema ai saina koma ayi wadda za'ayi ko?".
Ya fada yana dage Mata girarsa ta dama.
Wani ruwan idanunta suka kawo alamun zatayi masa halin.
Bata fuska yayi ya Zama serious din nan.
"Wallahi naga digon hawayenki saina sakaki kukan gaske, kuji min yarinya sai shagwaba, ai Naga kin Fara
sallah gara na cire Miki yarintar Nan ko kin nutsu ki fuskanci aurenki, dan Naga alamar har yanzu Baki
yarda da igiyar aurena ba a kanki tunda na kasa banbance Miki tsakanin Aya da tsakuwa ko?".
Mukus ta hadiye kukan tana qiqqifta Idanu, Jin ya b'aro magana, to a Ina yaga tana sallah har yake fada
Mata hakan?.
Kafin ta samu zarafin magana wayar da take jikinsa ta dauki wani kidan larabawa Mai Dadi.
Dagawa yayi Yana fadin "ok gani Nan Amma ka tabbata komai ya Zama ready kafin na shigo, dan Allah kace
mommy ta bani aron Rukayya ta shigo Nan Hausawa Bawo road ta Taya 'yar rigimar Nan Zama zuwa
yamma, ka Bata address din gidan".
Ya fada yana sauketa daga jikinsa ya Bata light kiss ya manna Mata a saman goshinta Yana fadin "Zan dauki
Aron motar ki na fita da ita kinji my previous, anyi min izini?
Kai ta gyada Masa tana fadin.
"Allah ya tsare".
Harya juya ya nufi hanyar barin parlourn ya dawo ya Mika Mata wayar hannunsa,.
"Kiyi amfani da ita sabon sim ne a ciki Sameer kawai nake Kira da shi kafin a kawo Miki Taki tunda na
fadawa yayan mu yau Zan Baki wayarki".
Hannu ta saka ta karbi wayar iPhone 16 plus ce da sauri ta dago ta kalleshi alamar mamaki fal cike da
fuskarta da kallon tuhuma Dan ba da ita tayi ways da Amma ba.
"Ya akayi Kika tsareni da kallo ko batayi miki ba".
Ta bude Baki zatayi magana ya daga mata hannu.
"Bari na dawo saina amsa tambayoyinki a nutse ai cewa nayi Miki aro bi kyauta ba ko?".
Ya fice da sauri, da alama uzurinsa Mai girma ne, tun bayan fitarasa take juya wayar a hannunta idan ba
bataga daidai ba a mbc taga tallarta 1.48 million naira ne kudin ta in Nigerian Price.
To wai waye shi ne Dan Allah? Duk lokacin da wani Abu irin haka ya gitta a tsakaninsu baya yarda ya tsaya
yayi Mata bayanin komai.
Ajeta tayi a gefen da take zaune ta Zuba uban tagumi da hannu biyu tana nazarin wasu abubuwan da take
gani tun shigowar su Kano abun ya canza salo gaba Daya, ta rasa Wanda zasu tattauna da dashi Aunty
Hussina ce to babu waya a hannunta ta mayar da kanta kurma.
Kamar an tsikareta ta Mike ta nufi upstairs da wayar a hannunta tana fadin Bari na Kira bestie musha hurar
yaushe gamo da ita".
Duk yanda zahra taso ta fada Mata wani Abu Daya shafi Mahmud saita kasa fada Mata Kuma da alama
Ummansu Bata fada Mata taje gidan ba koda wasa, saima wani abun mamaki da sajidar ta fadawa zahrar
cewar Mahmud yace zasuzo har syprus gurinta tare Amma yace kada ta fada Mata, sun dauki lokaci suna
wayar har sajidar ke tsokanar Zahra tana fad'in "ke Kullum canza layi kamar wata marar gaskiy".
Dan nisawa Zahra tayi kafin tace "ki Bari bestie kawai wallahi ba laifina bane shine yake kwace min wayar
Kuma idan ya tashi Kuma ba ita Ze bani ba sai dai ya bani wata, jiya fa da muka fita unguwa ya shiga sahad
na Nan zoo road muka hadu da Musbahu bakiga yanda ya yi, ba Banda Allah ya Soni ba da inaga sai yayi
min duka ma da Allah yasa nayi tsautsayi munyi magana dashi".
Dariya sajidar tayi tana fadin Namijin duniya kenan Wanda ke kishin iyalinsa, nifa Daman harga Allah
musbahun nan ba wani yi min yayi ba, kawai dai baka hana nutum abinda yakeso ne, Amma Ina hadin be
hadu ba ko alama wallahi,ban qara sanin haka ba Saida sarkin yaqi ya bayyana".
Ta fada tana kyalkyalewa da dariya.
"Wallahi bestie Baki da kirki ki ringa Jin tsoro Allah, musbahun ne haka? Amma Ina cewa harda ke a masuyi
Masa campaign a wancan lokacin"..
"Manta kawai bestie ya zaman past, yanzu ta Wanda Allah ya zaba Mana mukeyi, yauwa munyi magana da
Baffa yace akwai saukar Alqur'ani da ake Miki in Sha Allah babu wani Abu daze sake tasiri a cikin rayuwarki
in dai sihiri ne yace kiyi ta Hakuri mijinki Mai jama'a ne".
"Hummm! Bari kawai bestie nifa mutumin nan tsoro yake bani".
"Tsoro kuma? Kamar Yaya?"
Tsaki tayi kadan.
"Ba Zaki gane ba kwata kwata ba Wanda Kika zani bane wannan wani ne daban, kinsan ya maidoni Kano
daga zuwa ganin likata yace nida Azare sai ganin gida, Kuma Kinga wasu mahaukatan gidaje da yake yawo
Dani a cikinsu Kamar baza'a mutu ba wallahi, Kinga wannan wayar dake hannuna yanzu wallahi iPhone 16
plus ce ya bani Wai ga aro kafin ya kawo min tawa. Allah Lamainsa Yana damuna Kuma yaki yayi min
bayanin komai sai sabgar gabansa yakeyi kawai"..
Tunda Zahra ta shiga bayani sajida ke murmushi Dan tasan za'ayi haka Ya Abba ya kirata dazu ya fada mata
waye mijin da zahra ta aura kawai ya bada kafa ne wanda shima baisan dalilinsa na yin hakan ba.
"To ke meye naki na sai kin San waye shi yanzu kiyi Hakuri Mana ai yau da gobe tafi karfin Wasa ba dai
Kuna tare ba, ai wata Rana gaskiya zatayi halinta abinda nakeso kiyi kawai ki saka a ranki mijinki ba
macucin da ze cutar dake bane, Kuma bata haramtacciyar hanya yake samun kudinsa ba,Kika sani ko wani
mashahurin Dan kasuwa ne Allah ya Baki".
"Kin jiki aikin fa NGOs fa yakeyi Dan dai wata tsohuwa ta fada min wasu maganganu Wanda ta sakani a
confusing sosai".
"Ki manta kawai ki fiskanci zahiri tunda gashi gaki bada labari Kuma ai ya Kare keme reality a gabanki,kawai
dai ki zama Mai lura da lamarinsa da kyau, kiyi kokarin Kare Masa Sha'awarsa kada ki zama lusara mijinki
yaro ne Mai jini a jika Wanda Mata irinsa suke rububi Koda aure ko Kuma ayi shashanci gaskiya sai kin dage
in ba haka ba garin kallon ruwa kwado yayi Miki kafa".
"Kamar Yaya?"
"Au Baki gane ba to ki ringa bashi hakkinsa Dan Naga alama kamar zakiyi son jiki ta wannan fannin Ni
Kuma yanda nake ganinsa ba ragon namiji bane".
"Inna fatahana laka fatahan mubina! Bestie yaushe Kika Zama haka wallahi badan nayi Miki farin sani ba da
cewa zanyi kina wata sabgar a bayan fage, to wallahi Ni har yanzu in nan yanda nake shi ba yanda kike
tunani yake ba a Nan dai sai nace kinyi failed tunaninki ya kasa.."
Wata irin dariya tayi tana fadin Dan Allah mu koma video call Naga idanunki su kadai Zan kalla na tantance
maganarki"
"Ba zanyi ba sai anjima tunda kin Zama abinda Kika Zama sai neman sauki gaskiya Ya Abdul Hakeem ya
gamu da gamonsa a Ido kamar saliha nasan idan Kika shiga gidan sai yayi Dan wuya tunda Naga alama kina
cikin.... Allah dai ya kyauta kawai".
"Kai! Sharrin da zakiyi min kenan shi kenan Zan rama".
Sun dauki lokaci suna Hira har sajidar ke fada Mata Hameeda ta kirata tana kuka akan abunda tayi Mata
Wai Mama da Salma ne suka sakata, Bata gane kuskuren da tayi ba Saida ta dawo gida, abinda yasa suka
samu sabani da Salma kenan har ita Hameedar tayi tafiyar ta Jos Saida zasu koma Jigawa sannan ta koma
gida.
"Lah ki fada Mata Ni a gurina ya Dade da wucewa wayace lokacin babu a hannuna Dana kirata tuntuni
Amma idan nayi waya Zan nemeta ai karo Daya masu magana sukace Koda kusa ai yi akeyi, Hameeda tawa
ce".
"Kiyi dai taka tsan-tsan da lamarin ta kinsan ance jini yafi ruwa kauri duk rintsi ba zataqi uwarta a kanki ba,
ko Zaki Kara karbarta kisan irin zaman da zakuyi da ita, Ni garama Daya daukoki daga can yayi maganin
abubuwa da yawa wata qila Kuma da abinda ya lura dashi yasa ya yanke wannan hukuncin".
Shigowar su Aneesa dakin sun dawo daga lectures yasa suka canza akalar hirar sun gaisa da Zahrar suna ta
korafin taji dadin aure ta manta dasu ko wayarta ba'a samu saboda tayi nitso cikin kogin soyayya, ita dai
saikokarin Kare Kanta takeyi sajida na tayata.
Da haka sukayi sallama.
Aunty Husaina ta Kira itama tayi Mata nata fadar rashin samunta a wayar sannan ta Kara dubata da jiki tare
da tambayarta yanda sukayi da Asibitin? ta fada Mata fada har yanda sukayi da doctor din, da Kuma
maganin da Hajiyar makwarari ta Bata, sannan ta fada Mata abinda yake faruwa da ita a Nan kanon Bata
rufe Mata komai ba, tayi mamaki kwarai sai dai tun farko Daman ta yiwa lamarin sa question mark, tun
ganin irin kudin da aka narkar a kankanin lokacin gyaran gidan da aka bashi a nan Azaren.
Kamar hadin Baki itama Aunty Husainar cewa tayi ta Zuba Masa Ido ta Kuma yi masa biyayya, sannan
sukayi sallama.
Kusan awa Daya da tafiyar Mahmud Zahra taji bell na Kara alamar anyi bako.
Saukowa tayi ta nufi kofar ta bude Aunty Rukayya ta gani a tsaye da basket din abinci a hannunta dayan
hannun Kuma da karamar jaka irinta matafiya.
(Maman Fateemah)
Page 52
______
Cikin Jin dadi Zahra tayi zarya ta karbi jakar hannun Aunty Rukayya tana fadin. "sannu da zuwa Aunty Ni
harna cire rai da naji shiru ga babu Wanda ze tabo min ke a waya tunda number ki tana Kan waccen
wayar". Ta fad'a tana Bata hanyar shiga.
"Wowooo! Masha Allah, gaskiya Ya Mahmud Yana shagwaba ki yarinyar nan, irin wannan babbar harka
haka".
Ta fad'a tana karewa parlourn kallo, handbag din dake hannunta ta aje tana fadin Ina zuwa ta juya da sauri
ta koma waje, zahra na tsaye Aunty Rukayyar ta dawo da basket Babba fal Kaya a cikinsa ta shigo.
"Kai Aunty daga ina haka da wadannan Kaya?.
Zama tayi tana Kakabin haduwar gurin. Itama Zahrar zaman tayi kusa da ita.
"Bari kawai wallahi aikin mommy ne, daman ko Ya Mahmud be kirani ba Mommy zata tasoni takanas ta
garin Nan na kawo Miki sakon nan, ai jiya Kuna barin gidan naji ta Kira Hajiya Salima 'yar Sokoto tana Mata
wani bayanin dayasa na sulale nabar parlourn".
Ta fada tana dariya.
"Kamar ya Aunty?"
Wata dariyar tayi tana fad'in "ji nayi fa tana Kiran a Kara gyara Mata diyarta tasan Shirin wancen yayi sanyi
tunda ta fuskanci diyar tata Bata Fara Amarci ba, Kinga kuwa ai Zama Bai ganni ba a gurin, Wai hadi za'ayi
Miki bana Wasa ba"..
Hannu zahra ta saka ta rufe fuskarta wata irin kunya ta rufeta.
"Dan Allah bude idonki ni zakiji kunya? Ni nan Nima zuwa bayi na Dora Miki karatu Naga kin fiye Sanya ba
wani abubuwa masu zafi da kikeyi ko wannan shigar batayi min ba, ki zage kina tsula fitinannun shiga
wadda Zaki gigita Masa lissafi, humm wallahi Naga alama bakisanta true colour din ya Mahmud ba".
Da sauri zahra ta bude Ido tayi wuri-wuri tana duban Rukayya.
"Aunty waye shi dan Allah? Dan duniya ne ko?".
Wani sakaran duba Rukayya tayi Mata. "Amma ke wallahi anyi marar wayo, meya hada magana ta da bariki
kuma? Allah yayi masa tsari da wannan sabgar, Kinga mubar maganar tunda kin Bata zancen sai wani jikon
Kuma".
"Dan Allah Aunty kiyi Hakuri kiyi min bayani, a'a wallahi Naga alama sai an qara gasa Miki bakinki".
Ta fad'a tana janyo basket din gabansu.
Abincin da mommy ta bayar a kawo ta cire suka Kai Kan dining suka dawo wasu food flask ta Ciro guda biyu
Daya kazace wadda aka dafa da saiwar Malmo sai kamshin spices ke tashi ga habbahan Nan guda guda a
ciki.
Sai dayan wani irin romone na kwai da Albasa da wani Abu a ciki kamar hanta.
Sai Kuma wasu madaidaitan robobi masu kamar girman na swan medium, had'in Zuma ne pure da
magunguna,sai wasu Kuma na tsimi da robobin gumbar aya da dabino, a hankali Rukayya ta shiga Yi Mata
bayanin yanda zatayi amfani dasu wata Leda ta Mika Mata wannan Kuma da bayaninsu a cikin kowanne.
Ta karasa tana dariya.
"Wani bayanin sai a takarda ki duba koni ba'a fad'a min ba".
Rufe fuska zahra ta karayi tana fad'in, "nagode Allah ya sakawa mommy da Alkhairi".
"Allahumma Amin, wato su Mommy ana gyarawa d'a Mata yanda..... Umhh ".
Ta rufe bakinta tana wata dariyar.
Hannu Rukayya tasa ta dauko wayar da zahra ta aje a tsakaninsu ta Fara juyata tana kallon zahra.
"Mrs Dange! Masha Allah yaushe ya gwangwajeki da wannan me zafin?".
Dan warrr tayi da ido tana duban Aunty Rukayyar..
"Ba tawa bace aro ya bani da ya dauke min tawa" .
"Kamar ya?".
Labarin abinda ya faru ta Bata.
" Ke ai gobarar Titi a Jos, ba gashi kin samu waya daga sama ba".
Baki ta bude tana fad'in. "Kai Aunty Ina Akuya zata da Kayan Cali, wallahi wannan tafi karfina".
"Naki wasa ne yarinya kinsan waye mijinki kuwa Naga alama anyi Miki lillibin biri, bazakiji mutuwar sarki a
bakina ba Amma ki zaman very curious a Kan duk wani motsinsa da lamuransa da kanki Zaki bani labari".
Dan narainarai tayi da ido.
"Wallahi na kasa gane komai a Kansa Kuma an rasa Wanda ze min cikakken karatun da Zan fahimta".
Wayar Aunty Rukayyar ta aje a kusa da Zahrar tana fad'in. "haba Auntyn mu meye na gaggawa yaushe
akayi Daren da shashhsawa zata b'ata ku tafi a yanda aka dauko.tafiyar kamar hakan ze taimaka Miki ki
Zuba mulkin da kikeso Kuma tun yanzu ya kamata ki koyar dashi yanda kike son ku rayu, ko Nan gaba
sauyin yazo bazezo Miki da wani abin mamaki ba, Abu Daya Zan fad'a Miki gidan da kuka sauka a Sultan
road mallakin Ya Mahmud ne Dan naji Hajiyar makwarari suna cakusawa da Ya Sameer da tace ta fad'a
Miki tsakaninsu da Ya Mahmud din ta fad'a Masa kin tambaya gidan na waye ta fad'a Miki mallakin mijinki
ne, Ina fatan bakiyi maganar dashi ba?"
Zahra ta fada Yana kokarin Hawa stairs, sai Mai lura ze kula da Dan kallon da yayi Mata a fusge baice komai
ba yayi hayewar.
"Auntyn mu haka kike tarbarsa idan ya dawo? Maimakon ki tafi ki shige jikinsa ki ringume kayanki ki bashi
happiness, saiki zauna kina fadin wasu local words ai masu fadar haka sai irin mu kanne da saura hadimai".
Baki ta turo.
"Kuma a gabanki Zan Masa hakan? Wlh bazan iya ba".
Wayar Rukayya ce ta dauki qara alamar Kira ya shigo tana cirowa taga sunan ya Sameer.
Tana dagawa tace "gani Nan".
Ta wurga wayar jaka ta nufi kofar fita,da sauri zahra tabi bayanta da babbar ledar da karama tana fadin.
Aunty Rukayya Baki dauki kayanki ba".
Da sauri ta dawo tana Fadi Babu abinda zan karba kije kiji da Yayana Yana bukatarki kusa dashi" .
"Allah sai kin karba ko naje na fada masa ya Baki da Kansa".
"To kawo ki koma ki tarairayi kayanki Kinga an kusa Kiran magriba, na gode kwarai da gaske"
Ya fada yana sakar mata hot kiss a wuyanta, hannuwansa suna Kai kawo a jikinta, cikin rawar murya ta Fara
fadin "Pls Amor meu (my love) Dan Allah".
"Dan Allah me? Eu amo vocè (I love you).
Ya fada cikin kunnenta.
Kankameshi tayi Dan ba karya sakon Yana zuwa inda aka aike shi, cikin muryar data jiku da desire ya fara
Mata magana cikin kunnenta "Wai Baki San Ina tare da kishirwarki ba? ki barni in rage zafi Mana babu
abinda zan Miki ai har yanzu bamu shiga master bedroom ba Wanda akayi shi is for you only,kin gane ki
barni nayi Wanda nakeso a Fara rage wannan kunyar da zata cutar Dani,sabuwa Kar zan kaiwa Ammina ke
ta ganki a yarinyar ki ban taba komai ba".
Runtse Ido tayi kalamansa sun mata nauyi, ita fa wani lokacin mamaki yake Bata yanda yake treating nata
kamar ya shiga zuciyar ta yaga yanda take son tsara future dinta.
Sabgarsa yaci gaba dayi karshe ma daukarta yayi ya nufi bedroom din Daya kwana ciki yayi musu masauki a
tsakiyar gadon,da gaske dai fitinar yakeji ta gasken gaske.Dan ba Karamar yamutsa Masa lissafi ganinta
yayi ba, abubuwan Daya saka tayi Masa sun girmewa saninta duk tsumar da jikinta keyi Bai saurara Mata
ba Saida ya samu nutsuwa sannan ya kwanta a Kanta Yana sauke numfashi.
Shiru sukayi Kamar Allah Bai hallici mutane a dakin ba, a hankali ya rada Mata.
"Precious fada min me kike tsoro ne naji har yanzu jikinki Yana rawa?"
Juya masa Kai tayi gefe, ita ya kyaleta da abinda yayi Mata ma Mana sai Kuma ya Kama tambayarta salon
ya hanata sakat kenan, batayi magana ba saima rife ido da tayi.
"Za kiyi bayani ne, Ina nan zakizo kina nemana Ina Miki yanga ki Bari ki Zama 'yar hannu ina ganin saina
ringa guduwa dan Naga alama bazaki saurara min ba irin wannan styles tab, rufe idon gulma ne kawai kike
min tun yanzu kina bani irin wannan inaga labari ya Sha banban, gaskiya Allah ya sakawa su Abba da Baba
malam da Alkhairi da suka gwangwajeni da irin wannan gwanar, Allah ya biya Ammah da Alkhairi data Baki
cikakkiyar tarbiyya, ya jikan su Ummee da Abie yasa Aljanna makomarsu".
Shashshekar kukanta yaji "ya Salam menene kuma?"
Ya juyo da ita suna facing juna, Kai ta girgiza alamar ba komai.
"Ki fada min meye?.
"Ba komai kawai ka tuno min da mahaifana ne Wanda ban taba sanin ya dadin iyaye yake ba,duk da ban
taso cikin kukan maraici ba Ammah ta tsaya tsayin daka ta hanani wannan kukan".
"In Sha Allah Nima har abada bazaki kukan marairaicin ba a zamantakewar mu, Zan Baki farin ciki Zan
zamar Miki komai na rayuwarki, daina kuka kinji my precious, idan da abinda bana son na gani a rayuwata
to kukanki ne, yana taba min zuciya".
Lallashinta ya shiga yi da kalamai masu kwantar da zuciya a haka har ya shagalar da ita ganin Yana neman
komawa ruwa yasa ta kwace Kanta ta matsa gefe tana maida numfashi tare da fadar.
"Ana Kiran sallah".
Mirginowa yayi Yana fadin "Naji ba wani Abu zakiyi min ba, ki Bari na Kara Jin duminki Dan Allah".
Tanaji tana gani ya Kara kanainayeta a jikinsa, da gaske fitina yakeji Kuma so yake ya bude Mata Idanu
dole.nan ya lalace ba zato ya tsinkayo ana tada kabbarar sallah mirginawa yayi gefe ya Mike yasa hannu ya
daukota ya nufi toilet.
Ruwa ya hada suka shiga tare Nan ma ba karamin kauda Kai yayi ba da saiya sake yamutsa ta shifa gaskiya
dole yayi abinda ya kamata a kwana kusa din nan, ya rigata fitowa a gaggauce ya wuce masallacin duk da
an Gama sallar.
Bata Dade ba itama ta fito tayi ta tattarra abinda ya kamata ta wuce dakin tada bawa kanta.
Bayan ta Idar da sallah ta tashi ta koma ta gyara dakin ta cire bedsheet din yaje ya saka a injin wanki, ta
canza wani bedsheet din ta Kara karfin A/C ta fesa freshner ta Kara Zuba wani a burner ta kunna ta janyo
dakin, ta koma ta gyara wancan ma ta saka wasu fitinannun kananun Kaya riga da wando ta karasa busar
da gashinta ta shafa man gashi da hair spray ta matse gashin da pink din band kalar rigar, lokacin da aka
Kira insha'i after dress ta Dora tayi sallah tana azkar din yamma da Bata Sami damar yiba ya shigo dakin,
ganin tana Addu'oin yasa ya juya ya fita.
Maman Fateema.
Page 53.
_________Zahra na gama azkar ta cire after dress din ta fito, bude dayan bedroom din tayi baya ciki,
batayi attempting din shiga dayan bama tunda bataga an bude shi ba. Ita fa jiya ya barta da tarin damuwa
da tunani Wai kaurace mata yayi kenan? Wato ita matar shige ce ko? Da wadda ya gurzu da zafin soyayyar
ta ne dole ya ringa ririta ta duk tsiyar da zata shuka Masa, amma ita Bata jiba Bata gani ba ya mayar da ita
sakarai, shiya Kaita gurin da suka hadu da musbahun amma yazo Yana Mata zafin Kai haka kawai badan
Allah yayi Mata gyadar dogo ba sama 'ya'ya kasa 'ya'ya da yanzu labarin yasha banban wata qila da Tasha
dinkin likita Dan a yanda yake din nan kanin fyade ze mata, yarfe santala santalan hannuwanta tayi farare
sol tana jinjina Kai.
A hankali Cikin takunta na nutsuwa da rausaya kamar bishiyar da iska ke kadawa, ta sauko kasa, parkour na
biyu shiru baka jin komai sai sanyin A/C da sansanyan kamshi, kamshinsa ne ya doki hancinta duk inda ya
gitta saiya bar wannan mayen kamshin nasa ita tun ranar da sukayi wannan arangamar a soron gidan Baba
malam dashi ta San shi, Kuma har yanzu Bata Gama tantance wane turarene ke da tashin kamshin nan ba.
Main parlour ma baya nan kitchen ta nufa ta Dora cus-cus Daman tayi vegetables soup tun yamma ita da
Aunty Rukayya.
Sauran kazarta ta dauko daga freezer ta Dora a wuta.
Fridge din dake gefe Wanda drinks ke ciki ta bude ta dauko masa Shani ita Kuma ta dauki Madara hollandia
da ruwa Nestle.
Minti goma ta Gama dafa cus-cus din, sauran kazarta ma a bowl ta juye ta fita dasu dining ta jera, ta koma
hadu fruit salad ne ya gangaro daga sama cikin kananun Kaya Yana daura agogo Rolex a hannunsa, tsayawa
yayi cak daga tafiyar da yake ya Zuba mata idanu ganinta yayi tamkar an canza Masa ita, hankalinta be Kai
Kansa ba Amma kamshinsa shi ya fallasa shi, Dan tsai tayi tana duba cikin parlourn, a tsaye ta ganshi ya
Zuba Mata ido.
Limshe Ido tayi, gani tayi yayi Mata wani irin fitinannan kyau, sauda yawa tana Jin wani irin Abu a cikin
zuciyar ta game dashi, Amma ita Kanta Bata San ko asalin menene ba. Jin kamshin nasa a daf da ita yasa
tayi bude sexy eyes dinta a hankali ta sauke shi a Kansa, matsota yayi sosai har suna musayar numfashi.
Hannu yasa ya karbi bowl din data zubo fruit salad din, Bata Hana shi ba ya rik'e bowl din da hannu Daya.
Daya hannun ya riko nata suka nufi dining din.
Bowl din ya aje sannan ya gyara Mata kujera ta zauna, abincin ya shiga budewa.
"Wow! Irin wannan delicious, Dan Allah a Ina Kika koyi girkin Nan ne? Gaki Nan a ido kamar raguwa Mai
son jiki, amman a zahiri Kuma ba hakan bane, Allah yasa a ko Ina ma haka kike".
Shiru tayi masa ta yunkura zata tashi ya mayar da ita da sauri Yana fadin.
"Ai kin gama naki aikin yanzu duty na ne, daga yanzu Kullum in dai Ina gida aiki nane nayi serving din mu,
Ina ga girkin ma Zaki koya mun duk da na dan iya a gurin Hajiya Inna da Aunty Badi'a, Amma naki yafi nasu
Dadi nesa ba kusa, ai zaki kowa mun ko? Tunda ni dai bana son abincin masu aiki Kinga ko Ammina ita take
min abincina da kanta".
Hannu yasa ya rufe bakinsa da alama ya saki layin da Bai shirya Masa ba, sai ya b'arar da zancen da fadin.
"Wai Kinga yanda kika canza kuwa?duk Wanda ya ganki zeyi zaton nayi ajiya fa, ko Azare muka koma zasu
dauka mun samo Dan Kano ko 'yar kano"..
Sarai ta gane bada kafa yayi, sai itama ta share Bata nuna ta fuskanci abinda ya sharewar ba.
Dagowa tayi tana fadin.
"Ka cire shiga kitchen a Cikin abubuwan da zaka koya a gurina babu wannan meye amfanina in dai zaka
shiga kitchen da sunan girki ai umarni ne kawai naka" .
Gefen fuskar ta ya shafa.
"Ko?"
"Gaskiya Kam".
"To idan Kika samu ciki Mai laulayi fa Yaya zamuyi kenan?".
Rufe ido tayi da hannunta.
"Gaskiya a bar maganar shike nan the chapter is closed, muci abincin nasan ba lallai kaci wani abu ba fa?".
Saida ya matso da komai sannan ya zauna Yana fadin..
"Ai kin kosar Dani, kawai fruit salad din Zan Sha bana son Abu Mai nauyi da dare".
Dan shagwab'e fuska tayi tana bude flask din data Zuba cus-cus din tana fadin..
"Bafa Mai nauyi na dafa mata ba ka gani".
Ta dauko Masa ta nuna Masa.
"Ok, to bari na Zuba Mana kadan da gaske bana Jin yunwa fa".
Abincin ya Zuba musu sukaci tare ba laifi yaci sosai Dan Saida yayi mamakin abincin da yaci.
Bowl din sauran pepper soup din da mommy ta aiko Mata ta janyo ta tura masa gabansa.
"Menene wannan din Naga wasu itace a ciki?"
"Kaci kaji Mana mommy ce ta bada aka kawo min dazu da Aunty Rukayya tazo".
Wani killer smile yayi.
"A'a na koshi ki cinye abinki kawai kizo muje ki rakani wani guri".
Ture Naman tayi tana fadin.
"Nifa kaina ragewa naci nawa na koshi".
"A'a ki aje a fridge ki cinye abinki da safe ai sakon babu ni a lissafin"
Ya fada Yana Zuba Mata madara a cup, lemonsa ya bude Yana Sha. Saida ya Taya ta suka kwashe kayan
wurin suka Kai kitchen, Yana tsaye Yana Mata Hira ta wanke kayan da suka b'ata.
Taso ta sake wanka ya Hana yace ze tafi ya barta Yana son yayi abu Mai mashimmanci ne, after dress din ta
Dora ta gyara rolling din suka nufo kasa sai kallonsa take kasa kasa Dan ba karya yayi wata irin haduwa sak
matashi Dan hutu ajin farko, duk Wanda ya kalleshi Saiya kara, Sumar Nan Tasha gyara tayi kwance sai
walkiya takeyi.
Motarta ta gani a kofar parlourn, da alama da ita zasu fita duk da taga bakin motoci a gidan, da kansa ya
bude Mata ta shiga ta zauna.
Gurin malam Musa yaje sukayi maganar sannan ya dawo ya shiga motar ya tuqa suka fice daga gidan,
malam musa na fadin A dawo lafiya yallabai.
Direct hadejia road ya nufa suna tafe yana Mata bayanin abubuwa da guraren da Bata sani ba.
Be tsaya a ko Ina ba sai welcare, tare suka shiga bangaren magunguna suka nufa wani magani ya dauko.
A bangaren kayan kwalam da makwalashe lodarsau yasa tayi kamar ba gobe, yaje ya Basu Kati suka cire
kudinsu.
Aka Kai musu mota, ta dauka gida zasu koma sai taga sun Kara gaba, Ring road suka shiga basuyi nisa ba
Sosai taga sun shiga wata kwana bata tantance Ina sukazo ba Saida taga sign board din Asibiti M.D.S.
Abin ya Bata mamaki to me zasuyi a Asibiti?. A mota ya barta ya shiga Cikin be Dade ba ya dawo Yana fada
Mata ta fito tazo, ba musu ta fito suka jera wasu majiyyata sai kwllonsu suke, ofis din Dr. Suka shiga.
Mutum me fara'a ya karbesu hannu bibiyu suka gaisa da Mahmud sosai, da alamar ba wannan ne haduwar
su ta farko ba, da sanayya.
Zahra ma ta gaishe da likintan. Sannan suka zauna, Mahmud bayanin Dan abinda ya sani yayi masa.
Tambayoyi Dr din ya Fara jerawa zahra daga karshe shima yace Bari ayi hoto da wasu test a Nan ze
tabbatar da abinda yeke tunani.
Sun dauki titin da ze fitar dasu HOTORO NNPC ne wayar Mahmud tayi K'ara alamar shigowar massage.
Ciro ta yayi ya duba, gefen titi ya gangara yayi parking.
Sannan yayi dialing din number da akayi Masa text din da ita, ba Bata lokaci daga can aka daga.
"Yi min cikakken bayani".
Abinda Mahmud din ya fada kenan, daga can Daya bangaren aka Fara Masa bayani sai jinjina Kai kawai
take yi har ya aka gama fada masa duk abinda ya nema a fada masan.
"Kana jina Zan fadawa Bilyaminu ya kawota Nan Kano can sallari za'a ajeta zanzo in Sha Allah ayi Mata duk
abinda ya kamata".
Ya yanke kiran, ita dai Zahra ido ne nata, wani zance yakeyi Wanda ta kasa fahimta, wacece me za'a kawota
tayi shi me zeyi idan yaje gidan da yace a kaita? Nan da Nan taji faduwar gaba kada fa ko Yana harkar
mata, taga ba sauki idan ya rikice, ko zuwa zeyi yayi... Da sauri ta girgaiza Kai tana runtse Ido.
"Ya akayi ne 'yan Mata naga kin shiga dogon tunani?".
Kankance idanu tayi tana Masa wani kallo na tuhuma.
"Wa kenan za'a kawo maka". Wata dariyar rainin wayo yayi Yana kallonta kasa - kasa.
"Mace Mana, tunda kin hanani ai gara na nemi mafaka inda Zan rage zafi, ko so kike na kasa amfanuwa,
idan har ban samu nutsuwa ba saina kwanta gadon Asibiti, kinsan ya nakeji kuwa?".
Ya wani Yi mik'a Yana kokarin janyota jikinsa.
Da sauri tayi baya tana fadin.
"Allah ya tsari gatari da Saran shuka,ni me Zan baka ai ban cika mace ba, Daman ni me zakayi Dani da aka
k'ak'aba maka sadaka bani da wata qima ko daraja a gurinka tunda bakasan darajata ba, da bakinka fa kace
an fada maka duk Wanda suka nemi aurena sai sun Gama Dani suke barina kaga kana min kallon fasiqa
Mai ma'amala da maza kenan me ze Hana ka Kira a kawo maka mace a gabana, wallahi tallahi bazan
zauna da fasiqi ba sai dai ka rabu dani wallahi ban taba kebancewa da wani namiji ba a duniyar nan bayan
Kai, bazaka shafa min wahala ba ka gudu ka barni, tunda har gobe ba Wanda yasan daga ina kake, Kuma
rayuwar garin Nan ai mun santa komai ma na haya ne, haka kawai ka cuceni ka gudu ka barni da Jangwam
idan da gaskiya wa yake gudun asalinsa ai duk lalacewar gida yafi daji ka koma Mana idan ba fitsare gurin
kayi ba da abin kunya ba ka gudo nan".
Tana kawowa Nan sai kuka, shi ikon Allah ya tsaya Yana kallo yanda ta zage tana tsula Masa rashin kunya
wato Mata ba sauki gurin kishi, Dan murmushi yayi yana ayyana 'yar daru kawai.
Dauko ta yayi cak kamar 'yar baby ya kwantar da kujera ya sakata cikin jikinsa ya zagaye ta da hannunsa.
Tana ta mutsu-mutsun kwacewa Amma yayi Mata kyakykyawan riko.
"Mai maita min abinda kikace waye Dan iskan? Ni zaki kalli idona kina fada min abinda ranki ya Raya miki?
Idan matan zanbi kin isa ki hanani ne, nace a kaita sallarin Kuma Billahillazi mace ce kuma gurinta zanje ko
Zaki hana ne, an fada Miki ina sonki ne kunya da kawaici yasa na karba amma badan kinyi min ba, Kuma ki
rubuta ki aje har abada bazan taba sakinki ba idan ma kinayi dan naji haushi na rabu dake ne ki sake
dabara, Kuma dake zamuje can din na ajeki na shiga nayi abinda nakeso mu koma Kuma kiyi min wanka,
gida Kuma eh abun kunya nayi na gudo nan, yarinya na yiwa ciki Dan haka ki shirya rike yarinyar da aka
Haifa min nan gaba kadan".
Naman Fateemah.
Page 54.
...........Sun Kai kusan minti goma a haka, tana jikinsa a haka tayi kukanta Mai isarta, baris yayi da ita Yana
Jin tana ajiyar zuciya, Shima da gaske ta tunzura Masa zuciya Wai "fasiqa"
kalma mafi Muni Daya tabaji daga bakinta, dole ta karbi hukunci Wanda ko Nan gaba ba zata Kara
marmarin fada Masa makamanciyar irinta ba.
Sauke ta yayi daga jikinsa ya gyara kujerar ya tada motar, baiko Kara kallon inda take ba ta fisgeta da wani
irin mahaukaciya gudu.
"Wayyo Allah Nan Dan Allah kada ka kashe mu, na shiga uku". Ta fasa masa kuka Dan da gaske ta tsorata
da yanda ya saki motar.
Bai tanka Mata ba amma ya sassauta gudun, shiga Nan fita can taga sun shiga wata unguwa Mai karancin
gine-gine duk tayi zuru-zuru da ita kofar wani katafaren gida ya tsaya ya Danna horn da karfi da gudu aka
bude gate din ba wata wata ya Danna Kai cikin gidan.
A tsakiyar gidan ya Parker motar, wasu kartin maza ta gani sun nufo motar da sauri kusan su shida
dukkansu majiya karfi, take jikin zahra ya dauki rawa, Yana kallonta ta gefen Ido yanda take mazari, Amma
ya share ta.
Kofar ya bude dai dai lokacin da suka karaso suna kwasar gaisuwa.
"Sagir tana Ina?".
Mahmud ya fada Yana duban Wanda ya kira da sagir.
"Tana ciki yanzu ba dadewa bilya ya kawo ta".
"Ok.kuna iya tafiya Amma kafin Nan ku sako min little da barbar tsakar compund din nan. Yayi gaba abinsa
ya nufi wata katafariyar kofar parlour.
Zahra tayi mutuwar zaune Dan gaba daya tsoro ya cika Mata zuciya ganin wannan mutanen kawai tasan ba
abin arziki ake qullawa a gidan Nan ba, Wanda taga ya nufi wani guri can baya ya taho tare da wasu irin
karnunka masu wani irin gashi a jikinsu bula bula dasu, wani irin kara Mai Kama da fito yayi musu suka Fara
zagaye motar suna wani irin gurnani, wata mota hilux taga sun shiga sai mutum biyu suka Bari a gidan suka
wuce.
Zahra idanunta na ganin karnukan na zagaya motar hantar cikinta ta Kama rawa, a duniya tana tsoron Kare
bare wadannan data gani masu Kama da kura ai Bata San lokacin da jib'i ya rufeta ba duk da sanyin AC
dake motar, wannan wane irin wulakanci ne yayi Mata Yana can Yana aikata masha'a ya sakar Mata
karnuka wadanda zasu hanata fita ko Nan da can.
Daya daga cikin biyun da suka rage a gidan ne ya nufi cikin gidan ya Zama daga Zahra sai Wanda take
tunanin Mai gadi ne sai Kuma masu gadinta Dan taga alama saboda ita aka kawo karnukan nan, Bata San
lokacin da kuka ya kwace Mata ba tana fadin.
"Wayyo Allah! Abba kazo kaga yanda ake wulakantani karnuka ke gadina Kamar wata criminal".
Motsin kirki ta kasayi gani take kamar idan ta motsa zasu fasa glass din su shigo ciki, ba abin tashin hankali
irin gurnanin da sukeyi.
**
Cikin takunsa na mazantaka ya shigo parlourn sai da yazo tsakiya yaja ya tsaya Yana karewa gurin kallo
kamar yau ya Fara shigowa, ba motsin komai, da sassarfa ya Haye steps din da ze sada shi da dakunan
barcin, kofa ta farko ya bude da karfi abinda ya sakata zabura kenan ta Dora hannu a ka jikinta ya dauki
karkarwa tana fadin.
"Wallahi Allah sani akayi bani nake Mata wannan abun ba".
"Shiii! Kept quiet!".
Ya daka Mata tsawa, Yana kusanto inda ta takure a jikin katafaren gadon, kafa Daya ya Dora a Kan gadon
dayar tana dire a kasa Yana Kare Mata kallo tun daga sama har kasa sai wani bashi yake tashi daga jikinta.
Sadda Kai tayi kasa tana tsuma.
Cikin izza da rashin son wargi ya bude bakinsa da kyar yace Mata.
"Meya hadaki da rayuwar iyalina? Meta tsare miki? Keda waye kuka saka rayuwarta gaba? Waya sakaki
bibiyar lamarinta gurin kawo sakonnin mugun Abu? Waye ya sakaki jefo abinda Kika jefa a gidan ranar da
Zayyan ya kamaki? Kada ki kuskura kiyi min karya duk da kin haifeni Zan nuna mini true colour din yanzun
nan, sai kinyi Dana sanin sanin Wanda kikewa aiki wallahi Dan Allah sai nasa an wulakantaki".
Zayyan ne ya shigo.
"Sir akwai damuwa Naga hankalinta ya tashi kamar tana kuka, da alama tsoronsu takeji ko a mayar dasu
ne?".
Wani banzan kallo ya watso masa.
"Sorry sir".
Ya fada Yana sadda Kai kasa.
Kuka ta fasa tana fadin "Dan Allah kayi min Rai yallabai wallahi bani nake Mata wadannan abubuwan ba,
wallahi Hajiya Mama ce duk Aurenta da ake fasawa ma ita ce take yin asirin da ake fasawar saboda an fada
Mata duk cikin yaran gidan Zahra tafi kowa sa'ar rayuwa,mijin da zata aura ba ita ba wani ma saiya huta a
jikinta,uwa uba Kuma tafi duk yaran gidan kyau da cika irin ta Mata ga nasaba ta bangaren mahaifiyarta,ko
rashin zuwan kakarta kasar Nan da hannun Hajiya mamar a ciki, abinda nakai na farko Wanda wannan ya
karba, ta nuna Zayyan, Shima maganine a cikin turaren wutar Wanda akace idan ta turara ka shaki kamshin
bazaka Kara Zama a Azaren ba har abada, zaka kuma manta da ita Zahrar sai dai kotu ta raba Auren, na
ranar Nan Kuma wallahi bansan Kona meye ba tace daga Jos aka kawo Mata wayata ma babu caji har gida
tazo ita da dureba ta aikeni naje Tasha na karbo ta fada min duk yanda zanyi ta bani duba hamsin tace
ladar aikina ce, wallahi iya abinda na sani kenan, kayi min Rai wallahi na daina har abada ka rufa min asiri
wallahi na baro mahaifiyata babu lafiya ni nake kula da ita, kudin da nake samu a gurinta dasu muke cin
abinci na Kuma sayawa tsohuwa ta magani".
Ta fada tana yarfe gumi daga fuskarta duk da sanyin AC dake ratsa dakin.
Tsayuwarsa ya gyara Yana jinjina maganganunta a zuciyarsa, shi yana Jin chakwakiya kala kala Amma ta
zahra ta bashi mamaki wannan wace irin kiyayya ce haka.
"Kinsan abinda yasa Zan kyaleki?"
Da saurinta ta girgaiza Kai.
"Saboda ke 'yar aike ce, shi Kuma jakada Bai taba laifi ba sai ke kin bada gudun mawa gurin cutar da
marainiyar Allah Wadda bataji ba Bata gani ba, kunyi ta kokarin kada ta cimma abinda Allah ya hukunta a
Kanta Ashe Taki kuke zubawa gonarta,ku Baku isa ku Hana Allah s.w.a ciki Alkawarinsa ba a Kanta, hassada
ga Mai rabo Taki ce, Kuma dare ga Mai rabo hantsi ne, duk da ta auri Almajirin malam baku saurara Mata
ba dole sai ta wulakanta ko? To Allah ya nuna muku Kaidin ku ba komai bane da sannu zaku girbi abinda
kuka shuka, babu abinda zanyiwa Hajiya Mama taci darajar mijinta.Amma ke gargadi na farko Kuma na
karshe da Zan Miki kada naji ko labarin ki a Azare duk ranar da naji labarin an ganki saina saka an batar
dake har abada, ga Bilyaminu nan ze mayar dake kutattara ku nemi wani gurin ko arear Bauchi kada naji
labarin an ganki, na bashi sako ze Baki idan dan talauci ne kika Zama jakadiyar yada barna to ki nemi sana'a
ki Kuma tuba ga Allah Mai gafara ne Mai jinkai".
Wani kukan ne ya kwacewa Asabe Bata taba tunanin ze Zama me rangwame a gareta ba,duba da yanda
Zayyan da bilyamu suka ringa surfa Mata Mari har Saida kumatunta suka Haye kamar ta kunsa biredi a ciki.
"Na gode! Nagode! Yallabai Allah ya saka maka da Alkhairi lallai ka cika mumini Mai imani ka saka sharri da
Alkhairi in Sha Allah gobe zamu koma gida Zuru daman nina Kiya da innata tace mu koma mahaifarta Ina
kwadayin abinda nake samu da Mama".
Bai Kara tofa ko kalma daya ba ya juya ya fice daga dakin Zayyan ya biyo shi a baya.
Wani bangaren ya nufa yayin da Zayyan yayi waje, har lokacin su barbar suna nasu aikin, sagir Zayyan ya
kwalawa Kira ya taso daga bakin gate ya nufo shi.
"Dan Allah meyasa baka da lissafi ne Wai? Kasan wacece a motar Nan daka bawa karnukan ku umarnin
nan?"
Kwafa yayi to matar oga ce wallahi idan ta ganeka sai tayi maganinka, da alama wani abun tayi masa kasan
boss ba sauki idan aka taba shi, kasan meye bani mamaki besa nayi bij-biji da wannan matar ba saima ma
makudan kudi da ya bada a bata".
Ya fada Yana tsaki.
"Kai rabu da wannan muyi magana Mai mahimmanci. Dan Allah da gaske ne da ake fadin oga yayi aure?
Wallahi na dauka duk shafta ce kawai".
"Matsa Nan, naka Wasa ne yanzu ka janye su salin alin ka tafi dasu gurinka yanda baze gane Kai ka janyesu
sai yayi zaton sun gaji ne suka zo gurinka".
"Haka za'ayi Bari ka gani".
Ya juya da sauri Yana wani irin fito a hankali, da gudu sukayo gurinsa ya nufi gate suka bishi suna kada jela.
Wata ajiyar zuciya zahra ta saki Dan tayi kukan har ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido.
Bayan fitowar Zayyan Mahmud yakai minti Sha biyar sannan ya fito cikin sabuwar shiga ta wasu kananun
kayan, ash colour T.shirt da black trouser Yana baza kanshinsa kamar ko yaushe.
Da sauri Zayyan ya nufo shi, ganin Basu little a gurin motar yasa Mahmud din yiwa Zayyan Wani kallo,
shafa Kai yayi yana fadin.
"Tuba muke oga, hukuncin yayi tsauri".
Be ce Masa komai ba har suka karasa gurin motar saida ya bude sannan ya dubi Zayyan din Yana Mika
masa key.
"Ungo bari mu koma baya kayi driving din mu na gaji bazan iya mayar damu gida ba".
Ya zagaya ya bude side din zahra take zaune Yana fadin.
"Precious" ya Mika Mata hannu alamar ta kama ta fito...
Tun wayewar gari Hajiya Mama ke jiran Asabe ta kawo Mata sauran magungunan da zatayi amfani dasu
mahadin Wanda ta tura a jefa gidan Zahra, har akayi sallar azzahar babu labarin Asabe, la'asar shiru gashi
har bayan insha'i babu ko duriyarta a gidan gashi wayarta a rufe. Ganin zaman tsammani baze yuwu ba
yasa Mamar fitowa neman sahura, can inda dakunansu suke ta nufa tana tufka da warwara, tashin
hankalinta Daya Bata aiwatar da abinda akace tayi tun safe ba, a daki ta samu sahura ta Bata kudin
adaidaita ya kaita gurin Asabe ta fada Mata tazo tana nemanta.
Labarin da sahura ta dawowa Mama dashi yayi matukar daga Mata hankali, Dan 'yan gidan abokan hayarsu
sun tabbatarwa da sahura tun fitar da sukayi Hajiya Mama Bata dawo gidan ba har lokacin.
Maman Fateemah.
Page 55.
_____Zayyan Yana fitowa yaga yanda zahra ke tsuma sai yaji ba Dadi, gaskiya oga Bai kyauta ba, da
alama ta hadosu ne yake horata ta wannan hanyar wato halinsa Yana Nan na rashin son wargi, itama Bata
tsira ba saiya nuna Mata Hali.
Gurin sagir ya nufa, Yana Jin babu Dadi a cikin ransa, ga wadda za'a hada da barbar Nan yayi kaca-kaca
da banza, Amma ya wani kyaleta taci bulus sai wannan Mace Mai daraja ze hada da wadannan karnukan
nasa masu kama da kuraye su tsare yarinyar mutane, shi ko tausayinta bayaji ya wani yi zamansa a ciki idan
ma sumewa zatayi bashi da damuwa, Allah idan ya wuce saiya casa waccan karamar 'yar iskar dan yaga
alama tsohuwar Yar duniya ce ta kware a gurin munafurci.
A zaune ya samu sagir Yana jin wakar boda katsina.
"Dallah kashe Mana! Kai ko imani ma baka dashi, ka sakarwa baiwar Allah karnukanku marasa mutunci
kazo kana shakatawa,to Bari na fada maka, idan kayi Wasa ka kusa cin taliyar karshe a karkashin oga
wallahi, dan ba kowa ka sakarwa karnuka ba sai amaryar oga, idan tayi marking dinka kana zaune za'ace ka
Kara gaba".
Ya fada yana Jan tsaki yayi gaba abinsa. Sororo sagir yayi yabi Zayyan da kallo sai Kuma ya tashi da sauri
yabi bayansa.
"Dan Allah Zayyan tsaya, fada min gaskiya wallahi na dauka irin masu kawo kansu din Nan ne yake so ya
koya Mata hankali, tunda mun shaida oga baya harkar Mata, shi yasa nayi biris da lamarin su".
"Yayi kyau, wallahil azim nasan hankalinsa Yana Kanta dari bisa dari kawai dai so yake ya nuna mata shi din
Jan wuya ne baya daukar shirme, tun wuri kasan yanda zakayi ka mayar dasu muhallinsu kafin lokacin
fitowarsu yayi su fito patrol"
Fitoh daya sagir yayi musu suka nufo inda suke tsaye, gaban sagir din suka turje gaba yayi suka rufa Masa
baya.
Mahmud ne ya fito sharr dashi da gani wanka yayi ya sake wata shigar kananan kayan sai zuba kanshinsa
yake as usual, tsaye yayi Yana yiwa Zayyan Wani kallon tuhuma sadda Kai yayi Yana shafa sumarsa.
"Sorry sir, Naga ta takura ne kamar zata shide Ni Kuma Naga kada ta Kira maka ruwa".
*******
Hajiya Mama cikin tashin hankali ta dubi sahura.
"Ina kike tunanin Asabe na zuwa kije ki dubo min ita".
Dan jim sahurar tayi kafin tace. "Ina na sani Mama, Daman a gidan nan na Santa ta dalilinki bansan komai
a Kanta ba, gidan da suke ma ai kece Kika kwatanta mini lokacin da Zaki Fara aikena gidan gurinta".
Tsaki mamar tayi, ita duk lamuran sun lalace Mata, to Ina Asabe ta shiga tun jiya? ga number ta Bata shiga
tayi nemanta har ta gaji amsar Daya ce a rufe Layin yake.
Number Aunty Ladi ta nema ta fada Mata ga halin da ake ciki, amma itama layin baya shiga, sallamar
sahura tayi, ga abin fada amma ba Hali tunda sahura iya tsegumin cikin gida kawai ta sani bata da
masaniyar badak'alar karkashin kasar da akeyi a gidan.
Part din Abba ta nufa duk da ba ranar aikinta bane inda sabo ta Saba irin wannan kutsen, a tufe ta samu
part din abinda ya Bata mamaki kenan, juyowa tayi tana tunanin ko wani waje ya fita, to ko bayanan ai ya
kamata gurin ya Zama a bude tunda Ammah zata shiga.
Haka ta koma part dinta tana zancen zuci, bayan kamar minti talatin ta sake komawa kamar dazu gurin a
rufe dai yake,kiran wayarsa tayi, ta shiga Amma ba'a dauka ba, abinda ya Kara daure mata Kai kenan ta
nufi part din Ammah.
Parlourn ba kowa sai TV a kunne volume ta rage tayi sallama shiru ba motsin kowa, wata sallamar ta Karayi
daga can kitchen Alawiyya ta amsa Mata ta fito tana gaishe da Mamar.
"Ina Ammah ne na shigo naji shiru inata sallama" .
Cikin girmamawa Alawiyya tace Mata "tana wancan bangaren na bayan nan".
"Wanne kina nufin sabon ginin da akayi?".
Kaita gyada Mata alamar eh.
Mamaki ne ya cika Hajiya Mama.
"kije ki fada Mata Ina son Zan ganta ne yanzu"
"To ai Mama suna tare da Abba ne, kuma tace kowaye yake nemanta kada a kira ta".
Jiki ba kwari ta juya ta koma part dinta, taso taga Abban kwarai sai dai ta tuna da maganar Daya fada Mata
kwanaki yace kada ya sake ganin kafarata da dare Idan ba aikinta bane, kome take nema ta fada Masa kafin
lokacinta ya wuce karshe ma yace Mata dole ya raba kowa ya mallaki dakinsa a part dinta,wato shine aka
tashi wancan ginin saboda matar so, ita Kuma ta zauna a tsohon gurin da suka Gama dabdala su biyu,
kwafa tayi tana ayyana wani abu a karkashin zuciyarta.
Har karfe goma Bata samu wadanda take nema ba ga Abba ma shiru be shigo ba, be kuma biyo kiranta ba
har lokacin karshe ma network din wayar gaba Daya ya dauke abinda ya tilastawa Mama hakura Dole
Kenan.
**
Zahra barci dai sai barawo amma kusan yanda taga Rana haka taga dare, tayi Dana sanin zamanta a Nigeria
ma kwata-kwata da ba'a nan ta rayu ba da wataqila kalar kaddarar ba haka take ba, tunda tayi sallah ta
Gama arzkar ta nade a gado wani irin barci yayi awon gaba da ita tunda shi ba'a cin bashinsa sai an biya.
Har karfe bakwai Mahmud be shigo gidan ba anyi meeting ne na 'yan unguwar yanda za'a Zuba matakan
tsaro saboda b'atagarin dake neman damun mutanen unguwar, Mahmud ya bada kaso mafi yawa na
gudunmawa da alkawarin bada salary ga "yan vigilant din da zasu rinqa patrol din, abunda ya bawa wasu
da yawa mamaki Kenan dan ba Wani zama yake a unguwar ba sai ayi wata shida ba'aga giccinsa ba,
ballantana wannan karon ya kusa shekara ma be zo ba sai yanzu.
Baibi takan Zahrar ba duk kuwa da yanda zuciyarsa ke azalzalarsa akan yaje din, yaga Idan ba da gasken
gaske ya iya danne son da yake Mata ba Nan gaba baze iya sarrafata ba Idan ta gano itace weakness dinsa
akwai damuwa.
Sameer ya Kira ya fada masa yayi musu order din break fast madam Bata Jin dadi, ze Fara masa surutu ya
kashe wayar Yana fadin.
"Allah ya shirya ka Sameer kayi zaton kowa irinka ne mayen Mata kawai".. Wanka ya shiga so yake su fita
da wuri akwai abubuwan da yake so suyi su Gama kafin yabar kanon.
Awa Daya Mai kyau Sameer ya diro gidan da abincin da Fateeha ya hada, da yake itama gwanace gurin
girkin Kuma Mahmud yana cin abincin ta.
Saida Mahmud yaci ya koshi sannan suka fice daga gidan,Sameer beyi karambanin tambayar Zahra ba
duba da yanda yaga fuskar Mahmud din kamar baya cikin walwala, sai Shima ya Share kawai.
Zahra ba ita ta tashi ba sai gurin Sha Daya da rabi,tayi mamakin yanda lokaci yaja haka, wanka tayi ta shirya
ta saka wata rigar shadda purple dark saita fito da asalin kyawunta da hasken fatarta sosai, Bata daura
dankwalin ba ta yafa gyale tayi gaba tana Zuba nata kamshin. Tunda ta fito taji kamshinsa ya cika mata
hanci tasan Yana gidan kamar zata koma sai Kuma tayi ta maza ta gangaro stairs din.
Ba kowa a duka parlours din da alama kamar baya gidan , gurin dining din ta wuce ganin kayan abinci a Kai,
tana zuwa taga anci abincin, kenan shiya nemo yaci nasa ya fice daga gidan Bata cuci Kanta ba ta zauna
tana duba abubuwan dake cikin sinasir ne da miyar agushi sai Naman Kan saniya da kunun gyada, ba
karamin Dadi taji ba sai taji tana kewar Ammah kusan haka take yiwa Abba duk weekend idan Yana gida
yafi son abincin gargajiya, zubawa tayi taci Mai isarta ta koshi ta kwashe sauran ta Kai kitchen ta saka a
fridge ta dawo ta gyara gurin.
Ta nemi guri ta Zauna tana jiran ta inda Mahmud ze bullu ayita ta Kare zama dashi dai ta Gama duk yanda
za'ayi sai dai ayi.
Wayar Daya Bata ta bude ta Kira number Ammah. Auta ne ya dauka Jin muryar Zahra ya Fara murna da
tsalle yana Kiran. "Ammah ga Adda zahra a waya".
Ya falla da gudu a kofar kitchen suka hadu ita ta fito Jin yana kwalla Mata Kira Yana ambaton zahra Shi
Kuma ze shiga, wayar ya Mika Mata.
Jin Ammah ta karba zahra ta Fara magana.
"Ammah ina kwana".
Dan Jim Ammar tayi Jin muryar Zahrar tayi ba yanda ya kamata taji ba.
"Lafiya kalau, Kuna lafiya dai ko?"
Ammah ta tambayeta tasan zahra Bata Mata karya matukar da damuwa zata fada Mata Koda ba directly
ba.
"Eh, amma Dan Allah Ammah kisaka Baki a fada masa ya dawo dani gida wallahi nan din babu dadi tafiya
yake Yana barina a gidan ba kowa gashi yaki mayar Dani inda Aunty zilai take ko waya bamayi tinda ban
rike sabuwar number dinta ba, Kuma ya karbe wayar da layin". Ta fada kamar zata fasa Mata kuka Dan
zuciyar a kusa take Banda Bata son dagawa Ammar hankali da kukan zata saka Mata.
Bayan sun gama da Auta Amatu ta Kira Saida tayi kamar Kiran ze tsinke sannan ta dauka.
" 'yar rainin hankali da bazaki dauki Kiran ba?"
Zahra ta fada tana murmushi.
Wayar Amah ta cire ta duba number sabuwa ce ba wadda take da ita bace.
"Zahra! Irin wannan surprised haka? Na nemeki yafi sau goma bana samunki naje har gidanki na dubaki da
naji labarin Baki da lafiya, sai Wani guy na tarar yace min kinje Asibiti Kano, ya jikin? Ga Aunty safiya ma
tace a dubaki".
"Da sauki ciwon mara ne irin na period fa shine duk ya tashi hankalin mutane shi sai an duba anga
menene, shine fa ya saka aka tarkatoni kano, kinsan abinda ya daure min Kai Amah?".
"A'a sai kin fada min".
"Hummm! Bari kawai Amah Kinga wasu mahaukatan gidaje da yake yawo Dani a cikinsu, wallahi Amah
tsoron guy din Nan nakeyi ba Wanda muka zauna dashi bane a Nan wannan wani ne daban,ko dressing din
da yake Amah... Bari kawai gashi yace bazan Kara zaman Azare ba Wai sokoto ze kaini garinsu".
Wani kallon kallo sukayi tsakanin Amatu da Auntu safiyya, Aunty safiyar na Mata kallon Mena fada Miki.
"To ke zahra meye naki na damuwa inda me Kai ya nuna ba a Nan ake masa shukku ba? Inda yakeso ku
rayu ba Nan ze ajeki ba, kice sai munzo Kano ko sokoto suna".
"Amah! Bazaki gane ba, yanda kike daukar abin ba haka yake ba, yafi karfin tunaninki fa. Nina fadawa
Ammah ta taikama min ta fadawa Abba yasa Baki na dawo Azare,kinsan cewa tayi nayi hakuri na zauna
inda yake so".
Aunty safiyar ce ta karbi wayar duk da a speaker take.
"Kina jina zahra, karki kuskura ki koyi yiwa mijinki gardama duk abinda ya fada kiyi Masa biyayya nasan har
abada baze citar dake ba, ki saka a ranki Allah ne ya duba lamarinki ya hadaki da Mahmud, na sanshi Dan
garin mu ne duk da shi ba sanina yayi ba. Baki da tantama a Kansa har gidan iyayensa na sani Zan iya kaiki
har dakin mahaifarsa, ki nutsu ki rike Aurenki sauran bayani sai mun hadu Amma yanzu dai ki sakawa ranki
hakuri kawai ba lallai ya amince ya dawo dake nan ba gaskiya".. sallama sukayi da Amah.
Tana kashe wayar Amatu ta kalli Aunty safiyar.
"Me Kika fashimta Aunty?".
Amatu ta tambayi Aunty safiya.
"Mefa na fashimta Banda abinda nake hasashensa tun ganina dashi na farko a gidansu na Nan garin, amma
nayi mamakin yanda akayi hakan ta faru gaskiya, MAHMUD DANGE a nan garin a irin wannan rayuwar?
Amatu kinsan waye guy Nan kuwa wallahi multi million ne ke ko body guard dinsa kike aure a kalleki a Kara
bare Kuma managers dinsa, gaskiya Allah yayiwa zahra wata irin sakayya wadda ita Kanta Bata San gatan
da Allah yayi Mata ba sai Nan gaba wallahi makiyan yarinyar Nan sai sunyi kuka da idaniyarsu".
Amatu jinjina kai kawai take Dan abin girmamemata yayi kamar a Almara Dan kwanaki Saida Aunty safiya
ta nuna Mata hoton zainab a parlourn gidanta a Nan taga duniya iya ganinta, to marasa wadatar family din
Kenan inaga Mai gayya Mai aikin Kuma?.
Bayan Gama wayarsu sakato zahra tayi,Wai Aunty safiya tasan shi, to meyasa lokacin da dukazo gidana
Bata nuna ta sanshi ba,to ai tace shi Bai Santa ba, kenan duk abinda yake fada Mata Babu Wasa a ciki da
gasken dai basakkwacen ne.
Haka ta zauna har gurin biyu, tayi ta neman Ummee Bata samu ba ta hakuri.
Bata girka komai ba da tayi sallar azzahar kasan ta dawo coconut cookies dinta ta dauko taci Tasha
ruwa,kallo ta kunna ko banza ta rage zaman shiru.
Bata Jima da Zama ba taji ana Danna bell din kofa tashi tayi ta bude.
"Lah Aunty Rukayya Daman da gaske Zaki dawo?"
Zahra ta fada tana Bata hanyar shiga, Su biyu ne Ashe tare suke da wata buduruwa kamar sa'ar Zahrar.
Tunda suka shigo take kallon Zahrar da parlourn, Saida suka zauna sannan zahra ta gaishe da Aunty
Rukayyar sannan suka gaisa da wadda sukazo tare.
Kitchen zahra ta shiga ta dauko musu abin motsa Baki da drinks.
Tana dawowa taga Aunty Rukayya na dariya harda hawaye. Ita Kuma dayar tana ta rokon Aunty Rukayyar
da alama akwai abinda ta fad'a da yasa Aunty Rukayyar dariya.
"Meya faru ne Aunty, Naga kina dariya?"
"Bari kawai matar big bro, wallahi Asma'u ce ta bani dariya, Wai Daman ke bahaushiya ce, Kuma Dan
tsabar kauyanci Wai ya akayi taga hadari da wata da taurari a saman rufin dakin Nan gashi ba dare bane
Amma tana shigowa taga dare yayi".
Ta karasa fad'a tana kwasar wata dariyar.
"Kai haba Aunty wallahi Mai sunan Ammah bazatayi haka ba gaskiya ko Mamana? Ai ba kauyanci kikayi ba
ki sake Nan gidan diyarki ne kiyi yanda kikeso ba kwab'a".
"A to Aunty Ashe ma mune masu gidan".
"Gaskiya kam ki mik'e kafa sai abinda kikeso za'ayi".
Zahra ta fad'a tana aje musu tray din a Kan coffee table.
Saida suka huta ana ta hira, sannan Aunty Rukayya ta cewa Zahra.
"Ga fa mai gyaran gashin nan da kunshin".
Bata fuska tayi.
"Gaskiya bana son kunshi sai gyaran gashin dai".
"Ok ba damuwa sai ayi gyaran gashin kawai, sama suka haura a can akayi Mata gyaran, Asma'un kamar ta
mayar da gashin Kanta sai santinsa takeyi, har gurin magariba suna gidan, da zasu tafi Sha Tara ta arziki
Zahra ta hadawa Asma'un har gurin mota ta rakosu sannan ta koma, har akayi sallar insha'i babu labarin
Mahmud, Wasa Wasa har Sha Daya babu labarinsa a gidan, duk sai taji tsoro ya kamata ko ba komai namiji
karone a gida duk da akwai Mai gadi.
Tashin hankali be gama samunta ba Saida taga Sha biyu ta wuce Daya ta kawo jiki.
Ta kasa zaune ta kasa tsaye, hankalinta In yayi dubu to ya tashi Ina ya shiga? ko Kuma ya gudu yayi
tafiyarsa ya barta a gidan haya azo ayi bolinta da safe.
Ita dai barci Sai barawo Kiran sallar farko ta tashi figigit tana salati Dan mafarki tayi da Mahmud din a cikin
wani yanayi Wanda ya tada Mata hankali.
Alwala tayo ta Fara jera nafila har akayi Kiran assalatu sannan tayi sallah ta zauna tana Addu'oi, har gari ya
waye babu ko motsinsa a gidan, ko kasa kasa saukowa tayi ko break fast Bata sauko tayi ba, ta rasa wa zata
Kira ta tambaya wayar Daya Bata ta dauko da sauri ta duba yace Mata Sameer kawai yake Kira da layin
cikin ikon Allah taga number sa, da sauri tayi dialing number sai dai an fada Mata baya arear da yake da
network.
Da kyar ta samu Tasha hollandia da biscuit's Wanda suka taho dasu jiya tunda a fridge din daki ta zubasu
dazu da safe duk da an Sha dabi jiyan Kayan kwalama dai ba'ayi zuciya dasu ba.
Abu kamar Wasa har yamma babu labarin Mahmud ko a waya, zulumin duniyar nan ya Turu ya rufe Zahrar,
taso ta Kira Ammah ta fada Mata sai Kuma ta fasa kada ta Zama marar sirri komai saita fada, tasan tana
fada Mata zata tayar da hankalinta.
Har dare shiru number Sameer din ma taqi shiga, gashi Bata da number Fateeha a ka duk suna Kan layinta
Wanda ya karbe.
Bata gama sarewa ba Saida taga Wani Daren ya Kara zuwa harya raba tsakiya, kukanta Tasha Dan nafilar
ma kasayi tayi har kusan Asuba tana zaune ta Zuba uban tagumi ta rasa ta inda zata bullowa lamarin taga
alama rufa-rufa ba zata yuwu ba saita fadawa wani halin da ake ciki.
Da sunan Allah Mai Rahama Mai jinqai salati da daukaka da Aminci su tabbata ga shugaban mu Annabin
Rahama Muhammad s.a.w .w.
Maman Fateemah.
Page 56.
_____Tunda garin Allah ya waye Zahra Bata sauko kasa ba tana sama snack kawai taci sai chocolate da
Madara ta shiga hada kayan da mommy ta Bata da Wanda Fateeha ta hado Mata da duk abinda tasan tana
da jibi dashi ta shirya tsab tana ayyana yau Kota halin Yaya saita bar gidan Nan Kano ai ba bakuwar ta
bace,zatayi nisa da duk inda ake tunanin za'a ganta,daga Nan direct branch dinta zataje na bank tayi
requesting din ATM sannan ta Ciro kudi tunda ya Maida ita faqarahun dole.
Doguwar rigar ta saka Egyptian tayi rolling ta dauki Jakarta ta hannu sannan ta dauko wadda ta Zuba
kayanta saboda da gaske ba nan kusa zata Zauna ba Dan ya dauke Mata passport ai ba Yana nufi ze hanata
abinda tayi niyya bane.
A hankali take saukowa daga saman har ta sauko kasa Wanda yayi daidai da Danna door bell din kofar
falon jakar kayan ta aje taje ta waye yake kofar.
Tana budewa tayi arba da Zayyan Dan ta gane shi Sarai yanzu, gaisheta yayi, sannan ya Dora fa fadin.
"Oga ne yace bazo na mayar dake Nasarawa".
Ya fada yaja bakinsa yayi shiru.
Shirun itama zahra tayi gaba daya budget dinta ya rushe kenan? Ba yanda za'ayi tace ba zataje ba ina taga
wannan courage din ita da aka sakarwa kare a gabansa wace fuffuka zatayi kuma.
"Ok ba matsala".
Ta fada tana juyawa gurin data ajiye jakar ta dauko ta fito, Ashe su biyu ne da sauri dayan ya karbi jakar
hannunta lokacin Zayyan din ya koma mota ya dauko Wani Abu a Leda ya nufosu.
Madam bari na aje wannan sakon na kashe kayan wutar na fito mu tafi ya fada Yana shigewa da sauri,
Wanda ya karbi jakar ya bude Mata bayan wata Mercedes Benz blue black sai sheki take a Rana da alama
ma sabuwa ce.
Sai ta daidaita zaman ta sannan ya rufe ya koma ya saka jakar, Zayyan ne ya fito da sauri ya rufe kofar
parlourn ya gangaro steps din ya nufo seat din driver ya bude dayan ma ya shigo, ya tada motar suka nufi
gate, da sauri malam musa ya bude musu suka fice fit Yana fadin.
"Allah ya tsare".
Ita dai zahra lamura sun tsaya Mata ba haka taso ba, Saida suka fita daga layin na kusa da Zayyan din yayi
magana.
"Kasan na hadu da Sauban last week a kaduna kuwa?"
"Kai haba dai"
"Wallahi a unguwar sarki suna siyar da breads".
"Siyar da bread Kuma".
"Wallahi kuwa kasan har hawaye yayi Daya ganni Wai Dan Allah na bawa oga hakuri ya daina abinda yake
wallahi sharrin shedan ne ya tuba ya Dena".
Wata dariyar mugunta Zayyan yayi kafin yace.
Waya fada masa lahira ana Dan wake fada da
"Amma baka da man Kai na Fadi sakonsa ko?", "kace Nima ayi waje Dani kenan yanda oga ya tsani Zina ko
sunanta baya sonji ai nasan daga ranar Nima zece halinmu Daya dashi".
"Ai Idan kana son ganin bacin ran oga kazo Masa da maganar matan banza yanzu zakuyi uwar watsi dashi
ko yaya kuke dashi kuwa, katuna karonsu da oga Sameer? Ai wallahi nayi zaton da wasa yake Masa a Kan
Fateeha Ashe da gaske yake Sai da aka ce an daura aure na Kara sarewa da lamarinsa".
Dariya Aliyu yayi.
"Ai lamarin oga ba sauki fa, Wai meya faru ne naji sagir nata bawa oga Sameer sakon bada hakuri gurin
oga?".
Tsaki Zayyan yayi Yana kwafa.
"Bari kawai Aliyu wallahi sagir ba karamin marar tunani bane Wai kawai daga oga yace ya sako su little zasu
yi masa gadi wai ashe shi dauka yayi irin masu kawowa oga kansu ne yake so ya koya mata hankali, tunda a
bude take kowa ya sani oga ba mazunaci bane duk damar daya samu Yana da karancin shekaru kuwa yafi
gane yayi azumi, idan Kuma abin Yana neman fin karfinsa yasha magani kawai, shi lokacin of a interrview
zeyi da wata 'yar shegiya Dana kamo daga can Azare tana Zuba tsubbu a gidansa ta baya, wallahi naso a
ranar ya barni na lakada Mata shegen duka, Amma kasan halinsa karshe ma kudi ya bada a Bata masu
kauri amma da sharadin tabar garin in dai Dan babu take wannan aikin taje tayi sana'a, kasan Allah Aliyu
Idan nine sai nasaka barbar yayi Mata katsa katsa yanda a gaba idan taga Wani zeyi ta irin abinda tayi ta
bashi labarin abinda akayi Mata sanadin munafurci".
Ita dai zahra tunda suka Fara labarinsu taji hankalinta yayi matukar tashi kenan abinda take zargi ba haka
bane, to wacece aka kamo daga Azaren kenan baya so taga ko wacece yasa aka sakar Mata karnuka, ji tayi
wani jibi ya rufeta.
Take ta Fara wata irin nadama tayi Masa cin fuska na karshe akan abinda wataqila saboda ita yake yakin, ita
Ina hankalinta ya tafi a lokacin. Innailaihi!.
Wato hikimar Ubangiji da yawa take, su hirarsu sukeyi ita kuma ta zamar Mata mabudin abinda ya shige
Mata duhu ne, ya tsani ko Mai yin zina Yana raba jaha dashi ko sunanta baya kaunar ji to kenan ranar data
dubi tsabar idonsa tace Masa FASIQI Yaya yaji a zuciyarsa? Kenan shi yasa yayi tafiyarsa ya kyaleta?.
Har sukazo Sultan road din Bata sani ba tayi zurfi a tunani, Saida taji anyi horn sannan ta ankare da sun
karaso.
Har kofar sabon gurin Zayyan ya kaita ya Parker motar ya fito da sauri ya bude Mata, jiki ba kwari ta fito da
sauri Zayyan din yaje ya bude Mata parlourn ya dawo Yana fadin.
"Bismillah, oga yace a fada Miki ki bude wayar hannunki".
"Ok in Sha Allah, nagode kwarai".
Tayi gaba da sauri ta shige tana Jin takun Zayyan din daga bayanta ya shigo da jakar. A Nan ta Zauna Kamar
kazar da kwai ya Mace Mata a ciki, tasan maganar ta bude waya kawai ba da kafa ne kada Zayyan din ya
Dora alamar tambayar rashin fada Mata zezo daukarta.
Tana shiga parlourn ta tsaya cak Dan Wani irin gyara akayi Masa na fitar hankali, ba Dan taga gurin daga
waje ba zata taba yarda inda ta Zauna bane, mamakin duniyar Nan ya rufeta Wai shi wane shine Dan
Allah? tana bukatar ya magantu kafin kwakwalwarta ta samu matsala, ita dai tasan mijinta Almajirin
malam ne, Amma wannan Bata gane waye ba.
Bata Jima da Zama ba taji alamun taba door bell din kofar, tashi tayi take ta bude Aunty zilai ce a tsaye, tayi
wani tas da ita a 'yan kwanakin da tayi Bata ganta ba.
"Masha Allah uwar dakin Kinga yanda Kika Zama kuwa? Kai Alhamdulillahi! Allah na gode maka yau ga 'yar
da mahassada suka tauye a baya yau ta zama sararin samaniya wadda tayiwa yaro nisa sai dai ya tada Kai
ya gano, kin zama murucin Kan Dutse Baki fito ba sai da Kika shirya, Ubangiji ya tsare gabanki da bayanki
ya yiwa rayuwar Aurenki Albarka ko yanzu na koma ga Allah baurina ya ciki Allah ka dubi maraicin yarinyar
nan".
Sai hawaye.
Matsa Mata hanya Zahra tayi, ta shigo tana share hawaye.
"Haba Aunty zilai meye na kuka Kuma ai ba Bata nayi ba Nima kina raina wallahi wayar tawa ce ya karbe
tana gurinsa".
"Ba kukan takaici nake ba, kukan Dadi ne yanda Allah ya rufa Miki asiri nake godewa Allah Kinga yanda Kika
Zama kuwa? Wallahi kamar kasar Kika Bari ai Allah ya sakawa Alhaji da malam da Alkhairi ya biya musu
bukatunsu na Alkhairi Dan su suka kulla wannan Alkhairin, kinsan kuwa yanda mijinki ke sonki? Jiya wuni
guda ana aikin cikin bangaren Nan sai da aka canza komai, Ni nayi zaton ma ko yau zasu dawo daga Niger
din Ashe ke akewa hidima".
Ta fada tana Zama a Kan center carpet Mai laushi.
"Haba Aunty zila ki tashi daga kasa ki Zauna magana zamuyi dake wadda ko Ammah Bana son taji".
"Ba komai ba Saina hau sama ba Ina saurarenki".
"Yaya za'ayi ki Samar Mana hanyar fita daga gidan Nan wallahi Ina Jin kunyar haduwa dashi idan ya dawo
nayi Masa rashin kirki ba kadan ba Wanda har tasa yace min baya Sona kunya kawai tasaka ya barbeni a
matsayin Mata shine nake son nayi nesa dashi nasan ko yaci gaba da Zama Dani sai don kunyar su Baba
malam badan so ba, tun ranar da abun ya faru ban Kara ganinsa ba har yanzu ko waya baya mini bansan
ma inda ya tafi ba sai yanzu a bakinki".
Nan da Nan idanunta suka ciko da ruwa.
Shiru Aunty Zilan tana kallon zahra abinda ta gani a ranar da sukaje gidanta da sahura ya fado Mata a Rai
ko dai Bata yarda dashi bane har yanzu?
"Zahra ki nutsu ki bi mijinki kowa da haka ya girma, ko dai har yanzu Baki bashi hadin Kai bane, har Kika
tunzura shi yayi Miki kaura?".
Ita kunya ma maganar Aunty Zilan ta Bata ta rasa me Zata ce Mata kuma.
"Ba Wai so nake naji meke faruwa ba Amma dai ki canza tunani Ashe bazaki godewa Allah da tukwaicin da
yayi miki ba idan na fitar dake kije ina? Da kike fadar kina Jin kunyar haduwa dashi bakin da yayi tsiwar shi
ze bada hakuri, ai macece ke kinsan yanda Zaki gyaro kayanki baya sonki ya taso mutum daga jihar TAWA
Dan kawai ya daukoki daga wata unguwar zuwa wata nasan ko rantsuwa nayi babu kaffara gyaran da aka
yiwa gurin Nan ba kananun kudi aka kashe ba ki duba Nan, ki kalli can ki shiga dakunan barcin kiga duniya
a baya sonki yake wannan rawar jikin a kanki eyeh?"
"Aunty Zilai bazaki gane ba nifa har yanzu bansan waye nake aure ba sai dai nayi ta Jin jita-jita a bakin
mutane, yace min wannan gidan abokinsu ne Hajiya kakar oga Sameer tace min gidansa ne, tace Sameer
yaron Mahmud ne to ta Yaya Zan samu nutsuwa yace min shi Dan Sokoto ne, Hajiyar ma haka ta fada
min,gara muje gida yazo yayi musu bayani da bakinsa tunda Ni dake abinda muke gani daban abinda muka
baro daban".
"Haba uwar dakina ai ba sai anyi Miki wannan aikin ba a dare Daya Zaki Gama abinki ta Ina Allah ya rageki
ai ke kadai gayyace haba kada ki bani kunya Mana,ai yakin ko yafi haka nasan Zaki iya, Kinga yanda yake
mini Ni kaina da yasan matsayina ba kowa bace face 'yar aiki, kinsan Kullum sau biyu yake Kiran Ammah
Yana gaisheta, duk cikin rashin son ne?".
Rasa abin fada zahra tayi, jakar da Zayyan ya aje Aunty Zilan ta dauka tana fadin tashi na shigar Miki da
jakar naje na samo Miki abinda zakiçi nasan Baki karya ba".
Tashi tayi suka nufi steps din da ze shgar da Kai Daya parlourn, Zahra na tambayar iya Rahane.
Aunty Zilan tace Mata aita koma tun washe garin da suka bar gidan.
"Kinga Karamar arzikin da aka bawa Iya Rahane kewa? Banda kudi zunzurutu".
*****
Tunda ya gama ganawa da masu ruwa da tsaki a matakin kasa da jaha akan batun kamfanin cement da ze
bude a jihar TAWA ya dawo masaukinsu ya kwanta Dan da gaske ya gaji hutu kawai yake bukata, a kalla ya
shafe awa uku Yana barci lokaci Daya farka har anyi sallar azzahar a gurguje yayi wanka yayi sallah, wayarsa
ya kunna Yana mamakin abinda ya Hana Sameer dawowa tunda yasan aikin Daya baro yana yi baze wuce
one hour ba ze Gama shi.
App din da yayi connecting da CCTV ya shiga Yana kallon komai har Zuwan su zahra gidan da duk abinda ya
faru tsakaninta da Zilan.
Nan da Nan yaji garin ya gundure shi gida yake so, da baya ganinta ya iya daurewa Amma ganin Nan nata
kawai ya tayar masa da tsohon tsimi, rashin Jin ko muryarta ta tada Masa zaune tsaye, ba arziki ya tura
Zayyan ya mayar da ita Nasarawa saboda Nan ba'a Gama saka CCTV din ba. Shi Kuma ya Matsu yaga
abarsa hoton waya Bai isar Masa ba.
Kiran Sameer ne ya shigo.
"Ina ka shiga har yanzu baka dawo ba?"
"Wallahi uncle Ishaq ne ya tsare Ni lallai saina nuna Masa inda ka sauka bansan waye ya fada masa ka
shigo Niger ba da jihar da kake da kyar ya yarda cewar ka koma inda ka fito, amma yayi fada kamar ya Ari
Baki yace idan anyi maka laifi a Nigeria su meya shafesu a ciki da har zaka shigo Niger kaki nemansu to na
fada maka lallai Yana jiranka a DAMAGARAM".
Sai daya Gama sauraren Sameer din sannan yace.
Kayi Mana booking flight zuwa Kano ya kashe wayar.
Dan mumushi Sameer yayi Yana fadin.
"Bayani zakayi kaketa wani kauce-kauce zaka shiga hannu ne lokacin ne zaka banbance tsakanin aya da
tsakuwa ba dai Kuna tare ba idan zabo na yawo kere na yawo wata rana zasu hadu, haka kawai ka
haramtawa kanka abinda yake halas gareka ka Wani bige da Shan magani Kullum.
💞💞
Maman fateemah.
Page 57.
______ Basu samu flight direct zuwa Kano ba Saina Abuja, karfe shida da minti hamsin da bakwai
girginsu ya sauka a Abuja Namdi Azekwe International airport.
Wani tickets din Sameer ya saya musu online na Abuja to Kano karfe Tara da kwata ze tashi.
Bayan zahra ta Idar da sallar insha'i ta nufo falon farko inda kitchen yake ta Fara aikin Dan kwarya-
kwaryar abinci vegetable macaroni tayi tare da pepper chicken,sai tayi cocktail fruit, komai kadan tayi dai-
dai cikinta drink ne da pepper chicken ne tayi da yawa tunda tana so ta bawa Aunty Zilai dasu Zayyan idan
Yana Nan, komawa tayi bed room bayan ta Gama komai wanka tayi haka Nan taji tana son saka wasu
fitinannun Riga da siket.
English wears ne kalar sea green da ratsin fari a jikin rigar sai bandana kalar sea green din kayan ko bra
basa bukata, gashin ta matse da Ribom ta saka bandanar ta saki sauran gashin baya sai tayi wani irin kyau
na ban mamaki jikin Nan nata sai glowing yakeyi yarintarta saita kara fitowa sosai, ita Kanta tasan yes ba
karya tayi kyau ba Dan kadan ba, tunda Aunty zila tayi Mata fada dazu da Nasiha ta samu tace Mata ta
sake tayi rayuwar ta Kamar ko wace Mace a gidan mijinta tabar ganin nan a wani bakon wuri, duk inda ya
kaita ta sake a gurin radin Kansa ne ya fada Mata waye shi radin Kansa ne yaki fada mata cikinsa, Amma
dai a ko Ina tayi kokarin Zama matar gida bawai ki Zama kamar 'yar tsaron gida ba.
Takalmi ta dauko ta saka cikin wadanda ta gani kalar fari tas, parlourn ta dawo tana baza kamshin
turarenta kamar ko yaushe.
Aunty Zulai ta Kira a waya tace tazo tana nemanta, Bata Dade da Zama ba Aunty zilan ta shigo, tunda ta
shigo Aunth zilan take kallon zahra, daga karshe kasa hakuri tayi ta Fara fadin "Masha Allah, uwar dakina
Allah ya kade hau da bala'i Ina ma yallabai Yana garin Nan da sai ya bada tukwuicin kwalliya nan, haka nake
son ganinki ki nuna Masa rainon Ammah ce ke, na rasa abinda yasa Kika tsaya sanya ai ki rikita Masa lissafi
da gasken gaske wani ma yayi rawa bare d'an makadi, ki dauki makaman yaki kiyi kaca-kaca da lissafinsa
yasan Mata suna suka Tara yasan da gaske Zahra ce cikin taurari".
Mamaki Aunty zilan ta rinka bawa Zahra.
Baza kace ita ke fadar wadannan maganganun ba duba da ba ilimi Mai zurfi tayi ba iyakarta aji uku na
Karamar secondary aka cire ta akayi Mata aure. Ta gane Zama da Ammah yau da gobe ne ya kawo haka.
"Aunty zilai kenan ko yana Nan ba Wani yabawa zeyi ba kedai abar kaza cikin gashinta kawai, wa yasan
ranar dawowarsa tinda ba fada min tafiyarsa yayi ba menene nawa na bin diddigin yaushe ze dawo".
Dan murmushi Aunty zilan tayi, ."Haka kike gani wallahi nasan duk inda yake a duniya kina maqake a
zuciyarsa ba irinki ake yiwa rikon sakainar juji ba ki rubuta ki aje wannan maganar Dana fada, Baya Nan
Amma ta Yaya ya taso mutum tun daga TAWA Dan kawai ya daukoki, Kinga kenan ko mu"amalarki bada
kowa ya aminta ba tunda gidan Nan cike yake da ma'aikata kala kala, ko Rukayya ya fadawa zata dawo
dake Amma hakan be Masa ba saboda yanayin rayuwa da ake ciki gara ya kashe ko nawa ne a kawo Masa
ke cikin aminci".
Itama zahrar dan murmushi tayi.
Aunty zilai kenan, haka kike gani?
"Kwarai kuwa, Aina fada Miki d'azu"
Sun Dade suna hira da Aunty zilan kafi tayiwa Zahra sallama, da kyar zahra ta bari zilan ta koma part din da
take, Wai tsoro takeji ita Daya a wannan gurin, pepper chicken din ta Bata Wanda ta Zuba Mata ta, ta Bata
Kuma Wanda ta zubawa su zayyan din, ta amsa tana godiya.
Karfe goma da minti minti ashirin su Mahmud suka sauka a filin sauka da tashi na malam Aminu Kano,cikin
suit yake ash colour sai laptop dinsa dake rike a hannun Bilyaminu, cikin takunsa na cikakken namiji ya
gangaro steps din jirgin, Zayyan ne yazo daukarsa.
Sameer yaso ya raka Mahmud gida Amma sai ya nuna Masa yaje gurin iyalinsa kawai, har mota binya ya
Kai Masa laptop din, ya koma Sameer ya tafi dashi tunda a nan airport din yabar motarsa.
Tunda Aunty zilai ta tafi zahra ta tashi ta nufi dining din ji tayi abincin ya fice Mata daga rai pepper chicken
din kawai taci kadan ta Zuba cocktail fruit a cup ta Fara Sha, cup din na bakinta ta lumshe Ido saboda yayi
Mata Dadi sosai, kawai ji tayi atmosphere din falon ya canza wannan fitinannan kamshin ya had'e falon,
kasa bude idon tayi don ita tsoro ne ya rufeta ita dai tasan ita daya ce a parlourn ba Wanda ya shigo itace
me bude kofar Kuma Bata bude ba, ko cup din ta kasa saukewa kuma Jin kamshinsa take Yana Kara kusanto
ta, ji tayi zuciyarta ta tsinke Bata San wace kaddarar ce Kuma ke kusanto ta ba, ba alaman.shigowar mutum
sai kaji kamshinsa ya cika guri.
A hankali ya tako kamar me slow motion ya karaso gurinta ya saka hannu ya zare cup din, ya danyi sipping
na drink din nata,sanyin ya ratsa Masa kirji, ita dai zahra ta kasa ko motsin karki, taki Kuma bude idanun
taga ko wanene duk da taji shine.
"Precious".
Ya Kira sunanta
Shiru tayi taki magana, cup din ya aje a gefe ya Dan rankwafa daidai fuskarta Yana Kare Mata kallo Yana
tasbihi ga Allah s.w.a da yayi Masa wannan kyautar.
"Wai bazaki bude idanun ba?".
Hannu ta saka ta Kara rufe fuskarta.
Ikon Allah ya tsaya kallo,wato yarinyar nan Kullum da irin salon da Zata fito Masa dashi, idan ta murzawa
idanunta toka tamkar Bata taba saninsa ba, yanzu Kuma Dan tsabar kinibibi ta Wani lullube ido, ai karya ne
Bata wani Jin nauyinsa tunda Zata iya fada Masa duk abinda yayi Mata Dadi a ranta.
"Wallahi ki bude ki kalleni har wata kunyata kikeji da Kika casheni tas, yanzu Kuma kizo kina Wani kinibibi".
Kujerar ta ja baya kadan ta tashi tana, ta bude idon kamar yanda yayi umarni Amma taqi kallonsa.
Ai Yana ganin ta Mike din ya Zuba Mata lumsassun idanunsa yana Kare Mata kallo tayi Masa wani irin kyau
na ban mamaki, ga kayan wasu fitinannu ne ta saka masu motsa jam'iyya, dai ya fada Mata zuwansu da sai
yace Dan ta tsokane shi tayi shirgar to be fada Mata ba, kawai radin Kanta ne sai akayi arashi Kuma ya
tarar.
Kara matseta yayi a jikinsa, ji tayi jikin nasa kamar yana shaking, Bata San lokacin data kankameshi ba sosai
tana fadin.
"Pls! meu Amor wallahi na daina fada maka makamanciyar kalmar har abada, kayi min hukuncin Daya
Dace da laifina matukar zaka huce, wallahi badan ka min shigar sauri ba da bazaka sameni a garin Nan ba
da wane idon Zan Kara kallonka kalamaina sunyi Muni".
Sun dauki digon lokaci a haka Zahra nata sauke numfashi.
Kalamanta na karshen sun doki zuciyarsa, da me take Shirin aikatawa ke Nan?
"Thank God".
Ya fada a zuciyarsa.
Saida yaji tsayuwar na kokarin gagararsa sannan ya zaunar dasu a kujerar dining din tana jikinsa, bandanar
da ribom din ya zare yana Kara shafa gashin Daya Sha gyara.
Harshensa yasa ya laso hawayen Daya gangaro Mata daga ido, Wani yarrrr taji gaba Daya a jikinta.
A hankali ya furta.
"Meye na kuka Kuma? gani na dawo kuka Kuma ai ya Kare, tashi ki bani abinci yunwa nakeji tun safe ta
kasa cin komai".
Gashin ya shiga hade Mata da ribom din Daya zare ya dauko bandanar ya mayar mata, sannan ya gyara
Mata rigar Daya kusan cireta daga jikinta, Yana Kara shafar gefen fuskarta Yana manna Mata light kiss a Kan
tsinin hancinta.
Lumshe Ido tayi ta bude a hankali, kashe mata Ido Daya yayi Yana fadar.
"Ki bani abinci kada ki maye gurbinsa fa, naga alamar son abin a cikin idanunki, Bari na Gama mu shiga ki
fada min yaushe Kika Zama haka a yan kwanakin Nan da Bana Nan?".
Shiru tayi Masa Dan ba karya yayi ba ji tayi kamar karta rabu da jikinsa sabanin da.
A hankali ta tashi daga jikinsa Amma fa sai Wani sadda Kai takeyi.
Vegetables macaronin ta Zuba masa ta Zuba Masa pepper chicken din da drinks.
Ta matso dasu gabansa tana fadin.
"Bismillah".
Coat din jikinsa ya cire ya Miko Mata Yana fadar.
"Kaita can inda na aje laptop din can kizo muci nasan ba kici komai ba".
Bata fuska tayi cikin shagwaba tace.
"Naci nawa fa wannan naka ne na aje maka".
"Kinsan zanzo ne?"
Kai ta gyada Masa.
"Banda karya fa?"
Dan smile tayi Wanda ya Kara Mata sirrin kyau.
Saida yaci ya koshi ya Dora drinks sannan ya ja abarsa suka nufi bedroom din, Yana shiga yaga dakin yayi
Masa yanda yake so.
Ruwan wanka ta hada masa Bata Kai ga fiowa ba ya shigo daga Baya ya sako hannunsa akan cikinta ya Dan
kwanto jikinta. Baya gajiya da shakar kamshin jikinta.
"Bazaki tayani wankan ba?".
Ya fada Yana Dan shinshinar gefen wuyanta, Yana Kuma kokarin rabata da kayan jikinta.
Cikin kasalalliyar murya tace Masa.
"Yanzu ba dadewa nayi wanka kada nayi mura".
"Bazakiyi ba ai kina da maganinta a kusa, pls ki Bari mu samu body contact Mana kinsan yanda na azabtu
kuwa? Ki sassautawa Dan Husainin Ammi Mana kada fa Hajiya Inna tace kin mallake Mata jika tayi bore
tace saina Miki kishiya ta uku tunda kina da uwar gida".
Ya fada Yana ida zare Mata rigar da sauri ta kankameshi tana saka hannu a kirjinta, kafin ta Sami bakin
korafi yayo kasa da Kansa dai-dai bakinta ya hade bakinsu.
Sunfi minti biyar a haka kowa na sauke numfashi, da kyar ya iya hakuri sukayi wankan Nan ma Saida suka
Bata lokaci sosai sannan ya sassauta Mata.
Gurin kwanciyar ma haka ya hanata saka abin kirki sai wata nighty wadda da ita da babu duk daya.
Darasin karatu yake Dora Mata Wanda ya girmewa shekarunta da wayewarta, ita mamaki yake Bata ba
Wani yawan shekaru ke gareshi ba dududu baifi sa'an su Ya Abdul Hakeem ba, amma abinda yake Mata
sunfi karfin shekarunsa, ya gigitata iya gigitawa, Dan Saida ya goge Mata hadda tsab ya sakata wata irin
rayuwa wadda Bata taba tunanin da akwaita ba yayi mata wasu abubuwa da bakinta baze iya fada ba, ya
Kai bakinsa inda Bata taba tunanin ze kaiba, Wani sabon Mahmud take gani Wanda bashi da ta Ido ko
misqalazarratin, ya fada Mata wasu maganganu masu nauyin fada, Dan har ta saddaqar Mai afkuwa ce
zata afku, amma sai taga ba hakan bane amma ko hakan ba sauki, dan sun Kai karfe biyu da rabi kafin su
koma toilet yin wanka a can ma Saida ya Kara cakusata da kyar ya saurara mata.
Bayan fito ne sun kwanta janyo yayi jikinsa yasa hannu ya zare rigar jikinta.
"Na shiga goma Ni Fatimah".
Zahra ta fada a zuciyarta, Dan da gaske da wata irin fitina ya dawo Mata, Bata taba zatonsa a haka ba, tana
mamakin me yake dakatar dashi Dan taga fitina iya ganinta a tare dashi,wallahi tsotonsa take da gaske
yake Ashe lokacin Daya ce Mata shi sadauki ne taga zahiri.
"Wash!!! Allah na Dan Allah ka Bari barci nakeji".
Ta fada cikin raunin murya Dan da gaske taji a jikinta.
"Ba abinda zanyi Miki kiyi barcinki Mana. Ya fada Mata cikin low voice, abinda ya Kara yi Mata yasa ta rike
Masa hannu da sauri tana fadin Dan Allah fa!"
"Naji ki Bari na Kara Jin duminki mana precious nifa kamar jaririn Daya wuni baisha.... Ai kin gane". Yasa
hannu ya Kai shafa gurin.
Tanaji Tana gani yaci gaba da sabgarsa Saida ya gaji Dan Kansa ya kyaleta.
Cikin ikon Allah Basu makara sallar Asuba ba, lokacin Daya dawo harta Gama Azkar dinta ta koma ta shige
blanket ta Fara barci.
Shima barcin ne a idanunsa fal jallabiyar jikinsa kawai ya cire ya Zama daga shi sai boxer short,ya shige
jikinta ya gyara musu blanket din.
Sai kusan karfe goma da kwata Mahmud ya farka, zare jiknsa daga nata ya tasheta itama.
Tare sakayi wanka suka shiga kitchen,.wunin ranar haka Sukayi shi, duk inda ta saka k'afarta Yana Maida
tasa har girki tare sukeyi tana bashi abubuwa Yana taimaka Mata da yankawa ko wankewa, har lokacin ba
Wanda yaga duriyar Zahra Shima masallacin kawai ke fitar dashi da dare ba yanda beyi su fita ba amma ta
qiya daga karshe ma cewa tayi ta daina fita dashi a garin Nan tunda anyi biyu basu dawo gida lafiya ba,
baza'ayi na uku da ita ba, shi dariya ta bashi yanaji yana gani dole ya hakura da fitar.
A sati Daya sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki wadda ta saka musu soyayyar juna kamar su cinye
junansu.
Babu abinda ke fitar da Mahmud sai sallah, Su duka sukayi wani irin fresh dasu, bare ma zahrar ko Ina ta
cicciko kamar me yaron ciki.
Gatan duniyar Nan Mahmud ya nuna Mata wani lokacin har tausayi yake Bata, bashi da lokacin Kansa sai
nata Koda yaushe Yana makale da ita, tun zilai na damuwa da rashin ganin Zahra harta hakura, ba ita take
musu abinci ba da gyaran part din, ita Kanta Zahra Batasan waye yake gyarawa ba ba Kuma ta damu da
sanin me yin ba, bedrooms din ne dai ita ke gyarawa ta saka turaren wuta Kuma duka gidan.
Satinsu biyu cur suna manne da juna, ko part din sau biyu ta fita daga ciki lokacin da yace suje lambu tayi
mamakin girman gidan Dan kafin mutum yaje lambun da tafiya, kayan marmari ne sosai a ciki harda Apple
dasu grapes, ta sauran su mango dasu Papaya, ranar yasha tambaya lokacin Dan kasa hakuri tayi da suka
nufi bargar dawaki da bangaren da ake kiwon jimina da su dawisu. Ta jefa Masa tambayar Wai wannan
gidan na waye Daya sakar maka ka Mike kafa kamar bazaka fita ba?
Dariya yayi Mata Yana fadar "ba ance Hajiyar makwarari ta fada miki gidana bane tunda kinji daga bakin
kakata ai inaga nawan ne tunda kike Kama maganarta wadda rikicin tsufa kawai ta iya".
Shiru tayi Masa tasan tunda ya ambaci haka babu abunda ze fada Mata akan tambayar ta.
Har doki ya dorata a ranar yayi Mata hotuna da yawa Dan kayan sport suka saka saita kalar fari da ja it's ta
Dora hijabi a Kai da suka kebe Kuma ta cire, sunyi hotuna sosai masu matukar kyau bare na garden din sai
background din yayi kyau sosai.
Da dare suna zaune a parlour tayi pillow da cinyarsa yana kallon tashar super sport ana nuna wasan
realmadrid hannunsa Kuma yana. Wasa da gashin Kanta Wanda ya Sha gyara, sai kamshin hairspray ke
tashi duk ya yamutsa Mata shi taga alamar da bayani a tare dashi. Wayarsa ce tayi dauki slow music na
wakar wata tshowar mawakiyar America brandy.
Tashi tayi tsam ta nufi wayar ta dauko sunan Habib ta gani Yana yawo akan screen din tana kawo Masa
Kiran na yankewa, kiransa yayi gefe ya koma ta Zauna saboda Bata San me zasuyi tattauna ba, tana can
tana kallon wani penalty da aka bawa Barcelona suka zubar, sai ji tayi ya tashi da sauri Yana fadar.
"Innailaihi wa Inna ilaihi raji'un! Yaushe ne abin ya faru, subahanallahi gamu Nan zuwa Azaren da safe in
Sha Allah".
Naman Fateemah
Page 58.
................Da wani irin sauri da sassarfa ta karaso inda Mahmud din yake tsaye rike da wayar Yana salati,
hannunsa ta rike tana jijjigawa tana fad'in.
Waye ya mutu a Azaren, wayyo Allah Ammah ta, shikenan Ashe munyi sallama kenan"
Ta rukumkume shi sai kuka.
Da kyar ya banbare ta daga jikinsa yana fad'in.
"Menene haka precious Wai? Waye ya fada Miki mutuwa akayi da Zaki tada hankalinki, Nima ki tada min
nawa".
Zaunar da ita yayi, sannan shima ya Zauna suna facing din juna tana matse hawaye daga idonta.
Hannunta ya kama ya rik'e Yana fad'in.
"Ki nutsu ba Wanda ya mutu fa Baba malam ne ya Fadi dazu bayan sallar insha'i a kofar masallaci yazo
tsallake kwalbatin da ake gyara ya taka slap ya zame dashi sai Kuma slap din ya biyo shi ya fada Masa a
bayansa,bayan an Ciro shi daga ciki sai Kuma sai tafiya ta gagara suka nufi Asibiti to a can ne suka yiwa Su
Habib bayanin ya
Samu matsalar data Hana kafafunsa tafiya, yanzu haka Yana F. M. C likitoci na tsaye a Kansa Wai suna
tunanin ya Samu Spinal cord injury ne".
Wani irin zaro idanu zahra tayi tana fadin.
"Innailaihi wa Inna ilaihi raji'un mun shiga Tara "spinal cord injury? shikenan Baba malam sai yanda Allah
yayi" .
Sai wasu sabbin hawayen.
"Kiyi hakuri kuka baya magani sai addu'a kawai".
Basu Dade a parlourn ba suka koma ciki Dan kallo dai ya tashi, ya Dade Yana lallashinta kafin ta saurara da
kukan, ya sani sunyi wani irin sabo da Baba malam Yana kaunarta sosai Dan sauda yawa Yana ganin Yana
saka Almajirai Yi Mata Addu'oin na musamman, itama sauda yawa Yana ganinta da Leda a hannu ta
kawowa malam din.
Kwana Sukayi ba nutsuwa Kota sisin kwabo a tare dasu Malam ubane na gaske Mai nuna kauna da karamci
ga kowa.
Dan Mahmud kusan kwana Sukayi suna waya da Habib sun Kai uku da Rabi Saida likitoci suka gama
dubashi sukayi Masa Allurar barci sannan ya samu nutsuwa, zahra ma har lokaci batayi barcin ba.
Bayan ya aje wayar be kwanta ba toilet ya shige ya Jima kafin ya fito da bathrobe da karamin towel a
hannunsa Yana tsane ruwa, jallabiya ya zura ya Fara nafila, ganin haka ya saka Zahra tashi itama tayo
alwalar ta dosa nafilar itama, suna zaune har akayi Kiran assalatu.
Shi ya fice, sai kuma gashi ya dawo tana niyyar tayar da sallah, tsayawa tayi saboda gurin da take ya nufo.
"Ki shirya kafin na dawo da wuri zamu wuce Azaren".
"To, insha Allah".
Ya juya ya fice ita Kuma ta tayar da sallah zuciyarta fal murna abunda ta cire Rai dashi kenan kwana kusa,
Ashe basu sani ba a kusa zasuje garin, ikon Allah Kennan sallar ta tayar.
Babu Bata lokaci ta shirya har ta shiga kitchen tayi simple Abu kamar yanda taga Ammah nayi idan Abba
zeyi irin wannan tafiyar takance lusarar Mace ce ke barin mijinta ya fita neman abin breakfast a hanyar
tafiya, wadda tasan kanta Bata barin mijinta neman abincin titi yayin sakakkon tafiya.
Kafin ya shigo ta hada basket tsab a bedroom ya sameta tana kokarin saka doguwar rigar abaya 'yar Dubai
a cikin kayan dake dakin ta ganta ba karya ta amsa sunanta, a hankali ya karaso da sallama a bakinsa Yana
zuwa rigar ya karba ya saka Mata ya dauko veil din ya dauki clip din me zanen heart da stones a jiki yayi
Mata rolling, ita har mamaki ya Bata ganin yanda yayi Mata dos ba Wani mistake.
"Kinyi mamaki ko? A gurin Aisha na iya Ni nake Mata idan zamu fita unguwa tunda da Mace aka hadoni ai
dole na iya sabgar mata".
Yayi gaba da sauri ya nufi toilet.
Da idanu tabi shi tasan wani wankan ze sake, ita batasan wane irin jikine dashi ba sanyin ruwa baya Masa
komai a zamansu dashi ta fuskanci ma'abocin son ruwa ne shi.
Handbag Mai Dan girma ta dauko ta Zuba turaruka da Dan abinda baza'a rasa ba a ciki.
Yana fitowa daga toilet din ya fice Yana fadin ta jirashi a parlourn farko.
Ba tafi minti biyu da Zama ba taji alamun tsayuwar mota a kusa da parlourn, tashi tayi ta shige kitchen ta
dauko basket din, ta fito kenan shi kuma ya Gama gangaro steps din kenan, cikin wani yadin filtex ruwan
sararin samaniya da hula itama sky-blue din Yana daura agogo a hannunsa, wani irin kyau taga yayi Mata
kana ganinsa kasan yarone matashi Maiji da kuruciya ga Wani sirrin kyau da yake fita daga fuskarsa,
ganinta da basket ya bashi mamaki karasowa yayi Yana fadar.
"Wannan fa".
Ya nuna Mata abinda ke hannunta.
"Is for you".
Ta fada tana nufar inda ta aje handbag dunta.
"Thanks, wato so kike na koma kamar yaron goye ko?".
Dan juya masa sexy eyes dinta tayi kawai.
Karbar basket din yayi suka jera sun bala'in kyau Kamar ka daukesu ka boye saboda yanda sukayi wata irin
dacewa kana ganinsu kasan couple ne da suke cikin ganiyarsu.
Suna fita Zayyan yayo zarya ya karbi basket din daga hannun Mahmud Yana fadin.
"Good morning sir".
"Morning"
Ya amsa masa, sannan ya gaishe da zahra.
Da sauri Zayyan ya budewa Mahmud back seat ya zagaya ya budewa zahra dayan gefen itama, har ze shiga
seat din driver Mahmud yace yaje side din da Aunty zilai take ya fada ta shirya zuwa goma Sameer zezo su
tafi.
Tare da Aunty zilan suka dawo jiki na Mata tsuma har kasa ta tsuguna ta gaishe da Mahmud sanan Zahra ta
gaishe ta, zahrar tayi Mata bayanin halin da ake ciki, cikin nuna jimami ta jajantawa Mahmud din tare da
Addu'ar fatan samun lafiya.
Saida aka bude musu gate suka fice sannan Aunty zilan ta koma da sauri tayi abinda zatayi na abincin da
take dafawa saboda hadiman gidan ta shirya kada a jirata.
Saida suka bar kano sannan Mahmud ya Danna wani guri jikin kujerar gaba, take wani covering ya raba
tsakaninsu da Zayyan da yake aikin tukinsa.
Janyota jikinsa yayi ya kwantar da ita baice Mata komai ba itama batace masa ba sai fuskarta da yake Dan
shafawa lokaci zuwa lokaci Batasan sanda barci yayi awon gaba da ita ba, Bata farka ba Saida suka kusa
shiga Azare Shima wayar da sukeyi da Habib ce ta tasheta.
Warrr tayi da Ido tana kallonsa.
"Kin tashi?"
Kaita gyada Masa tana janye jikinta daga nasa.
Directly FMC suka nufa a parking space suka tarar da Habib yana tsaye Sam be gane su waye a motar data
wuce shi tayi parking a nesa kadan dashi, hundred percent hankalinsa na Kan wata mota Mai shigowa, da
sauri Zayyan ya budewa Mahmud kofa ya fito Yana rike da hannun zahra kamar me tsoron kada ta Bata,
duk yanda taso ta zame hannunta yayi mirsisi ta qiya, gurin da Habib yake suka nufa kafin su karaso Habib
ya juyo da sauri Jin turaren Mahmud daga bayansa.
"Masha Allah"
Ya fada a zuciyarsa, ganin yanda sukayi wata irin dacewa gaba daya gani yayi sun canza Masa tamkar masu
rayuwa a kasashen Europe din nan.
Da sauri ya nufo Mahmud Yana fadin "wallahi banyi zaton ku bane a waccan motar kaga wadda nafi maida
hankalina a kanta Nan".
ya nuna irin motar Zahra.
"A'a ata yallabai mukazo tare da drivernsa, ya fada Yana tsare zayyan da Ido.
Zasuyi musabiha da Habib Zahra ta samu zare hannunta daga cikin nasa, idan shi bakone ita garinsu ne
yanzu da anyi dace idon sani ya gansu zance ze cika unguwa Daman ya lafiyar kusa ita da komai nata a baki
yake, ga unguwar tasu ta 'yan gargajiya.
Gaishe da Habib zahra tayi tare da tambayarsa Mai jiki, sannan suka gaisa da Zayyan ma.
Habib yayi musu jagora zuwa dakin da aka kwantar da Baba malam vip ne Nan Abba ya saka Abdul
Hakeem ya biya aka saka shi duk da Abban baya garin.
Lokacin da suka shiga ya koma barci ba kowa a dakin sai Abubakar kadai duk yawanci sai bayan anyi sallar
Asuba suka koma gida.
Kai tsaye gurin gadon Mahmud ya nufa, ya tsaya dai dai Kan malam din, gani yayi yayi wata irin rama
fuskarsa tayi wani fayau sai qananun raunika a gefen idonsa na dama da gefen kumatunsa.
Kujera Abubakar ya gyarawa zahra sannan suka gaisa tayi Masa jajan jikin malam, gurin Mahmud ya karasa
sukayi musabaha tare da jajantawa juna.
Ya Dade a tsaye a gaban gadon daga shi sai mahaliccinsa suka San Abinda yake saqawa a cikin zuciyarsa.
Juyowa yayi Yana facing din Abubakar da Habib.
"A hannun wane doctor case din malam yake?".
Habib ne yace.
"Yana hannun doctor Omole consultant ne a bangaren Orthopedic, yanzu ma ba dadewa suka bar dakin
lokacin ma inaga kun shigo garin".
"Ok ba matsala, muje ka rakani na gansa".
Ya fada Yana nufar kofar da wannan azamar tasa, su Abubakar suka rufa Masa baya.
Zayyan ma ya bisu dakin ya rage daga Baba malam da yake barcin dole sai Kuma ita zahrar dake zaune tana
duba wayarta.
Office din likitan suka nufa a hanyar suka hadu dasu salisu sun dawo harda Mu'az a cikinsu, tasu batazo
Daya ba da shi sam saboda yanda baya iya kauda Kai akan mata, kuma salisu ya taba fada Masa har ciki ya
taba yiwa wata yarinya 'yar Mai aikin gidansu finkarfi yasa aka dannesu aka bawa wani marar gata.
Sun gaisa tare da jajantawa Mahmud.
Salisu ne ya kalli Habib Yana fadin.
"Wai Dan Allah a Ina mutumin ya maqale ne? ko wayarsa fa na Dade ban samu ba, ka fada Masa wallahi
zamu kwace kanwar mu tunda haka ze Mana gara ta dawo kusa damu yanda zamu ringa ganinsa.À Amma
ka dauke yarinya kayi shiru sai wani kyallin jiki kake Kamar Mace".
Dan murmushi Mahmud yayi yana fadin.
"Ka dauki bashi Zan biya, kanwarku Kuma sai yanda nakeso zanyi da abata haka kawai Zan ajeta sakaka
kowa Yana gane min ita, Mai tsada ce".
Ya fada Yana tafiya tare da cewa.
"Bari muga doctor"
Har sun Fara tafiya Mahmud ya tsaya ya Dan koma baya gurin Zayyan da suka bashi 'yar tazara.
"Kaje maza kafin zugarcan su Karasa dakin ka Kai precious can gidansu kace Zan kirata".
Ya juyo shima Zayyan ya juya da sauri.
Suna zuwa kofar doctor din wani matshin doctor ya fito da sauri sauran kadan suyi karo da Habin ya danja
da baya Yana fadin.
"Sorry".
"Ba komai".
Habib ya fada, sai Kuma doctorn ya kalli Habib sosai.
"Habib Abubakar ko?"
Kai Habib din ya gyada masa.
"Ok. Bismillah daman kiranka zani akan issue din Babanka".
Tare suka shiga ciki Mahmud da Abubakar na biye dasu a Bata.
Sun samu doctors kamar biyar sun zagaye doctor Omolen Yana ta bayani sun saka hoto X-RAY a tsakiya
wasu na yin jotting na abinda yake musu bayani.
Matsawa wasu sukayi Habib da wannan likitan suka tsaya suma, doctor Omolen ne ya dago lokacin da
doctor Hafeez yake Masa ga yaron patient din Nan harma da wasu yaran nasa ya fada Yana nuna su
Mahmud da Abubakar.
Umarnin tasowa doctorn yayi musu, ba musu suka taso.
Bayani ya Farayi musu Yana nuna musu inda ya samu matsalar k'ashin bayansa k'asusuwan ne suka matse
sakamakon fadowar da slap din yayi Masa a gadon bayansa, su suka matse spinal cord dinsa har ta samu
injury Wanda ake Kira (spinal cord injury).
Yanzu Abu biyu ne zuwa uku na farko ko a turasu National Orthopedic na Dala Kano ko ibadan ko Kuma su
fita dashi India wani Asibitin Fortis hospital dake new Delhi ko Kuma Max orthopedic surgeon hospital
shima dai a Indian.
Take jikin Habib ya Kama tsuma Saida Mahmud ya zaunar dashi a resting chairs na cikin office din Yana
Zama ya fasa kuka kamar mace.
Abubakar ya fita da Habib waje Yana bashi magana akan ya dangana yayi Masa Addu'ar samun lafiya da
Kuma mafita.
Saida suka fice Mahmud ya fuskanci doctor din Yana tambayarsa wane Asibitin ne yake ganin shine best a
cikin biyun Daya fada musu na Indian.
Wani daga cikin doctors din ne yace abunfa ba Mai sauki bane za'aci millions of naira a Kan aikin ga kudin
flight.
Dan murmushi Mahmud yayi Yana fadin.
"Ba komai Allah ze rufa asiri, a bani website dinsu duka zamu bibiyesu muga wanne zamuje in Sha Allah".
Ba Bata lokaci aka bashi address din duka biyun da wasu sabbin magungunan da za'a saya da Allurai yayi
musu godiya ya nufo kofa likitan da yayi musu jagora ne ya biyo Mahmud Yana fadin.
Idan babu damuwa zanyi magana da Kai,akwai wani Dan uwana da yake zaune can Indian Zan hadaku
dashi Dan ku samu saukin abubuwa"
"Ok Nagode in Sha Allah zanyi maka magana idan komai ya kammala".
Sukayi musabaha doctor din ya koma shi Kuma Mahmud ya nufi inda ya hangi su Habib Abubakar nata
watsa hannu da alam fada yake yiwa Habib din.
Koda ya karaso Baice musu komai ya zauna kusa da Habib Yana sauke numfashi.
"Ya ake ciki'. Abubakar ya tambayi mahmud.
Ba komai in Sha Allah za'ayi abinda ya kamata jiran zuwan oga Sameer nakeyi baze gagara ba suna aikin da
yafi wannan ma ai qungiyoyin suna da kudi sosai. Dan wannan aikin ba wani Abu bane yanzu Kai Habib
idan malam ya tashi ka tambaye shi inda za'aga passport dinsa kaima kaida Abubakar sai ayi muku tare da
Visa tunda daku ya kamata aje".
Yana Gama fada ya mikawa Abubakar takardun da za'a sawo magani tare da ATM card dinsa yana fadar a
karbo wadannan magunganan.
Tunda su zahra suka fito daga Asibitin ta ringa Alla Alla su Karasa gida taga Ammah. Suna shiga harabar
gidan Bata jira Zayyan dake kokarin fitowa bude Mata ba ta fito da sauri tamakar zata kwasa a guje,
Musaddiq ne ya fito Yana zuburar Baki da gani aikensa akayi baya son zuwa.
Ai Yana ganin zahra ya kwala qara yana fadin.
"Yehhhh! Adda Zahra!"
Ya kwasa a guje ya koma ciki yada kwadawa Ammah Kira.
"Ammah! Amma! Ammah! Ki fito ga Adda zahra tazo".
Mama dake tsaye a balcony din dakinta da waya a hannu ta gangaro da sauri ta nufo part din Ammah,
Mama na kokarin shiga su Kuma su Ammah da Musaddiq na kokarin fitowa Ammah na fadin.
"Bana son shashanci wace zahrar Kuma yanzu ko karfe tara Bata karasa ba nasan hal......"
Bata karasa ba zahra ta shigo, ai suna arba da Ammah ta jefar da handbag din ta karaso da gudu-gudu ta
shige jikin Ammah sai ta saki wani siririn kuka, tana fadin.
"I missed you Ammata! I really missed you, kinki zuwa ki ganni Ni Kuma ya hanani zuwa".
Tunda zahra ta shigo wani fitinannan kamshi ya doki hanci Mama ta rude ga uwa uba yanda zahrar ta koma
ko makaho ya shafata yasan taji dadin masauki, Dan ba karamin kyau da Wani irin fresh tayi ba.
"Ke Kuma menene haka idan koroki yayi ba sai kiyi bayani ba ai kuka baya magani Daman kowa ya sayi
rariya yasa zata zubar da ruwa Kuma tsintacciyar mage ai Bata mage".
Mama ta fada tana kallon zahra data shige jikin Ammah.
Dan murmushi Ammar tayi tana fadin.
"Zahra kuje daga ciki gani Nan, ya jikin malam din ko Baku shiga can ba?".
"Munje Yana barci ne, kuma gurin da maza sosai shine yace a kawoni gida zuwa dare sai muje na duba
shi".
"Ok, shikenan ku shiga Allah ya bashi lafiya".
Ammah ta fada ta wuce main kitchen dinsu sata dauko wasu abubuwan tunda Alawiyya Bata Nan ta aiketa
gidan Hajiya kaltume.
Nan suka bar Mama sororo da tarin kunya wato amsa aka Bata a kaikaice.
Jiki ba kwari ta koma part dinta.
Su zahra suna shiga Musaddiq ya mika Mata Jakarta Yana fadin. Kai Adda kike yarda Jakarki da kudi da
yawa Kuma a ciki".
Kansa ta shafa tana fadin "Ni bani da wasu kudi a ciki, Wai Ina zaka Naga kana Bata rai?"
"Ba Ammah bace ta bada kyautar biscuits dina da chocolates da suka rage ba a kaiwa jikar Hajiya kaltume
data aiki Aunty Alawiyya Ni Kuma Ina son All butter Kuma babu a Nan kusa sai naje store Kuma Zazzabi
nakeyi".
"Ah gaskiya ba'ayi daidai ba, kayi hakuri na bude opay sai na yiwa magaji transfer saiya sawo maka"
"Kai! Adda ki duba da kudi fa a jakar sosai".
Budewa tayi taga da gaske yakeyi to tana tunani lokacin da tayi barci ya Zuba matasu.
Mama ce a daki tana ta faman Kai kawo da waya a hannu ganin zahra ya daga Mata hankali ba kadan ba, a
fill ta Fara fadin.
"Jar uba wallahi baze yuwu ba wannan ce matar Almajirin? Da sake wallahi Alhaji munafuttarta yayi yasan
ko waye ya dauko agola ya bawa ga 'ya'yansa na cikinsa be Basu ba, wato ni za'a yiwa lullubin biri ko? Wai
Ina Kika shiga ne Asabe! Naje gidan,na tura babu ke babu mahaifiyarki na Kira wayarki Bata aiki Kuma
mahadin cimma burina Yana hannunki tunda Kika karbo ban Kara jin ko labarin Wanda ya ganki ba"
Ita kadai a daki tana ta buga sambatu kamar sabon kamu, Aunty Ladi ta Kira akace Mata wayar a rufe take
jefar da wayar tayi Kan gado tana buga tsaki tana fadin. Wallahil da sake dole nayi Wani Abu yau ba sai
gobe ba".
08055362975
* MAMAN FATEEMAH*
Page 59
.......... Abincin kawai Ammah ta zubowa zahra ta fito mata dashi, lokaci Ahmad din yazo zahra ta bashi
kudin da za'a sawowa Auta kayan kwalam, Ammah ce ta tsawatar Jin yawan abinda za'a sawo.
"Ki Bari a sawo masa kawai Ammah ba sai ya rinqa zuwa makaranta dasu ba tunda yace nasa kinyi kyauta
dasu"
Tana Ciro kudin magaji ya shigo da manyan ledoji a hannu Yana fadin.
"Ina Ammah Bari kiga Aunty zilai yanda ta zama inaga supplement Tasha ta Zama haka naga alama harda
bleaching takeyi Kinga yanda ta ...
Bai karasa ba yaja birki Yana ware idanu.
"Kam bala'i! Wannan yarinyar yaushe kikazo? Gaskiya kinci Amana koki nemeni duk amincin dake
tsakaninmu dake har kizo garin nan ki mike kafa kiyi awanni Baki bada cigita ba,wato kin Zama DONE ko?
yanzu na baro mijinki a Asibiti shima ya wani zama Jan wuya,da gani Yana Gane garin Dan ba haka yabar
garin Nan ba, ku fad'i gaskiya dai ko kun danne Kan dollars din America na qungiyoyin da kuke yiwa aiki?".
Pillown kujera karami zahra ta jefa Masa daga inda take zaune.
"Allah ya shirye ka magaji, Kai Kullum baka girma, shi yasa nafi son Zama da Ya Imam wallahi saboda komai
nasa gentle yake yinsa, amma Kai kamar rikon kauye,gaskiya da a kauye akayi ka da anga tabargaza, Wai
nice yarinya ka tafi ka nemi yarinya ni yanzu yayarka ce dole kace min Adda, sauran amsar Kuma sai mun
kebe Zan baka ita".
Dariya ya dauka Yana tafa hannu.
"Very good, inye yaushe kikayi Baki irin haka? Da sake wallahi Nima azo ayi maganar manya auren nan
zanyi, kuga yarinya ta zanzare tayi bulbul sai magana fal cikinta".
"Magaji! Magaji! Wallahi ka fice kada na Bata maka Rai yanzu, daga zuwanka zaka damu mutane, ka Dade
bakayi auren ba mutumin musawa".
Hannuwa ya hade irin yanda indiyawa sukeyi.
"Sorry Ammah idan na fita dawa zatayi Hira ki Bari mu Dan cukusa kadan dan Allah".
Sallamar zilai ce ta katsewa Ammah hanzari abinda zata fada.
"Lah! Aunty zilai har kun karaso? Sannu da hanya".
Zahra ta fada, tana kallon magajin.
Yara ne suka shigo da Kaya suka sauke suna gaishe da Ammah, sannan suka gaishe da zahra.
Da sauri magaji ya fita Yana Fadar.
"Ina Zuwa ya fice.
Wasu kayan ya dauko, zahra na ganinsu ta gane Wanda Zayyan ya aje a gidan dake BAWO ROAD ne, sai
yanzu taga Ashe kilishi ne dasu dabino da cukui sai tarkacen kayan zaki dasu BAMA.
Sauran Kuma suna cikin ledoji.
Gurin da Ammah ke zaune Zilai ta karasa ta tsuguna tana fadin.
"Sannu da gida Ammah mun sameku lafiya? Ashe Kuma Baba malam haka tsautsayi ya sameshi, Allah ya
bashi lafiya, Kuma nagode Ammah Allah ya jikan mahaifa ya yiwa zuri'a Albarka a tayani godiya gurin
yallabai nagode, nagode".
Sai hawaye.
"Ikon Allah! ku kuma da 'yan kuka kuke shigowa garin? itama mutuniyar da kukan ta shigo min, amma na
fashimci kukan Dadi kukayi gaku nan kun zama wanke hannu ka taba".
Yar dariya zilai tayi tana goge hawaye.
"Wallahi Ammah duk yanda Zan fada Miki karamcin da akayi min Ni kaina baze misaltu ba Kinga waccan
jakar wallahi duk suturu ne babu ta karamin kudi a ciki Kinga yauma abinda oga Sameer ya bani".
Ta dauko envelope brown ta dora a gefen kujera inda Ammar ke zaune.
"Tab Aunty zilai kice shagalinku kuke a kanon kun ninke mu a nan, da gaske Ammah wannan yarinyar ma
kukan tayi Miki?".
"Innalillahi! Magiya fice Dan Allah".
" Kiyi hakuri Ammah, Amman fa ba inda zani nabar wannan sabgar Arzikin Kinga fa".
Ya fada yana nuna kayan dake zube a tsakiyar parlourn.
"Allah ya shirya"
"Amin" suka fada, gurin zilan Ammah ta juya.
"Lafiya kalau muke, wallahi kuwa Haka Allah ya kawo wannan kaddarar sai fatan Allah ya bashi lafiya, ki
dauke abunki an gode madallah".
Harta yunkura zata tashi ta koma tana fadin.
"Ga kayan tsara Nan inji oga Sameer yace a kawo Niger sukaje aiki".
***
Baba malam bashi ya farka ba sai kusan hudu da 'yan mintina, lokacin Mahmud ne kadai a dakin Shima ya
rigasu fitowa daga masallacin ne, da sauri ya taso ya karasa kusa dashi.
"Sannu Baba ya jikin?"
Mahmud ya fada Yana rik'e hannun malam Daya Miko Masa.
"Alhamdulillahi Ala kulli halin, duk abinda Ubangiji ya yiwa bawa akwai hikima a cikinsa, Kuma bawa baya
wuce K'addararsa sai dai neman sauki,Haka Allah ya hukunta tun ran gini tun ran Zane rubutaccen
al'amarine baya canzuwa,ita kaddara haka take sai dai fatan Allah ya bani juriyar da dangana, inaga iyakar
takawar kenan wadda akayi a baya na gode da kokarin ku naji jiya kaima bakayi barci ba, Allah yayi muku
Albarka ya saka muku da mafificin Alkhairinsa, ka shigo cikin rayuwarmu ka zamar Mana fitar data haske
Mana duhu, Ina hadaka da girman Allah kayi hakuri bisa abinda akayi maka ka koma ga mahaifanka nasan
ba manta garinku kayi ba na dai kyaleka ne saboda halin bacin ran da nake ganinka a ciki,naso idan ka
dawo na sakaka a gaba muje ga iyayenka kodan halin damuwa da nake ganin mahaifiyarka a ciki, gata da
matsakaitan shekaru sai a tausaya Mata, Mahmuda ba'a fushi da iyaye kaji, sun 'yan lallabone, to sai ga
kaddarar data sameni Kuma lallai naso yin wannan Alkhairn Amma bamu San abinda Ubangiji ke nufi da
hakan ba shi Allah s.w.a baya da sabon aiki".
Tunda Baba malam ya Fara magana Mahmud ya sadda Kansa kasa Bai dago ba Saida yaji ya saka aya a
maganarsa, amma fa maganar ta doki zuciyarsa ba kadan ba.
A hankali Mahmud ya dago idanunsa Wanda sukayi jajur badan Yana namijin duniya ba da kuka ze fasa
kamar mace, hannun Baba malam ya Kara rik'ewa cikin nasa.
"Baba ka daina fadar haka in Sha Allah saika cigaba da taka kafafunka Kuma niyyarka ta Alkhairi saika idata
da izinin Allah in dai akwai inda suke magance matsala irin taka da Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w sai an
kaika, daman Nima nayi tunanin fada maka asalina idan na shigo garin sai Kuma wannan ibtila'in ya faru,
kayi hakuri Allah ya baka lafiya yasa kaffara ne, yanzu ka kwantar da hankalinka ka cire damuwa in Sha
Allah zaka warke, ai sunce ba wata damuwa Mai yawa bace bayan ne ya Dan bugu, harma oga sameer yazo
ya gana da likitocin bansan dai yanda suyi ba, sai ya shigo muji yanda za'ayi"
Habib da Sameer ne suka shigo tare da zugar dattawan unguwa masu zuwa dubiya tun safe Dan mutum be
yanke ba tafe suke maza da Mata, Dan ma iya Abu na gida tunda tazo da safe taga jikin ta Fara koke koke
Habib ya mayar da ita gida.
Sun Jima suna Masa Addu'ar samun lafiya sannan suka tafi tare da ajje Masa kudi masu Dan kauri.
Mahmud da Habib suka Kai shi toilet suka taimaka Masa yayi alwala suka dawo dashi suka kwantar yayi
ramuwar sallar da ake binsa.
* * * * *
Tunda Mama taga shigowar zilai da yanda taga zilan ma ta koma, sai hankalinta ya qara duguzuma ya tashi,
nan da nan ta shige toilet dinta dole ta nemo malam na Bande.
Cikin sa'a ringing Daya ya dauka Yana fadin.
"Idan kin Kira ta baci kenan, yaya ake ciki!?"
Babu Bata lokaci ta Fara bayanin.
"Malam da matsala sosai Dan komai nema yake ya cukude, da Alama Alhaji munafutta yayi ance an bawa
yarinyar nan Almajiri Qolo,amma wallahi kaga yanda ta koma kamar matar shugaban Qasa, ko Mai aikin
mu da suka tafi tare ta Zama abin kallo duka a cikin 'yan satiitka Dan Allah ayi wani Abu kada bakin cikin su
ya kasheni, malam ga Kuma na nemi Asabe na rasa duk komai Yana neman lalace min".
Wata dariyar marasa nutsuwa yayi duk da yawan shekarunsa Yana fadin.
"Ai daman na fada muku ayi duk yanda za'ayi ta turara turaren wutar nan sai kukayi sake kayan suka fada a
hannun yaron mijinta, sannan Kuma Kika kasa hakuri mu karkare Kika canza guri, wannan shiya rusa duka
ayyukanki na baya,maganar Asabe Kuma bana Jin zaku Kara haduwa da ita nan kusa dan naga tayi nisa
sosai da nan din, naga alamar kamar korarta akayi daga garin saboda Wani asirinki Daya tuno ban dai
fashimci abunba sosai gaskiya amma Yana da nasaba da ita wannan yarinyar gaskiya sai dai itama kanta
yarinyar Bata sani ba".
Karkarwa jikinta ya dauka ta Fara hada jibi.
"Dan Allah malam ka taimaka mini kada maganar nan ta fito har abada, kayi duk yanda zakayi ita kanta
Asaben a dauke Mata hankalinta daga garin dama jahar Baki Daya. ko nawa ne Zan baka fatana kada asirin
ya tuno, ita Kuma kayi abinda zakayi kada ya Kara marmarin Zama da ita har abada yanda ya kawota ya tafi
ya barta a nan kada ya Kara tunawa da ko sunanta dama garin gaba daya".
"Ki kwantar da hankalinki, Naga tafiya Mai nisa da zeyi Kuma gaskiya banganta a kusa dashi ba, zata zauna
Dan Zama kam Amma Kamar yanda nasha fada Miki Banga rabuwa a cikin aurensu ba in dai shine ze
saketa to bangani ba".
"Zan turo maka da sako ayi duk abinda ya Kamata kawai".
Ta fada tana sauke wayar daga kunnenta, iska Mai zafi ta buso daga bakinta tana fadin.
"Haba biri yayi Kama da mutum shi yasa na nemi Asabe na rasa kaura wambai tayi batan dabo, to waye ya
Kamata har malam yace asiri ya tuno kenan wayarta ma ankwace tare da sauran sakonnin da zata kawo
min, Kuma sakon farkon ma hannun yaron mijinta ya fada".
Ta maimaita yaron mijinta yafi sau biyar.
"Me hakan ke nufi kenan? Ina ga ko cikin yaran makarantar ne, amma a cikinsu waye ze budewa Asabe Ido
har ya iya koreta daga garin irin haka afujajan da gaggawa?".
Haka ta zauna tana faman kullawa da kwancewa babu Mai Bata amsa.
Abincin kusan kala uku Ammah ta saka Alawiyya tayi tunda itama ba laifi Ammah ta horata, zilai ce ta shiga
ta tayata duk da Ammah tace ta huta ita da ta dauko hanya, Amma Sam taqi Zama ta shiga sukayi tare, a
manyan warmers aka Zuba abinci, magaji Ammah ta Kira yazo ya Kai Asibitin.
Zahra bacin da Bata samu ba jiya ta shige bedroom din Ammah tayi kwanciyar ta daga ita sai vest da Wani
wando skintight ta saka wata hula Mai budedden Baki ta zubo da gashinta baya ta Fara barci hankalinta
kwance.
Sai da Ammah ta Gama sallamar magaji ta shigo dakin, tsayawa tayi tana Qarewa zahra kallo, yanda ta
ganta komai nata ya kara cikowa kirjinta da kasanta suka ciko sai zuciyarta ta shiga kokonton anya babu
yaron ciki a jikinta kuwa? duk da bangaren ta ne da yake abin anzo Kan 'yarta ne sai ta samu confused.
Abinda zata dauka ta dauka ta fice daga dakin.
Sai kusan magariba zahra ta farka, wanka tayi ta shirya ciki rigar Atampha royal blue da ratsin Baki Mai
manyan ganye, dinkin yaso ya matseta daga kirji abinda ya Bata mamaki ke nan dan kasa fitowa tayi Saida
ta rufa da gyale sannan ta iya fitowa, sabanin da rigar har Dan yawa tayi Mata daga wurin breast cup din.
Su Aunty zilai ta samu suna gyara parlourn, Zama tayi tana tana musu sannu, Alawiyya ce tace.
"Aunty zahra a Zuba miki Abinci?".
Dan yamutsa fuska tayi.
"A'a bana Jin yunwa duk cikin ma bana jin Dadinsa, ki hado min salad kawai ya isheni sai ki hado min da
fruits salad ya isa".
"To Bari naje na hado miki" .
Ta fada tana barin gurin.
"Aunty zilai Ina Ammah ne naji shiru ba motsinta?".
"Tana sabon part din Abba na bayan Nan kinsan Ammar mu Bata daukar raini ta dawo da Abba nan ta raba
musu turaka ita da Mama, kinsan halin Mama har Saida takai hakurin Ammah karshe ta yiwa part din can
yaji ta nuna sai dai a raba ko Kuma ta hakura ta barmata mijin duka shine ya dawo sabon nan".
Baki zahra ta rike tana kallon Aunty zilai.
"To ke Aunty zilai waya Baki wannan dogon labarin naga daga ni har ke bama garin Nan?".
"Sahura ce ta bani labari dazu Dana shiga part din mu Zan aje kayana".
Tsaki zahra tayi tana fadin "Kai Allah wadaran naka ya lalace, har abada sahura bazata daina gulma ba na
tsani mutum Mai fuska biyu".
Hira sukaci gaba har Alawiyya ta kawo Mata hadin salad din.
Kiran sallah ya tashe su daga parlourn.
Zahra na sallah Ammah ta shigo, cikin sabuwar kwalliya sai kamshi take bazawa, Abu ta dauka a wardrobe
dinta ta fice, zama zahra tayi tana Addu'ointa har aka Kira sallar insha'i.
Tana cikin sallar ne wayarta ta dauki Kara, sau biyu ana kira tana tsinkewa, Saida ta Idar ta dauka *Amor
mue* ta gani Dan murmushi tayi.
Kiransa tayi lokacin ya fito harabar Asibitin duk ya gaji so yake ya kwanta ya huta kiranta yayi ya fada Mata
ga Zayyan nan ze daukota ta duba Baba malam din shine Kira biyu Bata dauka ba Yana niyyar na uku saiga
kiranta ya shigo.
Picking yayi tare da amsa sallamar ta.
"Ina sallah ne ka kira, ya jikin Baba malam din?"
"Jikinsa Alhamdulillahi, ga Zayyan nan na turo shi ya daukoki kizo ki duba shi".
Shagwab'e fuska tayi kamar yana ganinta.
"Nayi zaton sai gobe tunda dare yayi, pls ka kirashi kace ya dawo Dan Allah kaji".
"Do what I said".
Ya kashe wayar gaba Daya.
Ta gumi ta Zuba tana zancen zuci.
"Yanzu ko kwana dayan baze barni nayi a gidan nan ba saboda Allah shi yafi son Kullum Yana manne Dani
kamar yaron goye"
Dago Kan da zatayi taga Ammah tana tsaye ta Zuba Mata Ido.
Karasowa tayi tana fadin.
"Lafiya Naga kin hade rai?".
"Ba shine yake Wai ya turo a daukeni naje ba duba Baba malam ba, nace ya Bari Saida safe yanzu dare yayi
shine yace A'a".
Godiya ga Allah Ammah tayi a zuciyarta yayi maganinta yarinya da muhallin ku kice bazaki tafi ba.
Amman a zahiri sai tace.
"Aida kinsan Baki duba shi ba da tun yamma zilai ta rakaki kunje tare, nima Abbanku ne da baya garin da
tun safe naje naga jikin nasa, Amma Zuwa safe in Sha Allah Zan shiga na duba shi tunda Abban naku Yana
hanya".
A wata sharceciyar mota Zayyan yazo daukarta,ba wadda sukazo a ciki bace ita lamarin nasu ya daina Bata
mamaki dukkansu fuska biyu ke garesu a nan daban a gefe ma daban.
Sun dauki Ido lokacin da suka fito da Alama tun shigowarsa ake dakon ganin waye a ciki, dadin abin ma da
ba'asan waye a cikin ba tunda daga cikin gidan suke fitowa ko shiga, Kuma ansan Mai gidan Shima a jikensa
yake danma shi ba mutum bane me fariya.
Har suka karaso Yana waje a tsaye, fitowa Zayyan yayi daga mazaunin driver ya nufi inda Mahmud din yake
tsaye, magana taga Mahmud din yana yiwa Zayyan kafi ya juya ya nufi parking lot na Asibitin,shi Kuma ya
tako ya nufo ta Yana amsa waya
Hannu ya saka ya bude side din da take zaune baice Mata komai ba hannunta kawai ya riko ya fito da ita.
Saida ya gama wayar wadda ta fuskanci akan dai lalurar Baba malam ne yake yinta.
"Precious guduna kikeyi ko?".
Ya fada Yana kokarin rungumota jikinsa.
"Dan Allah ka Bari da mutane fa kaga can".
Ta nuna Masa wasu Mata da suka doso gurin da suke tsayen.
"Shine me Dan sun gani haramun na aikata?".
Kai ta girgiza tana Fadin.
"A'a Amma ana barin halas ko dan kunya, wata Kila ma nasansu".
Bai Kara ce Mata komai ba saboda mutanen sun doso inda suke.
Ba zato zahra taji an ambaci sunanta, da sauri ta juya, Maman mujiba ce da wasu matan unguwa suka
shigo diba malam din,da sauri zahra ta Dan ja baya tana fadin.
"Sammunku Mama, Ina yininku".
Da fara'a suka gaisa, sannan Mahmud ya gaishesu, har wata daga cikin matan ke fadin.
"Ko shine Almajirin na Malam".
Kafin zahra ta samu zarafin magana Mahmud ya rigata.
"Eh nine Mama"
"Kai Dan Nan! To ai babu kama, mu ba haka labarin yazo Mana ba wallahi gaka nan wanke hannu daka
tab'a, kamar Dan gidan shugaban Qasa".
Kafin suje har Zayyan ya bude kofar parlourn tana shiga taga tamakar an dauko parlourn gidan BAWO
ROAD an aje a Nan. Bata kulashi ba ta wuce ciki.
Ba Wani bakunta harta Saba da irin wannan rayuwar itama, Bata da kayan kah babu na rataya duk inda
suka Sauka gida ne.
Ba Wani bayanin wanka tunda yanzu ba dadewa tayi, canza Kaya kawai tayi ta saka nighty tayi kwanciyar
tana cika tana batsewa shi be San haushinsa take ji ba ya hanata kwana a gurin Ammarta kamar wani
abun azo a gani zatayi masa.
Har tayi barci be shigo ba Batasan inda ya makale ba.
Tunda Mahmud ya shigo dakin da yake kusa da Wanda Zahra ta shiga yake faman research akan Asibiticin
guda biyu Daya karbi website dinsu ya shiga yayi bincike sosai,sunyi commucating sosai da Sameer akan
maganar Asibitin Daya Dace, daga karshe Mahmud yace Sameer din ya biya chargers din komai na Max
surgeon din idan da yuwuwar gani doctor daban Fortis din Suma sai aje. Bashi ya shigo bedroom din da
zahra take ba sai kusan karfe biyu da kwata na dare, barcinta take sadidan da Alama ta tattarra shi ta Zuba
a dust bin.
Wani murmushi ne ya sille Masa,kalamanta ya tuno na dazu Wai matar Dan kidnapping.
"Zakiga kidnapping iya ganinki Dan idan na sakayaki Zaki gane na iya kidnapping na kirki.
Saida ya gama duk abubuwan da zeyi sanan ya hayo Kan gadon kusa da ita yana zare blanket din, jikinta ya
shige ya sakata a jikinsa sosai ya maida blanket din ya rufe su, lif tayi a jikinsa kamar Daman jira take.
Gyara Mata kanta yayi a gefen kafadarsa, a hankali ta sauke numfashi, Shima ajiyar zuciyar ya saki barci
yakeji sosai dan yayi mamakin yanda har ya Kara Kai wannan time din baiyi barci ba.
Bayan sallar Asuba ma Kara komawa barci sukayi manne da juna, da gaske zahra ta dauki Shawarar Aunty
zilai data ce Mata duk inda ya kaita ta karbeshi a gidanta ne kawai, kenan da hasashen da tayi a Dan zaman
da tayi dasu.
Ring tone din wayar ta ya tashi Mahmud lokacin goma da Arba'in da biyu Hannu ya saka ya dauko wayar.
*AMMAHTA* ya gani baro-baro a Kan screen din Yana yawo, nauyin daukar Kiran yaji saiya shiga Yi Mata
abunda dole ta tashi.
"Wash Allah menene haka Dan Allah?"
Dan bakin ya sakarwa kiss Yana Mika Mata wayar Yana fadin "Ammah na Kira yayi toilet. Dan ba karamin
barci sukayi ba yaso ace karfe tara ya wuce Asibitin to shi barci ba'a ci Masa bashi.
Kiran Ammar zahrar tayi.
"Ina kwana Ammah".
"Lafiya kalau Alhamdulillahi, Abincin break fast ne magaji da Musaddiq suka kawo muku sunata knocking
ba'a bude ba sunce babu alamun mutane ma a gidan".
Ajiyar zuciya zahra ta sauke cikin raunin murya tace.
"Ammah! yanda kike tunanin abun yafi nan fa, ina wannan sabuwar unguwar dana taba raka Hameeda
wadda nake baki labarin ta? Wallahi nan ya kawo mu nayi masa magana yayi min banza,Dan Allah kizo kiga
gidan sai kiyi Mana shari'a".
"Ikon Allah, Ina tambayarki kina min korafi kiyi hakuri Mana abi komai a sannu, yanzu dai ki Fadi Address
din sai su kawo muku".
"To ai Nima bansan sunan unguwar Nan ba fa wallahi na manta ".
"Ikon Allah, Bari magaji ya Kira mijin naki saiya fada Masa".
"To Ammata saina zo anjima".
Tayi saurin kashe wayar Dan ma kada ta hanata Dan wallahi Qafarsa Qafarta.
Blanket din ta ture ta tashi daidai lokacin da Mahmud ya fito Yana kokarin zare pyjamas din jikinsa Kira ya
shigo, magaji ya gani bayan sun gaisa ya shiga yi Masa kwatancen gidan.
Armless da three quarter ya saka farare sol na kamfanin Adidas ya dauki wayarsa ya fice daga dakin.
Har waje ya fito Yana son yanayin unguwar babu hayaniya sosai, tun daga nesa magajin ya hango Mahmud
a ransa ya ayyana.
"Ba dai daga wannan gidan ya fito ba?".
Har suka Karaso be gaskata abinda idanunsa ke fada Masa ba, dan totally shi kansa Mahmud din bana
gidan Baba malam bane wannan wani ne yaje gani daban a gabansa Mai wata irin haiba da Kamala, dan
hutu domin ko ba'a fada ba fatar jikinsa kadai ta nuna kanta, suna kokarin tsayawa sukaga an bude
katafaren gate din.
Bai shiga parking lot ba inda yaga motoci a kalla sun Kai hudu ko wacce ta millions of naira.
Fitowa magaji yayi suka gaisa da Mahmud Musaddiq ma ya gaishe shi sun gaisa da Zayyan ma, backseat ya
bude ya Ciro babban basket da Wani k'arami kuma, Zayyan ne ya amsa da sauri yayi ciki dasu, ba yanda
Mahmud beyi da magaji ba ya shiga ciki ba Amma yace a'a sai Wani lokacin, Ammah na jiransu ze kaita
duba baba malam,Musaddiq ne ya kwabe fuska kamar zeyi kuka dole magaji ya jira shi a mota Yabi
Mahmud ciki.
Gidan kawai magaji yake kallo Yana jinjina Kai a fili yace.
There's something behind".
Basu Dade da shiga ba suka fito harda zahrar ta saka wata abaya baka all stones sai walainiya take.
Magaji yaso yayi halin nasa na tsokana sai Kuma yaji baze iya ba sunyi Masa wani irin kwarjini ita da mijin
duk yanda taso ta ta tabo shi saiya share ta.
Saida suka fice sannan ya rungumeta suka koma ciki Zayyan dai sai kauda Kai yayi, yana mamakin ogan
nasa yana son yarinyar sosai Saida hakan Bai Hana ya gwada Mata halinsa ba.
Ai Auta kamar jira yake magaji ya tsaya ya Kama kofa ze bude ya jita a rufe, magajin ya kalla.
"Ya magaji ka bude min".
Ido ya zare Masa Yana fadin.
"Na rantse da Allah naji maganar zahra da gidan daka nace saika shiga a bakinka ka fadawa wani saina
zaneka tas, kaji abinda na fada maka?".
Kaiya gyada.
"Oya fita.
Yaron ya fito jiki ba kwari yaso ya kwasa a guje tin kafin ya shiga daki ya Fara fesa labari, sai Kuma magaji
yayi Masa karan tsaye.
Sai wurin Daya su zahra suka baro gidan Dan tasashi gaba tayi da shagwabar data saka Saida ya Dan mayar
da yawunsa sannan sukayi wanka suka fito.
Yaso ya wuce Asibitin direct to Saidai baya son zuwa da ita da dare ma sun dauki idanu bare da rana, motar
ta suka shigo gidan Baba malam suka Fara zuwa a kofar gida ta barshi suna gaisawa da dalibai manya da
Yara anata jajantawa juna, masu gaje gani sunata Yi Masa Dan biki akan canjin da suka gani a tare dashi.
A tsakar gida zahra ta samu iya Abu tare da wasu matan unguwa sunzo jajanta mata, da farko Basu gane
zahrar ba Saida ya matso kusa sun dai amsa sallamar ta, rike Baki Iya Abu tayi.
"Wace bakuwar jidda nake gani haka? Zahra'u haka Kika koma Masha Allah! Dana ya iya kiwo wannan
kikayi shekara ai sai an duba fuska a jikinki".
Ta fada tana dariya.
"Kai Mamana".
Karaf a kunnen Mahmud da yayi sallam ya shigo.
Bai San lokacin da murmushi ya kubce Masa ba sai yaji ta Kara Qima da daraja a idanunsa,wato maganar
Daya taba fada Mata, akan fadin Iya Abu da takeyi gatsal tayi tasiri kenan a zuciyarta.
Gaishesu tayi tare da jajanta Mata jikin Baba malam tana fadin.
"Na daina kaka dake Ni yanzu uwata ce ke Kuma kin.....
Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji matan na gaisawa dashi Sam bataji shigowar sa ba tunda baya ta
bawa kofar shigowar.
Har kusa da iya Abu ya zagaya ya gaisheta tare da Kara jajantawa juna tana fadin.
"Kaji sabon kinibibi gurin zahra'u ko? Wai nice mamarta saboda ta aure min da shine zata Fara ladabin
gangan".
Dan kallonta yayi a fakaice, baice komai ba ya tashi ya fita waje.
Bata Jima sosai ba ta fito can ta hange shi suna magana da wasu matasan unguwar, wucewa tayi ta nufi
gidansu Yana kallon yanda Idanu sukayi Mata caaaa kamar yaje ya boye abarsa.
Lokacin data shiga Abba na kokarin fita a mota shi da Bala driver.
Yana ganin zahra ya saka Balan tsayawa harta karaso inda suke cikin murna take fadin.
"Abbana ka manta dani ko?".
"Haba uwata kin taba ganin da ya manta da uwarsa kina raina Kullum ai muna waya da mijin naki Yana
kirana ya gaisheni yaron kirki wallahi malam Bala sai yanzu nake ganin alfanun had a uwata da yaron Nan,
tun ranar da muka ganshi nasan Mai nagarta ne"
MAMAN FATEEMAH.
Da sunan Allah Mai Rahama Mai jinkai salati da daukaka da Aminci su tabbata ga shugaban mu Annabin
Rahama Muhammad s.a.w.w.
Page 60.
_____Suna biye da doctors din har suka shiga dakin abinda suka gani ya daga musu hankali, jikin Baba
malam ne yake wata irin jijjiga Kamar Wanda yake ciwon tsintsinko irin na Mata masu haihuwa Abba dasu
Abubakar suna ta faman tofa Masa addu'a, ganin lotoci sun shigo yasa su Abba suka matsa suka Basu guri,
tamabaya likitan ya jefo musu.
"Ko akwai abinda ya faru Wanda ya haddasa Masa hakan ko Kuma an fada Masa abinda ya tada Masa
hankali ne?".
"A'a Babu komai doctor daga barci ya tashi da wannan abun".
Abubakar ya fada, yayin da Abba ya Kara da "kwarai kuwa muna zaune ya farka da wannan shivering din".
Jinjina Kai doctor Omolen Yaya Yana faman gwaje-gwajensa, rubuta yayi a takarda ya Miko Yana fadin.
"Ayi maza a kawo wannan alluran yanzu za'ayi Masa".
Habib ne ya karba ya nufi kofa,mahmud ne ya ya biyo shi da sauri suka fito, sun Fara tafiya mahmud yaga
jikin Habib sai tsuma yake tamkar ze Fadi shima, rikeshi Habib yayi Yana fadin.
"Wallahi kaina juyawa yake yi".
Ya fada Yana dafe Kansa.
"Haba Mana Habib take it easy, kada ka jawowa kanka wani problem din, zauna a Nan Ina zuwa".
Ya nuna Masa wani Dan bencin a gefen baranda da sauri yayi gaba da takardar a hannunsa, maganar Abdul
Hakeem yaji daga bayansa Yana fadin.
"Muje kawai Naga Habib ma Kamar Baya cikin nutsuwarsa".
Tare suka jera har pharmacy suna tattaunawa Kan yanayin lalurar malam din.
Allurai biyu aka samu a cikin ukun Daya rubuta, a Nan pharmacy din suka fada musu dayar tana da wahalar
samu sai dai su duba a manyan chemist cikin gari ko za'a dace, biyun suka Fara kaiwa suka fadawa doctor
dayar babu amma zasu duba a cikin gari ko za'a samu, wani chemist ya fada musu yace suje in dai Babu a
can su dawo kawai ba za'a samu ba a ko Ina.
Tare da Abdul Hakeem suka tafi shi yake driving din, sunje babu sun basu tabbacin sai dai a kano ko Bauchi.
Lokacin da suka dawo doctor Omolen suka samu shi kadai saura doctors din ya sallame su, shima Baba
malam din ya Sami barci jijjigawa ta lafa.
Bayanin da masu chemist din sukayi musu suka fada masa, Abba ya kalla yace Yana son ganinsu a office.
Ya fita da sauri irin Basu na likitoci, Abba da mahmud da Abdul Hakeem sukabi doctor yayin da Habib da
Abubakar suka rufawa doctor baya.
Ya rigasu shiga office din suna zuwa suka same shi a tsaye Yana kaiwa da kawawa, shigowar su yasa ya
dakata ya nuna musu resting chairs na office din yace su zauna, bayani ya Fara musu Yana kallon Abba.
"Alhaji dole a samo wannan allurar yau ayi Masa Kuma yanda ka'idarta take dole Wanda za'a yiwa Yana
kusa ma'ana ba'a fito da ita daga fridge har sai Wanda za'a yiwa Yana kusa Bata minti biyar a zafi zata
lalace Dan haka dole mu turaku Kano ko Bauchi a yau din Nan saboda idan aka dauki lokaci ba'ayi Masa ita
ba za'a shiga want condition din Kuma Wanda bama fata tunda Kansa ne ya bugu lokacin Daya samu
tsautsayin munga casa din to munyi zaton minor case ne, saida hakan ta faru Kuma muka tabbatar da
abinda muka gani, yanzu Shawara ta rage taku sai ku zabi Inda kuke ganin yafi dacewa sai ku tafi kafin visa
din ku ta fito ana son ayi Masa wannan allurar Kamar sau hudu duk bayan Twelve hours are yinta" .
Kafin Abba ya samu zarafin magana mahmud yayi saurin fadin.
"Ina ganin doctor gara muje kanon tunda ta kanon zamu tashi, idan mukaje Bauchi Kamar mun koma baya
kenan, ai kace ko gida za'a iya Zama indai akwai Wanda zeyi allurar?"
Kai ya gyada masa alamar tabbatarwa.
Abba ne yace "Mahmud Ina ganin Kamar abin zeyi muku yawa abin fa bana Wasa bane kana ganin su
mutanen naku zasuyi abinda ya kamata? Dazu yaron Nan Sameer ya kirani yayi min bayanin komai har
booking din Asibitin ya fada min ya gama komai Yana ganin daga nan zuwa gobe ko jibi za'a iya samun visa,
ya fada min wait uwata Bata samu visa ba yaso ya hada da ita saboda lalurar ta, nace Masa ba komai
hakan ma Allah ya saka muku da Alkhairi, na saka Masa wani Abu a account dinsa kafin na biyo ku muga
abinda Hali yayi, yanzu ma Abdul Hakeem ze saka Mata kudi account dinka saboda wannan data taso".
Godiya mahmud da Abdul Hakeem sukayi Masa sannan suka fito suka bar Abba da docy Yana Kara fada
Masa irin yanda yanayin ciwon yake.
Har suka dawo dakin da Baba malam din ke ciki suna tattaunawa dai Kan fitar da za'ayi da baba malam din.
Suna zuwa Mahmud ya cewa Habib da Abubakar su maza su koma su shirya zasu wuce Kano yanzu su taho
da Iya Abu, key din motar da mahmud yazo da ita ya mikawa Habib yace suje a ciki,sai bayan sun wuce ne
Abba ya shigo tare da wasu manyan mutane suka jajanta musu jikin malam din tunda barci yake, kudi
masu dama suka mikawa Abdul Hakeem suka fita suna masa fatan samun lafiya.
Malam Bala ne ya shigo da sauri ya mikawa Abba waya Yana fadin.
"Yallabai gashi Ina ganin bakin sun karaso gidan gonar".
Wayar ya amsa yaga sune, kafin ya Kira an Kara Kira..
Dauka yayi ya amsa sallamar kafin ya Dora da fadin.
"Dan Allah ki jira Ina da patient ne a Asibiti".
Ya kashe Kiran.
Mahmud ya duba Yana fadin.
"Mahmud Bari naje nayi Baki daga Abuja Wadanda zasuyi aikin titina da office dina ya kawo cikin gari da
Kuma gyaran gadar jama'are, yanzu malam Bala ze dawo saiya kaiku kanon ya tayaku neman gurin Kwana
kafin ku tafi sai kuyi amfani da wannan kudin idan Basu Isa ba kayi min magana kada kaji nauyi na Nima
mahaifinka ne".
Cikin ladabi Mahmud din yace.
"Nagode Abba Allah ya Kara sutura, basai Malam Balan ya dawo ba akwai motar da oga Sameer ya Bari jiya
sai Habib ya tukamu a ciki kawai, Kuma akawai gidan da zamu zauna a Nan kusa da Asibitin malan Aminu
kanon tunda doctor yace suna da allaurar a can".
"To babu laifi Allah yayi Albarka yasa a Dace"
Su duka suka amsa da "Amin".
Har gurin motar mahmud ya rako Abba, tare da Abdul Hakeem suka wuce saboda yawanci idan irin
wannan project din yaso Abdul Hakeem keyi Masa monitoring na aikin.
Su Habib Basu Bata lokaci ba suka dawo da Iyayen jakunkuna take mahmud yace ba Wanda ze dauki kaya,
Dan murmushi Abubakar yayi yasan za'a Rina babu yanda beyi da Habib akan kada su dauki Kaya yayi Masa
musu Dan haka ya biye Masa suka dauko, tare sukazo da iya Abu, Mahmud ya gaisheta ya Kara jajanta
Mata jikin malam, daidai saitin kansa taje ta tsaya tana kallonsa, Fara matse hawaye tayi tana fadin .
*Malam haka Allah yayi da Kai? Ubangiji ya baka lafiya idan na tafiya ya kaika da sa'a ya baka ikon cikawa
da kalmatushshahada , na yafe maka duk abinda kayi min da gangan ki da gaske Allah ya yafe maka, saita
fashe da kuka sosai, Habib ne ya janyota gefe Mahmud Kuma ya fita da ita Yana fadin.
"Kiyi hakuri cuta ita ke shiga Nan da Nan sauki sai a hankali, kici gaba da yi Masa Addu'a kawai ita yafi
bukata a yanzu".
Gefen hijabinta ta saka tana share hawayenta tana fadin.
*Kayya Dan nan malam sai abinda Allah yayi dubi fa yanda yake Sambal a kwance Kamar gawa ga want
numfashi da yake da sauri da sauri ".
Sai wasu hawayen, bai Bari ta koma ciki ba key kawai yace Habib ya Miko Masa, ta tasata gaba suka bar
Asibitin.
Har cikin parlourn ta Mahmud ya rakata shida Bilyaminu daya samu a kofar gidan Yana bawa wasu Yara
wani aikin gyaran itacen da aka kawo Wanda ake musu girki dashi, sun Jima suna Bata Baki kafin ta hakura
da kukan da take kudi mahmud ya aje mata Wanda har sukazo su taoratata, sannan yace .
"Ga Bilyaminu Nan shine zeci gaba da kula da komai na gidan duk abinda babu shi za'a tambaya Kuma idan
mun Isa India Zan Kira shi ya ringa kawo Miki wayar kina ganin yanda jikin nasa yake".
Godiya ta dunga Jero Masa da addu'ar fatan Alkhairi har suka fice.
Directly gidan su zahra ya wuce, magaji ya Nemo a waya yayi sa'a Yana gida yace ya fadawa Ammah ze
shigo ya gaisheta.
Lokacin da suka shiga ciki,Mama na kofar main kitchen dinsu tana yiwa sahura magana, a mutunce
mahmud ya gaisheta sahura ta garzayo ta gaishe shi, har suka shige part din Ammah kamshinsa Yana gurin
da Ido Mama ta bisu. Saida suka bacewa ganinsu sannan sahura ta matso kusa da Mama tana fadin "Wai
Mama Baki gane wannan yaron bane Naga kin bisu da kallo".
Lemon da take Sha a cup ta kurba tana duban sahura.
"Ina fa na wani gane shi nasan 'ya'yan manyan kasar Nan ne dubk yanda yake Mana ko Ina magaji ya samo
shi Dan shishshigi har gurin uwa aka kawo shi to dai Babu 'yar da za'a lika Masa Daya ce agola Kuma ta bige
da yaron malam".
Ta fada tana cigaba da Kora ruwan lemon ta.
"Mama Wai kina nufin Baki gane mijin Zahra bane ba?".
Ai da fadin da kwarewar Mama ba'afi minti Daya ba, Nan da Nan sai tari Kamar zata sik'e da gudu sahura
ta dauko Mata ruwan ta watsa gishiri a ciki ta Bata Tasha.
Magaji na gaba Mahmud na bayansa suka shiga parlourn Ammah, komai tsab ba abinda kakeji sai sanyi AC
da sansanyan kamshin turaren wuta Mai Kama daki da freshner, gurin Zama magajin ya nuna Masa ya
wuce corridor da ze sada shi da bedrooms dinta,a Kan carpet Mahmud ya zauna, tare da magajin suka fito
Ammah tana sauko steps din tana Masa sallama.
Cikin nuna tsantsar girmamawa mahmud ya amsa sallamar Yana fadin.
"Barka fitowa Ammah".
"Barka kadai , an shigo kenan ya wajen Mai jikin?".Ta fada tana Zama a Dan nesa dashi.
Gaishe ta ya farayi sannan ya amsa Mata da.
"Mai jiki Alhamdulillahi, yanzu ma zuwa nayi nayi Miki sallama zamu wuce Kano dashi, jikin ne babu Dadi
Kuma a Nan Basu da allurar Daya kamata ayi Masa shine zamu wuce yau Ina Jin gobe in dai visa ta Zama
ready zamu wuce Indian in Sha Allah".
Tunda ya Fara Kora Mata bayani take jinjina Kai daga ita sai Allahn Daya halicceta suka sa me take
kissimawa a zuciyarta.
Cikin nuna alhinin abin Ammah yace.."Ikon Allah kowa da irin tasa kaddarar, Allah ya yayewa muslmi
wahala yasa kaffararsa ce wannan".
"Allahumma Amin".
Mahmud ya fada, sai Kuma parlourn yayi tsit, ga magana a bakin Ammah amman sai taji yaron yayi Mata
masifar kwarjini, yanda ta kare Masa kallo yau ita abin har tsoro ya Bata yanda ta ganshi, da ganinsa kasan
ba mutumin banza bane.
Da gyara Zama Mahmud yayi ciki karfin Hali yace.
"Ammah gata Nan Dan Allah zata zauna a garin Nan Bata son Kano ko kadan naso tayi zamanta Amma ta
nuna Bata so, sai su zauna da matar da sukaje Kano tare kafin muga abinda Allah zeyi akan lamarin, Kuma
Dan Allah Ammah a kula da Wanda ze Bata Abu taci a cikin gidan nan in da hali ma ke kadai Zaki Bata Abu
taci itama Matar a fada Mata ta kula kada kowa ya Bata Abu ta bawa zahra Dan Allah".
Ita Ammah duk ya sakata a duhu, to meya kawo wannan maganar da gani har cikin zuciyarsa abinda ya
fada, Bata zafafa ba tace.
"In Sha Allah za'a kula, Allah ya tsare".
"Allahumma Amin".
Ya fada Zama ya gyara, ganin haka yasa Ammah mikewa tana fadin.
"Ka Karasa tana wancan dakin ta nuna Masa da hannu tayi gaba wurin hanyar kitchen.
Cikin nutsuwa ya ratsa parlourn ya nufi bedroom din da Ammah ta nuna masa, a hankali ya Kama handle
din kofar ya shiga, idonta a rufe da earpiece a kunnenta be Karasa Inda take ba jikin kofar ya jingina ya
Zuba Mata idanun dake Bata tsoro a da.
A hankali scent dinsa ya shiga hancinta da sauri ta juyi Inda take jiyo shi carab idanunsu ya sarke, tashi tayi
zaune da sauri tana rarraba sexy eyes dinta.
Hannuwa ya bude Mata alamun ta taso ta tazo gurinsa.
Ita fa tsoro ne ya kamata kada fa Aljani yayi siffarsa ya biyo ta, to ta Ina ma ze shigo har nan.
Wani killer smile yayi mata.
"Kina mamakin yanda akayi na shigo ko? To Ammah ta turoni nazo na samu lada".
Dan turo baki tayi irin na shagwababbun yaran nan.
"Wallahi ka bani tsoro, ta Ina ka shigo Nan? Ina Ammah?".
Takowa yayi a hankali ya karaso Inda take ya zauna very close to her ya cire Mata dayan earpiece din daga
kunnenta.
"Ki daina sakawa Yana damage din ear drum na kunne kinji kada ki tashi hankalina, yanzu ki taso mu tafi
Kano zamu wuce da Baba malam daga can Kuma zamu wuce Indian din, naso mu tafi tare to duk iya kokari
Sameer yayi Amma abun yaki yuwuwa, taso muje kiji dani".
Ya fada Yana kwantar da Kansa a jikin wuyanta,ya saka hannu ya tallabo fuskarta ya hade bakinsu, da sauri
ta janye tana nuna Masa kofa tana fadin.
"Ammahhhh..."
"Da saninta na shigo ba satar guri nayi ba, taso muje lokaci Yana tafiya".
Narai narai tayi da ido.
"Dan Allah ka barni na zauna a Nan wallahi tsoron gidan nan nakeyi yayi min girma ga unguwar babu
mutane da yawa".
Tashi yayi ya nufi kofa Yana Fadin.
"Ina jiranki a parlour ya fice, har lokacin ba kowa sai kayan Abinci da fruits a Kan table mat a tsakiyar
parlourn.
Zahra ce ta fito tana Dan gyara rolling din kanta bedroom din Ammah ta nufa ta fito da handbag dinta ta
wuce ta nufi kitchen inda ta samu Alawiyya tana aiki.
"Ina Ammah?".
Zahra ta tambayeta.
"Tana bangaren Abba zata dauko sakon Daya turo a daukar masa, tana Nan Ammah ta shigo da takardu ta
mikawa Alawiyya ta kaiwa malam Bala driver.
. lokacin da suka fito zahra nata zabgawa Ammah magiyar da besan kota mecece ba, zahra Ammah ta kalla.
"Ya haka Baki bashi abincin bane?".
Dan narke fuska tayi.
"Ni ai bansan na waye ba, a Nan na gani kawai na dauka Baki zakiyi".
Harara Ammah ta zabga mata.
"Amma ke bansan yaushe Zaki nutsu ba wallahi to maza Zuba Masa shida zeyi tafiya".
"A'a Ammah zamu tafi dashi can kada na makara".
Mahmud ya fada Yana kokarin tashi.
"To shike nan Bari Alawiyya ta Kai muku mota, maza fada Mata ta dauko basket ta Zuba".
Kitchen din zahra ta koma, Ammah Kuma ta fuskanci Mahmud dake fadin.
"Zamu tafi Ammah kiyi min addu'a".
Sai taji yaron ya Kara shiga ranta duk Inda ya fito ya samu uwa ta gari, cikin nuna kauna tace Masa.
"Ubangiji yayi Albarka ya taimaka ya kaiku lafiya ya bada abinda akaje nema".
" Allahumma Amin, nagode".
Ya tashi yayi waje, Yana fita zahra ta matso kusa da Ammah.
"Yanzu Ammah ki rokar min ko sati Daya ya Bari nayi Amma kika Kiya shikenan".
"Kina son na Zama uwar banza kenan? yaron Nan bansan abinda ya gano ba tunda harya iya tunkarata da
irin maganar Daya fada min kije kawai ki yiwa mijinki biyayya idan anjima da magariba magaji ze kawo zilan
sai ku zauna, kije Yana jiranki kada ya kosa".
Tare suka fito da Alawiyya data dauko Abinci.
Tunda suka dauki hanya yake amsa waya da alama da likita yake magana a yanayin yanda ta fuskanta.
Lokacin da suka shiga gidan wani daban ta gani ba zayyan ba sai safwan tunda shi tasan shi a kano.
Gurin motar suka karaso, da sauri safwan ya bude masa ya fito.
Dayan ya duba yace.
"Naseer ka kula da gidan Nan kafin zayyan ya dawo idan an Jima wani yaro ze kawo wata mata, daga su
ban amince wani ya shigo gidan nan ba har zayyan ya dawo, sannan ya juya gurin safwan ka Zama ready
Zan fito Nan da ten minutes in Sha Allah".
"To suka amsa sannan suka koma Inda suke.
Dayan side din mahmud ya koma ya bude Mata ta fito a yangace Yana nazarce da ita ba haka taso ba so
tayi a ajeta a can ta Zama nama shi Kuma abinda bazeyi tolerating ba kenan.
Ta baya yabi da ita tayi mamakin ganin kofar kenan ginin dai sak irin na Kano ne, suna wuce idanun jama'a
ta dauketa cak Bai direta a ko Ina ba sai bedroom dinsu ya ajeta, wata irin soyayya ya kwada Mata Mai
wuyar mantawa tare sukayi wanka shaf-shaf suka suka shirya da kyar ta matsa Masa yaci abincin, Yana
mak'ale da ita suka fito, cikin motar suka shiga tare a Nan ma saida yayi son ransa kafin ya barta ta fito.
Saida ta juya ta Fara tafiya sannan safwan ya taso, fitowa mahmud din yayi.
"Precious...."
Ya fada Yana Jan sunan.
Cak ta tsaya Amma Bata juyo ba Dan idanunta fal da hawaye ji take Kamar ta bishi su tafi Batasan tayi
mugun sabo dashi Kamar haka ba sai yanzu da zeyi Mata nisa, Saida ta shanye hawayen sannan ta juyo,
wani kiss yayi Mata blowing dinsa sannan yace.
"I missed you my previous, I really missed you".
"And me too...." Ta fada tana shigewa ciki.
Jikinsa ba karamin sanyi yayi ba a haka suka fice daga gidan.
Mahmud Basu shiga Kano ba sai kusan magariba sultan road suka nufa, Saida ya huta yayi wanka sannan
ya kirawo Sameer ya fada Masa ya shigo yazo ya sameshi a sultan road, ta Tarauni suka biya suka sai musu
fruits sannan suka wuce can court road din.
MAMAN FATEEMAH.
08055362975
____
My WhatsApp number
09061432330
Page 61.
.............Ana Kiran sallar insha'i suka shiga unguwar, a masallaci suka tsaya sukayi sallah, su Kuma su Habib
a masallacin kusa da gidan sukayi sallah, gurin Mai gadi suka zauna suna Hira Abu daya ya ringa bawa
Habib mamaki yanda Mai gadin ke yiwa Abubakar wasu maganganun dake nuna da sanayya a tsakaninsu
Koda ba Mai yawa bace sai dai shi Abubakar din Yana waskewa ya basar dashi, suna cikin wata hirar da tayi
matukar bawa Habib mamaki ne sukaji Horn din mota daga waje da sauri Mai gadin ya tashi yana fadin.
"Ga Oga nan da kansa, gaskiya ba karamin matsayi bawan Allahn nan ke dashi a gurin yallabai ba, yaushe
Rabon da wani ya ganshi sai irin ku Abubakar 'yan gaban goshinsa".
Ya fada yana nufar gate din cikin azama, ya bude kofar motar ta kunno kai ciki.
Mai gadin ne ya Fara jera Masa kirari yana fadar.
"Allah ya taimaketa barka da sauka fari Mai farar aniya! Allah ya Kare maka mutuwar zuciya kaga Wanda
yayi gadon arziki uwa da uba. Ubangiji ya Kara maka daukaka da daraja, baya Mai goya marayu kaga Dan
sakwkwatan Asalin jikan zabarmawan Niger ubangiji ya Kara maka daukaka da arziki Mai Albarka, ya tsone
idon maqiya da mahassada a kanka, jikan Hajiya Inna Mai abin mamaki"..
Haka ya biyo motar Yana zabga Masa kirari, in da sabo Mahmud ya saba da halin malam sule tamkar
maroki haka yake.
Abubakar da Habib ma tasowa sukayi suka nufosu, Amma fa zuciyar Habib fal mamaki, to me hakan ke
nufi? be Kara shiga rudani ba Saida yaga Mahmud ya fito ma'aikatan gidan suna nufosu da sassarfa suna
kwasar gaisuwa, shi in ba idanunsa ke fada Masa karya ba sai yaga wannan na tsayen ba Mahmud dinsu
bane, Dan totally ya canza a idanunsa Bai gaskata shi bane Saida yayi magana lokacin da hadiman gidan ke
kwasar gaisuwa.
A gurguje yake amsawa ya nufi bangaren da baba malam din ke ciki,duuuu suka bishi a baya, Koda Wasa
Mahmud be yarda sun hada Ido da Habib ba.
Lokacin da suka shiga Malam ya farka Yana sallah, Sauran hadiman juyawa sukayi suka koma dakin ya rage
daga su Mahmud sai nurses din da suke kula da shi. Cikin girmamawa suka gaishe da Su Mahmud din.
Saida Baba malam ya shafa Addu'oinsa sannan ya dubi gefen dasu Mahmud ke tsaye, ganin ya idar da
sallar yasa Mahmud matsawa kusa dashi Yana murmushi, shima Baba malam din murmushin karfin Hali
yake mayar Masa, gefen gadon ya zauna kusa dashi sosai ya riko hannunsa.
"Sannu Baba malam, ya jikin naka?".
"Masha Allah. Alhamdulillahi jiki da sauki kam, Allah yayi Albarka".
"Amin ya Rabbi.Allah ya baka lafiya gobe karfe shida da rabi na safe zamu tafi in Sha Allah".
Dan Jim malam din yayi kafin yace.
"Zuwa Ina Kuma mahmudu?"
Sameer ne ya matso Yana gaishe da baba malam din sannan yayi masa bayanin halin da ake ciki.
Shiru yayi Basu yi zato ba sai ganin hawaye sukayi yana bin gefen idon Baba malam.
Cikin rudewa Mahmud da su Habib suka shiga tambayarsa.
Menene? Ina yake Masa ciwo? Har Daya daga cikin nurses din ya Ciro waya ze Kira doctor Mahmud ya
daga Masa hannu alamun ya jira.
"Babu komai, me zance muku yaran Nan Ubangiji yayi Albarka, ya biyaku da Aljanna madaukakiya"
"Allahumma Amin,Allah ya baka lafiya".
Daga nan yaja Bakinsa yayi shiru, Suma babu Wanda ya Kara cewa komai.
Key din motar Sameer ya mikawa Abubakar yace.
"kuje ku shigo da Kaya".
Nurses din Sameer ne ya tambayi nurses din ko akwai abinda suke bukata? Sukace masu babu duk abinda
ake bukata daga Nan zuwa safe akwai shi.
Ledoji ne manya suka shigo dasu, da Ido baba malam ya bisu kawai har suka aje, shi tun ganin gidan da
aka kawo shi da irin yanda aka dauko Masa manyan likitoci suka zo suka zauna zaman jiran zuwansa da irin
yanda yaji Wani Yana fadiwa abokin aikinsa yana Abuja DANGE ya katse Masa tafiyarsa dole ya dawo duba
patient dinsa, ga ma'aikatan jinya an aje su duba shi,yasan abun bana Wasa bane, da abinda Allah s.w.a ke
nufi da kawo wannan yaron cikin rayuwarsa ya Dade Yana mamakin halayyarsa da yanda yake mu'mala da
jama'a zuwan gurin tamkar kofar arziki aka bude musu taimako da tallafi Kota ina, a she ubangiji ya
sallad'o wata kaddarar da tafi karfin tunaninsa shi wannan yaron ze zaman sanadin tallafawa rayuwarsa,
Hamdala kadai ta kamace shi, a zuciyarsa ya dunga maimaita ta, ya Kara girmama girman ubangiji, wato
duk abinda Allah s w.a yayi akwai hikima a cikinsa sai wani abun ya faru kasan wani connection din yafi
gaban karamin tunanin mutum.
Mahmud Bai bar gurin Baba malam ba Saida ya matsa din yaci Naman kazo yasha fruits sosai, misalin
goma da rabi suka fice daga gidan Muhmud be koma Nasarawa ba Nan Bawo road Sameer ya ajeshi, bayan
sameer ya wuce ya dade Yana ta kokarin ya samun visa zahra abin yaci tura, duk Wanda yake tunanin
zasuyi masa aikin duk ya rasa su, abin ya bashi matukar mamaki Dan wannan shine first time da irin haka
ta faru dashi, dole ya hakura ya sakawa sarautar Allah Ido besan abinda Allah yake nufi da Hana samuwar
visar ta taba.
Su Habib ma sunso kwana a gurin Baba malam, Anna kememe nurses din suka Hana sukace aikin da aka
biyasu makudan kudi suyi kenan,idan yallabai yaji labarin sun Kwana a Nan za'a samu matsala dan ba
karamin warning aka kada musu ba, dole suka hakura suka wuce nasu masauki daura da Inda Baba malam
din yake.
Gida ne na Alfarma tamkar gidan want gwamnan komai na Jin dadin rayuwa an tana deshi hatta da suturar
sakawa gasu Nan sabbi sai da ka saka Wanda yayi dai dai da kai, Abinci sai Wanda kake bukata za'a kawo
maka tunda suka sauka ake hidima dasu Baga Abinci ba Baga snacks ba Baga drinks ba, komai enough
gashi nan, gurin malam sule suka koma sukaci gaba da Hira a Nan Habib yaji shima Ashe Abubakar Dan
Sokoto ne.
Saida sukayi Shirin kwanciya sannan Habib ya kalli Abubakar.
"Dan Allah ka fada min gaskiya Daman kasan Mahmud ne kafin kaddarar data kawo shi nan Azare? Naji
Mai gadi Yana maka wasu maganganun da suka sakani a duhu?".
Dan Jim yayi Yana nazarin maganar Habib, kafin yace.
"kayi hakuri nayi maka Alkawarin fada maka Amma Dan Allah ba yanzu ba".
Jinjina Kai kawai Habib yayi, alamar gamsuwa, Bai Kara cewa komai ba ya kwanta zuciyarsa fal tambayoyin
rab'ab'a wanda bashi da amsarsu.
Mama tun Rana da tayi muguwar kwarewa har dare tana fama da kanta duk abinda ya kamata, Tasha ta
Sha Amma dai Abun yaki Zama dai faint Dan ji take wani Abu ya tsaya Mata a kirji yaki wucewa, da kyar
wurin goma na dare ta samu number Aunty Larai ta kirata cikin nuna damuwa ta zayyane Mata komai da
yanda taga Mahmud, da zargin da take yiwa Abba akan Yana da masaniyar ko waye yaron har canzawa da
Zahra da Mai aikinsu zilai Saida ta fada mata, bala'i Aunty Larai ta Fara tana zuga Mama dole tayi Abun da
zata wargaza rayuwar yarinyar gaba Daya tunda Asabe ta nunafrceta ta gudu da wadannan magungunan
da aka kawo Wanda da anyi yanda akace da yanzu ba wannan labarin akeyi ba, kudi masu yawa Mama ta
turawa Aunty Larai tace tayi duk abina ya kamata, sun Dade suna tattaunawa kafin suyi sallama da
alkawarin da safe zata bazama gurin arnan Kan Dutse.
Aje wayar Mama tayi tana fadin.
"Wallahi Asma'u keda wannan Fara farar yarinyar kun shiga uku, kuda kwanciyar hankali kunyi ban Kwana
Ina Raye bazanga bakin ciki ba, wannan yaron ace shine mijin zahra? Wato a baya kallon tsoro nayi Masa
kenan,wallahi sai kwanciyar hankali ta gagare ku, Dan karya malam na Bande ze want ce bega rabuwa ba a
cikin aurensu Naga kashin awaki saina rabasu yanda naji niyya saina tagayyara rauwar Zahra babu fashi
Dan halak ka fasa".
Ta debo wata ashariya ta lafta tana kwafa duk idanunta sun firfito saboda bacin Rai ga azabar data Sha ta
kwarewa.
*****
Tun bayan tafiyar magaji zahra da Aunty zilai suka shiga kitchen sukayi simple girki, Aunty zilai ce ta
mikawa Naseer,Bayan ta dawo ne take fadin.
"Uwar dakina wato lamarin yallabai Yana bani mamaki gashi dai yaro Karami amma fa Naga alamar kowa a
Karkashinsa yake,dan oga Sameer na fuskanci a nan ne yake oga amma a waje yaron oga ne". Ta fada tana
dariya.
Dan yatsina fuska zahra tayi.
"Nifa na aje lamarin su a gefe,ita dai ai karya ai fure take Bata 'ya'ya, ni meye nawa tunda Kika min fada a
kano na sakawa Raina salama na iya kaina tunda Naga abun nasu ba Mai karewa bane, Kullum da wani
sabon salon da Zaki gani a gurinsu basai mitum ya Zuba musu idanu ba Randa suka shirya magantuwa sai
su magantu".
"Gaskiya dai kam, Nima da farko na shiga razani lokacin da aka Kaimu Kano Amma Dana ji bayani daga
bakin Iya Rahane saina fashimci duk Inda mijinki ya fito ba daga Karamin gida ya fito ba,Kuma naji kishin-
kishin din bacin Rai ne ya fito dashi Dan iya ta fada min sai dai tace Bata San takamaimai menene ba itama
tsintar zancen tayi mommy da oga Sameer sunayi ta shigo ta kofar kitchen ta baya, abunda nakeso dake
uwar dakina duk Inda rayuwa ta kaiki ki Zama Mai takatsantsan da mutane yanda naji labarin nasa dai sai
kin nutsu sosai Dan na fuskanci mijin naki ko a cikin dangain na daban ne shi gaskiya, bare yanda naji iya
Rahane na fada sai Wanda ya gani, Kinga dai yanda akayi ta samun akasi akan Aurenki Kuma Billahillazi
asirai ne aka dunga yi nasan Allah ne ya nunawa ko waye ma iyakarsa ya Baki miji Daya da daya, wallahi a
gaban idona anyi dariya an Kara akan an aura Miki Almajir Qolo Wanda Bai aje ba Bai bada ajiya ba, ance
sai aga ta taqamar kyau an Kare a Almajiri mane min tsaba".
Ta fada cikin nuna bacin Rai.
"Kai haba Aunty zilai meye na tuna abinda ze Bata Miki Rai, ba gashi ya Zama fast ba, Ni nasan mutum be
Isa yayi min abinda babu Shi a cikin kaddarar da Allah s.w.a ya rubuta min ba. Daman haka take kaddarar
sai dai a jahilci irin na mutum yaga abinda yayi ne yayi tasiri,sun manta Alkawarin Allah baya canzawa". Kai
Aunty zilai ta jinjina tana fadin.
"Wannan gaskiya ne Allah ya Kara Miki tawakkali da qarfin imani ya doraki a Kan mak'iya da mahassada,
yasa wata Rana ki Zamar musu kadangaren bakin tulu a barka ka bara ruwa a karka a Kar tulu, Allah ka
nuna min ranar da karya zata Kare gaskiya tayi halinta in Sha Allahu sai kin zamar musu ciwon Ido ba yanda
za'ayi dake sai hakuri, in Sha sai munga karshe masu hassada da muna furci".
"Allahumma Amin".
Sun Dade suna hira kafin zahra ta nunawa Aunty zilai wani daki a cikin parlour na biyu daga cikin corridor
da yake fitar da mutum waje, daki ne comfortable yaji Turkish bed Mai shegen kyau yasha ubansun
bedsheet sai sanyi A/C da kamshin roomfreshner dake tashi, sallama zahra tayi Mata ta wuce nata
bedroom din.
Wanka tayi ta Saka sleeping dress tayi shafa'i da wutiri sannan ta kwanta, lamban tayi a gado, duk kewarsa
ta dameta Amma tana Jin nauyin kiransa a wannan lokacin rabonsu da waya tunda ya kirata yace Yana
Dutse, da magariba tayi ta try Bata same shi ba tasan yanayi network duk da tayi marking da wuya a Kira
wayarsa Bata shiga ba.
Data ta bude tana duba sakonnin da suka shigo Mata ba tunda ta mayar da master layinta Daya Bata dazu.
Reply din sajida ta Fara dubawa, saina Aunty Rukayya data tura mata sallama ta fada Mata itace, sakon
karin jajanta rashin lafiyar malam ta turo mata har tana tsokanar ta akan meya Hana balarabiya taje India
ta Sami ruwa biyu tunda kyau ne ke dukan kyau, Emoji na rufe Ido da hannu ta tura Mata.
Ba zato kawai kiransa video call ya shigo, wani Abu taji ya tsirga Mata tsikar jikinta ta tashi, data tuno
moment dinsu na dazu.
Dauka tayi tana lumshe sexy eyes dinta.
"My previoussss.."
Ya fada a hankali, Yana bin fuskarta da kallo gani yayi Kamar Kara Mata kyau akeyi matukar zeyi some hours
Bai ganta ba.
Cikin nata salon ta bude idanunta dake Rita Masa lissafi ta saukesu a Kan nasa.
"Yesss.. meu Amorrrr..."
"Ya Salammmm.."
Ya furta a hankali tamkar Mai tsoron wani yaji abinda yake fada, da gaske yarinyar Nan so take nayi ta sakin
layi a gabanta.
"Cikin muryar data saka zahra a cikin wani yanayi yace.
"Inaga na fasa tafiyar Nan har sai kin samu visa Kona tafi akwai damuwa gaskiya".
Tashi zaune tana cire blanket daga jikinta tunda tana jingine da pillow ne a jikin face din gadon, rigar irin
transparent din nan ce Mai siririn hannu baqa sai ta Kara haskaka fatar Qirjinta sosai Nan da Nan ya nemi
nutsuwarsa ya rasa.
Cikin shagwabar data Fara zamar Mata jiki ta Fara fadin.
"Haba dai Dan Allah me Amor... kuje kawai babu Dadi Baba malam ne fa ba Wani ba,! Idan ma kazo to me
zanyi maka sai dai fa ka raba hankalinka biyu, Amma idan kuka tafi zakafi samun nutsuwar data Kamata,
kaji plsss.. Dan Allah".
Mak'e kafada yayi tamkar yaron goye Yana Mata wani kallon Daya sakata rufe idonta dole.
"Bude idonki bana son kinibibi, Kamar ba ke bace...... Bari dai nayi shiru kada na kirawowa kaina Ruwa
ko?".
Luuuu tayi da Idanu, sai Kuma ta hura Masa iskar bakinta saitin bakinsa Kamar Yana kusa da ita.
"Ki jirani komai dare dole nazo na biya wannan bashin".
A razane ta wartsake tana marairaice fuska, tana Dan jijjiga jikinta a hankali jikin Yana wani irin shaking a
hankali".
"Dan girman Allah da darajar Manzon Allah kayi zaman ka wallahi Zan nemi visa da kaina Zan biyo ka".
"It's too late, kiyi Shirin tarbar bako da safinsa".
Kafin ta Kara rokonsa ya kashe wayar.
08055362975
____
My WhatsApp number
09061432330
*MAMAN FATEEMAH*
Da sunan Allah Mai Rahama Mai jinkai salati da daukaka da Aminci su tabbata ga shugaban mu Annabin
Rahama Muhammad s.a.w.w
Page 62.
_______Karfe shida dot mahmud suka shiga Malam Aminu Kano international airport shida safwan Daya
kawo shi, kafin su Kai ga gyara parking motar su Baba malam ta shigo wadda zayyan ya tukosu, kafin
Safwan ya fito tuni Mahmud ya bude ya fice da sauri cikin wasu hadaddun suit army green sai wani wani
sanyi kamshi yake fitarwa idonsa sanye da siririn eyeglasses Mai haske sosai abinda wani be taba gani a
Azare ba kenan ya fito a mahmud dinsa, cikakken Dan boko da ganinsa kasan yes ba karya.
Wadannan nurses din ne tare dasu Habib suka kamo gadon daukar marasa lafiya suka fito da Baba malam
din. Gurinsu ya Karasa Yana fadin.
" Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Sallamar suka amsa Masa a tare, gaban gadon ya matsa yana fadin.
"Barka da Asuba Baba yaka kwana?".
"Jiki da sauki cikin Rahamar Allah, sannu da kokari kaji mahmudu Allah ya baka ya saka maka da Alkhairi".
"Allahumma Amin"
Ya fada sannan ya amsa gausuwar dasu Abubakar ke Masa, sukayi gaba shi Kuma ya koma mota ya zauna
yana Kiran wayar zahra. A Nan Sameer ya same shi tare da abincin break nasu Habib.
A cikin reception bangaren vip aka shiga da Baba malam, lokacin da Mahmud ya shigo su Habib suna gurin
screening, gurin Baba malam suka shiga da Sameer din ya duba shi har lokaci yaran Nan nurses suna tare
dashi.
Ma'aikatan jirginne suka shigo suka fita da Baba malam, Sameer ne ze koma da yaran ya sallamesu duk da
tun jiyan sunji alert me nauyi a account dinsu.
Har cikin jirgi Sameer ya raka Mahmud ya Kara duba Baba malam yayi Masa fatan Alkhairi tare da fada
Masa Shima ze shigo Daya Gama abinda yake yi.
A ciki ma vip Mahmud da Baba malam suke yayin da Abubakar da Habib suke a cikin jama'a.
Tunda suka tashi Mahmud ya bude Qur'an din cikin wayarsa Yana karatu lokaci bayan lokaci Yana duba
Baba malam tare da tambayarsa ko da abinda yake so? abincin da ake rabawa ma cewa yayi baze ci ba.
Bangaren su Abubakar,Habib kam ba baka sai kunne domin an shayar dashi mamaki ba kadan ba, yanda ya
fuskanta Mahmud dai uban gidan su oga Sameer ne harda Abubakar ma tunda a airport din Nan yaga
zahiri ba Wani boye-boye a ogansa ya fito sak, hatta ma'aikatan wani irin girma suke bashi.
'yar tv jikin seat din kujerar gabansa Habib ya kunne Yana ganin location din da jirgin kebi, sun kwashe awa
bakwai da minti hamsin da biyu a sama kafin suyi lending a Ethiopian, an fito da Baba malam ma ya huta
yaci Abinci yayi sallah, Habib sai kallon Abubakar da Mahmud yake mamaki na neman kashe shi da ransa,
rayuwarsu a Azare yake tunawa duk iya kwakwar mutum baze taba sanin da wata sanayya a tsakaninsu ba
ballantana kaga wani Abu Daya danganci yaro da uban gida.
Shi kuwa gogan yayi fuska Kamar be gane kallon da Habib ke Masa ba.
Awarsu Daya da minti goma suka sake tashi, jirginsu sai karfe shida da minti arba'in da biyar ya Sauka a
INDIRI GANDI INTERNATIONAL AIRPORT new Delhi India.
Suna fitowa suka iske ambulance din Max na jiran saukarsu Dan tun tasowarsu suka Fara communication
da Sameer, sai a Ethiopia ne sukayi da Mahmud, ba karamin mamaki mahmud ya bawa Habib ba a lokacin
Jin yana yaran indianci tamkar harshen tsohuwarsa.
Ma'aikatansu suka shigar dashi cikin, Mahmud ne ya bisu, yayin da yace Abubakar ya jira Mr Salahuddeen
zezo ya tafi dasu ya Kai Habib gida ya huta.
Shi dai Habib yaga abinda ya girmi nasa wayon nesa ba kusa ba.
Saida motar Asibitin ta bacewa ganinsu sannan Abubakar ya Dan daki kafadar Habib kadan yana fadin.
"Don't mind, in Sha Allah Baba malam da kafarsa ze dawo nan,shi yasa oga ya dage azo nan din yasan suna
da qualified doctors, kada ka damu yanzu muje gida ka huta tunda baka Saba da irin wannan doguwar
tafiyar ta kusan twelve hours ba".
"Nifa ba wannan bane damuwata ba yanda naganku da Mahmud daga jiya zuwa yau shi yafi bani mamaki
abin Kamar a Shirin film".
Dariya yayi Yana fadin.
" Share kawai lalura fa ta gitta ai babu maganar wani boye-boye Kuma kasan yanda oga yake son malam
kuwa?".
"Na sani Mana tunda tare muke dashi, kawai dai abin ne da mamaki yanda ko kadan babu wata kafa da
Wani ze fashimci hakan da kuka bada".
Dariya kawai Abubakar yayi ya basar da maganar, Shima Habib shiru yayi Bai sake cewa komai ba, Basu
jima a gurin ba kira ya shigo wayar Abubakar, picking yayi ya Fara magana cikin harshen turanci Yana yiwa
Mai Kiran kwatancen ta Inda suke.
Shi dai Habib lamarin naso ya Fara bashi tsoro, gaba Daya sun juye masa daga asalin yanda ya sansu sun
koma Masa wasu na daban.
Suna gurin Mr Salahuddeen ya karaso, musulmi ne mutumin Pakistan, da sauri ya fito ya rugune Abubakar
Yana fadin Daman Yana Nan lafiya ya yiwa india yaji tunda boss baya zuwa Shima ya dauke kafa. Dariya
sukayi Abubakar ya gabatar Masa da Habib a matsayin Dan uwan Mahmud, suka gaisa da fara'a sosai a
fuskarsa, Abubakar ya gabatar da Mr salahuddeen a matsayin drivern Mahmud ne duk lokacin Daya shigo
kasar Kuma
kamfaninsa na jewelry a Nan kasar.
Har sukaje gidan da zasu Sauka Abubakar suna Hira da Mr Salahuddeen yayin da Habib ya Zama Dan kallo.
Su Mahmud suna shiga Asibitin direct suka wuce zuwa vip ward inda Sameer yayi musu booking kenan, sai
suka da gyara baba malam tsab sannan suka wuce suna fadawa Mahmud yanzu masu bashi Abinci zasuzo.
Kana ganin baba malam kasan ya jigatu ba kadan ba, Mai lafiya ma Yana gajiya da Zama ballantana Wanda
yake a kwance, sallah suka rama kafin masu bada Abincin suzo, Mahmud Yana addu'a masu bashi abincin
suka shigo tare da wasu doctors biyu da nurses biyu suma, ba laifi yaci abincin da Dan dama tunda abincin
mu na Nigeria aka cike lokacin da Sameer ya cike komai, da suka Gama bashi suka dauki jininsa za'ayi gwaji
sukaci Baga da sauran bincike binciken su kafin daga karshe suka cewa Mahmud zasu shiga dashi dakin
bincike na musamman sai Nan da awa arba'in da takwas.
A gadon mararsa lafiya aka gungura shi zuwa dakin da za'ayi bincken, har kofar dakin Mahmud ya raka
Baba malam Yana masa Addu'ar samun lafiya, hannun Mahmud baba malam ya riko.
"Mahmudu ubangiji yayi maka Albarka ya amfani nemanka ya Kara maka budi na Alkhairi yanda ka jikaina
kaima Allah ya dawwama maka farin ciki, ko ban tashi ba kayi kokari ka sada Fadima da iyayenka ka basu
hakuri bisa yin gaban kanmu gurin aura Maka ita".
"Babu komai Baba Allah ya bada nasara, in Sha Allah sai kaje Sokoto da kafarka".
Murmushi yayi.
"Kayya gamu dai sai abinda Allah ya hukunta".
"Alkhairi in Sha Allah".
Yana tsaye suka shige dashi ciki, sai kuma yaji wata irin karaya a cikin zuciyarsa.
"Ubangiji ka duba niyyata ka bawa wannan bawan naka lafiya, ka tashi kafadunsa yanda mukazo kasar Nan
kasa na mayar dashi Lafiya".
Sai kusan biyu da rabi na dare Mahmud ya samu taxin cikin Asibitin ya nufi gida.
Lokacin Daya shiga ba kowa a parlourn, Mr Ajey ya Kira a waya kukun gidan ne, fada Masa yayi ya dafa
Masa coffee ya kawo Masa daki.
Yaso ya Kira precious Amma ya gaji hutu yake bukata dole ya hakura wanka yayi yasha coffeen da Mr Ajey
ya kawo Masa.
Tun bayan da zahra suka Gama waya da mahmud da safe ta rasa sukuni, data san haka kewarsa zata
dameta da Bata bata lallabashi ba a Kan ya hakura su tafi, Batasan wani jigo bane a rayuwarta saida yayi
nesa da ita tayi missing dinsa ba kadan just in one day kawai taji tana nema gazawa, Dan ko cikin barcinta
shine.
Da kyar ta tashi tayi wanka ta saka rigar Atampha purple Mai manyan flowers farara da ratsin yellow
simple make up tayi ta yafa karamin farin gyale ta fito parlourn farko, ba kowa an gyara shi da sai kamshi
yake yi ga sanyi ko Ina ya dauka, a hankali ta ratsa parlourn tana tafiyarta a nutse tamkar tana counting
steps dinta ta nufi kitchen inda take jiyo motsin Aunty zilai.
Kwanukan da tayi amfani dasu take wankewa, tsayawa tayi da wanke-wanken tana fuskantar zahrar dake
shigowa tare da sallama.
Sallamar ta amsa tare da fadin.
"Barda da Asuba uwar dakina, yanzu nake tunanin naje na duba ko lafiya Baki fito ba kada abicinki ya huce.
Zama tayi a Kan kujerar kitchen din tana fadin.
"Lafiya kalau wallahi kawai dai bansan meya sameni ba duk bana Jin dadin garin".
Dan murmushin manya Aunty zilai tayi tana fadin.
Ko canjin yanayi ne kinsan bazara tana da saka kasala, ga abincin ki nan a Kan dining ko Nan Zan kawo
miki?"
"A'a barshi a can kawai naje naci Wai me Kika dafa need? Allah yasa Zan iyaci ni har cikina bana Jin dadinsa
tun jiya".
"Allah ya saukake ko Asibiti zamuje ne?"
Wallahi ban San sunan unguwar ba Amma ki nemi magaji ya kawo ki tunda yazo sau biyu.
Sukayi sallama Aunty zilan ta cewa zahra "uwar dakina wai Hajiya Mama ce ta bada sako sahura ta kawo
miki wai nayi Mata kwatancen gidan shine nace ta nemi magaji tace ya rakota".
Shiru zahrar tayi tamkar Ruwa ya cinyeta, take gargadin mahmud ya dawo Mata a cikin kwakwalwarta.
"Kada ki yarda da kowa a gidanku idan ba Ammah ba, ba ruwanki da Mama Koda shiga dakinta da gaisuwa
ban amince ki mu'amalance ta ba duk abinda ta Baki kada kiyi amfani dashi ko kici"
Da sauri ta Tashi ta nufi daki tana ayyana Bari ta Kira magajin tace masa kada ya kawo sahura idan ta nemi
ya kawo ta yace sun koma kano, tun jiya da aka tafi da Baba malam.
Ta rasa meta tsarewa Mama a gidan duniyar Nan taki jininta ba kadan ba, to ko da abinda meu Amor ya
sani ne akan Mama Wanda ita Bata sani ba yake ja Mata dogon warning akan kowa Dan har Aunty zilai
Saida ya shata Mata wasu layuka yace kada ta wuce su a mu'amalarta da ita.
💞
* AUREN HUCE HAUSHI *
Maman Fateemah
Page 63.
"An Gama yallabiya, kinsan bazata Fara ma tunkarata da wannan maganar ba, ba sakar Mata fuska nakeyi
ba tunda na gane ita munafuka ce"
Tsaki zahra tayi.
"Can ta matse musu duk munafurcin mutum sai dai ya koma Kansa babu abinda ze sameni sai abinda Allah
ya hukunta min, Wai sako to sakon me? har wani abun arziki Mama zata taso mutum ya kawo min wadda
ko kallon arziki baya hadani da ita saboda tsabar kin jinina da tayi".
"Share kawai bakin ciki ne taga Allah yayi halitta a Nan take hasaada saboda nata 'ya'yan Kamar ka yanka
ka boye wukar, Ni bansan wace kaddara ta Kai Abba Aurenta ba, duk matan jihar Nan Saida ya tsallake ya
dauko ta Dan ma Allah yasa Basu da yawa da ansha kwantai".
Ya fada Yana wata dariyar rainin wayo.
Zahra ce ta katse shi tana fadin.
"Amma wallahi baka da kirki magaji 'yan uwanka nefa kake fada musu haka".
"Kema dai ai kinsan gaskiya na fada duba fa ki gani, kawai dai abar kaza cikin gashinta".
"Allah ya shiryeka wataran sai ka fada a gabanta, ta sauke maka ajja".
Tana Gama fada Masa ta yanke Kiran tasan sai su Kai minti goma shi ba gajiya zeyi ba.
Zahra Bata koma gurin Aunty zilan ba a Nan daki ta zauna, karatun Qur'an tayi sosai Dan Saida tayi surori
da yawa, sannan ta shafa Addu'a ta tashi.
*
Sahura ce ta shiga dakin Mama Jiki ba kwari, ganin ta shigo yasa Mama tashi zaune tana fadin.
"Meya faru Kika dawo? na dauka yanzu kinje can din?"
"Eh naje Amma gidan babu alamun da mutane a cikinsa gaskiya. Dan idan ba idona ne bega dai dai ba
babu wata alama data nuna giccin mutane ma a nan kusa a cikinsa, sai na Kirawo zilai nace ta fada min
suna Ina ne, sai cewa tayi Wai ita Bata San sunan unguwar da suke ba tunda ba fitowa tayi ba tunda ta
shiga gidan, Dan tsabar munafurci".
Ta fada tana aje kunshin kayan da za'a Kaiwa zahra.
Wata shariya Mama ta lafta tana fadin.
"Har yaushe raini irin wannan ya shiga tsakanina da zilai? Har ta Isa ta nuna min wuyanta ya Isa yanka,
wallahi idan tayi Wasa saina yi mata sanadin barin aikin kwata-kwata, ai dama matsiyaci be iya cin arziki
ba".
Hakuri sahurar ta ringa ringa bawa Mama ganin Nan da Nan ta ture sai masifa takeyi bakinta har kumfa
yake fitarwa saboda bala'in da take kwasa .
Ita dai sahura sai abin ya daure Mata Kai, to menene najin zafi haka, dan zanyi maka Alkhairi anje ba'a
sameka ba, ba sai nabar abuna ba ko na bawa wani tunda Inda nayi niyya ba rabonsu bane.
Cikin bacin Rai tace kije ko magaji ne ya rakaki Mana Zaki zo kiyi tsaye Kamar baki da wayo da dabara Dan
Allah wuce a gurin".
Kayan ta dauka ta nufi kofa tana fadin.
"Bari naje na gani ko Yana nan din".
Ta wuce ta fita.
Zugum Mama tayi tana nazarin yanda abubuwa suketa lalace Mata, Wai yarinyar Nan me take takama da
shine? duk abinda za'ayi da sunanta sai ya lalace,ko da tsiya-tsiya yau sai sakon Nan ya shiga gidanta duk
Inda ta koma ma saina lalubo shi Dan wallahi bazanga bakin cikin da ze hanani barci ba.
Duk iya kokarin sahura na taga magaji abun ya gagara wayar zilan ma an rufe ta, ko Kuma network yaki
bada hadin Kai.
Wata dabara ta fadowa sahura, da sauri ta nufi gurin Bala driver tana fatan samun mafita a gurinsa saboda
Bata fatan ta rasa abinda Mama ta kwadaita Mata zata Bata.
Yana aikin goge mota da alama fita zasuyi da Abba, sallama tayi Masa suka gaisa sannna tace Masa.
"Dan Allah malam Bala ko zaka taimaka ka kwatanta min gidan da yarinyar Nan zahra suka koma naji ance
sun tashi daga Nan hayin banki,Kuma na nemi duka lambobinsu ban samu ba".
Ta fada tana fatan samun abinda take so.
Tunda ta fara Kora bayani malam Bala ya dakata da aikin da yakeyi Yana kallon ta Saida ta Kai aya sannan
yace Mata.
"Haba sahura yaushe Zan dunga bin diddigin yarinyar da take gidan mijinta, ai wannan rashin lissafi nema
ma wallahi ai da kunya ki fito neman gidan Zahra a Nan gurin mu alhalin ga uwarta can a cikin gida, to ke
me zakiyi a can Wanda Baki son uwarta ta sani".
Cikin rashin yarda da Kai ta Fara fadin.
" A'a wallahi kasan wani abun alherin idan mutum zeyi baya son a gani sai dai shi yaron ya fadawa uwar
tasa daga baya".
"To shiga ciki ki nemi bayani dole"
Ya juya yaci gaba da aikinsa ya bawa banza ajiyar ta, it's Kuma ta koma ciki da ledarta a hannu, mita yake
shi kadai.
"Haba mutane sai halin tsiya, Nan gaba kadan wallahi wannan mijin nata ze shayar da mutane mamaki Dan
naji Alhaji Yana wani furuci jiya bansan dai dawa yake waya ba Amma Ina ganin da bincken da yake yi akan
yaron Nan Kuma jiya Wanda ya saka shi ya dawo Masa da amsa".
Sai kusan Sha biyu na agogn kasar India Habib ya tashi, yayi mamakin yanda lokaci yayi gudu haka, da sauri
ya nufi toilet Yana yiwa Kansa fadan me kenan yayi shida ya biyo marar lafiya Amma ya bige da dogon barci
irin haka, "ko Yaya Baba malam din yake?" Ya yiwa Kansa da Kansa tambaya.
A gaggauce yayi wanka ya fito, Bai wani Bata lokaci ba ya shirya ya fito yana ayyana Allah yasa Mahmud ya
dawo Dan jiya sun Dade suna dakon zuwansa Amma shiru dole suka hakura suka kwanta.
A parlour ya iske mahmud Yana ta faman aiki a cikin computer desktop wadda take girke a parlourn, daga
gefe Kuma wasu indiyawa ne su biyu Yana musu magana da harahen indianci suna amsa masa, da alama
Kamar Umarnin wani Abu yake basu, har Inda yake zaune Habib ya Karasa yayi Masa sallama ga
mamakinsa sai yaji gaba Daya sun amsa masa, Shima Mahmud barin abinda yake yayi ya juyo Yana sakin
murmushi ya mikawa mahmud hannu sukayi musabaha, sannan ya mikawa bakin mahmud suka gaisa,
ganin Kamar Habib na dari-dari dashi dan Yana kula da yanda yake tsare shi da ido, sai idan yaga zasu hada
Ido yayi saurin janye nashi, tashi muhmud yayi daga Kan computer ya riko hannun Habib Suma sauran
biyun suka rufo musu baya.
"Bakon india, nasan ka gajine shi yasa na Hana Abubakar tashinka nace ya barka kayi barcin gajiya tunda ka
gaji da yawa".
Ya fada suna Zama a kujera two seater,
"Bari kawai ni kaina nayi mamakin barcin da nayi, Ina Abubakar ne?".
"Sun fita da Mr Ajey kasuwa, inaga sun kusa dawowa ma yanzu, ga abinci nan kaci idan ka gama zaku fita
dasu Mr Salman zasu rakaka kuje a Sami kayan sakawa tun dazu suke jiran ka fito ku tafi baka tashi ba, ga
abincin can ka duba Wanda zaka iyaci sai ku wuce, nima Zan shiga naga doctors din dake kula da Baba
malam yanzu suka nemi ganina tunda tun jiya suka shiga dashi dakin bincike na musamman sai gobe za'a
fito dashi, kasan tsare-tsaren Asibitocin su da banbanci da namu na Nigeria"..
ATM mahmud ya mikowa Habib na bankiya juya Kuma yayiwa su Mr Salman maganar da Habib besan me
aka fada ba, ya wuce ciki Yana fadin.
"Kada ka dauko kaya kadan Dan bamu San how long samu zauna a Nan ba sai yanda Hali yayi".
Shi dai Habib kasa cewa komai yayi Dan ya gama Shan ruwan mamaki ba kadan ba, Mahmud din da suke
kwana su tashi tare ne wannan? ko a mafarki be taba kawo haka ba".
Cikin abinda be wuce minti latatin ba Mahmud ya fito cikin kananun Kaya yayi fresh dashi ya fice daga
gidan, har lokacin su Abubakar Basu dawo ba, da kanshi yake driving din, da Dan hanzari yake tafiya
saboda gaba Daya hankalinsa yayi Asibiti.
Lokacin Daya shiga direct office din consultant din ya nufa, be same shi a office ba Yana cikin ward inda
yake duba patient dinsa, baifi zaman minti goma ba doctor din ya dawo da zugar wasu dalibai a bayansa
Yana ganin mahmud ya gane shi, tunda yaji yana Jin yaransu yake Nan Nan dashi.
A cikin office din wasu hotuna ya dauko ya aje a Kan table dinsa yace mahmud da sauran daliban su
matso.Dalla Dalla ya shiga Yi musu bayanin yanda ciwon yake da yanda yake yiwa mutum illah idan har
ba'a Farga an kawo mutum Inda za'ayi Masa aikin gaggawa ba saboda yanda spinal cord din ta matse to
komai ze iya faruwa za'a iya rasa kafa da amfanin kasan Jiki na har abada, Dan haka daga Nan zuwa Kwana
uku za'ayi wannan aikin, Amma dole charges zasu karu tunda sun Kara gani karaya a kashin hakarkarinsa
na hagu guda biyu sai kashin mukamikinsa Daya goce".
Take a Nan mahmud ya nemi a bashi bill na Karin charges din da aka samu, yaje ya biya komai ba damar
ganin Baba malam haka dokar take,yana tafiya a Kan barandar Asibitin Yana sauri ya Karasa gurin Daya aje
mota yaji daga bayansa ance.
"Waye nake gani Kamar Mahmud Dange".
Da sauri ya juya Yana mamakin waye wannan yayi Masa farin sani haka.
Faisal ya gani kanin Aunty Surayya matar uncle Mustaphan zasuyi sa'anni da mahmud din, cikin fara'a
Mahmud ya Fara fadin.
"Faisal bungudu Long time, Daman talaka Yana ganinku?".
"Kaji ka da wani magana Kai ganin ku ai sai Mai sa'ar gaske, Nigeria kun Mata tawaye ma kwata-kwata
yaushe ake ganinku, meya kawo ka Nan ne haka ko patient gareka".
"Eh wallahi wani Babana ne ya samu spinal cord injury muka kawo shi Nan, Kai Kuma meya kawoka?"
"Wallahi Alhajin mu ne ya samu accident tun kusan wata hudu da suka wuce, karaya ya samu a cinya, anyi
gyara har sau uku abun yaki shine, wani doctor da muke gani a wani private orthopedic hospital a Sokoto
yayi Mana hanya mukazo nan, kaga jiya uncle Mustapha ya bar Nan kasar tunda shine ya kawo mu sai da
ya Gama Mana koma".
"Allah yasa ayi aikin cikin sa'a yasa da nasara yasa a dace.
"Allahumma Amin" Faisal ya fada.
Lokacin da suka shiga Alhajin Yana zaune a gadonsa Yana lazimi da casbaha dinsa.
Ganin Faisal ya dawo da wani yasa ya maida hanklinsa a Kansu, har suka karaso yana kallonsu.
Sallama Mahmud yayi masa ya amsa sannan Mahmud din ya gaishe shi da jiki.
Faisal ne ya yiwa mahaifansa bayanin Mahmud, cikin nuna Jin Dadi mahaifan na Faisal ya shiga jorowa
mahmud godiyar abinda akayi masa, Basu jima ba Mahmud ya aje Masa Dala dubu yayi masa sallama,
Mahmud yasha shi Albarka Kamar ze Bari Baki gurin godiya.
Shima Faisal godiyar ya dunga jerawa Mahmud Kamar me, shiya dauki Faisal ya Kai shi har masaukinsu
sannan Shima ya hada shi da dala dari biyar yayi gaba, wani irin shauki ke dibarsa akan yaje gidanta tunda
gari ya waye yaji ba abinda yakeso irin yaje ya ganta ita da yaran, amma wata zuciyar na fada Masa kada
kaje akwai k'ura Kuma wannan match din bazaka iya playing dinsa yanzu ba, kwabarka ce zatayi ruwa, dole
ya karkata Kan motar ya dauke daga direction din da ze Kai shi gidanta, Amma fa dole yaje gareta duk rintsi
Dan yanzu ma yasan Yana zuwa wani labarin za'ayi ba wannan ba Dan dole ballin ya tashi.
__
Har dare Zahra Bata Jin dadin jikinta Sam da mahmud ma ya Kira Basu Dade ba yace Yana da wani uzurin
da zeyi sukayi sallama.
Wurin karfe biyu da rabi ta farka sai taji Kamar an Zuba Mata ruwa, da sauri ta yunkura ta tashi zaune
abunda ta gani ya sakata tashin hankali ta sauko a zabure tana sallallami jikinta sai rawa yakeyi, period ne
yazo abinda Bata taba yiba kenan ai sai kowa yasan da zuwansa Amma wannan sai ganin Abu tayi da wata
irin Zuba ta tashin hankali.
"Na shiga Tara mezan gani haka?".
Toilet ta nufa tana cikin rudu ba kadan ba data shiga ta cire nighty din ta sakarwa kanta Ruwa ta wanka
Yana bin kafarta Zuba yake sosai har da guda guda, ganin abin bana hankali bane yasa ta fashe da kuka, da
kyar ta samu ya Dan tsagaita da Zuba ta hada pad biyu ta saka ta fito ta kunna wutar dakin yanda taga Kan
bed din sai hankalinta ya Kara tashi cire bedsheet din tayi tana share hawaye.
Cikin washing machine ta saka bedsheet din ta fito da towel a bucket da detergent ta Fara aikin gurin tana
cikin aikin tayi wata irin Zuba wadda har Saida ya biyo kafarta saboda yawa hannu ta Dora a ka ta fasa kuka
tana fadin.
"Na shigesu shikenan mutuwa zanyi".
Wayarta da dauko ta lalubo number Muhmud ta Kira ba tayi tunanin ko karfe nawa bane a can.
Yana zaune yana aiki a laptop dinsa yaji Kiran ta ya shigo agogon dake parlourn ya duba yasan yanzu a
Nigeria tsakar dare ne to lafiya yasan ba gwanar chart din dare bace bare yayi tunanin kiransa tayi suyi
Hira.
Yana dauka yaji shashshekar kukanta.
Cikin kidima ya tambayeta.
"Menene? Meya faru? Keda waye a dakin?" Kiyi min magana Mana ".
Duk ya jero Mata wadannan tambayoyin, Bata bashi amsa ba sai faman fadin ta shigesu take.
"Wai precious so kike Nima na fasa kukan ne? na tambaye ki kinyi min banza kina ta kuka, ko wani ne ya
mutu aka fada Miki kike wannan kukan ko wani Abu yake damunki ne?"
Ya fada Yana kwantar da murya Dan so yake tadan samu nutsuwar da zatayi masa bayanin damuwar data
saka tayi masa Kiran tsakar dare.
09061432330
My WhatsApp number.
Naman Fateemah.
Page 64.
Tana shiga ta cire rigar jikinta wani wankan ta sake, fitowa tayi daure da towel sky blue a jikinta, jinta take
wani iri Bata taba samun irin wannan bleeding din ba shi yasa duk ta takura.
Zama tayi tana shafa lotion na razac tana sonsa sosai, tana cikin shafawa taji ringing din wayarta a Kan
bedside tashi tayi tsam ta nufi gurin sunansa ta gani Yana yawo Kan screen din, wallahi tausayi yake Bata
ya kasa samun nutsuwa Kota sisin kwabo.
Video call ne, dauka tayi tana Masa sallama.
Tsura Mata Ido yayi yana tasbihi ga ubangijin da yayi wannan surar, wani yawu ya hadiye ba shiri, kashe
mata Ido Daya yayi Yana dage girarsa ta hagu.
"Precious..,"
Ya kirawo sunanta in a deep voice, lumshe Ido tayi Dan sai taji yau sunan ya zamar Mata wani so special.
Gefen bed ta zauna ta Dan jingina da pillow a jikin gadon, sexy eyes dinta ta Zuba Masu kamar Zaiba a ciki
kafin ta amsa Masa gently.
"Na'am.. meu Amor....".
Saida ya lashe lips dinsa saboda wani abu ya tsirga Masa cikin mararsa har Saida ya rufe Idanunsa, a
hankali ya sauke su a kanta fal fitina Yana Mata wani kallon kasa-kasa.
"Kin tashi hankalina fa ba kadan ba, na rasa nutsuwa ta, hakurin zamanki nesa Dani ya Kare gaskiya bazan
iya wannan jarumtar ba, gangar jina ke Nan Amma zuciyar tana Nan Kinga kuwa mutum ba zuciya ai babu
mutum, ya jikin naki? Me suka fada da sukayi scanning din? naji zayyan na fada min wai sun ce miscarriage
kikayi, nace a'a sai dai wani abun badai shi ba".
Gyara kwaciyarta tayi.
"Nima da farko haka suka fada Aunty zilai ma haka tace data gani, na fada musu bashi bane Amma Basu
yarda ba, sai doctor din data dubani da safen Nan tace fibroid din ne yayi dissolving ya biyo period shine ya
kawo heavy bleeding din, Kuma fa da har number din Ammah ta nemi na Bata Wai zatayi Mata bayanin
abinda ya faru Dani tasan hankalinta ba a kwance yake ba ance 'yarta budurwa tana dauke da ciki tayi bari,
gara ta fada Mata Babu wani Daya taba sanin yarta a matsayin mace lalura ce kawai, kasan muna dawowa
Aunty zilai ta tsareni da maganar bamu da wayo Ashe baka da lafiya muke zaune bamu fadawa kowa ba ita
zata fadawa Ammah a nemar maka magani tunda Amana ta turota gurina, da kyar fa na fashimtar da ita
nace babu ruwanta ta barka ka nemi maganinka".
Dan cute pink lips din ta yake bi da kallo harta Gama bashi statement din.
Kankance Idanunsa yayi Yana Mata wani kallo.
"Gaskiya Kam maganar doctor gaskiya ce, Ni nasan har yanzu rainon a Bata nake yi koba haka bane? Kice
da Auntyn ki ta Kira Mana Ruwa? da bazan Kara yarda mu hada ido da Ammah ba ai tonon sillil ne wannan
shikenan na Zama ragon maza a idanunta".
Ai zahra Bata gane ta saki layi ba Sai daga baya, kunya taji ta rufeta.
"Nifa labari na baka ba Wai wani Abu ba".
"A'a gara na saka shimma kada a zaci da gaske ne, yanzu ita ta yarda bani da kuzari fa sai dai tayi ta kallona
a haka koba haka bane?.
Kira ne ya shigo Masa daga Asibiti, da sauri ya yanke Kiran Yana fadin.
"Bari na daga kirane daga Asibiti.
Yana sauka daga online tayi ajiyar zuciya Allah ya taimaketa, da Allah kadai yasan meze baro Mata taga
alamar kamar hakurinsa Yana neman karewa, Dan wannan idanun nasa abinda suke fitarwa Yana Bata
tsoro.
______
Maganar canza lokacin aiki sukayi masa saboda wasu dalilai da suka saka za'ayi Masa aikin gobe Dan haka
suna iya shigowa sun fito da Baba Malam din daga investigation room din. Yana aje wayar Abubakar da
Habib suka shigo, tashi yayi Yana fada musu su shirya zasu wuce Asibiti gurin baba Malam Wai sun canza
ranar aikin gobe zasuyi Masa Ina ganin sun gano wani Abu daya zama dole aikin ya Zama emergency.
Cikin abinda Bai wuce minti talatin ba suka shiga Asibitin office din doctor suka nufa tunda ya bukaci ganin
mahmud saboda ze cike wasu forms ze Kuma yi signing a takardun da za'ayi aikin.
Basu Dade ba suka Gama da office din doctor suka nufi dakin da Baba Malam din yake.
Suna tafiya kawai Habib kallon mahmud yake ya rikide ya juye daga mahmud din Baba Malam ya koma
wani na daban Mai wani irin kwarjini da cikar Kamala ko Zama sukayi Hira irin ta da yanzu sai Habib yaji
baze iyaba sai fa mahmud ya matsa Masa sannan yake Dan sakewa, ga Abubakar wanda shine babban
guard dinsa Amma sukayi basaja ba Wanda ya gane, ga wani Karin abin mamakin Wai Bilyaminu ma yaran
mahmud ne.
Har suka karasa dakin yana ta faman tunanin abun.
Masha Allah ba karamin Dadi sukaji ba da ganin yanda jikin Baban yake.
Sallamar su ya amsa Yana sakin murmushi tamkar ba Mai lalura ba, gani ma sukayi har wani haske ya
Karayi duk da Daman farin mutum ne Shi, Yana kwance sandam da sauri mahmud ya Karasa kusa dashi
Yana fadin.
"Masha Allah! Baba jiki ya Fara kyau Alhamdulillahi, ya kaje jin jikin naka?".
"Alhamdulillahi Mahmud jiki ya Fara kyau ko yanda nakeji da banbanci akan kwana ukun baya, sannunku
da kokari Allah yayi Albarka yasa afi haka".
"Allahumma Amin".
Suka amsa su duka, Abubakar da Habib ne suka matso suna gaishe da shi da tambayar ya jikin nasa.
Ya amsa musu da sauki suma yayi musu godiyar dawainiyar da suketa faman yi dashi.
A Nan suka zauna har dare suna dauke Masa kewa mahmud ya cika Alkawari ya kirawo Bilyaminu video
call yace ya Kaiwa iya Abu zasuyi magana da Malam, taji dadin yanda taga jikin nasa Dan sun Jima suna
Hira har su mahmud sukaje suka Kara dubo Alhajin su Faisal.
Sai wurin goman dare na agogon kasar suka wuce daga asibitin, ba gida suka nufa ba, Abubakar ke driving
sai Habib dake zaune a gefensa sai Kuma oga kwata-kwata dake baya yana ta cinkunar wayarsa.
"Sir ina zamu Fara zuwa?"
Abubakar ya tambaya cikin ladabi.
Saida ya Gama duba results din club dinsa real Madrid, sunyi Wasa lokacin suna Asibiti shine yanzu yake
duba results din wasan.
"Wuce Africa Avenue kawai na gama ganawa dasu sai mu shiga Taj idan lokacin be Qure ba".
"Ok sir Leela palace kenan?".
"Eh a can nace musu zamu zauna"
"Ok."
Akalar motar ya canza daga hanyar da yake bi, shi dai Habib nasa ido ne Dan fadan da yafi karfinka sai ka
mayar dashi Wasa.
Ganawa ce mahmud din zeyi da managers na different companies dinsa ya Dade Basu hadu ba sai dai ta
Internet kawai, shine yayi amfani da wannan damar ya tarasu duk da yaso sai Nan gaba to wata kura ce ke
neman tasowa shine yayi musu Kiran gaggawa.
Habib yaso fita mahmud ya Hana shi, ba karamin abin al'jabi Habib ya gani ba yanda yaga manyan mutane
daga different countries suna Masa aiki a Nan Indian shifa har tsoro ya Fara kamashi waye Mahmud ne
Wai? Yanda yaji managers da Accountant suna bada lissafi saida jikinsa ya dauki tsuma, basu suka baro
Leela palace ba sai kusan Daya da rabi na dare.
Suna shiga gidan Mahmud ya wuce bedroom, requesting coffee kawai daga gurin Mr Ajey.
Su Habib dai sunci Abinci sannan suka wuce, kowa ya shige nasa, tun jiya aka hada dayan dakin Habib ya
koma ya barwa Abubakar wanda suka Fara sauka.
A gajiye mahmud ya shiga bedroom dinsa wayar da eyeglass din ya aje a Kan bedside ya wuce toilet.
Lokacin Daya fito Mr Ajey ya kawo masa coffee dinsa.
Saida ya saka pyjamas dinsa milk colour mai haske sannan ya zauna Yana sipping din coffee a hankali yana
Jin dadin yanda yake ratsa Masa makogwaro Yana gangarawa.
Kira ne ya shigo wayarsa yasan ba previous bace har ze share sai ya dauka ya duba Sameer ya gani.
"Sameer" ya ambaci sunan a fili sannan ya daga Kiran.
Daga can Sameer din ya Fara magana.
"Sir Naga sakonka, wallahi da kyar na samu visar madam yau Amma sai Monday zata taho in Sha Allah gara
nima dai na huta".
Ya fada Yana dariya.
"Au dariya ma kakeyi ko? wallahi idan tace na mayar dakai China da Zama Allah saika koma can,Kuma
Banda madam zaka tafi, sai bayan wata shida zaka ringa zuwa Kuna gaisawa shima sai ta amince, idan Bata
amince ba sai dai once in year".
"Tuba nakeyi gani nayi ka kasa hakurin rashinta a kusa da Kai tun yanzu to Yaya idan labarin yasha
banban"?".
Ya fada Yana dariya irin ta shakakikan friends.
"Allah ya shiryeka badai abinda zakaji Dan saka Ido kawai, ka aje komai jibi ka wuce Nigeria Kai da kanka
zaka kawota min ita Kano".
"Ok. In Sha Allah".
Sukayi sallama,wayar ya aje yana tunanin ko ya kirata ko Kuma ya kwanta ya huta.
** *** **
Barci sosai Zahra tayi Bata tashi ba sai kusan la'asar toilet ta shiga ta sake gyara jikinta.
Alhamdulillahi Abun ya Fara sauki sosai, amma dai ha lrokacin Yana Zuba over, Saida ta shirya ta nufo
parlour tana rike da wayarta, ba kowa a ciki sai kamshin turaren daki da tureren wuta.
A hankali ta ratsa ta nufi dining Abinci ta gani kala biyu coconut rice ce sai danbun shinkafa da yaji
vegetable a ciki, dambun ta Zuba kadan taci kadan ta tashi ta dawo parlour ta zauna. Aunty Hasana ta kiya
har sau biyu ba'a dauka ba saita tura mata text, Aunty Safiya ta Kirawo lokacin suna makaranta dalibai na
Exams, dauka tayi tana amsa sallamar zahra tana fadin.
"Kaga Mrs Dange, ya kanon?".
'yar dariya zahra tayi.
"Kaji dai Aunty Safiya, to Ina Azare Kuma kusa dake ma".
"Ahhh haba Dan Allah....!"
"Wallahi Ina layi na biyu bayan layinku".
Dan Jim Aunty Safiyar tayi tana tuna wani gida data gani lokacin da taje barka layin Wanda "yan layin suke
ce masa gidan Dan America, masu aikin ginin ne da wani ya tqmbayesu gidan waye sukace Mai gidan Yana
America shikenan suka sakawa Masa gidan Dan America.
"Kamar nasan gidan naje barkar haihuwa kwanaki baya Naga wani sabon gida akace mai shi baya kasar Ina
shine gamu Nan zamu shigo da Amatu in Sha Allah".
"A'a kice na tashi na shirya abin tarba, Ina jira, Dan Allah kuzo da wuri".
Bata kusa sai mommy ta dauka cikin ladabi zahra ta gaisheta mommyn ce tace Mata. "Ai kuwa Rukayya na
gidan Hajiyar makwarari dazu ta tafi ta manta wayar a gida garin sauri".
"To mommy Baki na Kira da layin Hajiyar na gode".
"To nagode Allah yayi Albarka, ya wajen Mai jikin Kuma Sameer yace sun wuce indai ko".
"Eh suna can da sauki".
"Allah ya bashi lafiya yasa ayi aikin a sa'a".
"Allahumma Amin nagode".
Sukayi sallama.
Akalar Kiran ta juya ga Hajiyar makwarari cikin sa'a wayar na hannunta ta Gama amsa wani Dan uwanta
Malam na Dala Kiran zahra ya shigo.
Dauka tayi tana fadin,
"Salamu Alaikum, waye yake Kira?".
"W/slm, Hajiya nice zahra".
Dan Jim tayi tana tuna Ina tasan muryar Nan.
"Zahra wace ce kenan? Ko Zahara,un Hajiya Fateen lalloki?".
"A'a ba ita bace".
Sai zahra ta rasa me zata ce Mata ne, tace zahrar mahmud abokon Sameer, sai taji da nauyi ta fada Mata
haka.
Rukayya ce ta shigo da cup din kunun tsamiya data damawa Hajiyar a hannunta.
"Wa Kika Sami haka naji kina ambatar zahrar lalloki".
"Ungo kiji ko wacece tayi shiru batayi min bayani ba ke kiji ko zata fada Miki".
Wayar Rukayya ta karba tana mikawa Hajiyar kunun a cup.
"Aunty Rukayya".
Zahra ta Kira sunanta.
Take ta dauki muryar zahrar.
"Au kice min amaryar big bro ce ai bayani Zaki yiwa Hajjaju, kince zahra Ina zata gane".
"Hajiya matar Ya Mahmud ce mutuniyar ki da Kika Gama maganarta dazu to gata 'yar halak ta kiraki".
"Ga Hajiyar ku Gama gaisawa Dan ba barina zatayi muyi hirar kirki ba idan Baku gaisa ba tunda nazo take
you min zancenki".
Wayar ta mayar Mata ta nemi guri ta zauna.
" 'yar Nan Daman kece ki kak'i yi min bayani dan Ashatta".
Gaishe da Hajiyar tayi tana fadin.
"Cewa nake Zaki ganeni fa, Daman kiranki nayi na gaisheki Kuma na fada Miki ciwon Nan na cikina ya narke
yanzu babu shi".
Wata zabura Hajiya tayi kamar yarinya tana fadin. "Kai Masha Allah kice nayo shiri na taho Azare na kawo
Mik wani maganin saboda bibiko da Kuma aasske- sassake saboda sanyin dake Hana Yara haihuwa kinsan
yanzu kuma sai a Fara shirye-shiyen haihuwa Kwana kadan ai sai laulayi, Dan ma naji labari mijin naki ya
Kara yin halin nasa ya fice daga kasar wallahi sai kin jajirce kin zamar masa karfen kafa sannan zakiji dadin
aure, Amma Kika zauna sanyin Nan sai kinyi tsa-tsa a banza Naga shi matan ma basa gabansa ta Neman
kudinsa kawai yake, Kullum mutum na sama kamar tsuntsu to kinji dai na fada Miki".
Baki bude Rukayya ke kallon Hajiyar.
MAMAN FATEEMAH.
Page 65
A nutse Amatullah ke driving dinsu, taso ta wuce gida saboda ta gaji sosai Amma jin zahra na garin Kuma
babu nisa da gidan yayar mamanta da take zaune a hannunta sai kawai tayi waya ta fada Mata zasuje
unguwa.
Tunda suka shigo layin Amatu ke Kakabin gidan tana fadin.
"Kambala'i wannan Kuma waye yayi one in town din Nan? lallai Aunty Safiya unguwar taku ta masu ido da
kwalli ce".
Murmushi tayi mata tana kokarin Kiran waya.
"Mun shigo ki turo a shiga damu".
Dan saurare tayi kafin tace.
"Ok muna jira".
Ta sauke wayar daga kunnenta.
"Kika ce menene?".
"Cewa nayi unguwar taku ta Zama ta masu Ido da kwalli".
"Bakiji ranar nan muna maganar layin Dan America ba? To ai gidan ne ake cewa gidan dan America".
Labarin yanda gidan ya Sami suna ta Bata.
Dai dai suna zuwa kofar katafaren gate din gidan.
"Dan tsaya a Nan mu jira muga ta Ina zata bullo Mai kaimu gidan".
Amma ita Safiyar ta hakikance matukar da gaske MAHMUD DANGEN ne da gaske mijin Zahra to babu ko
tantamar wannan gidansa ne.
Saka aya a tunaninta da bude Karamar kofar gate din ya Zama lokaci Daya.
Zilai Mai aikin gidansu zahra Amatu ta gani ta fito, zaro Ido tayi tana kallon Aunty Safiya.
Gyada Mata Kai tayi kawai, sannan ta bude kofar ta fito.
Gaisawa sukayi da Aunty zilan, sannan tace Mata.
"Ko kune Bakin Uwar dakina Zahra".
"Eh mune".
Aunty zilan juyawa tayi da sauri ta koma ta fadawa zayyan zahra tayi Baki.
Jim yayi Yana kallonta kafin ya samu zarafin fadin.
"Yallabai fa ya kafa dokar kada nabar kowa ya shigo gidan nan, Amma Bari na fada Masa duk da nasan ba
wadanda yake nufi bane.
Tana tsaye ya Kira Mahmud cikin sa'a ya sameshi, tun kafin ya fada masa wani Abu yace masa.
"I sw everything, just open the door".
Kawai ya katse Kiran Dan yana bibiyar gidan ne tun lokacin da yaga ta saka ayi wani girkin, Dan har a
kitchen Saida aka saka CCTV.
Gate din zayyan ya bude musu suka shigo, parking lot Amatu ta aje motar suka fito zilai tayi musu jagaba.
Amatu sai raba Ido take Dan wallahi gidan ya tafi da imaninta ba kadan ba.
Suna shiga zahra tayo wani tsalle tana fadin
.
*Wayyo Allah oyoyo! oyoyo!! Sannu da zuwan ku Amatu, Aunty safiya nagode da Kika kawo min Amah
wallahi Daman Ina nemanta.
Dan ja Baya Amatun rayi tana fadin.
"Ni ba gurinki nazo ba Aunty safiya na rako".
Hannunta zahra ta riko tana fadin.
"Haba my bestie kiyi hakuri Dan Allah na tuba kowane laifi nayj kada a tona"..
. dariya sukayi su duka, Ammatu dai 'yar kauye ta zama Dan Saida ta tada Kai taga yanda saman dakin yake
kamar sararin samaniya Dan harda taurari da wata.
Dauko wancan kawo wannan zahra da Aunty suka shiga yi, sai murna zahra keyi na ganinsu, sunci sun Sha
sannan suka Dora da hira har aka Kira sallar magariba hirar yaushe gamo akeyi, cikin hirar ne Zahra ke fadin
"Wai da gaske kinsan Mahmud?"
Zama ta gyara tana fadin.
"Wallahi ba karya har gidansu na sani sai dai shi nasan be sanni ba". Daga Nan ta tsaya itama Zahra Bata
zafafa ba taja bakinta tayi shiru.
Dakin kusa dana Aunty zilai zahra ta kaisu sukayi alwala, har Amatu zata Fara sallah ta tsaya ta dubi zahra.
"Ya Naga ke Baki tashi kinyo alwalar ba".
"To sa'i'dawa Ina ruwanki".
Gurin zahra Amatun dawo ta zauna a gefen gadon in da zahra ke zaune.
"Zahra Wai ya haka, ko dai planning kikeyi ne? Amma ace har yanzu babu wani labari, Ni da naganki kinyi
wani sirrin kyau nayi zaton ko an Mana ajiya ne? Kuma kice Wai bakya sallah".
Dariya zahra tayi tana Fadin.
"Cikin lafiya? Ai ni ban isa haihuwa ba".
Wata malalaciyar dariya Amatullah tayi.
"Kice min 'yar yaye aka kawo masa, Wai Ina yallaban? Ko yana ciki kin Hana shi fita Dan Naga yanda Kika
cika din Nan nasan baya Wasa gurin zagaya gonarsa tunda ga yabanya Nan tayi kyau da gani ana samun
ban Ruwa akai akai".
Ta fada tana Kara wata dariyar.
"Wallahi Amah ki daina wannan dabi'ar Baki da magana saita wannan sabgar Kinga fita ta, Ni idona da
sauran kunya a cikinsa Banda tsabar jaraba a gaban Aunty safiyar kike fadar irin wanna magana, Dan
tsabar gulma da kinibibi kinyi alwala Amma Kika zauna Zaki Fara zancen da ze karya Miki ita, wallahi mijinki
yaga ta Kansa irin ku ne maza suke guduwa daga gida saboda halinku".
Tana Gama fada ta Mike ta fice, wayar ta aje a Kan gadon.
Daukan wayar Amatullah tayi tana juyawa, ba karamin mamaki tayi ba da ganin wayar dake hannun Zahra.
"Wai ba zakiyi sallar ba kema Naga da alama ma kin Manta zakiyi sallar in dai lamarin gidan Nan ne bakiga
kamai ba, I'm telling you in dai 'yan wannan family din ne, kinsan Allah duk wannan Wasa ne ko ita kanta
Mai gayya Mai aikin Batasan wa take Aure ba, kin manta na fada Miki indai shine baze iya rayuwa da
matarsa a wancen gidan ba?".
Kai Amatullah ta gyada alamar haka ne, Bata iya tofa wata maganar ba saboda shigowar zahra.
"Au bakiyi sallar ba kenan? Gaskiya kina Wasa da sallah".
"Kema dai Kya fada Mata, gashi na baro baby na Dan ma tana cin Abinci shi yasa Honey Bai takura min da
Kira ba, suna cikin gari duka gidan Baba Dan lawan".
Tashi Amatullah tayi ta tayar da sallah.
Basu suka bar gidan ba sai bayan insha'i Shima Saida mijin Aunty safiyar ya Kira Dan bayan sunyi sallar
babin karatu Aunty safiyar ta budewa zahrar Dan idan ta Fadi wani abun rufe Ido zahrar takeyi Amah na
Mata tsinyar Wai muna furcine idan suka shige other room wata Kila ita ke Jan sitiyarin motar ai tasan ba'a
banza ba tayi irin wannan cikowar tasan ta gane garin.
Sai a Nan Zahrar ke fada musu mahmud din ma baya kasar Yana India an Kai malaminsu Asibiti ya samu
matsala a bayansa. Sun jajanta sosai, mayuka da turaruka Zahra ta basu, Aunty safiyar tayi mata Alkawarin
kawo Mata wasu kayan Mata dasu tureren mara Mai fitar da oga daga hayyacinsa duk iya yanda ya Kai ga
kame bakinsa, Amma Bata fada Mata hakan ba tasan halin kayanta sai taki amfani dashi.
Har gurin mota zahra da Aunty zilai suka rakosu, bayqn sun tafi ciki Zahra ta wuce wanka takeso Dan ki
take kamar ya Bata Mata jiki.
Basu Dade suna Hira ba Zahra taga Aunty zilai tana hamma sai tace Mata taje ta kwanta kawai tasan har
yanzu da sauran ramuwar barcin a idonta.
*********
Tun karfe shida na safe Mahmud ya wuce asibitin shida Mr salahuddeen, Saida ya jira doctor din yafi son
ya Gama da doctor din kafin yaje gurin Baba malam misalin bakwai da rabi doctor ya shigo office dinsa be
Jima da shiga ba mahmud ya shiga suka gaisa da yarensu na indianci, sannan yayi Masa bayanin yanzu
takwas dai-dai zasu shiga dashi suna tunanin zasu dauki awa goma Sha biyu suna aikin Dan ma lakkar Bata
tsinke ba. sallama sukayi ya nufi dakin da Baba malam din yake.
Lokacin da suka shiga har an shirya Baba malam cikin Kayan aiki.
Murmushi ya fara yi da yaga mahmud ya shigo.
Da sauri Shima ya nufe shi Bai taba jin karaya ba irin ta yau daya ganshi kwance sandam babu inda yake
motsawa daga kugunsa zuwa kafarsa.
"Sannunka jarimin namiji, ubangiji yayi Albarka Mahmud ko yanzu Allah ya bani abunda bani dashi da
namiji, kayi min komai Babu abinda zance maka sai godiya, idan Allah yasa na tashi falillahil hamdu idan
Kuma lokacin komawar yayi to muna rokon Allah yasa mu cika da imani, ga Zainabu Nan Dan Allah a kula
da ita, ga Kuma makaranta Nan Daman yanzu ni suna ne kawai na me makaranta, Amma kune ke
dawainiya da ita, to kada a kasa ko bayan Mana Nan bamu San abinda ubangiji ke nufi da kawoka gurinmu
ba shiya barwa Kansa sani, a kula da ibada da Kuma riko da gaskiya, Mai gaskiya baya tab'ewa kayi duk Mai
yuwuwa ka koma mahaifarka Dan girman Allah a rage fushi kaji mahmud bashi da kyau ko alama ka Zama
Mai yafiya kaima Allah ya yqfe maka kaji, Nima ka yafe min Zaman da mukayi Kona saba maka, Kuma ka
rokarmin sauran jama'ar da muka zauna dasu Suma a fada musu na yafewa kowa Nima su yafe min, Abu
na karshen da Zan fada maka ga yarinyar nan kaji tsoron Allah a Cikin lamarin ta nasha yin istikhara Ina
ganinka a Cikin wata irin wadata Wadda na kan samu kaina da tunanin abun to duk yanda rayuwa ta juya
ka kula da Amana ta Fadima marainiyar Allah ce".
Tunda Baba malam ya Fara Masa wannan magqngaun masu Kama da wasiyya jikinsa ke tsuma daga ciki
Yana ta faman rokon Allah akan ya rufa Masa asiri kada bawan Allahn nan aikin ya Zama sanadinsa.
"Idon jajur da gani kukan zuci yake ya Kara rike hannun Malam.
"Baba in Sha Allah lafiya za'ayi aikin nan a Gama Kuma ka warke in Sha Allah saika taka da kafarka ka
zagaya Asibitin Nan Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w, Allah ya baka lafiya yasa kaffara ne ya bada nasarar
aikin da za'ayi, ai sunce babu wata matsala Mai yawa dama mun zauna a Nigeria anyi aikin".
Kafin Baba malam ya fadi abinda yayi niyya ma'aikatan da zasu tafi dashi sun shigo da gadon da zasu tura
shi zuwa theater room din, lokacin da zasu canza Masa gado ya ringa fadin.
"Wash!!! Allah kuyi a hankali bayana bana son ana motsani" .
Da sauri Mahmud ya karaso Yana musu magana da yarensu, da sauri suka mayar dashi suka fita.
Sannu kawai mahmud ke jerawa Baba malam Nan da Nan jibi ya rufe shi.
Kusan mutum bakwai suka shigo suka hadu aka Dora shi a gadon sannan suka tura shi a hankali suka fice
daga dakin mahmud na biye dasu, har kofar karshe mahmud ya raka baba Malam Bai tsaya ba saboda
dauriya kawai yakeyi Amma Yana Daf da zubar da hawaye.
Guri ya nema ya zauna Yana kallon yanda manyan doctors manya da kananu suke Kai kawo kafin time ya
cika suka rufe kofar.
Yana Nan zaune har kusan one hour sannan Kiran Habib ya shigo Masa.
Cikin dari dari Habib ya Fara fadin.
"Yallabai ya maganar zuwa Asibitin ne munji shiru baka fito ba tun bayan da muka dawo daga sallar
Asuba".
Tsaki mahmud yayi dama duk ransa ba dadi ga wani sabon salon da Habib ta tarka Wai yallabai.
"Wallahi ka Kara kirana da wani yallabai sai munyi uwar watsi a kasar nan da Kai,ba dai ba barci kuzoyi ba
sai kuyi tayi, yanzu Baba malam ya samu good one hour a dakin tiyata, zaka wani ce min maganar
Asibiti,kaima wallahi inaga saina kaika Inda zaka Kwana a tsaye kana aiki ko Abinci sai dai kaci a tsaitsaye
sannan zaka fashinci namiji Allah yayi ka, ka fadawa dayan ya kawo ku yanzu Ni tun shida Ina nan".
Ya yanke Kiran ya dafe goshinsa da yake Sara Masa.
* *
Karfe bakwai da rabi dai dai Mai a dai daita ya sauke Salma a kofar katafaren gate din gidansu,kudin dake
hannunta ta Mika Masa ta wuce da sauri ta shige ciki, ba kowa a harabar gidan ko Mai gadi ma ya shiga
sallar insha'i.
Wuf tayi ta shige part din Mama cikin sa'a babu kowa a cikin parlourn directly master bedroom dinta ta
wuce, can ta hango Mama ta Zuba tagumi tana zaune duk tayi zumu ba wannan gayun da kwalisa, tunda ta
rasa tudun dafawa a Kan sakon da za'a kaiwa Zahra ta shiga halin ha'ula'i tunda Saida aka gindaya mata
sharadi ta amince gashi kuma kwabarta na neman yin Ruwa.
Ganin shigowar Salma ko sallama babu yasa Mama ta wani zabura ta taso tana fadin.
" Ke!!! Salma lafiya? Daga Ina kike da wannan tsohon daren? Ina Hameeda Kuma?".
Zama tayi a gefen gado tana sadda Kai kasa tayi shiru.
"Wai ba magana nake Miki ba Dan ubanki kin mayar Dani banza".
Kuka ta fasa Mata Mai cin Rai, Wanda ya firgita 'yar sauran nutsuwar Mama.
Naman Fateemah
Page 66.
........... Ai kukan da Salma ta fasa sai ya Zama kamar rura wutar bala'i akayi a zuciyar Mama, nan da nan
tayo Kan Salma da manya manyan zagi kamar diyar maguzawa.
"Kukan uban me ki kazo Kika sakani gaba kina mini ko wata jaraba Kika kwaso min Ina zaman zamana".
Ita dai kukanta take ba kakkautawa.
"Wallahi Zan Miki dukan bala'i yanzun nan dan kin raina ni sai ki sakani gaba kina min kukan babu gaira
babu dalili".
"Na shiga uku mama ciki ne daniiiiii...."
Ai ita kanta mamar batasan yanda akayi ta doro gaban Salma ba jikinta kamar ana kada Mata gangi sai
mazari take tamkar Wadda jaura tabi ta kanta, wata irin Shaka ta kaiwa Salma tana fadin.
"Wallahi gara na kasheki na huta da inga wannan bakin cikin".
Kakari Salma ta Kama nan da nan idanunta suka firfito daman ga jiki ba kwari Kullum Zazzabi.
Cikin Rahamar Allah Hamza ya shigo daman ita ta aike shi tace Idan ya dawo ya shigo tana ciki ya kawo
mata, badan haka ba zati iya yiwa Salma mummunan lahani.
Da sauri ya nufo Mama Yana fadin.
"Mama Lafiyar ki kuwa? Me tayi Miki haka? Yaushe ma tazo garin? Meta kawota?".
Lokaci Daya ya shiga Jero Mata wadannan tambayoyin.
Ganin kamar Bata cikin hankalinta yasa shi saka karfi ya banbare hannun Mama daga wuyan Salma.
Faduwa tayi sharab a sume Nan da Nan hankalin Hamza ya tashi da gudu ya fita kitchen ya dauko ruwa Mai
sanyi ya kwara mata, ya Kara Zuba Mata sannan ta kawo numfashi a wahale, har lokacin jikin mama Bari
yake, kamata Hamza yayi ya zaunar yana tambayarta meya faru zata dauki doka a hannunta kome Salma
tayi Mata ai bazayi Mata irin wannan danyan aikin ba da Allah baisa yazo ba da Allah kadai yasan abinda ze
faru kenan.
Kuka ta fasa Masa tana fadin.
"Wallahi gara ta mutu da wannan abun kunyar data dauko mini, yanzu ina Zan saka kaina Ni Rabi'a shike
nan duk wata fuffuka ta Kuma ta Kare a gidan nan kin tozartani kin wulakantani".
Ta saki wani gunjin kuka.
"Wai nifa har yanzu Baki fada min me tayi Miki ba Ni wannan zancen ba gane shi nakeyi ba fa".
Ido jazur Mama ta dago ta kalli Hamza.
"Cikin shege jake tayo a makaranta"..
Hamza jin maganar yayi tamkar saukar aradu a Cikin Kansa.
"Cikin shege Kuma how comes?"
Ya fada yana kallo Salma Wadda ke fidda numfashi da kyar ga ruwan hawaye tamkar an bude lataccen
famfo.
"Bazakiyi magana ba Saina Ida aikin da Mama ta fara?".
Cikin galabaitacciyar murya Salma tace wallahi Ya Hamza Nima bansani ba lokacin da naje Jos ne Ya
Mukarram din Mama Ladi yace nazo na rakashi duba abokinsa a Asibiti da mukaje Asibitin bamu ganshi ba
shine ya kirawosa a waya yace ai suna gida tun safe shine yace muje ya duba shi tunda ya riga ya sayi kayan
dubiya, da mukaje gidan bamu samu kowa ba Daya kirasa a waya sai yace mu zauna yaje allura ne chemist,
shine muka shiga mun Dade sosai baizo ba sai Ya Mukarram din ya Ciro Mana freshyo biyu yace musha
tunda ko ruwa babu a gidan, wallahi daga lokacin Dana Sha zuwa yin barcina baifi minti biyar ba daga nan
wallahi bansan meya faru ba sai tashi nayi na ganni a wani yanayin Yana ta bani hakuri Wai aikin shedan
ne".
Ta karasa tana sakin wani kuka.
Dafe Kai yayi ya tafi taga-taga ya zauna a Kan sofar dake dakin.
"Innailaihi wa innailaihi raji'un, wannan wace irin masifa ce? Shi yasa har Raina bana son zuwan da sukeyi
Jos din Nan saboda gudun irin haka yanzu Dan Allah wa gari ya waya? Kin lalata future dinki totally Baki da
sauran wata Qima ta Diya mace kin Bata record dinki har jikan jika wallahi".
Yayi tsaki ya tashi har ya Kai bakin kofa ze bar dakin Dan idan ya tsaya saiya yi Mata fiye Dana mamar,
ganin idan ya fita ba tare ta yiwa tubkar hanci ba ze iya zuwa ya Kira abbansu ya fada masa.
"Kai dawo ka zauna zanyi magana da Kai"
Ba musu ya dawo ya zauna yana bin Salma da Ido wadda ta takure guri Daya tana sauke numfashi kadan-
kadan.
"Kanaji ba wannan maganar ta tsaya iyakacin mu ukun Nan idan najita ko a bakin Abban mu ban yafe
maka wallahi Dan fasa maganar Nan tamkar ka dauko wuka ne ka dabi min a cikina kaji abinda na fada ko?
yanzu idan an fito sallar asuba kazo ki wuce Jos ka kaita gidan murja Zan shigo Nima zata fito ta kofar baya
sai ka dauketa bana son wani yasan da zuwanta gidan nan".
Sadda Kai kasa yayi yana nazarin maganganunta.
Kada Abba yaji me kenan? Tana nufin baza'a fada Masa yasan halin da ake ciki ba ko me?.
Take ya aro jarumta ya yafa, ta tako ya shigo ciki sosai sannan ya zauna Inda ya tashi.
"Yanzu Mama menene hikimar hanawa a fada Masa wannan ba Karamar magana bace fa kiyi tunani
Mana".
zaburo Masa tayi tana zare masa manyan idanunta
"Wallahi naji maganar Nan sai ranka yayi bacin da Bai taba yiba yanda nace haka za'ayi, tashi ka bani guri
Wanda baya kishin 'yan uwansa yanzu kai ko cewa nayi kaje ka fada ai ka nuna ba haka ba abun ya Zama
sirri".
Tashi ka bani wuri saura Kuma ka Bari wannan munafikin Mai gadin yaga salmar ya fadawa Abbanku ka
dauki motarka ita ce me glass Mai duhu".
tana Gama fada ta tashi ta nufi toilet tana zabgawa Salma harara.
*****
Cikin lafiyayyan Turkish bed Zahra ce kwance tayi lif a Cikin blanket sanyi da kamshi freshner suna ratsata,
a hankali ta dauko wayarta tayi dialing number dinsa harta tsinke ba'a daga ba. Kiran ta sake Nan ma the
same thing, sai taji hankalinta ya tashi ta tashi zaune ta kunna wutar dakin ta zuro kafafaunta kasa tana
Kara Kiransa.
Tana kokarin Kara Kiran nasa Kiran ya shigo.
"Alhamdulillahi"
Ta fada a hankali tana sauke numfashi sannan ta daga Kiran.
"Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu".
Ta fada Yana gyara zamanta, sallamar ya amsa Mata a kasalance sai taji hankalinta ya tashi ba haka ya Saba
Mata ba.
Meu Amor, meya faru? naji kamar baka cikin mood me Dadi pls menene? Dan Allah fada min ko jikin Baba
Malam din ne?"
Saida ya danja fasali kafin yace mata.
"Precious Ina cikin damuwa sun shiga da Baba Malam za'ayi Masa aikin sunce twelve hours Amma har
yanzu fourteen hours ba'a fito dashi ba, ba kuma wani information da muka samu sai dai shige da fice da
yayi yawa a dakin mun tambaya sunce babu wata damuwa suna Kan aikin ne,Kinga ta Ina Zan same peace
of mind ne?".
"Au yau ne Daman za'ayi aikin da ba cewa sukayi sai wurin jibi zasuyi ba?".
"To ai da abinda suka gani ne shi yasa suka rage kwanakin aikin".
"Allah ya bashi lafiya,dan Allah kada kayi abinda ze karya masa gwiwa, you have to be very strong fa, ka
ringa bashi courage akan ze tashi".
"To ki tayani addu'a yanda na kawo shi Allah ya taimakani na maido shi gida lafiya, preciousss.. Baba
Malam ya karya min zuciya da yawa, nayi rashinki kusa dani nasan da kina kusa dani ko dumin jikinki kadai
ya Isa ya saka min nutsuwa bare nasan za'a taimaka min ai ko?"
Ya fada da wata murya Wadda ta motsata.
"Kaiiii... Meu amor pls ba kyau fa".
"Meye ba kyau din? Lallai nayi sake da yawa fa yanzu da kina dauke da babyn mu da baki Fadi wannan
maganar ba, yarinya ki shirya soon komai ze daidaita, ai kin gane?".
Shiru tayi masa.
"Oya Yi magana Mana".
"Me kake son na fada...?".
Komai ma ki fada min Ina so?"
Bata Kara tanka Masa ba,yayi nacinsa ya hakura, "kina jina"
"Eh..." ta amsa masa.
"Gobe in Sha Allah kije gidan Ammah kiyi Mata yini sai ku dawo gida,inaga Sameer zezo kuje kano".
Dan Jim tayi kafin tace "
"Plssss... Dan Allah meu amor ka barni na Kwana a gurinta Ina so naji duminta?".
"Ban fahimta ba? Kamar Yaya kiji duminta? Goyaki zatayi?". Ya jefa Mata tambayar. Jin tayi shiru ya sake
cewa
"Baki da damuwa akan wannan ki Bari kizo sai kiji Mai dalili, Amma dai maganar Kwana babu ita".
"Plssss... Dan Allah fa".
"Ok zuwan ma a hakura bazaki sakani a tension ba bayan Wanda nake ciki, wallahi idan na barki Kika
Kwana ai ko barcin kirki Bazan iya ba kinsan riskyn dake cikin zamanki a gidan kuwa?".
Mahmud na yanke Kiran ana fitowa da Baba Malam, a kalla ya samu good fifteen hours, da dan sassarfa
yabi bayansu, wani bangare suka nufa dashi nan ma VIP section ne dakin harya fi wancan tsari da komai
tamkar gida, Saida suka kwantar dashi suka kara karfin A/C sannan suka Fara yiwa mahmud bayanin yanda
ya kamata a ringa yi masa sannan ze dauki kaman thirty days a haka ba tare da an daga shi ba ko
kwakwkwaran motsi.sannan suka fice daga dakin, zuwa yayi ya saka shi a gaba yana jinjina Lamarin
ubangiji, tsoron Allah ya Kara shigarsa ganin yanda Dan talikin Nan ya Zama sai yanda akayi dashi, idan ma
fa da kwanan ya Kare shikenan, wani Abu ya gani kamar rigar roba an saka Masa a kirji ga wasu Abubuwan
a kugu Suma Yana kwance baya ko motsi Nan da Nan yaji hawaye sun cika masa Idanu, Rabon da yayi kuka
harya manta duk cimadadin da aka Sha a baya Bai taba zubar da hawaye ba, amma yau dai zuciyar ta
karye, ya godewa Allah da yasa su Habib basa Nan ya sender su gida tunda yaga Hankalin Habib ya tashi
ganin lokacin da aka ambata ya wuce da awa daya ya shiga rudu,Saida mahmud yayi masa fada sosai
sannan yadan Sami nutsuwa ganin hankalinsa ya kasa kwanciya yasa dole suka bar Asibitin.
Saida mahmud yayi kukansa sannan yaji Dan dama-dama, shi duk Lamarin rayuwa ya kwance Masa daga
kansa, Bai taba jin abinda yayi Bai kyauta ba sai yau yayi Dana sani yafi sau shurin masaki, wani irin fushi
yayi Wanda ba ragin daka sai da ya shafi kowa, a nan ya yanke hukuncin Kwana duk da lokacin Sha daya ne
na dare Amma sai yaji ko Nan da can baze iya matsawa yabar Baba Malam a haka ba Yana fatan idan Allah
ya nufi ya farka to ya Fara arba dashi a gabansa, tunanin Amminsa Yana damunsa kwanan nan idan da
Wanda yake ganin ya batawa Bai wuce ita ba duk rintsi ai uwa-uwa ce amma sai itama ya hada yayi musu
kudin goro, duk da yasan shirunta kusan shiya kawo Karin lalacewar abun Amma dai dole yaje kada
alhakinta ya Fara Kama shi fa.
Kiran wayar Abubakar yayi, lokacin suna zaune a parlour tun dawowarsu yake faman bawa Habib Baki akan
ya dangana yayi Masa Addu'a.
"Bazaka gane bane Abubakar nifa Baba Malam na sani a matsayin uwa da uba duka duk wani gata na
duniyar Nan babu Wanda bai min ba, dole na shiga tashin hankali Mana idan ya mutu Yaya zanyi?".
Sosai ya bawa Abubakar tausayi.
Yana kokarin hada kalaman da zeyi amfani dasu gurin nuna Masa abinda ya kamata sai Kiran mahmud ya
shigo.
Da sauri Habib ya dago Yana kallon Abubakar.
"Shi...ne yaaa kiii..ra ka ko?".
Ya Fadi maganar a rarrabe kamar sabon Dan koyon Karatun hausa.
Gyada Masa Kai yayi Yana amsa Wayar.
"Yes sir, to shikenan Allah ya bashi lafiya, eh gani nan"
Ya fada Yana mikawa Habib wayar.
"My man ka samu nutsuwa kaji, sun fito dashi tun dazu anyi aikin cikin nasara in Sha Allah".
Wata irin nutsuwa ta shigi Habib, Alhamdulillahi kawai yake fa.
Bayan anyone sallar Asuba Abba ya shigo ya samu Ammah ta Idar da sallah tana ninke hijabin,
"sannu da dawowa"
Ta fada sannan ta gaishe shi.
"Yau fa barci nakeson yi sosai da safen Nan saboda na zaunu a mota yanayin hazo ya hana jirgi tashi kwata-
kwata, ko Zaki tayani barcin tunda kin kawoni gurin da babu Mai takura Miki ki dama daddawarki da moda
babu Mai gani, Au Kinga Zan manta danki dai ya kasa hakuri matarsa yake so, d
Jiya ya kirani muna hanya yace an shiga da baba Malam aiki, sannan yace min yau Zahra zatazo ta wuni a
gurinki gobe su wuce kano zata bishi India din, Amma bana Jin ya fada Mata, na fada Miki dai Koda abinda
zakiyi Mata"
Gyaran murya Ammah tayi tana fadin.
"Yanzu Abban Yara bazaka bincko Mana asalin yaron Nan ba kadafa ya gudar mini da 'ya saboda Allah".
"Kai haba Asma'u ki cire wannan tunanin daga zuciyar ma Mahmud Dan mafita ne Ina nan Ina bincken
menene musabbabin abinda ya rabo shi da gida dole akwai dalilin dayasa ya baro komai nasa ya taho yayi
irin wannan rayuwar".
"Ban gane ba Abban Yara kayi min bayanin da Zan gane".
Dan tunani yayi kadan kafin yace Mata.
"Ki kwantar da hankalinki mahmud ba boyayye bane Dan cikin.garin sokoto ne a yanda aka fada mini
nasan mahaifinsa farin sani, sai dai har yanzu ban Gama yarda da shine mahaifinsa ba duk da tun ganina
na farko dashi Naga nasan fuskar amma na rasa Inda nasanta Saida aka fada min mahaifinsa Naga tabbas
fuskarsa nake gani ata mahmud, Dan haka ki kwantar da hankalinki in Sha Allah uwata saita Zama farin
wata Sha kallo duk bacin ran da aka shiga sai ance gara da hakan ta faru ki bani lokaci harna karasa nawa
binciken kinje".
Ya fada yana Dan murmushinsu na manya.
"To shi kenan Allah ya rufa asiri, nagode da kulawar ka garemu".
"Kada ki Kara yi min godiya akan al'amarin uwata yiwa Kaine Nina bada aurenta ga wannan yaro hakki
nane ba binciko komar daya dangance shi, sai daga baya muka fashinci gidan ne baya muradin komawa
yasa yace ya manta komai na rayuwarsa ta baya sai yanzu nake tunano maganar da mukayi ta saka hotonsa
a kafafen sada zumunta na zamani ko za'a dace da wadanda suka sanshi amma kinsan yaron nan cewa yayi
a''a ayi hakuri a hankali wata Rana ze tuna".
"Au haka kukayi baka fada min ba da wallahi sai ya kawo danginsa sannan za'a bashi ita".
Ta fada tana mokewa.
"Hannunta ya kamo.
Ki dawo ki tayani barcin Mana.
Ba musu ta dawo suka kwanta itama barcin take ji dan Shima Abban ba Sanya ga Ammar mu da daukar
gyara.
Karfe tara me kyau su zahra suka dira a famfon shanu, Aunty zilai ce ta dauko baskets guda biyu da Daya na
Ammah dayan kuma na Abba ne?
Suna shiga parlourn ba kowa sai buruntun Alawiyya a kitchen, Jin shigowar mutane yasa Alawiyya fitowa.
"Lah sannunku da Zuwa. "Ina Kwanan ku? Ta fada tana karbar ledar hannun Aunty.
"Kawo na Kai ciki"...
Alawiyya ta fada tana fadin sannu da kokari.
Maman Fateemah
Page. 67.
...….........
A nan parlour zahra ta zauna suna kwasar hira da Alawiyya saboda itama 'yar shafta ce ta gaske, suna nan
magaji ya shigo yana ganin zahra ya karaso da sauri yana fadin.
"Kai! A gidan nan kika kwana amma?".
"Eh mana da kana tunanin na sallama maka Ammar ne kai kadai? Nima ina son naji dumin uwata".
Wata dariya ya saki yana fadin.
"Naga wannan Allah yasa Ya mahmud ya daukeki ku tafi wata uwa duniya sai naga ta biniyar gida naga
alama irin kune matan da idan kuna cikin garinku kuke raba dai dan zama rabi kuma gidan miji rabi kuna
gidan iyayenku bare idan kun raina miji".
Maganar Ammah sukaji ba wanda yaji shigowarta ta sha gayu sai zuba kamshi takeyi sam ba zakace su
Aunty Hasana 'ya'yanta bane.
"Magaji wallahi ka fita daga idona wai me zahra ta tsare maka ne? Naga alama mun kusa saka kafar wando
daya da kai a gidan nan".
Duka suka juya suna kallon Ammah, zahra ce ta tashi ta nufi Ammah tana fadin.
"Rabu dashi Ammah wallahi duk bashi yake ci akwai ranar biya".
Dariya su Aunty zilai sukayi suna gaishe da Ammar itama zahra gaishe da Ammar tayi suna zama zahra ta
shige jikinta.
"Wallahi kiji tsaron Allah magidanciya dake ki tsaya kina zuba tabara dan tsabar samun guri".
"Nayi din, idan fitsari banza ne kazama tayi mana, kaida wannan cinyar sai gani sai hange".
Ta fada tana gyara kanta dake jikin kafadar Ammah.
Zilai ce ta dauko basket daya da leda sai kuma Alawiyya ma ta sauko sauran suka kawo gaban Ammah zilan
na fadin.
"Ammah gashi wannan na Abban uwar dakina ne sauran kuma naki ne".
"Masha Allah Allah yayi albarka, kwana kukayi kuna wannan aikin ne?".
"A'a ko daya tun asuba dai muka fara kinsan uwar dakin tawa babu abinda ta aje a halinki Ammah tasan
kanta".
Da sauri magaji ya matso yana kokarin bude warmers din yana fadin bari mu gani nasan duk abinda ya fito
daga wadannan masu two face din unique ne".
Dan murmushi tayi Ammar tana son zama dasu sauda yawa saboda ko bacin rai take sai taji ta samu farin
ciki tamkar Tom & Jerry haka suke.
Aunty zilan sallama ta yiwa Ammah da zahra tace zataje gida, har taje kofa Ammah ta kirata, tashi Ammar
tayi ta nufi bedroom dinta ganin haka yasa zilan bin bayanta, itama zahra dakin data mayar nata ta tashi ta
shige dan barci takeji bana sosai, tana jin magaji wanda ya cika baki da gas meat daya diba a plate yana
fadin.
"Dole ma kafarki kafa ta irin wannan gara ai nan da nan zan canza, ai nasan kin fadawa ya mahmud tare
akayi goyon mu".
Dariya zahra tayi kawai, lamarin magaji sai shi shidai yaci nama.
Sako Ammah ta bawa Zilai na ta biya gidan Hajiya Amina ta fada mata tana nemanta tun dazu take kokarin
kiranta network yaki bada hadin kai sam.
Parlour Ammah ta fito ba taga zahra ba sai magaji yana ta aikawa.
"To acici ina zahrar kuma?".
Da hannu ya nuna dakin data shiga saboda ya cika baki.
Can ta nufa tayi knocking, da masifarta ta taso zata saukewa magaji sai kuma taga Ammah ce.
"Kizo kije ku gaisa da Abbanku saiki tafar masa da abinda kika kawo masa tunda dama bai kai ga yin break
fast ba, idan kin dawo kema kizo kiyi naki nasan ba wani abun kirki kikaci ba".
"To Ammah bari na fito na dauka ya fita da naga duk su Ya Abdul Hakeem basu shigo ba".
"A'a yau inaga basu da fita ko ina kamar Abban nasu".
Ta juya ta koma zahra ma ta gyara rolling dinta ta fito tamkar dawisu tana tafiyar nan das-das.
Basket din ta dauka ta fice bata bi ta kan dan gidanta ba dayake ta zuba mata zance, wani lokacin har
mamakin yawan maganar Magaji take shi sam baya gajiya da magana.
Da sallama a bakinta ta shiga parlourn kasancewar a bude ta sameshi, suna dining area sanda ta shiga,
directly gurinsu ta nufa,Abba na ganinta ya fara murmushi yana fadin.
"Masha Allah, uwata ba raguwa bace har kin fito? Haka akeso ki zama mai himma".
Itama murmushin tayi tana karasawa gurinsa ta tsuguna har kasa.
"Abbana ina kwana?". Ta fada tana aje basket din.
"Lafiya kalau uwata".
Basket din ta dauko tana fadin.
"Yau dai abincina Abbana zaici gaskiya Ammah".
"Gaskiyarki uwata ai babu wanda zaiki abincin babarsa zuba mini Allah yayi Albarka ya baki masu yi miki
kema"
"Allahumma Amin". maganganu yake mata masu harshen damo daga karshe ya rufe da kara jaddada mata
mahimnacin hakuri, sannan ta baro sashen nasa duk jiki a mace.
Lokacin data shigo mutumin ya kunna tashar restling yana kallo.
Tana shigowa ya taso.
"Daman ke nake jira kizo na saida miki wannan jaridar".
"Jarida kuma".
Tsaki yayi yana tabe baki kamar mace.
"Ashe ke bakya daukar haske, to labari zan baki".
"Ok. Sai yanzu naje Ghana, bani na sha".
Zama sukayi nan kasa kan carpet.
"Kina jina wai dan Allah me yasa kikace kada na kawo sahura gidanki? Kinga yanda Mama ta damu kuwa
akan nace mata kuna kano kamar zata fasa kuka fa, ke bar wannan kada na manta abinda zan fada miki,
dazu da Asuba nayi shirin masallaci na saka J/C dina a leda na nufi kofar baya na aje idan an dawo daga
sallah na sulale ta baya na wuce training din ball, kinsan tun lokacin dana samu karaya Abba ya hana ball,
ni kuma idan babu ita da matsala gaskiya shine nake fita ta baya har na dawo babu wanda ya sani, to
dazun ina nufar gurin naga Mama da Ya Hamza da wannan 'yar rainin hankalin tana rusa kuka sun fice ta
kofar bayan ita da Ya Hamzan ita kuma Mamar ta dawo ta wuce ta gefen inda nake tana shafe hawaye da
gefen hijabin dake jikinta, harta wuce bata ganni ba nasan duk yanda akayi da magana a kasa tunda babu
wanda yasan da zuwan salma gidan nan".
Zuru zahra tayi masa tana kallonsa.
"Tab Allah ya kyauta can gasu gada, wai zomo yaji kidan masu farauta, ai idan kace ruwan wani ba zai
tafasa ba to in sha Allah naka ko zafi bazeyi ba, ayi dai mugani karya dai fure take bata 'ya'ya, ba dai mugun
abu suka zaba ba da saura ma basuga komai ba, kace kai baka son cigaban kowa to kaima yaushe zakaga
dai dai".
"Haka ne kam ai so nake Abba ya gama break naje na fada masa ya kira Ya Hamzan yaji meya faru kuma ina
suka tafi ko kuma nace Abban yaje makarantar da kansa ko daga can ne aka samu matsalar".
"Kai magaji ina ruwanka da sagbarsu,kasa ido idan tayi wari kowa zeji ne har wani zaka fadawa Abba meye
naka a ciki, ka manta hadisin Annabi Asalihissalam wanda yake cewa yana daga kyawun mutum ya bar
abunda babu ruwansa? To ka kyautata musulincinka kaima, ka nuna kamar baka san anyi ba idan wani
dalili yasa anzo gabar da zaka iya fadin abinda ka gani falillahil hamdu saika fada din".
"To shike nan bari naje nayi wani aiki kinsan mun fara project".
"Masha Allah Allah ya taimaka, ya dai fiye maka da guzirin tsegumi"
.
"Allahumma Amin, gaskiyarki yallabiya"
Yayi waje.
Ita kuma zahra ta tashi zata koma ciki taji ana knocking din kofa ta nufi gurin, tana budewa taga Hajiya
Amina mutuniyar Ammah ce sosai, tana sayar da turarika na jiki dana daki da kayan gyaran Aure dasu
dilkar Amare. Jakar hannunta zahra ta karba tana bata hanya tare da fadin.
"Sannu da zuwa Hajiya"
"Yauwa Amarya ya gida?".
"Lafiya kalau Hajiya, ina kwana?".
Lafiya kalau Alhamduliahi ya mai gidan naki?.
"Lafiya kalau" ta fafa tana sadda kai kasa.
"Bari na fadawa Ammar kinzo"
Kafin ta bata amsa har Ammar ta shigo, tana fadin.
"Lale marhabin da Hajiyar kamshi, lallai kinaji da wannan 'yar taki, nan da nan haka har kinzo".
0906143233
My WhatsApp number
Or
08055362975
MAMAN FATEEMAH.
WANNAN LITTAFIN BA MALLAKIN KOWA BANE GURIN JUYASHI ZUWA AUDIO KO WATA SIGA BADA IZININ
MARUBUCIYA BA DAN HAKA A KIYAYE.
Page 68.
.............
Cikin abinda Bai wuce minti talatin ba su Zahra suka Gama duk abinda ya kamata suyi a cikin gidan, suna
parlour ne Aunty Rukayya ta Dan kalli Zahra Wadda ta cika fam.
"Wai ke fushin na menene? Ni na tab'a ganin irin wannan Abu naki, idan wata ce da yanzu ta rasa Ina zata
tsoma ranta Dan Dadi gurin your love fa zakije ba Naga kin sakawa number dinsa haka ba? Ko a Baki sunan
ya tsaya kawai babu a aikace? Kije ki tarairayi kayanki ki bashi more happiness Mana! Kada kiyi Sanya Ina
ganin big bro dina fa me zafi ne, dan haka dole ki Zama irinsa koma ki Dara shi".
Narai narai tayi da idanunta tana kallon Rukayya da walainiyar hawaye a cikinsu sai sukayi wani irin kyau.
"Nifa Aunty Rukayya wallahi tsoronsa nakeji idan yana fada min wasu maganganun sai Naga shi Kansa sun
girme Masa ballentana ni, Kuma fa ina Jin Kamar wannan tafiyar zata canza min abubuwa, Kuma ma in fact
Ina tsoron haduwar mu wallahi".
"A'a ban fashimta ba? Kina tsoron haduwar ku Kamar Yaya?".
"Aunty bazaki gane ba, nifa still I am a vagina".
Hannu tasa ta rufe bakinta cikin bala'in mamaki.
"Are you sure?".
Kai ta gyada Mata.
"Yes..."
Neman gurin Zama Aunty Rukayya tayi, tana jinjina Lamarin big bro din, nisawa tayi tana kallon Zahra
Wadda Kamar ance Mata yanzu Lamarin ze tabbata.
"Amma gaskiya nayi mamaki kwarai da gaske, to shi wane irin waliyi ne akan Mata? Me Kamar ke ya Zuba
Miki ido Yana kallonki tsawon lokacin nan, ko dai bashi da lafiya ne?".
Ta jefawa Zahra tambayar.
"A'a wallahi lafiyarsa kalau kawai dai...."
Sai Kuma tayi shiru.
"Ki kwantar da hankalinki ba abinda ze faru, Ina sakon da mommy ta aiko Miki dasu kina kano?".
"Nayi amfani dasu yanda na gani a cikin bayanin".
"Good, yayi yanzu ma kici gaba da amfani da Wanda nazo miki dasu kinsan takanas ta tayo Miki order su
daga Birnin inda kanwata ke Aure, magunguna ne na gaske kada kiyi Wasa dasu Kuma idan mukaje Kano
zance Ya Sameer ya kaiki mommy tana son ganinki naji suna magana da Maman kwantagora zata Baki
Addu'oin da zakina yinsu" .
"Ok Nagode Aunty Rukayya Allah yabar kauna".
"Allahumma Amin".
Lokacin da suka dawo Ammah ta hadawa Zahra komai harda abubuwan amfanin kitchen kayan da Hajiyar
makwarari ma ta kawo Saida ta Zuba musu fin Rabin kayan.
A gurin Abba Zahra ta tarar da Hajiyar makwarari suna ta Hira dashi tamkar d'a da uwa, wata nasihar ya
Kara yiwa Zahra sosai Wadda ta karasa karyar Mata da zuciya sai taji tamkar yau ne zata rabu dasu zuwa
gidan auren nata. Lokacin da suka fito zasu tafi ne sahura ta dawo daga Aiken da Mama tayi Mata wani
gari a cikin Jigawa area din gwaram, da sauri tayi ciki ta nufi dakin Mama wadda duk yau babu Wanda ya
sakata a Idonsa idan ka dauke magaji, ko knocking Bata tsaya yi ba ta tura kofar ta shige ba kowa a
parlourn corridor din bedroom din ta shiga da sauri Kamar zata tuntsira knocking ta dunga yi Amma shiru
tamkar babu Mai rai a ciki haka ta gaji ta dawo parlour.
Har gurin mota Abba da Ammah da dasu Auta Saida motar tabar harabar sannan su Ammah suka koma
ciki,sun rabu da Hajiyar makwarari da alkawarin zataje kano har gida ta gaisheta.
Tunda suka taso Hajiya ke Zuba ita ta zauna a kusa da Ya Sameer har Kano bakinsa Bai huta ba ko yayi shiru
saita nemo abinda dole yayi magana.
Karfe biyar da kwata suka shigo Kano Hajiya yaso ya Fara saukewa tace ya wuce da ita gidan mommy sai da
dare direba ya kawo ta gida, ba yanda ya iya dole yayi yanda take so.
Kamar mommy ta goya Zahra haka ta dunga nan nan da ita.
Dakin Aunty Rukayya Zahra ta sauka, a nan mommy ta shigo ta sameta tayi tagumi tayi nisa cikin tunani.
"Meya faru ne diyata ko kina da damuwa ne?".
Mommy ta fada tana Zama kusa da Zahrar.
"Babu komai mommy".
"To Masha Allah, kina jina abinda Zan fada Miki ki rike Mijinki da kyau kada kiyi sakacin da wata zata samu
damar shige Masa suna da 'yan Mata a wannan families din nasa Kamar me Kuma kowace uwa gurinta
mijinki ta shinshina ta samu damar lika Masa 'yarta ga Addu'oi da Hajiya Mama tace na baki lokacin Dana
fada Mata a kawo Miki salon da Rukayya ta kai Miki, kina jina dauko wayarki ki rubuta a notepad din ciki".
"To mommy nagode".
"Kina jina da farko Zaki samu tsamiya Mai kyau ki jika da jiku da dare idan Zaki kwanta ki taci kadan ki tofa
YA WADUDU kafa bakwai duk kafa Daya ki Fadi sunan mahmud ki tofa haka zakiyi harki Gama saiki shanye,
haka Zaki ringa yi in Sha Allah soyayya dai Zaki gamta a gurinsa kinsan duk yanda kike a zuciyar mijinki kina
bukatar Karin samun daraja da soyayyar mijinki yaji babu kamarki a zuciyar kinji".
"Naji mommy in Sha Allah zanyi".
"To Allah ya kaiku lafiya kiyi ta hakuri Lamarin Zama da wasu dangin Saida hakuri zakiga abubuwan da suka
Sha banban da naku al'adun da dabi'u to sai kin nutsu sosai kin Zama Mai kula da koma da lura".
Karfe bakwai flight dinsu ya tashi daga Kano zuwa Abuja, harda Fateeha akazo airport din sai a lokacin
Zahra tasan da Oga Sameer zasu tafi.
A gidan kanin mommy suka kwana matar gidan yarinya ce duka haihuwarta biyu tunda Aunty suhaima
taga Zahra taji yarinyar ta kwanta Mata a rai da gani ta samu tarbiyya Bata da rawar Kai irin na yaran yanzu
more especially idan Allah yayi musu baiwar kyau zaka samesu da iyayi da fadin rain Koda ba 'ya'yan kowa
bane. Sun Dade suna Hira kafin Zahra ta kwanta saboda zasuyi sakkon fita tunda flight din seven fifteen
zasu bi.
Duk wani Kai kawo Fadi tashi Sameer ne yayi musu ga Zahra ta dauko kayan sakawa abinda basu Saba ba a
dabi'ar tafiye-tafiyensu, Aunty Rukayya ta zuga Zahra tace ki dauki duk kayan da kikasan kina sonsu kinga
dai wasu ba samunsu zakiyi a can ba,idan ma kin Sami to dinkin zakiga baiyi dai dai da ra,ayinki ba.
A VIP suka zauna, ko a Adis Ababa da sukayi lending Zahra batabdamu data fita ba, Saida suka kusa tashi ta
fito ta Sha minerals kawai da snacks.
MAMAN FATEEMAH.
Page 69.
..........washe gari basuje asibitin da safe ba daukar ta yayi suka fita,boutique suka shiga na kayan sakawa
suka loda ita abun har mamaki ya Bata, da farko cewa yayi ta zaba da kanta sai ta dauko kamar set shida
sai inner wears data dauka, Yana kallonta Yana ganin haka ya dauko babban basket ya Fara lodar Kaya da
na gurinsa ya cika ya dauko wani da taga abun nasa ba Mai karewa bane ta Fara hada shi da Allah akan ya
barsu haka bafa aaidawa zasuyi ba Kuma ita kadai ce bada wasu zasu ringa sakawa ba, sannan ya Bari
Shima ya dauki dai dai kun abun bukata irinsu Kayan shaving.
Credit card ya Basu suka cire kudin su ya bada Address din da za'a Kai , Kayan suka wuce.
Suna zuwa train station suka tarar da Mr Salahuddeen Yana jiransu cikin girmamawa ya gaishe da mahmud
cikin yaren indianci ita mamakinsa take yi yanda ya iya indianci ga yaren Portugal ma da yake ji can
kwanaki taji Yana oyaren french, cikin harshen turanci Mr Salahuddeen ya gaishe da Zahra. Wani card
Kamar ATM ya mikawa mahmud cikin ladabi Yana fada Masa magana, shi Kuma sai gyada Kai yake yi,
bayan ya gama saurarensa ya Mika Masa key din motar yayi ya juya ya nufi inda motar take, hannunta
Mahmud ya riko ya nufi cikin station din.
Gurin Zama ya nemar musu ya kawo Mata fresh milk me matsakaicin sanyi, tunda ta zauna wata yarinya da
gani 'yar Africa ce take binsu da kallo ko Ina mahmud yayi idonta Yana Kansa, ganin haka lokacin Daya
dawo da Coke na gwangwani a hannunsa ta shagwab'e Masa tana fadin.
"Pls meu amor mu canza guri bana son nan".
Hannu yasa ya dagota daga zaunen Yana fadin.
"Ok muje can ta baya ko?"
Gyada Masa Kai tayi suka nufi inda ya fada, sunzo karya kwana Zahra ta Dan juyo taga still dai ta biyosu da
wani mayen kallo Kamar tazo ta rungume Mata mijin, wata uwar harara Zahra ta zabga Mata tana jan
tsakin da Batasan ya fito ba.
Dan juyowa yayi Yana Mata wani kallon ke waye?
Dauke Kai tayi tana fadar "ba komai".
Be zafafa ba sukayi gaba.
Bayan sun zamu guri can gefe Zahra tace Masa.
"Wai Ina zamu ne haka?".
Dan lakuce lips dinta yayi Yana wani lunshe Ido.
"Jim Corbett national Park zamuje Yana can Uttarakhand state, Ina son muje huta kuma kiga number one
park a India anyi shi tun 1936, lokacin turawan mulkin mallaka".
"Ok, Naga ka kawo mu station na train da nisa a mota ne?".
"Eh Kamar hakan ne dai za'a Kamar tafyar five hours thirty minutes a train".
"Tab da nisa ya akayi kasan Ina son zuwa park ne?".
Saboda an fada min Yana daga cikin abinda Keke so ne".
Shigowar train din da zasu bi yasa hirar tasu ta yanke.
Suna zuwa ya zura katin ya saka musu kudinsu suka shige ciki har zasu zauna wani seat da babu kowa
Zahra taga kusa da wannan yarinyar ne tace Masa.
"Pls muyi ciki bana son kusa da hanya kowa ya shigo saiya ganka".
Nan da nan ya nufi inda ta nuna Masa.
Away biyar da mintuna shiga Uttarakhand Basu bata lokaci ba suka shiga taxi zuwa I.T.C HOTEL. Wanda yayi
booking dinsa tun jiya.
Sun huta sunyi wanka it's Kuma tayi wankan tsarki Dan cikin ikon Allah dif ya dauke, tana fitowa taga Kayan
sakawa a saman bed din ta dauki wata abaya baka ta saka ta tayar da sallah, tana ta fatan Allah yasa harta
Gama sallar Bai shigo ba, cikin taimakon Allah Bai shigo ba din Saida ta Gama sannan ya shigo Yana fadin.
"Taso muci abinci kisan bana son yunwa"
"Acici shugabannin tauna"
Ta fada kasa-kasa.
"Me Kika ce".
"Nothing"
Ta fada tana tashi tsaye tana Mika tare da salati
Kauda Kai yayi idan tana irin wadannan abubuwan labarin yana iya canzawa.
sunci Abinci sannan suka Dan fita harabar hotel din tana mamakin yanda ake binsu da Ido idan sun wuce,
taga sufa kasar ta kyawawa ce ko duniya ta Shaida hakan,amma sai ayi ta kallonta sun zagaya cikin hotel
din sosai sun Jima a gurin swimming pool ba yanda Mahmud beyi da Zahra ba ta yarda su shiga ta kiya Wai
tsoron ruwa take, Saida zasu kwanta suka dawo daki.
Abin mamaki da suka kwanta ya dai shigar da ita jikinsa amma daga haka babu abinda yayi Mata, da safe
da wuri ya fice tana barci, sai written ya aje Mata a kusa da ita ya fada Mata yaje New Delhi gurin Baba
Malam, ta Kira a kawo Mata abinci idan ta tashi.
Lokacin data tashi Rana tayi sosai ba Bata lokaci tayi wanka ta nemi abinda zataci.
Ammah ta Kira da sabon sim din Daya saka Mata na kasar sun dade suna Hira har take da fada Mata
Abbanta ma ya shigo kasar cikin dare, yazo yaga jikin Malam din, tayi takaici ba kadan ba Daya kawota Nan
ya saya yayi komawarsa can.
Ta Kira Aunty Hasana ma Saida tayi Mata fada sosai sannan ta amsa sallamarta akan tahowa Bata fada
Mata ba duk da Ammah tayi Mata bayanin yanda tafiyarta tazo, sunyi Hira itama irin ta wayyaun Yaya da
kanwarta Nan Aunty ta tinga fada Mata abubuwan Daya Kanata ta rike su zamar Mata makaman yakin
Zaman Aure, wani Abu idan Auntyn ta fada sai Zahra taking tamkar ta nutse, Wai Ashe kowa a wannan
fannin sai da ka kyaleshi kawai.
Har yamma mahmud bai dawo ba haka tayi wunin kadaici dan ma ta samu mujiba Wadda ungiyar su
Sameer suka Samar Mata da gurbin karatu a modibbo Adama University of Technology Adamawa duka
batafi wata Daya da tafiya ba.
Sun Dade suna tattaunawa a Kan yanda akayi Sameer yazo har gida da admission dinta tunda sun tab'a
karbar c/v dinta tun da dadewa lokacin anyi auren Zahra babu dadewa.
Bayan sallar magriba mahmud ya shigo tana zaune tana lazimi be zauna ba Shima alwalar yayo ya fice Yana
fadin "Bari nabi bus naje masallacin dake can cikin gari na samu jam'in insha'i"
Kafin ya dawo ta Shirya ciki wasu kananun Kaya riga da wando masu masifar kyau saita Zama Kamar 'yar
Baby a cikinsu turarikan da Hajiya Amina had'a Mata tayi amfani dasu, ita kanta tana Jin dadin turaren ba
kadan ba.
Ledojin Daya shigo dasu ta dauka ta bude kifi ne roasted one da kaza sai Kuma fresh milk dasu tarkacen
chocolates da biscuit's.
A parlour ya sameta tana kallon wani program da ake a gidan tv na Qasar Mai suna chair Lady sosai Shirin
ya dauki hankalinta har Bataji bude kofarsa ba sai kamshinsa taji kusa da ita.
Fuskarsa ya Kai daf da tata ya bata light kiss a chicks dinta.
"You look so cute my previous...'.
Ya fada Yana Zama very close to her.
Wani kamshi ya Shaka a jikinta Nan da Nan ya motsa Masa jamiyya, wata Mika yayi Yana riko hannunta
tare da fadin.
"Can I help me plssss....".
"Na shiga uku ni Zahra me Kuma ya kawo irin wanna sauyin Nan da nan".
Ta fada a zuciyarta, hannu yasa ya dago fuskarta ya kalleta da narkakkun idanunsa da suke razanata a can
baya.
"Meee.. kakeee sooo..."
Ta fada bakinta na rasa haka ma jikinta, lokaci Daya tayi zuru-zuru da ita.
Sai Kuma ta bashi tausayi yaji ze iya danne duk wani Abu da yake bijiro masa.
"Ba komai bani abinda zanci, yunwa nakeji".
Wata ajiyar zuciya ta sauke Wadda tasa ya dago ya Zuba Mata idanuwansa, yana ayyana.
"Tab za'a Sha drama a gurin yarinyar Nan da alama ta Mike kafa tana neman ta manta menene hadafin
auren".
Ya fada a zuciyarsa, suna cikin cin abincin ne yake fada Mata zuwan Abba, tace Masa Ammah ta fada Mata.
A bedroom yau dai Saida ya ragewa kansa zafi sannan ya Sami salama Dan da gaske turarenta ya tashi
hankalinsa ba kadan ba.
Satinsu biyu a Uttarakhand suna hutawa sunyi wani kyau ya zagaya da ita guraren tarihi na state din ya
kaita River Greek tayi kallon Ruwa sun huta sosai a gurin, ranar da yace Mata zasu koma new Delhi ji tayi
Kamar tace Masa su Kara wani sati biyun, da wuri suka baro Uttarakhand din Sha biyun Rana suna New
Delhi Asibiti suka wuce jikin baba Malam da sauki sosai Dan har an tada shi zaune saura koyon tafiya Kuma
Amma ana tsayar dashi ya rike karfen tafiya.
Bayan sun baro Asibiti tayi zaton leeha palace zasu wuce sai taga Yana fadawa Mai taxi din inda ze kaisu.
Bai bar Mai taxi din ya tafi ba yace ya jira su fito,. hannunta yaja suka nufi cikin wani plat house Mai kyau
sosai Kati ya zura ya bude main entrance din. Parlour ne Wanda yaji kayan more rayuwa wani corridor ya
nufa dasu Yana rike da hannunta har lokacin.
Dakina ne guda uku sai wata kofa Wadda Bata San Kota mecece ba.
Kofar dake hannun hagu ya zura Kati ya bude.
Kayanda suka zo dasu daga 9ja ta gani sai Kuma Wanda suka saya ya bada address din da za'a kawo, kallon
ta yayi ki dauki duk abinda Zaki bukata zamuje unguwa ne har abubuwan da Kika dauko na tsaraba ki fito
dasu. Ba musu ta shiga dauko luggage dinta da kayyayakin da aka hado Mata da Kuma abubuwan amfani
da Ammah ta hado Mata da Wanda Hajiyar makwarari ta kawo Mata.
Shi tsayawa yayi Yana kallonta ganin kayan da yawa.
"Wai Ina Zaki da wadannan kayan haka sai dai kiyi selecting na wasu gaskiya".
Ya fada yana daukan wasu ledoji yayi waje itama luggage din taja ta dauki Karamar jakar da aka Zuba Mata
kayan da Ammah ta dunga Mata gargadin yin amfani dasu da Kuma na wajen mommy bayansa tabi tana
fadin.
"Ya za'ayi na aje kayan Hausawa tunda Nan dai babu irinsu, kullum mutum yana fama da kananun kaya".
Yana ganin kayan yasan Bata rage ba haka Nan ya kyaleta ya shige ya dauko sauran. Inda ze kaisu da
number gidan ya fadawa Mai taxi din.
Tafiya ce Mai nisa daga inda suka baro dai dai gate din wani katafaren gida Dan taxi din ya tsaya, ya fito
Yana Ciro musu kayansu, hannu mahmud ya zura ya bude Karamar kofar gate din Yana fadin dauki luggage
dinki kiyi gaba kije kiyi pressing din door bell din gani Nan".
Jan luggage din tayi tana rike da handbag dinta ta nufi kofar.
Sau biyu tana latsawa sannan taji alamun an nufo kofar, wata matashiyar mace ce 'yar gayu irin Wanda
gayun ya Gama bayyana kansa a jikinsu ta bude kofar tana dauke da wata fine baby Fara sol da ita, kallon
kallo na rashin sani suka yiwa juna, Zahra ce ta Fara gaisheta cikin yaren hausa saboda taga doguwar rigar
atamfa a jikinta.
A mamakance ta amsa Mata Bata taba tunanin tasan ko zo da hausa ba.
Zahrar ta Dora da fadin.
Tare muke da Mahmud gashi can a waje.
"Mahmud Kuma daga Ina?".
Kafin ta tattaro yanda zatayi Mata bayani ya doso gurin Yana rige da sauran kayan a hannuwansa.
Wani irin Kara matar ta saki ta zabura Banda Allah yasa Zahra tayi azama gurin rike yarinyar ba da Tasha
kasa duk da haka Saida ta fasa kuka Dan ta tsorata sosai.
Babu wata-wata tana zuwa ta rugumeshi sai kuka tana fadin "me yasa ka tafi ka barmu? Ko zaka guji kowa
Banda ni kayi min alkawarin duk rintsi kana tare Dani me yasa ka Saba alkawarin mu?" Tana fada tana
kuka.
Ai Zahra a gurin ta sulale ta zauna Dan ji tayi gaba Daya garin Yana juya mata. Banda innailaihi wa Inna
ilaihi raji'un!!! babu abinda take maimaitawa, meye haka Daman da gaske yake da yake fada Mata ba ita
kadai bace ta iya ririta shi kada wata ta kwace shi.
Yaro ne ya shigo da alamar daga school yake baze wuce shekaru biyar ba zuwa da rabi, da sauri ya karaso
inda suke ya zagayo Yana duba fuskar Wanda yasa mamansa kuka.
Ai Shima kwalla Kiran Daddyyyy....
Yayi ya nufesu da gudu.
Tashin hankalin duniyar Nan ya saukarwa Zahra ji tayi makogwaronta na fitar da wani Abu Mai daci Nan da
Nan ganinta ya nemi daukewa.
Janye ta yayi daga jikinsa sai share hawaye take yi handkerchief ya mika Mata fari sol.
Tsugunnawa yayi ya dauki yaron Yana dariya, ya Fara Masa magana da indianci Kai kawai yaron yake gyada
masa, yaron ya gyarawa Zama a kafadarsa ya riko hannun uwar suka nufo kofar a zaune a gefen steps yaga
Zahra da baby a zauna ba karamin namijin kokari tayi ba gurin hiding din abinda yake Mata tuk'uqi a
zuciya.
Kallo daya ya yi Mata ya Gama gane condition din data shiga basarwa yayi Yana fadin.
"Hana Shatu haka ake karbar Baki kin bar yarinya a zube a Nan kin tafi kina yarinta har kinsa min yaro kuka,
sauko Babana na dauki bakuwa ko?".
Kai ya gyada.
Yana sauke shi ya nufi gurin da zahrar tayiwa kanta agajin Zama.
Sosai ya tsuguna Yana Mika hannu ze dauki yarinyar magana yayi Mata Wadda daga shi sai ita zasu ji.
" Ki nutsu bana son kuskure duk abinda na fada ki bishi kawai". Canak ya dauke yarinyar daga cinyarta, yayi
gaba.
08055362975
09061432330
MAMAN FATEEMAH.
Page 70.
.........…..
Luggage din da Zahra ta aje matar ta dauka tana fadin "taso mu shiga,wallahi nayi loosing control dina ne
wallahj abun ne da mamaki ban taba tunanin Zan ganshi a irin wannan lokacin dana hakura na sallama".
Jiki ba kwari Zahrar tabi bayanta suka shige ciki, a zaune suka same shi, yaron yana lik'e a jikinsa ya lafe sai
Karamar da yake yiwa wasa tana balbala dariya Kamar ba yanzu ta Gama tsandara kuka ba.
Suna shiga matar ta karasa inda ya zauna tana fadin.
"Yanzu ina alkwarin mu? Haka mukayi alkawari da Kai, ka bace bat a cikin duniya ka manta da kowa? Ba
waya ba sakon Email? Wallahi ka dauki Alhakin Ammi ba kadan ba, kasan yanda Hajiya Inna ta rude kuwa?
Abbie ma ba karamin tashin hankalin ya shiga ba, da farko ya dauka fushin 'yan kwanaki ne Saida yaga
tafiyar ta mik"a yasan da gaske ne, har nan ko ya taso takanas ta kano, Wai yasan ko baka fadawa kowa in
da kake ba yasan ni dole nasan inda kake".
Hannu ya daga Mata.
"Pls Aisha Dan Allah ki rage surutu, kin bar yarinya a tsaye ki kaita daki ta huta kinsan long journey din da
tayo? Ki tayata shiga da kayanta zata nuna Miki abinku na Mata da bakwa iya tafiya Saida tsaraba".
Wata harara ta wurga masa.
"Ai duk Kai ka jawo na manta da ita, sorry sister kinsan abin ne da al'jabi wallahi twins dina ne yayi batan
dabo a duniyar nan, nayi kukan rashinsa har naba uku Lada, zo muje".
Wata ni'ima Zahra taji tana shiga jikinta, sai lokacin ta Kare Mata kallo kamarsu Daya Dan dai shi namiji ita
mace.
"I am coming".
Ta fada tana haura stairs da sauri.
Tana bacewa ganinsu ya juyo Yana kallon Zahra.
"Precious".
Bata amsa ba Amma ta dago tana kallonsa kafin tayi magana Aishat ta sauko da sauri da keys a hannunta.
"Muje ko bakuwa ni ko introducing dinki Bros Bai yi min ba".
"Kije ki rakata Mana tunda na kawo Miki ita ai magana ta Kare, diyar uban gidana ce Bata da lafiya ne
zataga likita, sannan malamina ma Yana Nan anyi Masa aikin spinal cord ne da sauran fractures Daya samu.
Ya fada Yana fuskewa.
Daki ne comfortable yaji komai, na bayan more rayuwa.
Aisha Bata fita ba Saida ta Taya Zahra saka komai a muhallinsa sannan ta fito.
Zama Zahra tayi a gefen gadon tana nazarin maganganunsa, me yake nufi da diyar uban gidansa, Amma
zata raka shi taga iya gudun ruwansa Shima namiji ya iya danne abunda ke ransa bare ita mace.
Aishar ce ta Kara shigowa da tray an dora snacks da Ruwa da drinks.
Da murmushinta ta karaso tana fadin.
"Ashe Fateemah ce, sannu da hanya zahra, ya jikin naki nagi Bros yace Baki da lafiya, Ni Sunana Aishat
Muhammad Dange, twins din Al-husasain".
"Masha Allah, Aunty nagode kwarai sannu da kokari".
"Lah ba komai, ki Sha ruwan kiyi sallah saiki fito lokacin an shiya muku abinci"
Sallar zahra tayi ta Jima tana addu'ar neman mafita daga wata sabuwar rigimar da take hangowa.
Nan Kan sallayar ta Dan kwanta barci yayi awon gaba da ita.
****
Zaune suke Yana cin abinci ita Kuma tana duba sakonni whatApps har zata wuce salon Faisal saita dawo
saboda Basu fi minti goma da Gama ways dashi ba Yana Mata magiyar ta turo da kudi suyi sarin Kaya, ta
nuna masa ya jirata zasu shigo ganin jikin Abban nasu sai ayi abinda ya kamata, sai Kuma wata zuciyar ta
kwabeta akan ta duba ita me majiyyaci ai share sako ba nata bane.
Ta maimaita karanta sakon ya Kai sau biyar tana ganin kamar ba gaskiya bane.
Dialing din number Faisal Aunty Surayya tayi, Yana dauka Bata jira komai ba ta jefa Masa tambaya.
"Shin text din daka turo min gaskiya ne".
"Eh wallahi Aunty ko jiya ma yazo gurin Abba mantawa nayi na fada Miki bakiga yanda yake kula da Abba
ba kinsan har daki ya canza Mana mantawa nayi na fada Miki ayi Mana godiya gurin Auncle Mustapha".
"Ok shi kenan ina zuwa".
Ta fada tana yanke Kiran.
Auncle Mustapha ta juya tana kallo Wanda Shima ita ya zubawa idanu, batace Masa komai ba sakon ta
bude ta Mika Masa.
Yana Gama karantawa ya dago da sauri yana neman Karin bayani.
"Nima shine na Kira Faisal din ya bani tabbacin haka ne, Wai ya Kai wani Babansa ne".
Spoon din ya aje ya mike ya zari hularsa da key din mota ya fice, Surayya na Masa magana hannu kawai ya
daga Mata yayi gaba.
Duk yanda Aishat taso mahmud ya Bata hadin Kai suyi magana ya Kiya yace ta Bari sai dare zasu zauna suyi
magana sosai.
Abincin ta shirya a table ta nufi dakin da zahra take, samu tayi barci ya dauketa a saman sallar da tayi
sallah, Bata tasheta ba dawowa tayi tana fada Masa tayi barci da alama ta gaji.
Shida Abulkhairi sukaci abincin, yayin da Aishat ta dauki Afnan Wadda tayi barci ta haya da ita sama.
Kamar jira ake ta shiga bedroom dinta Kiran sweet heart ya shigo.
Tana dauka ya Fara fadin.
"Sweetie Ina Mahmud din yake Dan Allah?"
Saida taja fasali sannan tace Masa.
"Yana down stairs, wallahi sweet heart kamar Almara nake ganin abin duk na rude Dan Allah kazo kada ya
Kara tafiya... Yace matukar na fadawa Abbie ko Ammi Bazan Kara ganinsa ba".
Ta fada tana share hawaye.
"Cool down your temper my sweetie Babu inda zaya, ban tsoro ne kawai yake miki yasan idan yayi Miki
haka bazaki fadawa kowa ba, ki jirani zuwa gobe da safe in Sha Allah, ki daina yi min asarar hawayenki a
banza, a gurina suna da mahimmanci , ki kyaleni dashi yanzu basai an Jima ba zanyi informing din Abbie
gara ayita ta Kare tunda shi Abu baya wucewa a gurinsa".
"Gaskiya dai Kam ki shiga cikin Lamarin kuyi Masa taron dangi, kasan da wata yarinya yazo Wai 'yar gidan
uban gidansa ce ya kawota Asibiti, nifa I doubt much akan yarinyar Nan kasan dai halinsa baya sabga da
macen daba muharramarsa ba ya kake ganin ze dauko yarinya mace kamar wanna ka ganta kuwa? Allah
Ina Jin ta hada iri da Larabawa Dan she is very young and beautiful".
"Just ka bishi a yanda yake so idan na shigo zamu Yara da yaren garinmu rabu dashi".
Basu wani Dade ba yayi Mata sallama Yana Kara kwantar Mata da hankali akan tunda ya kawo kafarsa har
gida in Sha Allah komai yazo karshe.
A mota uncle Mustaphan ta karaso gidan duk da babu nisa Amma sai yaga idan yace ze tako a kafa kamar
baze zo ba.
Directly part din Ammah ya nufa Don baya son maganar ta fita tun kafin su tabbatar da abunda aka fada,
very lucky ya samu yayan nasa general a part din.
Batool ya bude Masa kofa ya shigo tana gaishe shi.
Ya amsa Yana fadin.
"Ina Abbie Amminku take?".
"Tana part din Abbie na cikin nan".
Ok, Bari na kira shi"
Ringing Daya ya dauka Yana fadin.
"Ko Ina kake Mustapha maza kazo Ina son ganinka ina kokarin kiranka naka Kiran ya shigo".
I
"To ai gani a part din Ammi Nima neman ka nakeyi".
Ya fada yana nufar kofar baya yabi corridorn da ze sada shi da part din General din".
Yana shiga da sallama a bakinsa yayi turus ganin Ammi tana shafe hawaye, a sanyaye ya karasa cikin
parlourn.
"Lafiya! meya faru?".
"Zauna Mustapha yanzu ne Abbas ya kirani daga Jamaica inda yaje aikin da nake fada maka, wai Aishat ta
kiwo shi ga Dan uwansa yazo Yana tare da ita".
Neman guri uncle Mustaphan yayi Yana tabbatar da gaskiyar maganar Faisal.
"To ai Nima abinda ya tasoni kenan na taho, kasan Alhajin su Surayya Yana can Indian an sake Masa gyaran
kafa shine suka hadu da mahmud din yaketa dawainiya dasu shine ya fadawa surayyar tayi min godiya
kasan ba kowa ne yasan case din da ya faru ba kawai dai an wayi gari ba'a ganinsa duk da zancen duniya
baya buya nasar Surayya Bata fada musu komai ba gaskiya, Ammin Yara ki daina kuka ko lokacin da ake
cikin tashin hankali ba Wanda yaga hawayenki sai yanzu da asking ya I gaban gashi".
Share hawayen tayi tana fadin "
dole nayi kuka ni kadai nasan dacin Dana ci a lokutan baya da dararen Dana Raya akan ubangijina ya dubi
Lamarin yaron nan ya juyo min da hankalinsa gida".
"To godiya ya kamata ki yiwa Allah Daya amshi addu'ar ki ba kuka ba".
Wani murmushi general yayi yana duban Mustapha.
"Ni bansan lokacin data aje karar 'ya'yan fari ba da ko me zakayi musu Bata daga Kai ta dubeka amma
yanzu dibi yanda take Kora bayani Kamar ba ita na".
"Kan barta tayi Yaya ai taking jarunta ma ba uwa duka ba, yanzu Yaya kenan za'ayi? Da nida madam zamuje
next week amma dole mu raba tafiyar a yau Zan shiga neman visa ko nawa Zan bayar saina samu nan da
jibi in Sha Allah Zan tafi Indian Zan kadi shi mu taho gida da izinin Allah. Amma dan Allah kada a fadawa
Hajiya Inna wallahi idan taji cewa zatayi kafarta kafa ta".
"Kaje kayi shiri zanyi magana akan visar taka, ka Zama cikin shiri kawai".
Tashi Ammi tayi ta shiga ciki ta barsu suna tattaunawa akan Lamarin.
*****
Saida zahta tayi barci Mai isarta sannan ta tashi, wanka ta shiga tana fitowa lokacin magariba ta kusa kawo
jiki, tayi mamakin dogon barcin da tayi.
Lotion kawai ta shafa sai roll-on da tasa sure sai body midt da normal turaruka da take amfani dasu
designers na kamfanin Alharamaini, rigar atamfa ta saka simple style A shape ta yafa Karamin gyale sai tayi
wani sansanyan kyau, a hankali ta bude kofar ta fito tana takunta gentle ta shigo parlourn Aishat ta gani a
zaune da Abulkhairi a gefenta tana koya masa homework, kafin tayi sallama har sansanyan kqmshinta ya
jewa Aishat.
Dago Kai tayi tana amsa sallamar da Zahra tayi.
"Masha Allah!"
Abinda Aishat ta fada kenan Dan babu karya yarinyar ta hadu ta ko Ina macece ga asalin kyau Dan gaske,
murmushinta Mai kayatarwa zahra tayi Mata tana fadin.
"Sannu da hutawa Aunty".
Hannu Hanan ke dagowa Zahra tana zillo daga cinyar mamanta.
Daukarta tayi tana Zama daga dayan gefe Kan wata kujerar.
"Yauwa sannu, Zahra ko?"
Kaita gyada Mata alamar eh.
"Kinsha barcin gajiya, ga abincinki can Kan table muje kici kin kwanta da yunwa, bro yace na fada Miki yaje
Asibiti sai dare ze dawo".
"Ok, nagode kiyk zamanki Bari muje da 'yar gidana Aunty ki bani ita Dan Allah Ina sonta".
Dan murmushi tayi idan mijin da Zaki aura ya amince ki dauka Ni tawa Mai sauki ne na Baki".
Gaba tayi tana dariya kasa-kasa ta nufi dining din save da Afnan.
Sun Dade suna Hira da Aunty Aishat har barci ya Fara Kama Zahra sannan tayi Mata sallama ta nufi inda
akayi Mata masauki, bayan ta wuce Aishat da Dade tana auna Lamarin Zahra a zahiri Sam batayi Kama da
yarinya marar tarbiyya ba ko masu budedden idanu Amma tayiwa tafiyarsu da Dan uwanta Question mark,
idan ta tuna da irin warning din da yayi Mata kafin ya bar gidan.
"Gata Nan amanace a gurinsa shi yasa na kawo ta Nan inda zata zauna safe, ki kula sosai nasan halin sayyid
a Kan mata duk da kince yayi tafiya to Koda za'a samu akasi yazo bana nan, to ki fada masa yarinyar nan da
mijinta Dan muna komawa za'ayi bikinta ya dauke idonsa daga kanta idan Kuma ba haka ba za'a iya samun
matsala.
"Maji ma ganj, an binne tsohuwa da Rai"
Ta fada a fili.
A Nan taci gaba da Zama tana jiran ta inda Dan uwanta ze bullo, wurin Sha Daya da minti goma ya bude ya
shigo gidan, ya yi mamakin ganin Aisha Ido biyu.
"Ashe dai Hali yana nan, yanzu Dan Allah bakiyi barci ba".
"Naka wasa ne kana tunanin Zan iya barci banji komai daga gareka ba Nima ban Amayar maka da abinda
ya faru bayan baka nan ba".
"To ai shikenan Bari nayi wanka na fito inaga kwanan zaune zamuyi yau".
Ya shige ainihin dakin da yake sauka idan yazo wani aiki kasar bata yarda ya sauka a hotel ko Daya daga
cikin gidajensa, inda Allah ya taimakesu Abbas Dan kanwar Abbie ne Kuma sa'anni suke da yayunsa gashi
tasu tazo Daya da mahmud sosai Dan kusan tare suke aiwatar da ayyukan kamfanonin Abbie.
Bai Dade ba ya fit Yana baza natural kamshinsa ya zauna yana fadin hada min coffee sai zance yafi tafiya
dai dai".
Ta tashi ta nufi kitchen tana fadin. "Bari na hada coffee maker yanzu na kawo maka".
Tashi yayi ya nufi dakin da Zahra take, a hankali ya tura kofar a kwance a tsakiyar bed din ya hangota da
wayar ta a yashe a gefe da gani batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba.
A hankali ya tako har gaban gadon Yana Kare Mata kallo a cikin dim light din dake dakin, Dan sunkuyawa
yayi daidai lips din ta ya Bata light kiss ya shafa gashin kanta a hankali, wayar ya dauke ya Dora Kan bed
side ya gyara Mata blanket din ya rage karfin A/Cn ya tofa Mata Addu'oi ya ja Mata kofar ya fice yana Jin
wata irin kewarta.
A tsaye ya samu Aisha da kallon tuhama ta bishi, yana kallonta Sarai yayi Mata fuska.
"Bani idan ya Zama ready".
Ya fada yana Mika Mata hannu.
Kada hakuri tayi ta kalleshi idi cikin ido.
"Wai wacece wannan yarinyar a gurinka? Kuma meye dangantakarka da ita Naga ka shiga inda take alhalin
ba muharraminta bane Kai?".
Ta fada tana tsare shi da Ido amma zuciyarta sai dokawa take Bata fatan abinda take sak'a Mata ya kasance
gaskiya.
"Ple Aisha zauna ki nutsu ki tambayeni duk abinda ya shige Miki duhu".
Bataki tasa ba zaman tayi tana Kara jaddada Masa tambayarta akan dangantakarsa da Zahra.
"Wai meye damuwar ki da ita ne na fada Miki 'yar uban gidana ce, daga haka me kike son ji Kuma?"
Lokacin da suke wannan maganganun ita Kuma Zahra kishirwa ta tasheta Karamin fridge din cikin dakin ta
duba Babu ruwa a ciki Wanda Kuma Auntyn ta shigo Mata dashi dazu ya huce bazeyi Mata dadin Sha ba.
Kofa ta bude ta fito da niyyar zuwa kitchen ta dauko ruwan ta saka ma a fridge din dakin, maganganu ta
rinka jiyowa kasa kasa da farko har tsoro ya kamata sai daga baya ta ringa jiyo maganar Mahmud ne da 'yar
uwarsa.
Abinda taji ya masifar daga hankalinta.
"Na fada miki babu komai a tsakanina da yarinyar nan kina ganin Zan iyayin gaban kaina nayi Aure ba tare
da sanin iyayena ba? ki rubuta ki aje duk abinda Ammi ta yanke a kaina na karba ita zata nemar min matar
aure da kanta, idan kin tuna ta taba fada tayi min Mata a Niger,Wadda har aka kawota tayi sati biyu a
lokacin Abbie ya Hana maganar to yanzu zanje natsuguna a gabanta na nemi yafiyar abinda nayi Mata
Kuma ta zabar min duk wadda tayi Mata Zan karba da hannu biyu tunda ni dai babu Wadda na gani ta
kwanta min da sunan Aure, Kinga gara ita ta zabar min da kanta"..
Ai jikin Zahra karkarwa ya fara me yake nufi duk abinda yake Mata pretending ne ba gaskiya ba kenan? Da
kyar ta Kai kanta dakin Dan tana shiga ta zube a kasa tana fadin .
Naga ta kaina Ni Zahra Ashe ni kadai nake kidin girbina bani da wata kima da daraja a idanun Dan tahalikin
nan?.
MAMAN FATEEMAH.
09061432330
Or
09055362975
Page 71
..…....
Sai da Zahra tayi kukanta ta bawa uku Lada sannan ta share hawayenta tana hakurkurtar da kanta, lallai
irin wannan cin fuskar da ciwo ita meta rasa da yake gudun nunata a matsayin matarsa? Wai 'yar
ubangidansa, To ita Kuma zata Kama Kanta in Sha Allah ba Kuma zata nuna taji hirar nan tasu ba.
"Ya ubangiji ka shiga cikin lamarinta ka Bani hakuri da dangana bisa jarabawar da kake jarantata da it's
Dan isar fiyayyan halitta Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w.".
Ta fada a fili tana tashi daga inda ta zauna tana kissima abubuwa da yawa a wannan karo.
Amma dole ta nemi tudun dafawa dole ta iya Kanta tunda abun yazo da cin fuska har ze ringa gudun hada
kansa da ita.
Ranar barci dai sai barawo, kwana tayi tana nafilfili da rokon ubangiji mafita.
Bayan tayi sallar Asuba ta koma ta kwanta lamo batajin zata iya fadawa kowa wannan maganar zatayi
hiding din kayanta taci gaba da addu'ar samun mafita a gurin lillahil wahidul Qahhar ya shiga duk
lamuranta.
Da safe kin fitowa tayi har Aunty Aishat ta biyota daki, Tana ganinta Zahra ta tashi zaune tana fadin.
"Ina kwana Aunty, Ina Afnan da Abul?"
"Lafiya kalau, ya bakunta Kuma? Afnan Kuma Bata tashi ba sai takai twelve tana barci in dai ta farka da
Asuba, shi kuma Babana ya tafi school"
"Ok. Allah sarki".
Zahra ta fada tana Dan Jan blanket din zuwa jikinta saboda yanda rigar barcin take sai a hankali.
Dan zama Aunty Aishat din tayi gefen gadon.
"Ki tashi ki shirya kiyi break yau zamu shiga Asibiti a duba ki,tun jiya nayi Mana booking na ganin doctor
din, kinsan Hussein sai a hankali idan yaso Abu to babu sauki bare Naga ya dauki lamarinki ba Nan kusa
ba".
"Nifa Aunty ki fada masa na warke tun a Nigeria fa,na biyoshi ne kawai saboda na duba jikin Baba
Malam,Kuma wallahi azumi nakeyi yau".
Tsare Zahra tayi da Ido sai taga yanayin yarinyar ya canza ba kamar jiya ba, Amma dai batace komai ba ta
tashi tana fadin.
"Bari na fada masa".
Ta fice duk zuciyarta babu Dadi da gaske yarinyar tayi wani irin collapse Wanda Bata San dalilnsa ba.
Tunda Aishat ta wuce yace duba tsadedden agogo Rolex dake hannunsa, shifa jiya da kyar ta iya barci ba
tare da ita ba a jikinsa sau uku Yana zuwa kofar yana jinta bam da key a rufe.
Sai Zuba Ido yake yaga ta bullo, Maimakon ya gansu su biyu sai yaga Aishat ita kadai ta dawo.
Kasa hakurin ta karaso yayi ya tashi ya nufi inda take.
"Tana Ina Kuma? Lokaci fa Yana tafiya nifa tun seven thirty na shirya".
Wani kallo tayi masa ganin duk ya wani rude.
"Tace ita babu inda zata ita ta warke, kuma da azumi ta tashi bazatayi break ba".
"What!! Bata da hankali ne? wane irin ta warke duka last week fa tayi ta fama da bleeding duk ta daga min
hankali, shine yanzu zata fadi haka, salon mu koma Kuma wata matsalar ta taso, tasan halin Dana shiga a
wancan lokaci Bari naje na sameta".
Ikon Allah Aishat ta tsaya tana kallo, lokaci Daya ya daga hankalinsa ya wani birkice, Wai me taji Yana fada
ne? Me kalamansa suke nufi idan ba Rami me ya kawo zancen Rami.
Da sauri ta rufa Masa baya duk ya wani susuce lokaci Daya ita ba taga abin daga hankali ba tace Bata so
Amma lafazinsa sun sakata a kokonto ba Dan kadan ba.
Da zafinsa ya Kama handle din kofar sai dai tayi locking dinta, a zafafe ya Fara dukan kofar Yana fadin.
"Precious me kike nufi da baza kije Asibitin ba? kina son ki tayar min da hankali ne ko? maza bude ki fito
mu tafi tun jiya aka Gama komai".
Tsayawa Aishat tayi turus Jin kalaman da yake fada Wai ko ya manta a Ina yake ne?.
"Previousss...."
Ta fada a hankali tana girgiza Kai komawa tayi tunda Allah baisa ya ganta ba.
Ita Kuma Zahra tana jinsa yanda ya ambaci precious sai taji wani irin bacin Rai ya lullibeta wata harara ta
zabgawa kofar tana gunguni a ciki.
"Saina shayar da Kai ruwan mamaki saika karyata kanka da kanka Wallahil Azim, Ni Zahra nafi qarfin cin
fuska gurin 'yan uwanka saina saiwa kaina kimar daka Zubar min sai ka nunawa duniya ni wani bqngare ce
ta rayuwarka".
Toilet ta shige taba iska ajiyarsa.
Kasa hakuri Aishat ta dawo, Bata karasa inda yake ba daga dan nesa dashi ta tsaya tamkar a yanzu ne ta
biyo shi. "
"Wai menene na tada jijiyar wuya, tace bataso ka qyaleta Mana ba lafiyar jikinta bace, ka wuce kawai Nima
Ina son na shiga kasuwa saboda wasu Abubuwan amfanin sunyi kasa".
Wani duban Baki da lissafi yayi mata.
"Wai kinsan wahalar da Tasha kuwa, Kinga yanda ta daga min hankali kuwa? Kin..."
Ai baisan lokacin Daya ci wani burki ba shaf ya manta Aishat fa Bata San komai dake tsakaninsu ba.
Tahowa yayi ransa a hade ta rufo Masa baya, Zama yayi ya dafe Kansa.
Daga sama ya tsinkayo maganar Aishat.
"Wai meya jawo dacin rai haka daga fadin Bata zuwa Asibiti,Kuma sai sakin magana kake kamar da wani
Abu a tsakaninka da wannan yarinyar ni ka fada min kamanta bama rufewa juna damuwa ko farin ciki tare
fa muke sharing".
Bai dago ba Bai Kuma tanka Mata ba.
"Miskili kawai".
Ta fada a zuciyarta.
Itama Bata Kara tofa tata ba tayi wucewar ta sama.
Da Ido ya rakata Yana ayyana subul da bakan da yayi.
Lokacin da Zahra ta fito daga wanka Bataji motsinsa ba, ta kuduri aniyar sai dai wani tsautsayin idan ya
gotta ya ganta Amma ta haramtawa kanta haduwa dashi.
Yafi zaman awa Daya da rabi ko motsinta Bai Kara jiba ya koma kusan sau uku, amma babu canji dakin dai a
rufe.
Dole da yaga Babu sarki sai Allah ya hakura ya wuce Asibitin gurin Baba malam.
Yana ficewa Aishat ta sauko kasa ta nufi dakin da Zahra take knocking tayi Tana Kiran sunanta.
Lokacin tana chart da sajida tana fada Mata next week zasuyi graduation, taji kiran da Aunty Aishat din ke
Mata, tsam ta taso ta bude kofar arba tayi da Afnan wadda akayi Mata gayu sosai sai kamshin Bom-bon
tajeyi zallo ta Fara tana dariya, hannu Zahra ta Mika ta amsheta tana matsawa daga hanya.
"Sannu Aunty,ko fita zakiyi ne?"
Zahra ta fada tana Zama a gefen gado ita Kuma Auntyn ta zauna a Kan sofar dake dakin, kallon Zahra tayi
Ido Cikin Ido.
"Me yasa Kika rufe daki kina Jin bro Yana Miki magana kikayi kunnen uwar shegu dashi ko da wani Abu a
tsakaninku dashi?".
Girgiza Kai tayi.
"Ba komai Aunty Ina wankane Kuma na rufe jacuzzi din shi yasa ban jiba, Kuma maganar asibiti mijina ne
yace na Bari ba sai naje ba tunda an tabbatar da narkewar ciwon kada a jogalo min wani Abu daban,
lokacin da muka taho Baya nan sai Abbana ya hadoni da Ya Mahmud tunda Shima zezo India din, sai a
dubani sosai to jiya bayan na shigo ya kirani yace sunyi magana da doctor Hajara tace babu komai kawai
dai nazo yawo ne, shine yace to kada naje wani asibiti zeyi magana da Ya mahmud din Ina ganin ya manta
ne ko sai yau ze fada Masa".
Ta karasa maganar kamar Dade duniya haka akayi ta.
Kallonta Aishat keyi tunda ta ambaci mijinta ita fa nema suke su caza Mata Kai kowa da nasa salon, shi
yana wani furuci dake nuni da ita din kamar suna da wata alaka da daf da daf Dan yanda ya ture dazu ita ya
saka Mata shakku a cikn furucin nasa, itama kuma gashi tayi wata magana wadda tayi karo da zarginta
kuma.
Nisawa tayi tana fadin "Allah ya rufa asiri".
"To Zaki zauna a gida ne keda Afnan ko kuma Zaki bini muje kasuwa? To ai Kuma kina azumi kada ki kwaso
kishirwa".
Zubut Zahra ta Mike da Afnan a hannu tana fadin.
"Muje Aunty Nima Ina son nayi sayyaya Naga gari Kuma".
"To kin fadawa mijinki zakiyi yawo ko?"
Ita ta rasa wane irin lamari ne haka idan ma da wani Abu a tsakaninsu to a Cikin gidan Nan ya faru Dan jiya
harta kwanta lafiya kalau suka rabu da ita, Amma wayewar garin yau aka tashi da wannan sabon canjin
daga gareta.
Har Abbas suka sauko Yana inda suka barshi,.bayan Abbas yaci abinci ya dawo kusa da mahmud ya zauna.
"Wai me yake damunka ne ko baka da lafiya mu wuce asibiti? Ko Kuma malantar ce tasa ka zama haka?
Kasan ku alarammomin nan da izza kuke".
Ya fada Yana dariya, shima mahmud din dariyar yayi.
"Kai Amma Aishat kin kware gurin kinibibi yanzu har kin fada masa wannan maganar gaskiya min Dena sirri
dake tinda yanzu babu Aminci a tsakaninmu kina da naki ma'amincin".
Itama dariyar tayi tana nufar corridor din dakin Zahra, tana tunanin wayon yarinyar da gani akwai abinda
suke boyewa su duka Dan da alama horo ne take Masa a Cikin ruwan sanyi Dan ko rantsuwa tayi bazatayi
kaffara ba da wata a kasa.
Cikin ikon Allah tana kokarin knocking taga Zahra ta bude kofar tana sabe da Yar gidanta Wanda ta tashi
daga barci.
"Sannu Aunty, gata ta tashi tun dazu batayi dai kuka ba na Bata fresh milk dai sai Naga gara Tasha natural
nata dai".
Ta fada tana Mika Mata Afnan din, abun mamaki sai yarinyar taki zuwa gurin uwar.
"Huta roro Nima na huta da tsotsa, amma kuzo muje ki gaisa da sweet heart ya dawo shine ma yake
tambayar Afnan din tunda yau Abulkhairi baya Nan yaje week end gidan Dr Suraj abokin Daddynsa".
"Allah sarki shi yasa banganshi ba Ashe baya gidan".
Bata bukatar komai Dan ta yafa wani veil Amma karamine ta saka abaya Dubai maroon Mai adon stones
kanana saita haskata sosai yarintarta ta Kara fitowa da wani sirrin kyau Dan asali ga kanshin turarenta da
Kuma irin Wanda Hajiya Amina ta hada Mata masu janyo Hankalin oga duk irin kamewarsa kuwa.
Tare suka Jero suna magana wadda tasa Zahra yin wani tsadedden murmushi sai akayi dace duk su biyun
suna facing din hanyar.
"Tabarakallahu ahasanil kaliqin".
Abbas ya fada.
Shi Kuma Dan gogan ya kasa dauke idanunsa daga kanta sai yaga murmushin kamar da gayya take yinsa.
Cikin takunsu na matan da suka San takan gayu suka karaso parlourn, sallama Zahra tayi.
Abbas ne ya samu zarafin amsawa shi kuwa mahmud tamkar an rufe Masa Baki, ai shi Abbas Bai zaci haka
zahrar take ba yanda sweetie ke bashi labarin ta Sai yaga ai Sam Bata iya fasalta mutum ba.
Afnan na ganin Daddy ta shiga irin rawar murnar kaga abinda kake so din nan da Yara sukeyi tana zillo
gurinsa zahrar ta nufa da nufin ta kaita.
Ita da duk saura ba Wanda yaga lokacin da mahmud ya diro gabanta Dan ja da baya tayi da sauri tana
fad'in.
"Subhanallahi! Lafiya meye faru?".
Baiyi wata wata ba ya rungumosu ita da Afnan din dake hannunta.
Kici kicin kwacewa take Dan Bata taba tunanin zeyi irin wannan danyan aikin ba.
"Na shiga uku! Aunty ku taimaka min Dan Allah ku janye shi inaga bashi da lafiya kada yayi Mana illah Ni da
yarinyar nan".
Ta fada tana kuka.
"Wallahi bazaki sakamin ciwon zuciya ba kin hanani sakat tun safe kin Hana ko fuskarki na gani,kinki yarda
muje asibiti, me nayi Miki Mai zafi haka har kike ikirarin Wai mijinki ya Hana kije Asibiti, waye mijin naki
bayan ni? Fada mini!!!..????"
Ya fada Yana hargagi abinda Bata taba gani ba kenan a iya zamanta dashi,kuka Afnan ta kwallah saboda
yanda ya matsesu ga Kuma hayaniya da yake musu.
Da sauri Abbas ya taso yaga mahmud din kamar baya cikin nutsuwarsa.
Hannunsa Daya ya kamo sai yaji jikin nasa na tsuma.
Daidai kunnensa Abbas yayi magana.
"Pls sakarta kaga ka saka yarinya kuka, ka nutsu ta fada maka me yasa tayi hakan kowa ai yasan taka ce Ina
ga da abinda kayi Mata Mai ciwo".
Da kyar ya yarda ya saketa ita da yarinyar. Zaunar dashi Abbas yayi ai Zahra na Dora yarinyar a cinyar
uwarta lokacin Abbas na can Yana bashi Baki ta fice.
Tana shiga tayi locking din door tana sauke numfashi tare da goge 'yan hawayenta na karya data kakarosu.
"Wallahi saina rama zakayi bayani da bakinka guy ni zaka yiwa cin fuskar da ze Zubar min da daraja da
kimata sai zuciyarta da Bakinka sun Fadi gaskiyar da kake boyewa, Kuma Wallahil Azim addu'ar tsamiya
yanzu na Fara har FAHAZAMUHUM BI'IZIMILLAHI YA WADUDU YA JAMI'U MALIKIN NASI MALIKI
YAUMIDDIN zanta zabga maka sai ka Raina kanka kasan Dan an baka kyautar zahra ba Yana nufi Zan Zama
matar shige ba, sai duniya ta shaida zahrar Zahra ce, tayi kwafa ko yanzu na rage tension ko ya yake tunda
kaima kaji a jikina ka Kuma karyata maganar daka fadawa 'yar uwarka jiya, Wai bakaga wadda tayi maka
ba, sai kasan bayanin da zakayi musu Kuma tunda magana zarar bunu ce bata komawa.
Lokacin da Abbas ya juyo da zummar yiwa Zahra magana yaga sai filin gurin kallon Ina take ya yiwa Aishat..
"Ta gudu Ina zata tsaya ya nakasa ta yayiwa mijinta asara,kuma saboda Allah sai ka kakume Matar mutane
da yammacin gari yaushe ka Zama haka yarinya da aurenta da komai wannan kasan haramun ne basai an
fada maka ba, Ina cewa gida Daya kuka zauna ba diyar malaminka bace me yasa kasan kana sonta kayi
shiru har wani ya aura ni Naga kokarinsa Daya amince ka taho Masa da irin wannan diamond baby din
wata uwa duniya baya tsoron sharri shaidan ya gitta tunda gashi a gaban mutane ka iya rungumeta yaya
idan daga Kai sai ita ne ai labarin ba irin wannan bane ki.."
"Stop!!!..... Aisha, ni kike fadawa abunda yazo bakinki? to Zahra halaliyata ce matata ce ta sunna".
Ya fada a zafafe tashi yayi ze fice da sauri Abbas ya riko shi.
" Dawo magana zamuyi ta fashimta".
Baiyi gardama ba ya dawo ya zauna, ita dai Aisha rasa ta cewa tayi wai barawo a hannun Mata.
Very close dashi Abbas ya zauna ya riko hannun mahmud Yana fadin.
"Munji matarka ce amma yanda sweetie ta fada min kace matar ubangidanka ce me yasa ka boye mata
Bata cancanci haka ba, kasan irin wahalar Dana Sha da ita lokacin da case din Nan ya taso? yanda kasan
zata zautu wallahi Amma sai ka dawo Mata da wata fuskar daba taka ba duk rintsi bakwa rufewa junanku
komai, kasan ta fada min cewar wallahi matarka ce Dan ta shaida bazaka taba yarda kayi tafiya da mace
irin wannan da mace kamar wannan babu alaka Mai karfi a tsakaninku".
Mahmud ji yayi duk ruwa ya cinye shi yarinya karama ta dagula masa lissafin da tasa ya saki layi duk yanda
yake shirya nasa planning din ta rusa a lokaci daya yayi amansa ya lashe.
"To tayi hakuri ni kaina bansan me yasa na kasa fada Mata ba Ina Jin nauyin yanda Zan tunkari Ammi da
Abbie da wannan maganar ba wallahi, sai Naga nayi wani Abu Daya sabawa al'adar mu ta Malam
bahaushe, Kuma ita na rasa abinda nayi mata lafiya kalau mukazo gidan Nan Amma ta sauya min na rasa
abinda yake min dadi wallahi Ya Abbas yarinyar nan itace weakness dina a rayuwa ni kaina nasan hakan,
itace fa wadda nake fada maka na gani da dadewa a jirgi ita da Abbanta ka tuna?".
"Off cause anyi haka,Amma how comes hakan ta faru?".
Furzar da iska yayi daga bakinsa.
"It's long story, idan ka huta zamu tattauna akai, yanzu dai ki tashi like kiyi min Biko tunda Naga alamar
kina da masaniyar laifina".
Baki Aishat ta dafe da hannu Wallahil Azim ban sani ba, nifa duk abin Nan hasashe nake yi ban tabbatar ba
sai yanzu, ni wannan aikin ba nawa bane Kai zaka gyaro kayanka da abinda kayi Mata tunda Naga Bata da
kwaramniya Sam, Kuma ya zakayi da ita kenan? Zakaje kace ga matata nan tsaraba fushin da nayi ko Yaya
za'a kayi?".
"Ki Bari kawai alkawarin da nakeso kuyi min mu rufe maganar nan a nan duk da Faruq ma ya sani amma
nasan tunda na kada Masa warning bazeyi karambanin fadawa kowa ba, nina taro match dina Ni zanyi
playing din kayana kawai kuyi min addu'ar samun nasara kada Ammah tayi min nak'i".
Ya fada Cikin raunin murya.
MAMAN FATEEMAH
09062432330
Or
O8055362975.
Page 72
........... Cikin kankanin lokaci mahmud yaji ya Dan samu nutsuwar Daya rasa, yarinya karama ta saka shi
sakin layi a gaban mutane, ita dai Aishat sai jijjiga Afnan takeyi wadda har lokacin take 'yar mita, tashi
Mahmud yayi da nufin barin gurin, Ya Abbas ne ya riko Masa hannu Yana girgiza masa Kai.
"Dawo magana zamuyi ta fashimta, baiyi gaddama ba.
"Kana ji yanzu ka Bata sarari ta huta ta Kuma Huce daga fushin da tayi da kai, idan so Samu ne ka koma
gidanka ka kame kanka, kada ka Bari ta Kara ganinka Nan kusa har sai an Kai wani limit da zata nemeka
ruwa a jallo ta rasa yanda ko kun hadu babu saura fishi sai dokin ganinka dole ba Zama very strong a fannin
soyayya Kaine namiji kada ka yarda ta gane itace rauninka, sannan dole ka koyi takatsantsan kasan inda na
dosa idan ba haka ba za"ayi amfani da wannan damar a cutar maka da ita Koda ta furucin Baki ne".
Shiru mahmud yayi Yana saurarensa wato shi kansa zaman takewar auren sai an shirya mata, Dan rausayar
da Kai yayai yana fad'in.
"Anyway shike nan,Amma da so nake ta yarda muje asibiti su dubata tukunna sai na wuce din".
Wani kallon me yake damunka Ya Abbas yayi Masa.
"For God sake! Ashe bazaka Zama Mai karfin ba kenan? Tunda nace ka kame kanka ai sai kayi yanda nace
ko, tashi mu fita ja rakani na dubo patient din namu ma ida discussion din a hanya tunda Naga alama ka
rifta da yawa".
Ya fada Yana Masa dariya, sumar kansa ya shafa shima Yana murmushi.
Bayan fitarsu Aishar Goya Afnan tayi so take tayi barci, Bata Kara bi takan Zahra ba ta shige kitchen ta Dora
ruwa ta dauko kaza ta Fara gyarawa ta Dora a wuta ta debo fresh fruits ta wanke ta Fara hada fruits salad
ta saka a fridge tayi lemon kankana da Madara pepper chicken tayi da chicken rice sai coslow data hada ta
dafa ruwan tea Mai hadin spices masu Dadi na dafa tea kafin magariba ta Gama komai, Babban tray ta
hadawa zahra kayan bude Baki ta aje a gefe sannan ta ringa fita da nasu zuwa dinning tana jerawa Saida ta
Gama komai ta dauki na zahra lokacin har duhun magariba yayi, knocking Daya tayi Zahra ta bude Mata ta
matsa gefe tana fad'in.
"Sannu Aunty da aiki Aunty".
Ta fada tana karbar kayan Amma taki yarda su hada Ido.
"Zanje nayi sallah idan na Gama zamu zauna dake Ina so mu tattauna wasu abubuwa".
Aishat ta fada tana juyawa.
"To Aunty zanzo basai kin dawo ba".
Dan dakatawa tayi da tafiya ta waiwayo.
"Kiyi zamanki ai Amare 'yan lalashi ne, ni zanzo on behalf of my beloved brother".
Ta fada tana dariya, itama zahra murmusawa tayi.
******Daga gida direct Asibiti su Mahmud suka nufa, sun samu Habib da Abubakar, Ya Abbas yayi
mamakin ganin Abubakar a gurin sosai Amma baice komai ba kenan da wadanda mahmud yayi hijirar
dasu.
Lokacin Baba malam Yana zaune suna Hira, har gabansa su mahmud suka karasa suka gaishe shi da Kara
suba shi, sannan su Habib suka gaishe dasu mahmud, Ya Abbas ne ya kalli Abubakar Yana fadar.
"Wato har Kai gurin kufe Mana gaskiya ko? Kana ji ana ta Fadi tashin nemansa kayi fumfurus kana kallon
kowa daga karshe ma akace ka canza gurin aikine".
Sadda Kai yayi yana Dan sosa gefen wuyansa, gyaran murya Baba malam yayi Dan duk da bayanin matsayin
Ya Abbas da mahmud yake basa baisa ya dauke hankalinsa daga maganar da Abbas din fada ba.
Jin gyaran muryar Malam yasa suka juyo gaba Daya suna kallonsa.
"Ayi Masa Afuwa shima Mai bin umarni ne,sai yanda akayi dashi kada aga laifinsa amanar kenan da baya
da Amana baze yarda dashi irin haka ba. Allah yayi albarka ya kiyaye gaba, ai karfin addu'a ne yasa komai
ya Zama tarihi naji dadin ganinka sosai Malam Abbas Dan Allah kayi min aikin Dana kasa ka maida min
Dana gida tare da iyalinsa ka bawa mahaifinku hakurin karambanin da mukayi musu wallahi nagarta muka
duba ba komai ba tunda Bamu San gaibu ba, in Sha Allah idan lafiya ta Samu Ina Nan zuwa sokoton da
kaina".
Waje su Habib suka fice, ya Zama daga Malam din sai su Ya Abbas.
"Babu komai Malam Allah ya baka lafiya, muke da godiya ya fada min duk dawainiya da kayi dashi tunda
kuka tsince shi har kawo yanzu ai kaima ubane ka Isa kayi yanda kaga dama dashi, Allah ya Kara lafiya da
sutura yasa kaffara akeyi in Sha Allah amanarka Zan idata, ai mu bamu da Bakin godiya sai dai ubangiji ne
ze biyaka".
Sun Jima suna tattaunawa anan Malam yake farawa Abbas yanda kayiwa mahmud makaru abinda Bai taba
fada Masa ba sai yanzu yakeji, har wasu hawayen gefen Ido Mahmud yaji sun taro Ashe haka akaso a
kassara Masa rayuwa Allah yayi Masa gada da Rahama ya kawo Habib ya gashi a gurin da yake a yashe a
kasa.
Anan sukayi magariba sukayi insha'i sannan sukayiwa Baba malam sallama, mahmud ne yace suje su duba
jikin Alhajin su Aunty surayyar uncle Mustaphan Shima Yana nan.
Shima sun samu 'ya'yansa maza biyu sunzo duba jikin nasa, sun gaisa tare da jajanta musu, shima Alhajin
jikin da sauki sosai Dan har Yana takawa shima da karfe.
Gida suka koma mahmud yayi dinner tare dasu, haka Nan yayi ta maza bai nemi zahra ba Suma babu
Wanda yayi maganar ta har suka gama, Mahmud Bai wani zauna ya shiga dakin da ya mayar nasa tun ba
yanzu ba ya dauko laptop din da wayoyinsa ya fito.
"Ka Bari na saukeka Nima Ina son fita ne".
Ya Abbas ya fada.
"No, ka barshi kawai nayi waya da Mr salahuddeen Yana kusa da isowa, kawai dai Alfarma za'ayi min twins
zasu shiga Nigeria a tsakanin kwanakin nan harna Fara musu processing na visa harda yaran duka".
"Ba damuwa Nima Ina son suje Nigeria din to saboda makarantar Abulkhairi ne, Amma yanzu dole suje
tunda ta Kama amma naji kana fadar kana nemar musu visa Kai kana Nan kenan?".
Kai ya girgiza Yana fadar "A'a akwai dalilin raba tafiyar ne jikina Yana bani wani Abu da bansan ko menene
ba".
"To Allah ya rufa asiri, Zan fadawa sweetie ka wuce tana can gurin 'yar daru ita da dare take tata rigimar
amma da Rana lafiya kalau za'a wuni da ita".
Dan murmushi Mahmud yayi Yana ayyana Wai babyn su ce da zahra suna tarairayarta.
Yana fitowa harabar gidan motar sayyid tana shigowa, dai dai gurin Mahmud ya tsaya ya kashe motar ya
fito da sauri ya rungime Mahmud Yana fad'in .
"Ina ka shiga a duniyar nan ka barmu da tashin hankali? Munyi nema har mun godewa Allah kasan Umma
cewa tayi a saka nemanka a jaridu da mujallu da kafafen sada zumunta na zamani,Su uncle Mustaphan ne
suka Hana sukace abun ze zama tonon sillil Wanda Bai sani bama ze sani".
Dan zare shi daga jikinsa mahmud din yayi Yana fad'in .
"Ai gashi Nan dawo sayyid ya karatu ace ka koma PhD ko?"
"Wallahi kuwa".
"To Masha Allah. Allah ya taimaka, Nima Zan wuce ne matar abokina na kawowa Aishat su zauna a Nan
asibiti sukazo zataga likita".
Ya mika Masa hannu yayi gaba, sayyid Yana da kirki amma fa gurin lamarin Mata sai a hankali, ko baya Zina
ta zahiri akwai 'yan tabe -tabe.
Yana fita ya turawa Aishat text message a waya.
Amma fa karfin Hali kawai yakeyi Sam zuciyarsa Bata nutsu ya tafi yabar zahra da wannan Karen farautar a
gidan ba, amma dole ya kauda Kansa yayi kawaici da Kara kada Ya Abbas yaga Bai dauki maganarsa ba.
Koda ya koma su Habib suna gida Suma sun baro asibitin, coffee ya bukac Mr Ajey ya kawo Masa ta wuce
ciki Saida yayi wanka ya bude laptop dinsa Yana aiki Yana sipping din coffeen, ya Kai kusan biyun dare Yana
Abu Daya Saida ya tabbatar da komai ya dai daita sannan ya kwanta zuciyarsa da gangar jikinsa suna
mararinta, filo ya rungime a haka barci yayi awon gaba dashi.
Bayan sun sallar Asuba barci mahmud ya koma knocking din da ake a kofar bedroom dinsa ya tashe shi
daga barcin da yake Mai Dadi Wanda ya saka shi nishadi.
Umarnin budewa ya bada Yana daga Cikin blanket dinsa.
Mr sunny ne Mai yin share share da goge goge.
P. 73
........... Tunda Zahra ta farka daga barci taji Sam Bata Jin Dadi jikinta ita ba Mai zazzabi ba duk jijinta ciwo
yake Mata, ta Kuma kasa fita Dan Bata son su hadu da Dan gidanta kada ya Kara Bata kunya Dan taga
alama tasa tayi kaura daga idanunsa sai ya iya yi Mata abinda yafi hugging ma ga Kuma uwa uba tana Jin
bala'in nauyi Ya Abbas tunda ko banza yayan mijinta ne ya wani kwakumeta ko kunya babu, agogon waya
ta duba karfe Tara saura kwata na agogon kasar, tattaunawrsu da Aunty Aisha ta ringa dawo Mata tiryan-
tiryan. Tasha mamakin halin da aka saka mahmud Ciki yaga masifa da tashin hankali ace kowa yayi maka
naqi, kuma dadin dadawa kowa ya kasa fashimtarsa, ta yarda kamar yanda Aunty Aishat din ta fada abun
an Dade ana shirya shi Saida aka Sha Kan kowa sannan aka fasa maganar, kuma tayi wani irin tasiri Banda
taimakon Allah da wani labarin akeyi ba wannan ba.
Yunkurawa tayi ta tashi sai taji tana bukatar kasancewa kusa dashi ta lallashe shi, abin tausayi be kuma
abunda ya fada gaskiya ne, sai yanzu ta gane gundarin me maganarsa take nufi duk da na gari dole yabi
iyayensa, kawai shedan ne ya tunzura ta ta hau dokin zuciya Mai mmakon ta Zuba Ido taga yanda abun ze
kasance sai ta kasa ta hau fushin fari, ai dole ma hakan ce zata kasance tunda Yana da magabatansa, idan
sun amince da auren da akayi Masa laba'asa idan Basu amince ba shikenan.
Tana zuwa wannan gab'ar taji wata irin faduwar gaba, kada fa iyayensa Suki yarda da ita a matsayin
mararsa.
"No!!!. In Sha Allah mutu ka raba takalmin kaza.".
Ta sauko daga gadon gara ta fita ko tayi arba dashi tayi yanda tayi ta Shawo Kan kayanta.
Wanka ta shiga shaf-shaf ta fito ta shirya ta saka rigar cotton lace marar nauyi tana baza kamshinta, bata
daura dankwalin lace din ba karamin gyale ta Dan rufe gashinta dashi ta sako plat shoes ta fito zata shiga
kitchen tayi musu abin break fast kada ta Zama cima zaune sai dai ayi a Bata.
Parlourn ba kowa shiru sai karar a/c kakeji kawai sai Kuma sansanyan kamshin turarukan daki tunda
gidansu akazo, kitchen ta nufa Kai tsaye saboda tana da yakinin masu gidan Basu tashi ba, da sauri tayo
baya ganin mutum tsaye Cikin kitchen din daga shi sai boxer short da singlet, shima Jin motsi daga bayansa
ga wani scent Mai shegen Dadi ya bakunci hancinsa yasa shi juyowa babu shiri.
"Ya subhanallahi!".
Ya fada lokacin daya Dora idanunsa Kan fuskar Zahra, da wani mahaukacin sauri ta juya fit ta fice daga Cikin
kitchen din, shima sayyid da sauri ya aje cup din Daya dauko ze Zuba coffee din daya dafa.
Ko duriyarta sayyid Bai gani ba sai dai kamshin da tabar Masa.
Zahra na shiga daki ta Danna Masa key tana maida numfashi.
"Waye wannan Kuma da yake da irin wannan freedom din a cikin gidan matar aure irin haka? Gaskiya
wannan rayuwar da sake, dole meu amor yazo su bar shi ai da matsala sosai gidan musulmi Kuma matar
gidan Matashiyar mace Mai jini a jika, shaidan ake gudu gaskiya.
Wayarta ta dauka tana neman Aunty Hassana su gaisa.
______
Mahmud yana fita kofar baya ya koma ya shiga bedroom dinsa ya dauko abokiyar tafiyarsa jakar laptop ya
shiga mota sai tashin motar uncle Mustapha yaji Dan ya fita har waje baiga mahmud din ba Bai Kuma kawo
Yana Cikin gidan ba.
Da sallama ya shiga dakina da aka kwantar da Baba Malam din Yana zaune shi kadai Yana lazimi ga kayan
break fast Nan an kawo Masa Bai Kai ga cinsa ba.
Sallamar Baba malam ya amsa Yana fadin.
"Sannu da zuwa mahmudu, Amma yau kayi sakko, ya Naga ran naka babu Dadi lafiya dai ko?"
Sayyid ya Jima a tsaye a parlour ko zaga ta inda Zahra zata bullo Amma yaga Shiru dole ya koma ya dauko
coffee dinsa ya wuce dakinsa.
Bai Jima da barin parlourn ba Aunty Aishar ta sakko Cikin gayunta kitchen ta shiga ta Fara aiki tana tunanin
irin yanda Hussein ya gindaya Mata dokoki akan matarsa tana ganin soyayya Amma sai take ganin Dan
uwan nata yayi zurfi da yawa.
Tana Cikin aiki Sayyid ya shigo yayi Shirin fita school.
"Aunty Ina kwanq?" Ya fada Yana shigowa ciki.
"Lafiya kalau Sayyid har an fito yau da wuri haka? Gashi ko break ban Gama hadawa ba".
"No Aunty I am ok, Nasha coffee tun dazu, Wai Ni Aunty bakuwa kikayi a gidan Nan ne ko Kuma gamo nayi
da safiyar Allah wata"Ala?".
Dariya tambayar ta bawa Aunty Aishar,duk yanda akayi yaga Zahra kenan, Amma sai tace masa.
"Meta faru Kuma kake wata magana irin haka?"
"Wallahi Aunty ba maganar jocking Naga yarinyar India ko larabawa a gidan Nan har fa Cikin kitchen din
nan ta shigo muna had a Ido ta fice kamar walkiya ko dana fita ko Mai kama da ita bangani ba wallahi".
"Eh bakuwa ce nayi Baku San juna bane shi yasa ita ma Bata San da zamanka a gidan bane shi yasa inaga
itama tsorata tayi gaskiya".
"Wow! Amma daga Ina Kika samo irin wannan Mai zafin haka? Gaskiya za'a da ita Dan Allah Ina kamu
wallahi daga wannan Kuma kallo ya Kare ki Fara min campaign Dan Allah".
Ya fada Yana hade hannu irin ba 'yan kabilar Hindi na nan Indian din🙏🙏.
Anzo gurin tab Allah kiyaye da mijinta baya nan da a gabansa zeyi wannan kwabar da kuwa sun kwashi 'yan
kallo.
"Wai kana nufi sonta jakeyi kenan?"
"Kwarai kuwa".
Ya fada da tabbatarwa.
"To ai matar Aure ce".
Dafe Kai yayi Yana fadin.
"Oh my God! Waye wannan Mai sa'ar da yayi min shigar sauri Dan Allah?".
"Wanda ya fika sonta ne ya dauke abarsa".
Langabar da Kai yayi Yana fadin.
"Shikenan na wuce school, Amma fa I really loved her".
"Matar Auren?"
Baice komai ba ya saka Kai ya fice daga kitchen din ransa babu Dadi. "Allah ya kyauta, wato mahmud ya
yiwa Sayyid wani irin farin sani kenan, yasan matukar zeyi arba da ita sai an samu matsala gashi kuwa ya
kasa ba marad'a kunya".
Sai da ta Gama komai ta dauko abincin data Zuba musu ita da zahrar a wani guri ta aje basket din ta koma
ta dauko wani Abu kaman story mat da table mat ya shinfida sannan ta koma sama lokacin sweet heart din
ya fito daga wanka, taimaka Masa tayi ya shirya tunda shi azumin litinin da alhamis yakeyi itama Aishar
lalurar mu ta Mata ta hanata dauka, fita zeyi Yana da wasu ayyuka da Mahmud ya turo Masa Wanda zeyi
masa su, tare suka gangaro Aishar ke fadar .
"Bari na kirawo Zahra ki gaisa tunda ba lallai yau ku hadu ba naji kace sai dare sosai zaka dawo aikin da
yawa".
Dan janyota yayi jikinsa.
"Kyaleta ai Dan uwanki ya dasa Mana 'yar kunya a tsakaninmu tunda yayi mata irin wannan wawar
rungumar a gabana kamar ze bude aiki kinji yanda jikinsa yake tsuma kuwa a lokacin?"
"Kai sweet heart Banda fa... Dan kaga baya kusa, shida abarsa har zakace Wai jikinsa Yana tsuma Kamar
wani sabon shiga".
"Ni dai abinda naji nake fada Miki bawai Qage nayi masa ba, Kika sani ko farin shigar ne koma Bai shigan
ba".
Ya fada yana dage Mata girar idonsa Daya.
"Wallahi Kai dai Yaya Babba ne, Banda irin haka da gani kasan ai Yana shanawa dubi fa yanda ya damu
daga Dan turza shi da tayi yanzu ma kaji yanda yake jaddada min na kular masa da ita kamar wata jaririya".
"Ke dai mubar maganar lokaci ne ze nuna".
Har gurin mota tayi masa Rakiya tana fada Masa zasu fita fa.
Sama ta koma ta dauko Afnan wadda ta koma barci tun da akayi Mata wanka Dan kada ta tashi suna can
bazajiyo kukanta ba.
Dakin Zahra ta Dan buga kadan tana fadin.
"Pls open the door" .
Jim muryar Aunty Aishar yasa Zahra tasowa da sauri ta bude kofar tana sakin murmushinta Mai kayatarwa.
"Ina kwana Aunty?"
Ta fada tana karbar Afnan dake barci, can tsakiyar gado Zahra ta kaita ta kwantar.
" Ki fito muyi break fast tun dazu na kawo na koma na sallami sweet heart ne shi yasa".
Tare suka jera zuwa gurin da tayi musu shinfida, abincin gargajiyar ba bahaushe tayi musu kunun tsamiya
ne da kosai sai pepper soup din cow legs.
Suna gamawa Zahra ta kwashe kayan ta mayar kitchen ta wanke su ta aje komai a muhallinsa, taso ta yiwa
Aunty Aishar magamar guy dai data gani sai wata Zuciyar ta kwabeta, Bata sani ba ko kaninta ne shaqiqi
muharraminta.
A gurin ta dawo ta Sami Aunty Aishar tana amsa waya daga ganin yanda take amsawa kasan ba wayar sawa
bace Mai wayar Yana da girma da kima a idanunta.
Zahra Bata zauna ba ciki ta shige tana shiga taga Afnan tana daddaga kafa tana Wasa ta tashi, daukarta tayi
tana fadin.
"My Afee Babyyy.."
Yarinyar na ganinta ta Fara dariya shaidar ta ganeta kenan.
A hanya ma sosai Aunty Aishar ta dinga bawa Zahra Baki harta Dan ware, sun shiaga manayan shagununan
kayan sakawa Ganin Zahra taki daukar komai yasa Aunty Aishar lodar kayan da take ganin sun dace, sunje
bangaren jewelry's ma ta dauka Kamar me shoes and bags ta dauka kamar Gori ita Zahra Abu har tsoro ya
Fara Bata kashe kudi ake kamar yayi daurin cargo aka yiwa kayan Aunty Aishar ta cike komai sannan suka
bar gurin, sun shiga kasuwa nan ma ba kananun kudi ta kashe ba suma awon cargo din tayi musu daga
karshe suka nufi gurin gyaran gashi da jiki Aunty Aishat ta saki kudi ba kadan ba anyi Mata gyara iya gyara,
suna Cikin Yi Mata gyaran jiki matar Mai gurin tazo tana tambayar Aunty Aishar cikin yaren indianci, tunda
su dai basa Jin turanci duk da India suma suna English.
Zaru Aishat din tayi domin ta rasa yanda zata tunkari Zahra da tambayar domin wani Abu matar ta sakawa
Zahra a hannu taga yaki Zama kuma a ka'idarsa na matan aure ne kuma an fada Mata matar Auren ce
gyara kawai za'a Kara yi mata, magana matar tayi Mata akan taje ta tambayar Mata ita saboda tasan wane
iri abubuwan zata yi Mata.
Aunty Aishar ji tayi abun yayi Mata nauyi gaskiya, ai da kunya taje tana titsiye yarinya da irin wannan
tambayar,cewa tayi suyi Mata na 'yan matan kawai mantawa tayi tace musu haka ashe Bata tare ba.
Zahra har Saida ta gaji da Shan abubuwa, Miko Mata ake tana shanyewa Saida taji tana neman yin amansu
sannan aka saurara Mata aka dosa tureren jiki, kunshi ne tace bata son irin nasu Mai yawan Nan sai akayi
Mata Dan kadan Mai azabar kyau, lokacin da aka Gama Mata komai ta fito Saida Aunty Aishar ta shiga
wani shock Dan yes matar bros ta wanku iya wankuwa Ina ma Yana Nan da yau dai saiya maida yawu
kenan maganar sweet heart da kamshin gaskiya kenan tunda idan ba Rami meya kawo zancen Rami ance
an saka Mata abun matan aure yaqi Zama kenan budurwa ce, ita kwamacalarsu nema take tafi karfin
tunaninta.
Sun dauki hanya sosai Afnan na jikin Zahra duk tayi laushi da gani ta gaji, sai 'yar mita take Auntyn ce da
Dan kallo inda suka tana ci gaba da driving din ta, tamabaya ta jefowa Zahra Wai dazu kun hadu da Sayyid
ne da safe?".
Dan Jim Zahra tayi sai Kuma tace "ko wani Dana gani a kitchen daga shi sai boxer short da singlet Yana
tsaye a gurin coffee maker?"
"Eh shi nake nufi".
"Na ganshi lokacin Dana fito da zummar na Dora abin break sai na gashi ba yanda ya kamata ba tunda
baligi ne shi Kuma ba gidansa bane, Kinga ai Bai kamata Yana fitowa a haka ba,ko Dan bansan ya kuke
dashi ba ko mamanku daya".
Wata kwana ta shiga kafin ta danyi tsaki..
"Wallahi kanin sweet heart ne, ni kaina bana son zamansa a gidan tunda idan Yana nan bana sakewa nayi
duk irin shigar da nakeso tunda Allah yasa shi Mutum ne Mai shegen son Mata dan haka yau a sama Zaki
kwana bana son samun matsala Daman abunda yasa na baki daki a kasa Ina muku wani zato ne ashae
hasashena gaskiya ne, yanzu kuwa da baya kasar saina shige dake ciki gudun samun matsalar da yaketa
jamin kunne a kanta".
Nisawa Zahra tayi tana fadin Allah ya kyauta.
Koda suka shigo Basu huta ba abin bude Baki suka yiwa masa.
A tsakanin kwana biyun nan Zahra ta gaji iya gajiya
Kuma Basu Kara haduwa da Sayyid ba,dan duk wata kafa Aishat din ta toshe ta yayi nacin har yayi zuciya
Dan ko kasa Bata saukowa.
Ranar da zasu tafi Mr salahuddeen yazo ya daukesu da kayansu sai a ranar Abulkhairi ya dawo gida, har
dashi za'ayi tafiyar.
Maman Fateemah.
Page 74
............. Mahmud ba Nigeria ya nufa ba lokacin Daya baro India Dubai ya wuce ya samu Sameer a can,
lokacin Daya je Sameer ya Gama duk abinda ya kamata ya hada da taimakon matar abokinsa Tajuddeen,
'yar Kano ce Khadija Basu Dade da Aure ba macece wadda tasan Asalin gayu, lefe ne aka hada na garari set
din akwatuna ashirin da hudu Banda manyan trolleys guda goma, Gold ma Saida aka ciki wani medium kit
dasu, ita kanta Khadija anyi Mata kyautar ban mamaki.
Saida yaga komai sannan yacewa Sameer ya aunasu Nigeria Amma gidansa jikin gidan Hajiya Inna za'a
ajesu sai Aishat ta gani Koda abunda za'a Kara ko za'a canza.
Tare da Sameer suka nufo Nigeria sun samu good 8 hours suna reto a sararin samaniya kafi ubangiji ya
saukesu lafiya a Lagos, lokacin karfe hudu da rabi na Asuba,tickets suka siya Lagos to Sokoto zasu bi flight
din karfe shida da rabi na safe, yayin da jirgin su zahra ya Sauka karfe biyar da rabi na safe a Kano, Suma
jirgin karfe Tara zasu bi zuwa Sokoto.
Cikin kamalarsa da kwarjininsa na halitta handsome guy dashi kana ganinsa kasan yana Cikin ganiyarsu
kkuruciyarsa a hankali yake gagarowa daga steps din jirgin yayin da Sameer ke bayansa rataye da jakarsa ta
laptop. Faruq ne ya tare shi da madaukakiyar murna ya rungime shi ji yake kamar ba gaske ba lokacin Daya
kirasa yake fada Masa yazo airport da mota yayi zaton da Wasa yake Masa duk da babu irin wannan a
tsakanin su, amma qila wa qala yazo bashi da tqbbacin zuwan nasa.
Dan janye Faruq din yayi daga jikinsa Yana Dan doka kafadarsa.
"Welcome back to Sokoto Ya mahmud, Allah ya tsare gaba yasa kafi haka ya doraka kan makiyarka gashi ka
dawo da ranka da lafiyar ka da kuma abinda basaso arzikin naka".
Faruq din ya fada bakinsa yaki rufuwa saboda tsabar farin ciki Dan yayi musu mugun bazata ya shqmmaci
kowa Dan jira kawai ake aga su uncle Mustapha sun taso Qeyarsa su kawo shi kamar wani Dan ta'adda,
domin duk Wanda Abbie yaso maganar kada ta fita Saida ta Zama abin tsegumi a cikin family.
"Just forget about this charpter ai it's past, bani key din sai kayi waya a kawo maka mota ku tafi kaida
Sameer".
Ya fada Yana Mika Masa hannu..
"Ka Bari Ya mahmud na kaika Mana ai zefi Ina Kai Ina driving daga saukarka, gara na kaika har gida Nima na
bada nawa surprised din asan Nima Ina da wani matsayi har yanzu a gurinka".
Ya fada Yana 'yar dariya da shilla kafa kamar Mai Wasa da ball.
"Bani kawai kasan lokacin Dana bar gidan? Ni kadai na fita ni kadai Zan koma I hope you understand".
Kai Faruq ya gyada Masa Yana Mika Masa key din.
Har gurin mota suka raka shi, Sameer ya saka Masa laptop din a back seat ya rufe.
A hankali ya Bata wuta ta Fara tafiya Zuciyar fal da nishadi sabanin lokacin Daya bar garin afujajan babu
nutsuwa Kota sisin kwabo a tare dashi. Tintac glass ne a motar a hankali yake tafiya Yana karewa garin
kallo ba laifi an Dan samu 'yan canje-canje, gidan Hajiya Inna ya nufa Yana ayyana ta inda aka hau ta Nan
ake Sauka.
Dai dai kofar katafaren gidanta ya tsaya sau biyu Yana latsa horn sannan security din ya leko Bai sheda
motar ba Dan haka ya fito kafin yazo mahmud ya sauke glass din a hankali, yana zuwa yayi tozali da
mahmud ai baisan lokacin Daya juya da gudu ba Yana fadin.
"Allah ya taimakeki barka da Sauka". Nan da nan ya saka remote control ya bude gate din mahmud ya
Danna kan motar ciki, wata irin Rahama yaji tana saukar masa kowa ya bar gida gida ya barshi, gidan ya
tsaya Yana karewa kallo a hankali ya furta.
"Masha Allah! Alhamdulillahi bi ni'imatihi tutimmussalihat".
Har abinda be fada bama Faruq yasa anyi, sabon part din da akayi daga gefen na Hajiya Inna ya kalla yayi
wani murmushi Wanda shi kadai yasan ma'anarsa.
"Shadi....." (My happiness)
Ya furta in a soft voice.
A hankali ya bude kofar ya fito, Nan da Nan Malam sabo security ya karaso ya zubewa Yana gaishe shi, tare
da yi Masa barka da sauka, da yake safiyar ce harabar gidan ba kowa sai daga can gefe wasu ma'aikatan su
biyu masu shara da ban ruwan flowers suka taho da sauri bakinsu kamar gonar auduga, daman tun
shigowar motar suka tsaya da ayyukan su suna jiran suga Wanda ze fito daga wannan walfefiyar motar
data shigo.
Ya dan Jima tare dasu daman kusan haka fabi'arsa take, da wuya ya shigo guri ya yiwa ma'aikatansa shaf-
shaf ya kan dauki lokaci tare dasu, to bare shi daya dauki dogon lokaci bai hadu dasu ba.
Bayan ya sallamesu ya nufi kofar parlourn yana Kara yaba yanda akayi renovating din gidan tamkar sake
ginin shima akayi.
Bude kofar yayi ya shiga gurin yayi masa kyau fiye da yanda yayi zato duk da Faruq ya turo Masa ta
whatApps, ya Jima yana tsaye a parlourn kafin yayi kunar bakin wake ya nufi bedroom din Hajiyar.
Dan knocking yayi kadan kamar na munafirci, gyaran murya tayi daga can nesa daga ji Bata Cikin dakin
tsayawa yayi tana karewa dakin kallo komai tsab tamkar dakin Amarya. Dan Hajiya Inna badai tsabta ba ga
kamshin itama ba'a barta a baya ba, a hankali ya zauna a Kan sofa Yana Dan kishingidawa a kai.
"Wai wane irin rashin Hankali ne irin wannan za'a shigowa Mutum daki baya Nan ana ji Kuma Ina gyaran
murya akayi min kunnen uwar shegu Dan an......"
Ai Bata karasa maganar ba tayi wani tsallen albarka tana fadin.
"La'ilaha illallahu Muhammadu Rasulullahi!! Innahu min sulaimanu wa innahu bismillahir Rahamanir
Rahim, me Zan gani a nan?".
Tashi zaune yayi Yana Kare Mata kallo, tanan yanda take sai abinda ba za'a rasa ba na karin kwanakin
rayuwa Dan ma tsufa ne na Jin Dadi.
"Sai ki karaso Mutum ne ba Aljani ba da kike zabga dogon salati, nine na dawo kizo mu Dora daga inda
muka tsaya".
"Kara matsawa tayi kofar toilet din tana Masa kallon rashin amincewa.
"Kai daga Ina idan shedani ne Kai me nayi Mata zaka shigo ka bude min Ido da siffar jikana Dan anga na
kwallafa Rai a Kansa".
Tashi yayi tsam ya nufi inda take Yana murmushi yaga alama ba fashintar yaren Bakinsa zatayi ba gara ya
matsa taga zahiri.
Saida ya karaso kusa da ita sosai ta tantance shine da gaske.
Hannu ta Dora a ka ta fasa kuka tana fadin.
"Yanzu saboda Allah ka kyauta kenan,kayi tafiyar ka barmu da tashin hankali sau uku ana kwantar Dani a
asibiti jinina Yana Hawa ya Kai dari biyar harda dori, nifa duk abinda na fada maka wallahi iya fatar bakina
ya tsaya ba har zuciyata na fada ba, Kai Kuma sai kayi fushin zuciya kayi Mana naki ka barmu da tashin
hankali munyi nema har mun gode Allah Amma babu ko labarin Wanda ya ganka".
Hannunta ya riko Yana fadin.
"Dan Allah ki daina kuka ai gani na dawo yanzu na sauka a garin Nan Kuma banje ko Ina ba duk yanda nake
da kishirwar ganin Ammi amma banje na ganta ba saida nazo na ganki".
Gefen gado ya zaunar da ita tana faman share hawaye.
"Ki daina kuka kinsan kina da hawan jini fa maimakon kiyi godiya ga Allah Daya dawo Miki Dani lafiya harda
ribar kafa, kada kisa 'ya'yan ki suce Zan karasa musu uwa daga dawowa ta"..
Ba zato yaji ta Zuba masa dundu, ya Dan gabtsare Yana fadin.
"Kai Ashe da sauranki irin wannan tsohon Kashi saiki karyani ki jawowa matata jinyar da Bata shirya Mata
ba".
"Ja'iri dubi yanda ka zama kamar a taba ka jini ya fito, da gani ka Sami kyakykyawan masauki, kana can ka
barmu da kwanan zaune da zulumin Ina ka shiga ya kake a Raye ko a mace, Ashe shi yasa wannan uban
iyar yazo ya tashi hankalina da aikin gyaran gida da wasu gine-gine anyi Masa tambayar duniyar Nan akan
aikin daya tarko Amma sai yace Daman da aikin tuntuni a hannunsa Yi ne Baiyi ba sai yanzu dole aka
kyaleshi Ashe da kukus a shinkafa".
"Allah wannan matar bakya gajiya da 'yar cewa ina laifin gyaran da yayi Miki gaki Nan kamar wata amarya,
ko Ina sai tashin kamshi yake Ni tashi ki samo min abinda zanci rabona da abinci tun a can inda na baro
saboda tsabar son ganinki da nake yi, amma sai welcome din dundu na samu inaga badan nayi alkawarin
kezan Fara gani ba da babu abinda ze hanani wucewa gidan mu, da a can ne yanzu da babu masakar tsinke
a gabana Amma ke ko Dan pure water ma babu".
Ya fada Yana mikewa tsaye.
" Ina Kuma zaka daga zuwa shanshani, Kai dai har abada baka Zama guri Daya kamar kifi".
"Ni babu inda zani dakina na kusa da naki Zan shiga na danyi wanka barci nakeji".
Wani kallon baka da man Kai tayi Masa tana tabe Baki.
"Ban gane barci zakayi ba kana nufin har yanzu baka Huce bane ko menene? Bazakaje kaga iyayenka ba
kake neman Mike kafa a nan!?"
Maman Fateemah.
09061432330
Or
08055362975.
Page 75
......... Tunda jirgin su zahra ya sauka a filin jirgin sultan saddiq Abubakar dake Sokoto gabanta ke
faduwa,tasan a Nan ne komai fa ze iya tabbata ko ayi ko a fasa gata a Sokoto sai Kuma abinda Rabbi Izzati
ya hukunta shi ne ze tabbata, Afnan ce a sabe a kafadarta tana takawa a hankali tamkar Bata son taka
kasar Dan da gaske ta Gama yin giving up a cikin Lamarinsu da mahmud.
Aunty Aishat ce tsaye a Kan kayan da sukazo dasu Saida komai ya kammala sannan ta nufo inda Zahra suke
ita da Afnan yayin da Abulkhairi yake biye da ita kafa ya kafa.
Kamar tare Aishat din suke da Sameer Dan tana karasowa shima Sameer Yana karasowa da waya a kunne
da alama doguwar waya yakeyi, saida ya Gama sannan su zahra suka gaishe dashi har Aunty Aishat na
fadin.
"Nayi fushi kaje har India amma ka kasa zuwa mu gaisa".
"Kiyi hakuri kinsan halin kayanki bashi da lokacina a lokacin Kuma infact ma dai bai barni na zauna ba".
"Ai shikenan Daman ku Ina kuke Zama guri Daya tamkar marasa gaskiya Baku da standard gurin Zama dole
ku canza yanzu kun aje iyali suna da hakki a kanku baze yuwu ki ringa Abu babu lisafi ba Daman kasan tun
farko Ammi Bata son wannan dabi'ar taku ko misqalazarratin Sai dai da yake Abbie ya tsaya muku ne yasa
dole ta hakura".
"Wannan gaskiya ne Auntyn mu za'a gyara in Sha Allah ko Baki fada ba zakiga canji ke dai kisa Ido kawai
zakice na fada Miki".
"Allah yasa hakan ta kasance".
"In Sha Allah".
Sameer ya fada yana Dan kallon zahra ta gefen Ido tana ta yiwa Afnan Wasa.
"Madam barka da sauka sokoto Allah yasa mun shigo kenan, yasa Albarka a cikin rayuwar da zakiyi a
cikinta".
Dan murmushi tayi, yayin da Aunty Aishat ta amsa da. "Allahumma Amin, ni jikina ya Gama bani zahra
Alkhairin mu ce".
Kayansu aka dunga jida ana kaiwa mota Sameer sai mita yake yiwa Aunty Aishat akan sun lodo Kaya bayan
Wanda suka turo jiya sukazo yauma ga wasu.
Kunnen uwar shegu tayi masa sufa sunfi son daga su sai kayan jikinsu, tunda suka dauko hanya zahra ke
kallon garin, yayi matukar burgeta ba kadan ba tayi santinsa duk da hankalinta ba a kwance yake ba Amma
ba karya sokoto tayi Mata 💯% sai dai Bata San meze biyo bayan zuwan nata ba, wata zuciyar ta fada Mata.
"Khairan in Sha Allah"
Take ta Fara addu'ar sauka a sabon garin da kaje ba garinku ba, Dan harga Allah ta manta.
"RABBI ANZILNI MUNZILAN MUBARAKAN WA ANTA KHAIRUN MUNZILIN".
Ta fada a zuciyarta tana rokon ubangiji ya dafa Mata a cikin lamuranta gata ta shigo garin da babu uwa ba
uba ba dangin iya babu na Baba sai wannan bawan Allahn shi kadai ta sani, kallon garin taci gaba dayi daga
kasan Zuciyar ta Kuma abubuwa ne rututu gasu Nan.
Wani katafaren gida taga Sameer ya dosa tamkar fadar shugaban kasa, Zahra hankalinta ta tattaro ta nutsu
taga Nan kuma Ina ne Sameer ya kawo su Yana tsayawa a kofar katafaren gate din Mai Kama Dana kofar
gari saboda girmansa wasu masu uniform suka taso su uku suka Karaso gurinsu Sameer kafin su Karaso
sameer ya sauke glasses dan bada da baya,suna sameer ne suka gaisa sannan suka gaisa da Aunty Aishat
da suke zaune a baya.
Katafaren gata din aka bude musu suka shige, " masha Allah".
Abinda zahra ta fada kenan a zuciyarta, wasu gine-gine take ganowa kamar a cikin film, an kawa gefen titin
da flowes masu kyau da fitilu compound din ba mutane sosai sai 'yan tsiraru masu banruwan flowers har
kofar part din Ammi na baya sameer ya kaisu ita dai zahra ba baka sai kunne Dan ba karya gidan gida ne
tamkar dauko ginin akayi aka Dora a gurin a zuciyarta take tunanin meya yi zafi da har Wanda yake rayuwa
a nan ze tsallake ya bar shi yaje yana rayuwar kwanan shago, ita dai saida Aunty Aishat ta Dan tabata ta
dawo hayyacinta.
"Mu shiga ciki?"
Fitowa tayi dauke da Afnan a kafadarta tabi bayan Aunty Aishar wadda me rike da hannun Abulkhairi,
numbers Auntyn ta saka ta bude kofar Dan juyowa tayi kadan tana fadin "Bismillah".
A hankali zahra tabi bayan wasu parlours suka ringa ratsawa na garari sai da suka wuce parlour biyar
sannan Aunty Aishar ta cewa zahra ta Dan jirata tana zuwa ta nufi upstairs tana rike da Abulkhairin.
A kan center carpet zahra ta zauna tana wasa da Afnan wadda duk tayi laushi ta gaji danma yarinya ce mai
hakuri, dogon tunani zahra ta shiga bata taba tunanin maganganun Hajiyar makwarari gaskiya bane sai Yau
wallahi duk a lokacin shirbtun tsufa ta dauki zancenta Ashe batama fada mata gaskiyar zancen ba.
A sama direct bedroom din Ammi Aunty Aisha ta nufa knocking tayi daga ciki taji Ammin na fadin "shigo
mana batool kinsan bana son yawan damu da safe"
A hankali tura kofar ta shiga da sallama, ai Abulkhairi na ganin Ammi ya Zane hannusa daga na mamansa
ya ruga ya rungume Ammi wadda tayi tsaye kawai tana duban Aishar Dan ba karamin mamaki ta bata
ba."surprise ko Ammina?"
Ta fada tana shgewa jikin Ammin tana dariya.
"Kin kyauta kenan ki dauko jiki daga uwa duniya Amma bazaki fada ba ko Addu'a ayi muku sai dai ba ganku
ba zato ba tsammani".
" Afuwan my Ammi nima bansan da tafiyar ba sai shekaran jiya waccan, kinsa dan gidanki baya jira".
"Ina kika ganshi ko kuma daman yana tare dake kika ki fada? Ina kuma Afnan din take?".
" suna master parlour da bakuwa mukazo fa".
"Bakuwa kuma?".
" Eh shigowa nayi na fada miki, to sannunku da hanya muje kasan a Samar muku abun break fast".
Suka nufo kasan takun takalmansu das das ya saka zahra dago kanta daga wasan da take yiwa Afnan tana
bulbula dariya, caraf suka hada ido da Ammi nan da nan taji gabanta ya fadi, itama Ammi wani shock ta
shiga babu ko tantama wannan fuskar take gani tare da Hussein dinta a mafarki yau gata a zahiri, tayi
mafarkin yarinyar nan yafi sau shurin masaki me hakan ke nufi kenan.
Suna shigowa kamshin Ammin ya hade parlourn.
Zahra ba tayi tunanin haka zataga Ammin ba, babu Wanda zece ita ta haifi su Aunty Aisha sai dai ace
yayarsu ce, 'yar gayu ce ta ajin karshe ga jindadin daya hana shekarunta nuna Kansu,a hankali take takowa
idanunta na kan zahra wadda taji wata irin kunya ta rufeta, gurin da suke zaune Ammin ta karasa tana
fadin.
"Sannunku da hanya, a kunya ce zahra ta bude bakinta tace.
" yauwa Ammy, ina kwana"..
"Lafiya kalau ya gajiyar hanya?".
Ta fada tana mika hannu zata dauki Afnan, makalewa tayi a jikin zahra alamar bazata zo ba.
Gaba Ammin tayi ta zauna tana fadin huta roro waken gizo yaqi 'ya'ya".
Aunty Aisha ce dubi Ammi tana fadin.
" Ammi ga zahra nan 'yar Amanar Hussein diyar mai gidansa ce bata da lafiya aka kaita India ganin likita
shine yace na taho da ita Nigeria kafin yazo su 'yan jihar bauchi ne katagum local government sunanta
Fateemah zahra".
Dan gyara zama Ammin tayi tana kara kallon zahrar from head to toe, haka nan taji wani Abu yana mata
kai kawo a kasan zuciyarta.
"Sannu fateemah ya jikin naki?".
Kanta na kasa bata yarda ta dago ba ta amsa.
" Da sauki Sosai".
"Masha Allah, Hasana rakata sama dakin fake opposite da bedroom din ki bude Mata tayi wanka kafin a
hada muku breakfast".
" To Ammi bari muje,ko kuma muje can gurina saita zauna tunda duk cikin part din nan ne".
Kaita girgiza "kaita sama inda sauran 'yan uwanta yara suka can gurinki ba zataji fadi ba nan kuwa gasu
Batool nan kuma ba kince bata jin dadi ba sai saida babba a kusa maza kuje lokaci yana tafiya gara taci
abinci ta kwanta ta huta tunda ba irin ujilarku ta iya ba".
A kunya ce zahra ta mike tana sabe da Afnan.
Saida suka bacewa ganin Ammi sannan ta dauke idonta daga kallon zahra.
" ya rabb kai kasan abinda ke boye da make nuna min yarinyar nan tare da Dana sauran sirrin kuma bani da
masaniyarsa, ubangiji ka tsareni jin abinda ze zamar min tashin hankali".
Ya fada a cikin murya mai rauni.
Suna shiga dakin Aunty Aishat din tace "wow! Lallai matarmu you are special ai bansan haka Ammi ta hada
wannan bedroom din ba, bari na sauka da wannan 'yar taki makale matar kawai"
Ta dauko ta tana kuka ta fice da ita, tana jin Zahra na magiyar ta dawo da ita tayi mata wanka Amma ta
wuce kawai.
Lokacin da Aishat din ta sauko bata samu Ammi da Abulkhairi ba itama wata hanya ta nufa tana dan jijjiga
Afnan.
Kafin minti arba'in an hadawa su Aishat breakfast mai rai da lafiya, zahra tana fitowa daga wanka tayi tsaye
a gaban mirror tana kallon kanta yanda tayi wani irin kyau na ban mamaki wato Inda ake gyaran jiki anayi
dan tamkar anyi mata wankan inji,lotion din data gani ta Shafa tunda nata da take shafawa yana can cikin
kayansu ba'a shigo dasu ba saida ta gama shafawa tayi turus Ashe bata da kayan sakawa kuma gashi towel
din jikinta ma karami ne kusan Rabin cinyoyinta duk a waje suke, gefen gado ta koma ta zauna ita dai
bazata iya mayar da kayan data cire ba, dan kwanciya tayi a jikin pillow dan tunda tayi wanka wata irin
kasala ta saukar mata ba, tayi minti biyu ba barci yayi awon gaba da ita.
Jin shirun zahrar yayi yawa yasa Ammi tacewa Aishat ta bita ta kirata ko nauyin saukowa takeji tunda taga
yarinyar akwaita da kunya.
Sau biyu tana knocking Amma shiru, kamar ba mutum a dakin a hankali ta murda handle din ta tura kofar
ganinta tayi tana barci,komawa tayi a hankali dan bazata so ta gashi taga ta ganta a haka ba, haba dole
bros ya rikice musu Ashe shi yasan sirrin kayansa Ashe a fuska wasa ne, tasan Allah ne yayi mass tukuicin
kazafin da akayi masa ya bashi irin wannan yarinyar.
Sai data fara gangarowa ta tuna Ashe bata da kayan sakawa a tare da ita.
"Ya salam! Wallahi shaf ta manta tunda su basa dauko kayan sakawa suna dasu a nan.
******
Saida Mahmud yayi barcinsa mai isarsa ya tashi, sau uku Hajiya Inna tana zuwa ta buga masa daki tana
jinsa a rufe, wanka yayi ya fito cikin yadin filtex mai laushi fari tas, a parlour ya samu Hajiyar da Aminiyarta
Innoni suna hira, kusa da Hajiya Innar ya zauna yana gaishe da innonin, kama haba tayi.
" kai kuma yaushe ka dawo garin namu?".
Tabe baki Inna tayi "kin gashi nan saida malamai suka gama karbar nasu rabon ya mula ya Mile ya dauko
jiki sinkin fakiti ya dawo, yazo kuma ya zaune min yaki ko leka kofar gidan nan, kofa gidan iyayen yaki zuwa
ni naga ta kaina kasan da irin wannan ranar amma ka tsallake kayi naka guri sai yanzu zaka zo kana
daddofar na kaika gidan".
Wata dariyar da bai shirya ba ta kubce masa.
" Amma wallahi matar nan kin gama dani ni zaki cewa ina kamun kafa fake ki kaini gida,ni kadai na fito ni
kadai zan koma kuma kinyi da dan halak idan na fice sai kin shekara baki sakani a idanunki ba".
Ya mike ya nufi kofa, nan da nan Hajiya inna ta rude.
"Idan ka bawa Annabi daraja ka dawo wallahi wasa nake maka ga abincinka can kazo kaci".
Ya tsaya Amma bai juyo ba.
"A aje min idan na dawo zanci lokacin magariba ya karato masallaci zani".
Yana gama fada ya bude kofa ya fice.
" miskili kawai idan ba haka nayi masa ba ko gidan baze leka yau ba duk kuwa yanda yake da kawa zucin
uwa".
"Ai mutumin naki sai ke".
Saida ya gaisa da masu gadi sannan ya shiga motar da yazo a ciki ya nufi unguwarsu tunda babu nisa daga
unguwar su Hajiyar, yana shiga ana kokarin tayar da sallah da sauri ya shiga cikin masallacin gidan nasu
tunda da alwalarsa.
Sahun bayan su Abbie dinsa yayi sallah da aka idar masu fita suka fita shi daman a dabi'arsu yawanci basa
fita sai sunyi insha'i zirillahi yaci gaba dayi Abbie din bai juyo ba shima bai matsa ba sai Babban yayansu
Ibrahim da yake daga jikin ginin masallacin ta kudu yake mamakin yaushe Mahmud din ya dawo kuma
uncle saminu ya dawo dazu yace Mahmud ya gudu daga India, uncle mustapha ya bazu nemansa to ga
Mahmud kuma a sokoto ga uncle mustapha ya sauka a abuja ze biyo jirgin karfe bakwai na dare zuwa
sokoto to me kenan hakan ke nufi? Shifa daman ya dade yana zargin uncle saminu da wasu abubuwa
marasa kyau a tsakaninsu.
Ana idar da insha'i Mahmud ya tashi ya fice kafin Abbie din su ya tashi, hannu kawai ya dagawa securities
din ya wucesu suna faman murna dan sunsan kakarsu ta yanke saka mai yiwa dawa ruwa bare gashi a
karkara,koda bayanan sakonsa yana iskesu to bare gashi ya dawo.
Ya dan jima a parking lot na gurin Ammi yana Karewa harabar gidan kallo ko ina haske ne tar ga wata iska
mai dadi da take busowa cikin motar tare da kamshin furanni mabanbanta, abubuwan da suka faru suka
dunga dawo masa daki-daki lumshe idanu yayi baiyi aune ba yaji ruwan hawaye suna bin kumatunsa
abinda baiyi ba kenan duk badaqalar da aka sha a gidan nan a lokacin, kansa ya kifa jikin sitiyarin motar
baiji alamun tafiya ko wani Abu sai dai jin hannun mutum yayi a bayansa bai dago ba, bubbuga kafadarsa
yaji an fara kafin ya tsinkayi muryar Abbie dinsa yana fadin.
"Haba! namiji baya kuka tunda ka iya jure kwaramniyar baya baka nuna rauni ba yanzu lokacin fuskantar
gaba ne taso mu shiga ciki kada kannanka suga kana kuka, su raina min kai".
Da Saudi ya dago jin furucin da bai zata ba daga bakin Abbie idan yayi la'akari da lokacin da guguwar abun
ta tashi tsine masa ne kawai baiyi ba Amma yayi masa wata irin tujara ta Ala tsine uwar mai karya.
Jikinsa ya fada yana fadin.
" wallahi Abbie ban aikata ba! Ban taba zina ba, ka bani Qur'ani zan rantse da Wanda ya halicceni idan na
taba zina a rayuwata Allah yayi min abinda yaso na azaba, ka yarda dani ka fadawa Ammi banyi ba sharri
ne akayi min na fada Amma Baku yarda ba...kum..."
Sai jikinsa ya langabe ya saki.
Da sauri Ya Ibrahim dake tsaye a gefe Wanda shima hawayen yakeyi ya zaburo yana fadin .
"Suma yayi Abbie bari na samo ruwa"
Ya tafi da gudu ya haura steps din part din Ammi, suna zaune ya bude kofar afujajun baiko kalli su Ammi ba
da saura yaran yayi kitchen da gudu ya dauko ruwan sanyi da sauri Ammi da Aishat da Batool suka rufa
masa baya Ammi na tambayarsa menene? Bai ko juyo ba yayi gaba,suma gurin daya nufa suka nufa turus
sukayi ganin Abbie a tsaye rungume da mutum Ya Ibrahim yana bulbula masa ruwan sanyi.
Ajiyar zuciya ya sauke tare da shashsheka abinya yake fada yaci gaba da fada.
Ka fadawa Ammi ni ba nazinaci bane ban aikata ba".
"Pls kayi shiru mana ta sani ka kwantar da hankalinka bama zarginka kaga Amminka tana jinka fa".
Da sauri ya juyo sai kuma jiri ya kwashe shi ze zubar Ya Ibrahim yayi saurin rike shi suna faman jera masa
sannu, juyawa Ammi tayi idanunta fal hawayen tausayin dan nata kenan duk tsawon lokacin nan yana
fama da wannan damuwar wadda sai yau ya fasata gashi zata janyo masa matsala a lafiyarsa.
" Allah ka biwa yaron nan haqqinsa".
"Allahumma Amin".
Taji su Batool sun fada sai lokacin tasan a fili tayi addu'ar.
Su zahra na tsaye tana dauke da Afnan tun shigowar Wanda ya dauki ruwa ya fita su Ammy suka bishi taji
gabanta yayi wata irin faduwa, ta mike tsaye ta kasa zaune ta kasa tsaye, sai kuma taga an shigo da
Mahmud din a rirrike yana layi kamar Wanda ya bugu da kayan maye.
Ai bata San yanda akayi ba ta dira a gabansa jikinta yana wata irin tsuma cikin rufewar idanu da manta a
ina ma take ne ta fara fadar
" Na shiga uku meya sameka meu amor...? Me akayi maka fada min dan Allah..."
Hannu Aunty Aishat da Dora a bakinta data bude tana fadin.
" kai? Wonderful...! the game is over".
Maman Fateemah.
Page 76.
.............. Aunty Aishat ce tayi sauri tazo gurin zahrar saboda kowa a gurin wutarsa daukewa tayi barema
Abbie da Ya Ibrahim da Basu da masaniyar da wata bakuwar fuska a gidan, itama zahrar sai data fada ta
dawo Cikin hayyacinta, wata irin kunya ce ta rufeta taji kamar kasa ta tsage ta shige Dan kunya, me tayi
kenan shike Nan tayi abun kunyar da zata Dade Bata hada Ido da Amm bai wallahi.
Kan kujerar dake kusa dasu su aje Mahmud Wanda tun dirowar Zahra gabansa yaji wata irin Rahama ta
saukar Masa a zuciyarsa badan a gaban iyayensa bane saiya Bata hot kisses na nuna godiyar nauyin data
sauke Masa Cikin kankanin lokaci ta isar da sakon Daya Dade Yana tunanin ta Ina ze bullo musu Sai gashi in
some minutes tayi musu aikin.
Aunty Aishat na rike da hannun zahra suka shige Cikin wani parlourn har lokacin jikinta Bai dawo normal
ba, Afnan Auntyn ta karbe daga hannunta suka zauna.
"Ki nutsu babu fa abinda ya same shi inaga farin ciki ne ya sakashi sumewa, kinsan mutumin naki da
kwakawar son iyaye kinsan kuwa haduwar ai Daman za'a iya samun irin haka".
Ita dai Zahra kasa daga Ido tayi ta kalli Aunty Aishar wannan abun kunya har Ina da farawa da iyawa ranar
data sauka a ranar ta baza abin fada to Wai ita meye ya shiga kanta ne ta kasa controlling kanta a gaban
mutane?.
Itama Aunty Aishat Bata dameta da yawan magana tasan tana Cikin Jimamin abunda tayi Wanda ya bude
wwani murfin da suka kasa budewa sai gashi wadda aketa kunbi kunbiyar bayyana wacece ita tayi ta bude
aiki da kanta ba tare da itama ta sani ba, ta Kara girmamawa girman Allah buwayi gagara misali Dan wani
connection din idan aka hada shi sai dai kayi kallo kawai, tashi tayi fice ta koma can main parlour din.
Da Ido Ya Ibrahim yabi su Aishat har suka fice daga parlourn Yana kissima abubuwa masu yawa a cikin
Zuciyarsa "kafa fa a gudu ba'a tsira ba".
Yayin da Ammi da Abbie suka dubi juna da alamar tambaya a fuskarsu, Ammi nayi masa wani duba na
Mena fada maka?.
Aishat na shigowa Hajiya Inna na shigowa atfujajan uncle Mustapha na biye da Auncle Autan Hajiya Inna.
" Muhammadu Rasulullahi! Ni Hadiza Naga abunda ya isheni Ashe haka ka dunga gararamba yaron Nan a
cikin kasar nan kamar marar gata? saida ubangiji ya tallafeka da mutanan kirki bayin Allah masuyi Dan
Allah yanzu Nan Mustapha yazo min da wannan labarin daya jiyo gurin bawan Allahn Daya tsinceshi a
yashe a kasa ko takalmi babu a kafarsa ko magana fa yace baya iya yinta a lokacin, wannan Dan taliki
Ubangiji yayi Masa sakayya da gidan Aljanna, duk Kuma Wanda yake da hannu gurin neman tagayyara min
rayuwar jika Allah ya wulakantashi tun anan duniya Kuma wannan yaron KAINUWA ne dashen Allah ba
dashen mutane ne ba, ita Kuma sameera mun barta da Allah suje suji da abun kunyarsu munafukarkar
banza da Ido kamar an rutsa mazuru a dakin tantabaru na godewa Allah da 'ya'yan da take haihuwa basa
Zama da yanzu ta tafi tabar mana mugun irin".
Ammi CE ta matsa kusa da Hajiya Innar tana fadin.
"Ayi hakuri Hajiya ai komai ya wuce ki daina tada hankalinki saboda lalurarki Bata son yawan bacin rai".
"Yo bacin rai na nawa Kuma zainab ai saidai kada a Kuma".
Shi dai Abbie ya yayi shiru Yana jujjuya Lamarin a zuci.
Gurin Zama Ammi ta raka Hajiya Inna ta zauna kusa da inda mahmud yake zaune idanunsa a rufe.
"Kai Kuma menene haka ta wani kike Riga sharaf ka kuma Kama ido ka rufe sai qif-qif kake dasu kamar
wani sabon makaho".
"Trouble woman".
Ya fada a zuciyarsa.
Abbie ne ya matso Yana gaishe da Hajiyar Yana fadin. "Haba Mustapha saboda me zaka dauko ta da Daren
Nan ku taho basai a barwa safiya ba".
"A'a nice nace baze taho ya barni ba kada ku taru ku nakasa shi a banza yanzu ma zuwa nayi mu tafi ko
abinci baici ba, gashi ya laimin kuwa nazo na tarar kunyi ira-ira da gani wani Abu kukayi masa. Kai bude
idonka ka fada min waye yayi maka wannan dibar albarkar ya jikeka sharaf haka?".
Abbie ne ya zauna daga gefenta Yana fadin.
"Babu Wanda yayi Masa komai murnar yaga Amminsa ce tasa ya sume Saida aka Zuba Masa ruwa sannnan
ya dawo hayyacinsa".
Tabe Baki tayi tana kallon Ammi wadda ta zauna daura da kafafuwan Hajiyar tana saurarenta.
"To Daman zuwa nayi na jawa kowa layi akan rayuawar yaron nan kada naji kada Kuma na gani, anyi Daya
babu Kari, Kuma na nazo Kan maganar waccen matar Mai idanu Yana gwarawa wallahi ko bayan raina ka
mayar da aurenta ban yafe ba sai Allah yayi Mana hisabi akan,haka me akeyi da wannan matar Mai bakar
aniya aini har abada bazan taba yafe Mata ba".
Ta fada tana kallon Abbie fuskarta a hade alamar ranta a bace yake.
Hakuri suka dunga Bata mahmud najinsu Kuma yayi mirsisi ya bude idanunsa.
"Saika tashi mu tafi ka Gama zaman gidan nan gara ma kayi aure inga ta karyar sharri Kuma haka kawai an
takura maka kowa neman lika maka 'yarsa yakeyi an mayar da Kai na mamajo, kazo muje Ina da yaran dana
zabar maka har hudu idan ma duka kake so saina shige maka gaba a aura makasu Rana Daya inga ta tsiyar
kawo maka rida Kuma".
Su dai hakurin dai suke Bata, shi kuwa da goyan tana ambatar ya tashi su tafi yayi wani Dan murmushi a
cikin Zuciyarsa.
"Tab ba inda zani yanzu dai da precious ke cikin gigita Sai taji dumina na kwantar Mata da hankali Nima
bana son mu zauna guri Daya matsla za'a samu gara muna Dan nesa".
"Wai bazaka tashin bane kayi min kunnen uwar shegu kana wani farfar da Idanu?".
Uncle Mustapha ne yace mata.
"Kiyi hakuri idan ya warware zuwa safe sai ya shigo ai Daman mahmud naki ne, bakiga a gurinki yayi
masauki ba daze tafi ma kece ta katshen daya gani kafin yabar gidan, kefa Dan gata har sakawa yake azo
takanas a kirashi video call Yana ganinki kofa tsiren da kikace Na Maru yana badawa a kawo Miki saboda
Alkawari tunda a gurinsa Mahmud yake sawo Miki Bai daina kawawa ba, da naje nasameshi ya bani bill da
adadin kudin tsiren Daya kawo Miki cewa yayi Wai an turo Masa kudin tsirenki na shekara ne, Yana fadin
haka nasan aikinsa ne, Dan haka tashi muje na mayar dake gida idan Allah ya kaimu gone saina kawo Miki
shi har gida" .
Yunkurawa tayi ta tashi sai lokacin idonta ya Kai Kan Aishat.
"Ke Kuma saukar yaushe Hasana? Ko Kuma ke Kika kawo shi kasar ne?".
"A'a bani na kawo shi ba arashi kawai akayi nazo shima yazo".
Mahmud naji suka wuce ita da uncle Mustaphan da uncle Aliyu.
Abbie da Ammi da Ya Ibrahim suka bisu a baya.
Saida yaji fitarsu sannan ya bude idanu Aishat da Batool kawai ya gani a parlourn duk sauran yaran sun
wuce ciki.
"Sannu Ya mahmud".
Batool ta fada tana Dan matsowa kusa dashi.
"Yauwa Batool"
ya fada Yana kallonta, Aishat din ya kalla Yana Mata inkiyar tana Ina?.
'yar dariya tayi tana fadin.
"Saboda Allah ka saka yarinya ta gigice irin haka har ta saki layi irin haka nasan saina amsa tuhuma a gurin
Ammi Dan Naga wani irin kallo da tayi min".
Batool ce ta Kara motsowa sosai ta kwantar da murya.
"Ya mahmud Wai da Allah wacece wannan? tunda na ganta naji Ina sonta ina sonta wallahi gata very wise
da ita, tana da kirki gashi duk abinda zata fada a Dan zaman da mukayi dazu zakiga da hikima a cikin
maganarta, hikimarta ta girmi shekarunta gaskiya, gashi Bata da Jin Kai Sam idan wata ce yanda Allah yayi
halitta a gurin ai sai yanda Hali yayi kawai".
"Yehhh... Yessss... Wallahi Ko yanzu Ya mahmud ka nuna kai jarimi ne ka dauko matar da babu irinta a
dukkan Family ai gara da akayi yunwa halin kowa ya fito".
Ta fada tana tsallen murna kamar Karamar yarinya.
A haka su Abbie suka shigo Amma ba Ya Ibrahim ya wuce parta dinsa da yake a Cikin estate din suke shida
saura yayunsa.
"Ke Kuma wane irin sakarci ne wannan da tshon dare kike yiwa mutane ihu haka?".
Jikin Ammi ta fada tana fadin.
"Wayyo Dadi Ammi Wai ashe Aunty Zahra matar ya Mahmud ce,".
Shi dai Abbie gurin mahmud ya nufa ya zauna kusa dashi ya Dan taba gefen wuyansa.
"Sannu me yake damunka yanzu?".
"Ba komai kawai kaina ne yake ciwon kadan".
"Ok.ai na yiwa doctor Hashim waya yace gashi Nan zuwa".
Jin abinda Abbie ya fada yasa Aunty Aishar da Batool suka nufi parlourn da Zahra ke zaune Basu tarar da
ita a gurin ba sama suka nufa Batool nata kakabin abin tana faman magiyar Auntyn ta fada Mata ita ce ta
hada Ya mahmud da Aunty Zahrar? Amsar Daya ce dai take fada Mata yanda ta ganta itama haka ta ganta.
Knocking biyu sukayi Zahra tace su shigo a kan sofa suka sameta ta Zuba tagumi tana aikin tunani Afnan ta
karba daga kafadar Auntyn wadda tayi barci kwantar da ita Zahra tayi.
"Kuma saiki gudo Baku gaisa da Abbie ba".
Sadda Kai tayi dan ji tayi Auntyn ma kunyar hada Ido takeyi da ita.
"Zamu gaisa ne ai yanzu bazan iya zuwa ba wallahi kunya nakeji, ji nake kamar nayi tsuntsuwa na gudu".
"Kaji Aunty meye abun kunyar a ciki keda ba rungumarsa kiyayi ba "Dan kin nuna damuwa a Kan halin da
yake ciki ai Kara kankarowa kanki mutunci kikayi su iyayensa, ai Dadi sukaji ko Basu fada ba irin wannan
rudewa da antayo soyyaya a gabansu sun San idan aka shiga other room Kuma sai yanda Hali yayi
kenan,gaskiya a gurinki zanyi degree harda masters ma akan soyyaya Naga alamar kina Dora Ya mahmud a
network".
Riqe Baki Aunty Aishat tayi tana kallon Batool.
"Yaushe Kika lalace haka? Wallahi Zan sami Ammi ayi gaggawar saka Miki Rana kece Mai fadar irin wannan
maganganun a gaban idanuna gara a yiwa tubkar hanci kinyi service din a gidan mijinki".
"Kai Aunty Mena fada Ina ce kece ya kamata ki zaunar dani kiyi min Karatun yanda Zan Kama mijin nawa,
Amma bakiyi ba sai kuma Kice Zaki hadani da Ammi Wai ayi bikin ko service banyi ba salon laulayin ciki ya
hanani yinsa cikin dadin rai".
"Allah ya shiryeki wannan yarinyar da Baki samu miji ba wallahi cewa zanyi Ammi ta fadawa Abbie ya
badaki sadaka Naga alamar idan Kika Kara watanni za'a iya samun matsala gaskiya".
Dr Hashim Bai Bata lokaci ba yazo bedroom din dake kasa wanda mahmud din ya mayar dakinsa suka shiga
Dr ya duba shi, ya auna B.p normal yace ya rage saka damuwa a zuciyarsa saboda kada ta shafi lafiyarsa a
irin wannan shekarun, tea yasa Ammi ta hado Masa ya Sha yayi Masa Allura ya bashi magunguna Yasha
sannan ya tafi.
Ba'afi minti biyar dayi Masa allurar ba ya Fara hamma zuwa minti goma yayi barci.
Karfin A/C Abbie ya rage masa sannan suka fice daga dakin.
Suna fitowa Ammi taja ta tsaya tana duban General.
"Kaga abinda naketa fada maka ko? Game da mafarkin wannan yarinyar wallahi itace zahiri ake nuna mini
a Cikin mafarkina suna tare dashi".
Hannunta ya kamo suka zauna.
"Ki kwantar da hankalinki lallai Allah ya nuna Miki wani sirrine da yaso ki fara gani kafin zahiri yazo Miki,
tun ranar talata Mustapha ya turo min hirarsa da malamin Daya ya rike Miki yaro lokacin da baya Cikin
hayyacinsa da yanda Sukayi ta fadi tashi akan nemar Masa magani da yanda ya fada anyi Masa asirin barin
garin na har abada da yanda akayi auka bashi wannan yarinyar yanzu haka dai in takaice Miki labari
matatmrsa ce ta sunnan wadda marikinta yayi Mata AUREN HUCE HAUSHI, saboda itama anata samun
matsaloli ne a dukkan lokacin da auernta ya tashi, shine markinta Kuma Aminin malamin ya yaba da
hankalinsa ya bashi aurenta ba tare da la'akari da irin matsayinsa na bako kuma Almajiri ya bashi ita, babu
irin surutun da ba'ayi Masa ba ya toshe kunnensa ana ta fadar Dan ba 'yarsa bace ya Bata marar gata. To
shi malamin ne ya gamu da jarabawar matsalar Spinal cord injury shi mahmud din ya fita dashi India
lokacin dashi malamin yake kokarin dawo dashi gida sai kuma ya gamu da wannan lalurar yace a bamu
hakuri sunyi kuskuren yi Masa Aure Amma mu dauka haka kaddarar take a rubuce gurin Ubangiji shiya
kawo aka samu matsalar da tasa mahmud ya tsallake yabar gida har hakan ta faru da ba'a samu wannan
matsalar ba da ta Ina zeje Azare ya zauna har a bashi auren yarinyar? Kinga Koda matarsa ce sai dai su
hadu ta wata fuskar badai wannan ba tunda Allah ya hukunta matarsa ce".
Jinjina Kai kawai Ammi keyi Tana Kara girmamawa girman Allah s.w.a idan yayi wani abun sai dai bawa ya
kalla da Ido kawai.
"Na fashimta bazan ja da hukuncin Allah ba, duk yanda yayi da bawa shine daidai naji Dadi da Allah yasa
Dan uwanka yazo da maganar nan bashi Hussein ya fada ba da kuma abinda ita yarinyar tayi yanzu a gaban
Dan uwansa Dan haka saika tarasu kasa Mustaphan ya kunna musu suji da kunnensu bazan dauki abinda
na dauka a baya ba, Kuma sabon biki za'ayi kamar yanda ake yiwa kowa a gidan Nan maganin tsegumi Dan
haka da safe Zan Kira Ya I Ishaq ya bani aron Aunty Badi'a zata rakata har Azare ta yiwa mamanta bayanin
sabon biki za'ayi kosu can Basu sake ba su hada jama'arsu za'a zo a dauketa kamar ko wace Amarya da
dangin mijinta suke zuwa su daukota, zatafi kima da daraja a Cikin family fiye da a wayi gari ace wai yazo
da Mata ai wani ma abin magana ze Zama ko Yaya kake gani? kasan tunanin mace da namji ba Daya bane".
"A maganarki babu gyara hakan yayi Amma idan har hakan za'ayi no need a ce sai kowa ya San gaskiyar
maganar kawai Mustaphan yace an daura aure ne yanzu bikin za'ayi kawai Daman suna Shirin dawo dashi
gida ubangidan nasa ya samu matsala Yana asibiti a India inda aka kawo labarin ganin mahmud din Ashe
jiyya sukeyi a can".
"Hakan yayi Allah ya Kara sutura"
"Allahumma Amin" Abbie ya fada, muje ki bani wani Abu marar nauyi naci tunda Naga Alamar murna ta
hanamu yin dinner a gidan nan, ki kawo min can part dina".
"Kaiiii Yallabai ayi min afuwa yau Daya dai Ina da bakuwa ai nayi entertaining dinta".
"Babu wannan kizo Ina jiranki ki bar musu Nan din kinsan dai zasu iya abinda zesa ki kusa nutsewa a kasa
Dan kunya kuma ma ke Ina ruwanki dasu ba tare Kika gansu ba kinsa auren nasu ya dauki watannin da
yinsa?".
Dan murmushi Ammin tayi.
"Ni fa Banga alamar yarinyar nan an mayar da ita mace ba gaskiya budurwa ce".
"Kamar yaya, yarinya da mijinta ki ringa fadar haka?"
Shiru tayi masa ita dai taga abinda ta gani tun ganinta da tayi dazu kafin ta sauki daga steps ta kiduri duba
abinda Hajjo ta fada Mata da yake nuna yarinya budurwa ce ko tana ma'amala da maza, da niyya taje da
niyyar daukar Afnan Saida ta gani sannan taji ta Samu nutsuwa.
Lokacin da Ammi ta haura saman shiru da alamar sun kwanta,Saida ta Gama duk abinda zatayi ta rufo
kofarta kamar zata shiga gurin zahrar saita juya ta nufi downstairs kawai tasan idan ta shiga kinya zata Bata
gara ta Bari abun ya Dan bi jiki tunnna, downstairs ta nufa tana ayyana sai ta Dan yamutsa musu lissafi ko
Yaya ya ne Dan su Kara sanin darajarta itafa tana kishin mace ganin an bashi yarinyar Nan a sama saiy
Zahra ta Dade tana tunanin makomar aurenta baran barama dai tariga tayi sai Kuma yanda ta yuwu Wai
Dan daudu a lahira.
"Koyaya jikin nasa?"
Ta fada a zuciyarta, ta Jima tana sakawa da kwancewa, gashi duk yanda taso ta Kira Aunty Hasana abun ya
faskara haka Ammah duk network yaki bada hadin kai. Sai wurin Daya saura tayi barci, can a Cikin barcinta
taji Kamar ana tabata, kwanciyarta ta gyara ba tare data bude Ido ba sai tajita a jikin mutum da wata irin
zabura ta yunkura zata Mike taji an mayar da ita Baki ta bude zata zabga ihu taji carab ya hade bakinsu sai
lokaci taji kanshin turarensa a hancinta, wata ajiyar zuciya ta sauke, tayi lif a jikinsa da gaske sunyi missing
din juna Saida yayi Mai isarsa sannan ya dan saurara Mata ya yanye bakinsa suna maida numfashi.
"Previous kin azabtar Dani whyyy... Me nayi Miki Kika haramta min ganinki kwata-kwata? Fada min kinsan
halin Dana shiga kuwa? Kikasa na kasa controlling kaina a gaban elder brother dina kin kyauta min
kenan?".
Ita dai mukus tayi to me zata fada masa tace labewa tayi taji shirarsu da Aunty Aishat ko tace Masa me
shirun shi yafi Alkhairi. Juyin duniyar Nan taki magana dole ya kyaleta ya koma wata shirar da ban.
"Wai dazu da rungumeni zakiyi a gaban su Ammi?".
Saka kanta tayi a kirjinsa Cikin kunya tana gigiza Masa Kai.
"Kin dauka Zan tafi na barkine ko? To muna Nan sai kin haifo Mana fine babies masu Kama dake".
Ya fada Yana Kai hannu akan cikinta Yana Dan shafawa.
"Ka Bari Dan Allah Ammi fa tana Nan ka tashi ka tafi Dan Allah kada wani ya ganka ka shigo yayi zaton wani
Abu fa".
"Kwantar da hankalinki ai kin Gama Mana aikin Dana kasa yinsa a Cikin kankanin lokaci meya rage kuma?
sai mu tattara mu tafi inda mukafi wayo Nima nasan nayi aure na huta da ragaita mu fuskanci rayuwa
kuma, badan nayi alkawarin kawowa Ammi ke a yarinyarki ba Aida yanzu muna Shirin tarbar babyn mu ko
ba haka ba?"
Wannan furucin nasa shi ya ankarar da ita akwai fa sauran Rina a kaba, Nan da Nan wani tsoro ya kamata
Nan ne fa karshen maganar, a Nan ne me afkuwa fa zata afku,tunda gata a sokoto har dakin mahaifiyarsa
saura da me ya rage kuma?.
Cikin shagwaba ta Fara fadar "Ni dai ka daina wannan maganar gaskiya wallahi ni Ina Nan kusa da Ammina
ai ba muyi haka da kaiba nifa tsoro nakejiiii..."
Wani special smile ya sakar Mata duk da dakin dimmer light ce Bata hanata ganin yanda dimple dinsa ya
lotsa ba.
"Wani abu nace zanyi Miki ne da zaki Fara tsorona? Ki zana feel free Dani har abada babu cutarwa a
tsakanin mu, kin manta Abba da Baba Malam Amanarki suka bani?".
Kai gyada Masa alamar eh.
Cikin jikinsa ya sakata Yana fadar muyi barci da sauran lokaci duka yanzu one thirty five am".
Kafada ta make tana kallonsa ta gefen ido ita fa da abinda yake figitata gaskiya.
"Dan Allah ka tafi kada kaja mini Ammi fa tana Nan kada ta ganka nidai babu ruwana wallahi".
"Nace Miki ki kwantar da hankalinki Amma Bata Nan fa tana gurin mijinta itama to Kinga Kota ganni ai ba
wata damuwa ko?".
Ita dai barci rabi da rabi tayi a kunnenta aka Kira sallar farko data biyu tana jinsa ta tashi ya shiga toilet ya
fito ya zura jallabiya Daya zo da ita Cikin ledarta ya Dan shafi gefen fuskarta wadda tayi fayau a Cikin Dan
hasken dake dakin.
"Tashi lokacin sallah yayi, Zan wuce masallacin daga can zanje gurin Hajiya inna, jiya Baki ganta ba ko
lokacin kin gudo tazo gidan Nan Wai zata tasani a gaba mu tafi Wai na daina zaman nan. Kin amince nayi
nesa dake?".
Jin za'a tada sallah yasa yayi sauri ya fice daga dakin, Karan rufe kofa yasa Ammi dawowa ta bude kofarta
wadda shigarta dakin kenan Dan yallabai na tafiya masallaci ta nufo part dinta, bayansa kawai ta iya gani
saboda saurin da yakeyi na kada ya rasa raka'ar farko, jinjina Kai tayi tana fadar.
"Dole ayi yanda za'ayi ku tattara ku Kama gabanku badani za'ayi wannan dibar Albarkar ba, wato abinda
general ke nufi kenan Daya tilastani zuwa gurinsa"
Sallah ta tayar ta zauna zaman azkar da lazimi Ala ala take shida da rabi tayi ta Mira Niger, Saida ya dai daici
lokacin dawowa daga masallacin yayan nata sannan ta Kira shi.
Yana ganin Kiran yasan ba lafiya ba Dan Yana dagawa ya Bai saurari gaisuwar da take masa ba ya Fara fadin.
"Zainab lafiya? Meya faru kuma?".
"Wallahi ba komai Yaya sai Alkhairi".
"To Alhamdulillahi, lfy kalau ya yaran da Mai gida"
"Kowa lafiya, daman Mira nayi na fada maka danka ya dawo harda tsarabar Mata aka Mata aka bashi tana
nan sunzo ita da 'yar uwarsa can ya Kai Mata ita"
Sai kuma ta dauko masa Asalin dalilin kiran nasa shima supporting dinta yayi harma ya Kara da fadin dole a
hada da babbar mace su tafi tare kamar zefi girma da daraja a gurin Iyayen nata, sunyi sallama akan idan
an samu tickets dinsu damagaram to sokoton zasuyi waya wata irin nutswa taji ta saukar mata, gara ayi a
wuce gurin.
Da gari ya Fara haske zahra ta tashi daga Kan sallayar da tayi sallah ta ninke ta kintsa gurin wanna tayi ta
shirya Cikin rigar material Mai budedden dinki San rigar Bata Kama Mata jiki ba tayi rolling da gyalen
material din Nan da Nan ta gyara dakin ta fesa roomfreshner ta fito Cikin so take ta gaishe da Ammi Amma
Bata San takamaimai Ina ne dakinta ba sannan kuma Batasan da wane Ido zata dubeta ba, tana kokarin
juyawa ta koma kenan kofar dakin Ammi ta bude ta fito Shar da ita tana baza kanshinta da mamaki a
fuskaerta ta fito tana fadin.
"Masha Allah, harkin tashi kenan?"
Ta tambayi Zahra.
Da sauri Zahra ta tsuguna tana fadin.
"Ina kwana Ammy".
"Lafiya kalau ya bakunta?".
"Lfy kalau".
Ta fada tana Wasa da gefen gyalen da tayi rolling, ta kasa hada Ido da Ammi din.
Ciki Ammi ta koma tana fadin
"Bari nayi wanka tunda Allah ya kawo min ke bana son na shiga wanka ba kowa a Musa dasu*
Wayar ta Kara a kunne tana sallama, amsawa yayi Yana fadin.
"Pls My preccious Kina jina, dan Allah anjima da yamma ki biyo Sister Aishat kuzo tare ki gaishe da Hajiya
inna Kuma na cika wani alkawarin Dana dauka tun ranar Dana bar gida nayi shi to shine nakeson cika shi ai
asan zaki tayani mu cika alkawarina ko?".
Ya fada da sigar rarrashi.